An haifi Malam Salihu ɗan Dawuda a girin Galinja da ke Kanon Dabo a shekarar 1920 zamanin Sarkin Kano Usman. Mashahurin mahaddaci mai baiwar tilawa da kaifin basira.
Malam Salihu Ɗangalinja ya yi tafiye-tafiyen neman karatu cikin ƙasar Gumel da Haɗeja; da garuruwa irin su Mainabindi da Kalali da Unguwar Jibrin.
Bayan Malam Ɗan Galinja ya samu AIƙur’ani, sai kuma ya tsunduma cikin fannonin ilmin Fiƙhu da tajwidi. Ya karanta littafai irinsu Hidayatul Rahman wajen malaminsa Shehu Rabi’u Ɗantinki da Malam Husaini Gwauron Dutse. Saboda irin baiwarsa ta karatu an ce a lokacin ƙuruciyarsa zai yi wuya a lissafa manyan tsangayun da ya je ya sha fari ya tashi; Wannan ya sa sa’o’insa su ka sallama masa.
Malam Salihu mutum ne mai yawan haƙuri da kawaici da kyautatawa ga almajiransa. Bayan girma ya kama shi sai ya kafa tsangayarsa da ke garin Ƙarfi a inda makaranta ke turuwa don sanin Alƙur’ani daga gare shi. Wadda hakan ya canza yanayin rayuwar mutanen Ƙarfi saboda maƙwabtakar da suka yi da ma’abota Alƙur’ani.
Malam Salihu Ɗan Galinja ya kasance yana yi wa ‘ya’yansa da almajiransa wasiya da riƙo da Alƙur’ani da kaucewa kwaɗayin duniya.
Malam Salihu ya rasu a shekarar 1997 ya bar ‘ya’ya da dama, kaɗan daga cikin mazan su ne:-
- Halifansa Malam Kabir Ɗan Galinja
- Malam Nafiu Ɗan Galinja
- Malam Ɗahiru Ɗan Galinja, da ‘ya’ya mata guda tara.
Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Mahiru Sharif Bala danna nan.
Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.