Tag: Sakina Yazid

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyar

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyar

    Haka rayuwarsu ta cigaba; duk yanda ya so Khadeeja ta dinga bin shi ɗakinsa gaba ɗaya ta ƙi. Don haka ba shi da zaɓi duk daren da yake buƙatarta sai dai ya bi ta ɗakinta su kwana, idan bai je ba sai dai kawai ta leƙa ɗakin nasa tace masa sai da safe. Sau da dama ya sha ƙyale ta ya ga ko za ta biyo shi amma da zarar ta shiga ɗakin tace masa sai da safe sai ta yi ficewarta.

    Da farko duk ranar kwananta idan bai ya buƙatarta ya yi kwanciyarsa a ɗakinsa haka yake kwana shi kaɗai, amma tunda Naja ta gane sai ta dinga bibiya; idan ta same shi shi kaɗai sai ta yi kwanciyarta a nan da uzirin laulayi. A zatonsu Khadeeja ba ta sani ba; sai dai ita ɗin ta zaɓi ta yi shiru ne tunda ta san yana yin hakan ne don ta hakura ta koma kwana ɗakinsa.

    Ita kuma har ga Allah gani take yi babu yanda za a yi kowa take aure ta kwana gadon da yake kwana da wata matar; musamman Naja wadda ba ta taɓa tsanar wata mace kamar ita ba. Tunda Khadeeja ta dawo daga gida kuma sai laulayi ya saka Naja a gaba. Haka za ta wuni jikinta babu ƙwari, abinci kuwa to idan dai ita ce ta dafa ba za ta iya ci ba dole sai dai ya siyo mata wanda zata ci.

    Yau Khadeeja take fita daga girki don haka a wajenta shi da yara suka ci abincin rana. Ragowar abincin ranan shi ta ɗiba ta zuba a flask ta ajiye musu ita da Hafsa saboda ta huta shiga kitchen da daddare. Tana zaune a parlor tana ba wa Hammad nono ya shigo parlor ɗin, bayan ta amsa sallamarsa ya zauna kusa da ita.

    Sai da ya gama kame-kamensa yace ‘Da-Allah ki yi abincin dare gaba ɗaya saboda Naja ba ta da lafiya, kin san na gaya miki ciki ne da ita kuma yana ba ta wahala. Ko da dai ba ta zata abinda ya zo faɗa kenan ba amma tana jiran wannan ɗin ma domin tun tuni yara suka gaya mata Najan ba ta da lafiya kuma ta fahimci menene ciwon.

    Ta cire Hammad daga nono ta saka shi a kafaɗa tana cewa ‘Ai kuwa ka ga yau ba girki zan yi ba ga ragowar abincin rana can shi na ajiye za mu ci da daddare. Allah ya ba ta lafiya. Ya sake ɓata rai ‘Khadeeja, da-Allah ki bari. Yarinyar nan ba ta da lafiya ko abincin ma ita ba ta iya ci, kuma ba ita nace ki yi wa girki ba. Ni da yara za ki girkawa, idan ta sami lafiya za ta karɓi girkinta.’

    Ta kwantar da Hammad a gefenta sannan ta fuskance shi gaba ɗaya don ba ta cikin yanayi na son zance, tace ‘To ai cikin ba wani abu ba ne, ko ka manta ne? Haka na dinga haɗawa da cikin da komai duka da ƙarancin shekaruna ga rashin mataimaki. Ita kuwa yanzu ka ga tana ma da mai aiki; ai babu wani abu da zai gagare ta. Idan dai kwana ya zagayo kaina insha Allahu zan yi kamar yanda muka saba.’

    A fusace ya kalle ta na ɗan lokaci sannan yace ‘Yanzu kenan ke babu halin a ce ki yi wani abu sai ki tuno abinda ya faru shekarun da suka wuce? Kuna zaune tare a gidan kina kallon ba ta da lafiya nace ki yi girkinta amma kina nema ki ce ba za ki yi ba? Wai ke me kike son zama ne? Babu wanda ya isa ya tanƙwara ki kenan saboda zaman kanki kike yi ko me?

    Ta sunkuyar da kai murya ƙasa-ƙasa tace ‘Ba haka ba ne, kawai dai ni ma mutum ce, yanda aka yi min na zata haka ake yi wa mutanen da ake so shi yasa nake so ko yaya ne a yi adalci. Ba ta saurari abinda zai faɗa ba ta miƙe ta ɗauki Hammad a hankali saboda ba ta son ta tashe shi ya fara bacci, ta wuce ɗakinta ta bar shi a nan.

    Yanda ta yi wannan tafiyar ya tabbatar ko me zai yi ba zata saurare shi ba; wanda hakan yake nufin shi da yaransa za su shiga halin rashin samun kulawa na tsawon wata takwas har Naja ta haihu, sai dai su sami kulawa kwana biyu kwana biyu kuma a bar su a gantale. Babu yanda za a yi a ce ya ɗauki wannan kuma a halin yana da mata biyu.

    A yanda cikin nan yake wahalar da Naja kuma dole Khadeeja ce za ta ɗauki wannan hidimar har zuwa lokacin da za ta haihu. Sai da ya gama lissafinsa sannan ya miƙe ya fice, kai tsaye ɗakinsa ya wuce ya ɗauki mukullan motarsa. Bai zame ko ina ba sai gidansu Khadeeja; ba ya son kai ƙara don ya kula ita ko ya kai ƙararta ma goya mata baya za su yi, sai dai yanzu ba shi da wani zaɓi da ya wuce hakan.

    Ya ci sa a yana shiga gidan Baffa yana shirin fita, a nan bakin gate ya tsaya ya yi masa bayanin halin da ake ciki. Cike da kulawa Baffa ya jijjiga kai yace ‘Subhanallahi, to Allah ya ba ta lafiya. Yanzu ka ga fita zan yi amma in sha Allahu idan na gama abinda nake zan zo har gidan na sami Khadeejan. Kada ma kace mata zan zo, ka ƙyale ni da ita zan zo na same ta ka ji.

    Ai ɗaya daga cikin amfanin ƙarin auren kenan ɗaya ta taimakawa ɗaya a irin wannan yanayin. Suka yi sallama kowa ya nufi inda zai je. Ba shi da tabbacin abinda Baffa zai yi a kan wannan matsalar amma dai yana saka ran Baffan zai fahimce shi ya saka Khadeeja ta dinga taimakawa Naja, a ƙalla a lokutan da ba ta da lafiya; idan ba haka ba menene ribar mata biyun ga namiji.

    Ba ta samu ta yi sallar isha’i a kan lokaci ba don haka har wajen 8:30pm tana zaune a kan dadduma, Hammad yana wajen Habib wanda yake zaune a parlor ɗinta yana kallon TV. Ta so ta jiyo muryar Baffanta suna gaisawa da Mustapha a tsakar gida, amma da yake bata sa rai da zuwan Baffan ba sai kawai ta zata kunnenta ne ya jiye mata ba daidai ba.

    Tana nan zaune Mustapha ya turo ƙofar ɗakin ya shigo da sallama, bayan ta amsa sallamarsa yace ‘Baffan Mommy ne yazo, ga shi nan a parlor na. Da mamaki ta kalli Mustaphan da alamomin tambaya a fuskarta, tace ‘Baffana? Ya yi ‘yar dariya saboda yanda ta tambaya sannan yace ‘Baffan Nabeela dai. Ita ma sai ta ɗan yi dariya tare da miƙewa tsaye; kwata-kwata ba ta yi zaton ƙararta Mustapha ya kai wajen Baffa ba.

    Ta yi zaton zuwa ya yi ya ga sabon gidansu kamar yanda take ta faman roƙonsa tunda suka tare ya zo ya ga gidan. Nan da nan ta tashi ta fice don zuwa ta taryi Baffan nata. Sai da ta shiga kitchen ta jera ruwa da lemo a faranti sanna ta fito, ta dubi Habib wanda yake zaune a parlor ɗin yana riƙe da Hammad tace ‘Yaya ku taso ku gaida Baffa ga shi nan a parlor ɗin Abbanku.’

    Tana shiga parlor ɗin ta same shi da Shukra da Nasreen yayin da Abban nasu yake zaune daga gefe a kan kafet; yanayin zaman da Mustaphan ya yi kawai ta kalla ta sha jinin jikinta. Ko da bai kai ƙararta gida ba to tabbas ta san a wannan ɗan zaman da Baffan ya yi ya gaya masa laifinta. Ta ƙarasa ta ajiye ruwan a gaban Baffa a daidai lokacin da Naja wadda ita ma ta shigo ta gaishe shi take ficewa daga parlor ɗin.

    Ta zauna daga gefen ƙafarsa sannan ta gaishe shi ya amsa cike da girmamawa. Sai da ya gama raha da yaran sannan ya zaro sababbin kuɗi a aljihunsa ya ba wa kowa naira dubu sannan ya sallame su suka wuce suka bar su daga shi sai Khadeejan da Mustapha. Ya dubi Khadeeja ya yi gyaran murya sannan yace ‘Deeje, garin yaya kika ce ba za ki taimaka ki karɓarwa abokiyar zamanki hidimar gida ba bayan ba ta da lafiya?

    Haba Khadeeja, hakan ai shi ne zaman tare tunda dai Allah ya haɗa ku. Ta yi shiru ta sunkuyar da kai tana tunanin ta inda za ta fara, ina ma da Baffa ya zo da Mommy. To ta ina za ta fara gaya wa Baffa yanda Mustapha ya yi mata lokacin tana nata laulayin? Kuma ya za a yi ta gaya wa Baffa cewa ita ba ta bin Mustapha ɗakinsa kuma duk ranar da ba ta bi shi ɗakinsa ba Naje yake kira ta taya shi kwana?

    To ai Baffa ma sai dai ya sake yi mata faɗan ƙin zuwa ɗakin miji domin tabbas abu ne da haka aka saba; kuma ta sani mata biyu ne da kakanta mahaifin baffa. Wanda da wayonta kafin dukansu su rasu ta san matan ne suke zuwa ɗakinsa. Wannan kam ai sai dai ta ƙara kai ƙarar kanta.

    Muryar Baffa ce ta katse ta yana cewa ‘Deeje me yasa ba za ki taimakawa abokiyar zamanki ba? Ta ɗan yi firgigit kamar wadda aka tasa daga bacci sannan tace ‘Uhm Baffa wallahi ni ma daurewa nake ina yin hidimar ranar girkina, tunda ga jego ina yi sannan kuma ina zuwa aiki. ‘Eh, ai wannan ba zai gagare ki ba tunda kin ga da a ce ke kaɗai ce a gidan ai duka za ki haɗa ko?’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci sannan daga baya tace ‘Baffa ni ma fa haka nake haɗa nawa laulayin da aikin gidan babu wwanda yake taya ni. Kuma ka ga Baffa akwai mai aiki fa wadda za ta iya yi mata duk abinda take so idan ta yi mata bayani. Baffa ya ɗan yi murmushi sannan yace ‘Na fahimce ki Khadeeja, amma dai ki yi haƙuri ki karɓar mata aikin.

    Tunda kin ga yanzu ke ma idan kika kuma samun wani cikin ai za ta karɓar miki ko? Ki yi haƙuri Deeje, ba na son taurin kai da yawa. Allah zai ba ki lada har kashi biyu, ladan biyayya wa miji da kuma ladan taimakon ‘yar uwarki musulma wadda take neman taimakon naki. Ki yi haƙuri kin ji, tunda ga yarinyarki nan tana taimaka miki ki zauna lafiya tunda dama yara duka naki ne tun kafin ma a auro ta.’

    Haka Baffa ya ɗauki lokaci yana ba ta haƙuri, daga ƙarshe kuma ya ba ta umarnin lallai ta taimaka wa Naja ta karɓi hidimar gidan. Bayan ya miƙe duka suka miƙe gaba ɗaya, a nan ya yi sallama da Khadeeja yace ta koma ciki. Suka fice shi da Mustapha wanda ya yi masa rakiya har wajen motarsa sannan ya yi masa sallama ya tafi.

    Ya san ko da ya koma wajenta a yanzu ba za ta saurare shi ba sai dai ma ta gaya masa maganganun da ba ya son ji, don haka ya wuce wajen Naja tunda dama kwananta ne. Har turiri take ji yana taso mata a ƙirjinta saboda tsabar yanda zuciyarta take tafasa; sai da ta yi da gaske sannan ta kai kanta ɗakinta ba tare da ta rushe da kuka ba. Ya za a yi a ce ta karɓarwa Naja girki saboda kawai tana da ciki?

    Bayan ita a lokacin da tana da nata cikin haka ya dinga barinta da duk wata hidima yana hana yaranshi su taya ta. Sannan kuma idan ta yi magana ya dinga nuna mata cewa laulayi ba komai ba ne kamar ma dai ita ce take son nuna raki. Yanzu kenan haka za ta kwashe wata takwas ko tara tana kula da yara yayin da Naja take kwana da miji tunda laulayin bai hana idan ta same shi shi kaɗai a ɗakin ta kai masa kanta ba?

    Tana shiga ta murza mukulli ta rufe ƙofar, sai da ta ƙarasa kan daddumar da ta tashi sannan ta zube da gwiwoyinta ta rushe da kuka. Shikenan ita ta zama baiwar Mustapha ne? Ya iya nunawa kowa ƙauna da tausayi a duniya amma banda ita? Anya za ta iya wannan rayuwar a gidan Mustapha kuwa? Amma ta san dole ne ta bi umarnin Baffanta, musamman da yake a gaban Mustapha ya ba ta umarnin. Ta kifa goshinta a ƙasa ta sake rushewa da kuka.

    Ya so ƙwarai kamar yanda ya saba leƙawa da daddare ya yi wa wadda ba ta da kwana sai da safe ya leƙa wajen Khadeeja, amma da yake bai shirya rigimarta ba sai kawai ya ƙyale ta suka shige ɗaki shi da Naja suka yi kwanciyarsu. Ba ƙaramin daɗi ya ji ba da ya dawo daga masallaci sallar asuba ya jiyo motsinta a kitchen, tabbas ya san ta ji maganar Baffanta.

    Ba tare da ɓata lokaci ba ta shirya su sannan ya fito ya kai su makarantar. Kafin ya dawo daga kai su makaranta ta gama nata shirin, a zaune ya same ta a parlor ɗinta tana karyawa. Babu yabo babu fallasa suka gaisa, sai dai daga gaisuwar ba ta sake ko da kallon inda yake ba. Jimawa kaɗan ya miƙe zai fice, tace ‘Idan na tsahi daga aiki zan je gidan Mommy.’

    Ya ɗan tsaya yana kallonta yana ƙoƙarin su haɗa ido ko zai karanto wani abu a fuskarta, sai dai ba ta ba shi damar ba. Daga tsayen yace ‘Ki gaishe min da mutanen gidan. Ya fice ita kuma ta cigaba da cin abincinta ba tare da ko da ta kalli inda ya wuce ba; gaba ɗaya ma a halin yanzu ko kallonsa ba ta son yi.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Huɗu

    Yana shiga parlor ɗinta ya kai hankalinsa kan dining table, yanda ya ga wajen a jere da kwanuka ya tabbatar abincin ne ta dafa ta ajiye masa. To me yasa ta yi hakan? Ya ƙarasa kan tanle ɗin ya buɗe kwanukan ya ga abinda ta dafa, sannan ya taɓa flask ɗin ruwan zafi ya ji shi a cike; tabbas ya san shayi ta dafa masa.

    Ya gyaɗa kai ya juya ya nufi ɗakinta. Duk da ita ba mace ce mai son mu’amala ta turaren wuta da humra ba amma dai tana son ƙamshi, tana da haɗaɗɗun turarkanta na jiki da na kaya waɗanda idan dai ta zauna a waje sai ka ji ƙamshinsu. Yana tura ƙofar ɗakin nata ƙamshin turarenta ya yi wa hancinsa maraba.

    Fitilar ɗakin a kashe take sai dai dim-light wadda take ajiye a kan durowar gefen gado ita ce a kunne; ga alama bacci ne ya kwashe ta ba tare da ta kashe fitilar ba. Ya ƙarasa kan gadon inda take kwance, ya leƙa fuskarta; bacci take yi hankalinta a kwance ga shi yanayin baccin ya yi wa fuskarta kyau. Kamar ya ƙyale ta sai kuma ya canza tunani, ya zauna a hankali a gefen gadon daidai inda ƙafafunta suke, ya ɗaga abinda ta rufa da shi ya sosa mata tafin ƙafa a hankali.

    Ta janye ƙafarta da sauri sannan ta buɗe ido a hankali hankalinta gaba ɗaya yana kan Hammad wanda yake kwance a cikin gadonsa na baby a gefen gadon nata. Ya yi dariya a daidai lokacin da ta gan shi, ya lakace mata hanci yana cewa ‘Yanzu mutum ɗaya ne a rayuwarki wato Hammad ko? Ke na taɓa amma ba abinda ya taɓa ki kike nema ba yaronki kike nema kada a taɓa miki shi.’

    Ta yi murmushi ta mutssike idonta tana gyara zama sannan tace ‘To ina laifi, ni ce gatansa ka ga kuwa dole na kula da amanar Allah. ‘Haka ne. To a taso a ba ni abincina yunwa nake ji sosai. Ta zubo ƙafafunta daga kan gadon ta miƙe tana cewa ‘Bari na wanko baki. Ta wuce ta gaban shi ta nufi banɗaki.

    Ya bi bayanta da kallo yana yaba yanda jego ya karɓe ta. Ya daɗe bai ganta a haka sanye da rigar bacci kamar wannan ta jikinta ba sai yau kuma ta yi matuƙar burge shi. Yana nan zaune yana lissafi ta fito daga banɗakin suka fito parlor ɗin. Sai da ya zauna a table ɗin sannan ta zuba masa abincin ta ajiye a gabansa, ta koma ta haɗa masa shayi kamar yanda yake so shi ma ta ajiye masa ta koma ta zauna a kujerar kusa da shi.

    Tun kafin ta zauna ya fara cin abincin saboda da gaske yunwar yake ji; bayan ya cinye lomar bakinsa ya dube ta yace ‘Ke kin ci abincin ne? Tace ‘Um, mun ci ni da yara mun ƙoshi tun ɗazu. Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan yana cin abincinsa yace ‘Wai me yasa ba ki saka abincin a parlor na ba kika kawo shi nan?’

    Ba tare da wata damuwa ba tace ‘Ba komai, kawai dai nan ɗin ya fi min kusa da kitchen saboda sauƙin aiki ko? Um haka ne. Ki dinga sakawa a parlor ɗin kawai kin ji can ɗin zai fi yanda duk wanda yake son ya ci zai iya ɗiba. ‘Ok, next time in sha Allah. Suka sake yin shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan ya ajiye cokalinsa ya fara shan shayin.

    Bayan ya kurɓa ya ajiye kofin sannan yace ‘Kuma na ga ba ki gyara mana ɗakin ba, yanzu za ki gyara kenan ko a haka kike so mu kwana? Ta kalle shi da mamaki tana ɗan zare ido ‘Duk gyaran da na yi kuwa? Ko dai ba ka kalli ɗakin ba? Koda yake ba ka kunna fitila shi yasa ba za ka ga ɗakin sosai ba amma na gyara sosai fa.’

    Ya kula da tana maganar hankalinta yana kan ƙofar ɗakinta kamar dai ta za ta ɗakinta yake nufi ba ta gyara ba, yace ‘Ba fa ɗakinki nake nufi ba, ɗakina nake nufi tunda ai a nan za mu kwana. ‘Oh,..’ sai kuma ta ɗan sunkuyar da kai kamar dai ta kasa faɗin abinda take son faɗa ne. Ya kurɓi shayi ya bi ta da kallo yana jira ta ƙarasa faɗin abinda ta fara faɗa.

    ‘Gaskiya mu kwana a dakina, in ya so duk ranar kwana kai sai ka dinga zuwa ɗakina muna kwana. Da mamaki yake kallonta yana dariyar yaƙe ‘Khadeeja a ina kika taɓa jin miji ya bi matarsa ɗakinta kawai saboda su biyu ne? shikenan yanzu duk wacce take da kwana ni ne zan je ɗakinta kenan? Ta ɗan ɓata rai ‘Ni fa ba haka nace ba, ita idan tana so ta dinga zuwa ɗakinka ba ni da matsala da hakan amma ni dai sai ka dinga zuwa ɗakina.’

    Dariya ma maganarta ta ta so ta ba shi; tunda yake bai taɓa jin inda maigida yake bin ɗakin matansa ba sai dai a inda ba shi da ɗakin saboda ƙanƙantar gidan ko kuma a gidan haya. Amma ya za a yi yana da gida kamar wannan ga ɗakinsa da parlor ɗinsa amma a ce shi ne zai dinga bin mace ɗakinta? Allah ma dai yasa Khadeeja wasa kawai take yi.

    ‘Tunda kike don Allah kin taɓa jin inda aka ce maigida kamar wannan yana bin matansa ɗaki saboda kwana madadin su su je ɗakinsa?’ Ya tambaye ta yana nuna gidan, sannan ya cigaba ‘Kuma ma a wanne karatun aka biya miki haka bayan ga yanda kika taso kika ga ana yi? Ta kalle shi ta marairaice da fuska tana cewa ‘Don Allah ka bari mana, na ga ɗakin nawa ma duk gidanka ne ai meye don ka kwana a ciki.

    Ita ma Najan idan tana buƙatar hakan ba sai ka je ɗakinta ka kwana ba? ‘Oh, ni ne ma zan dinga bin ku ina kai muku kwanan kenan? ‘To meye a ciki, abu ne fa wanda ya zo a tarihi ma. Ya ɗan zaro ido yana kallonta ‘Wanne tarihin Khadeeja? In ce ko dai tarihin tsumburbura ne? Ta kula dai so yake ya raina mata hankali, kuma idan ba ta yi da gaske ba so yake ta dinga zuwa ɗakinsa kwana.

    Ita kuma gaskiya ba ta jin za ta iya kwanciya gadon da ya kwanta da wata matar ko da kuwa ba Naja ɗin ba ce. Gara kawai ya dinga zuwa ɗakinta. Ta ƙara ɓata fuska tace ‘To a islamiyya dai tunda ake biya mana sirah sai dai a ce Annabi SAW ya je ɗakin Aisha, ko ya je ɗakin Hafsa da sauransu, duk bayanan da aka yi mana sun nuna shi yake zuwa ɗakin kowacce.

    Kuma tunda dai auren nan shi ake kwaikwayo SAW ai ba zai zama matsala ba idan an kwaikwayi wannan ɗin ma. Buɗe baki ya yi kawai yana kallonta; ya rasa yanda aka yi Khadeeja take lale shi haka har take samun damar gaya masa duk maganar da ta ga dama. Ya jijjiga kai yace ‘To idan nace ba zan zo ba fa sai dai ke ki zo ɗakin nawa?’

    Ta yi murmushinta wanda yake ƙara ba shi mamaki; kana cikin magana da ita fuska murtuke sai kuma ta koma murmushi har ka ga kamar da zuciyarta take murmushin, haka ma kuma idan tana walwala lokaci guda za ta sha kunu ka zata kamar ba ta taɓa murmushi ba.

    Muryarta ce ta katse masa tunanin tana cewa ‘Na san ma ba za ka ce hakan ba, kai da gidanka. Abinda ko a parlor ka kwana babu wanda zai nuna maka yatsa balle don ka kwana a ɗakin matarka? Bin ta kawai yake da kallo yana jijjiga kai, yace ‘Toh tsara ni Khadeeja. Ta yi dariya tana miƙewa tsaye tana cewa ‘To ina laifi, yaushe rabon da a tsara ka.

    Kasa magana ya yi kawai ya dinga bin ta da kallo har ta gama kwashe kwanukan. Buƙatar ta yake yi saboda shi kansa ya san ya yi kewarta, don haka ma ba ya son ya ja rigima a wannan daren da yake son ya huce gajiyarsa. Gashi sai kai wa da kawo wa take yi tana kwashe kwanuka tana juya jikinta kamar da gayya, ya ma rasa me zai ce mata.

    Bayan ta gama kwashe kwanukan ta dafa kafaɗarsa tace ‘Sai ka shigo. Ba ta ko saurari amsar shi ba ta wuce ɗakinta ta bar shi a nan. Sai yau ya tabbatar Khadeeja ta raina shi; tunda yake bai taɓa ganin matar da idan ta yi niyyar abu sai ta yi shi ba ko da tsiya ko da tsiya-tsiya sai Khadeeja.

    Anya kuwa ba wani abu Khadeeja ta yi masa ba; idan ta ga dama ta gwada masa taurin kai da fitina idan kuma ta ga dama ta mayar da shi kamar wani sakarai ta yi masa wayo? Amma dai gaskiya ba zai juri bin ta ɗakinta ba dole ta haƙura ta yi yanda aka saba wato duk mai kwana ta bi miji ɗakinsa.

    Babu yanda ya iya da yake shi ne yake da buƙatarta dole ya tashi ya bi ta ɗakinta; kafin ya je ma bacci ya riga ya kwashe ta. Don haka sai da ya tashe ta ta sake lallaɓa ta sannan ya sami biyan buƙatarsa.

    Washegari ya kama ranar Asabar ce don haka yara ba su da makaranta; ko da ya dawo daga masallaci a kan dadduma ya sami Khadeeja a ɗakinta tana azkar, bayan ta idar ta gaishe shi sannan tace ‘Mantawa fa na yi jiya ban gaya maka yau ne bikin su Fatin Baba Sani wanda na nuna maka invitation ɗin last week ba. ’Ya gyara pillow ya kashingiɗe a kan gadon yana cewa ‘Ok, Allah ya sanya alkhairi.

    Ai insha Allahu ni ma za ni ɗaurin aure don Baffa da kansa ya turo min kati. ‘Ok. Ni sai wajen azahar zan tafi don ka ga ban je yawon arba’in ba sai na haɗa gaba ɗaya, idan na kwana biyu a gidan Mommy ranar Litinin sai na dawo. Ya ɗan ɓata fuska ‘Kuma shi ne har kwana biyu? Ai na zata a gidan bikin za ki ga duk wani wanda ya kamata ki je masa yawon.’

    Ta yi ‘yar dariya sanna tace ‘Kada fa ka manta bikin na dangin Baffa ne, ‘yan uwan Mommy su kuma ai sai dai na je musu gida yawon arba’n ɗin ko? Hajiya Nana dama ban kai mata baby ba ga su Anti Halima da Baba Usman. Ka ga yau a gidan biki zan wuni, gobe kuma tun safe za mu fara da Nabila; dama za mu kai musu katin bikinta tunda ka ga an fara rabo duk da dai bikin saura sati uku.’

    ‘Uhm, sai kun dawo. ‘Mun dawo kuma? Ni kaɗai fa zan tafi, Hafsa kawai zan ɗauka saboda Hammad. Ya tashi zaune yana fuskantarta ‘Na zata ke da yara za ki tafi kamar yanda kuka saba. Ta jijjiga kai tana dariya ‘Haba dai, yawon arba’in ɗin na kwashi yara har huɗu? Dama saboda babu mai kula da su ne yanzu kuma ka ga Antinsu tana nan. Ni kaɗai zan tafi.’

    Duk yanda ya so ta tafi da yaran nan haka ya haƙura ya ƙyale ta domin ta ci alwashin ba za ta sake tafiya da su danginta ba tunda yanzu suna da uwar ɗakin da za su dinga kawowa gulma. A kan lokaci ta gama abincin safe, sai dai da yake yana nan babu yanda ta iya haka ta jera a dining table ɗin parlor ɗinsa. Dankalin bature ta soya da ragowar sauce ɗin jiya da aka ci abincin dare sannan kuma da soyayyen ƙwai.

    Kowa a plate ɗinsa ta zuba masa har shi Mustaphan ta saka sauce a gefe da kuma soyayyen ƙwai. Nashi ta fara ajiye masa tare da na Shukra sannan ta juya ta koma kitchen ɗin. Tana shigewa kitchen ɗin ya dubi Afaf yace ‘Je ki ƙasa ki kirawo Antinki ta zo mu yi breakfast.’

    Nan da na ta miƙe ta fice, ya dubi Habib ya miƙe yana shirin ya bi Khadeeja kitchen ya karɓo nashi abincin yace ‘Shiga parlor ɗin Anti ka ɗauko kujerar dining guda ɗaya a ƙara. Don haka ya bi bayan Khadeejan. A hanya ta haɗu da shi ta riƙo plate biyu, tana ƙoƙarin miƙa masa yace ‘Abba ne yace na ɗaukowa Anti Naja kujera tare za a yi breakfast ɗin da ita.

    Kafin ta gama fahimtar abinda ya faɗa ya wuce ta ya nufi dining; tana ƙarasowa ta ajiye farantan hannunta ɗaya a gaban Nasreen ta zagayo da ɗayan za ta ajiye a kujerar da take kusa da Mustaphan a daidai lokacin da Afaf ta shigo tare da Naja suna tafe suna hira. Kafin ta yi magana ta zauna a kujerar da take kusa da Mustapha daga damansa a daidai lokacin da Khadeejan take shirin ajiye nata abincin a wajen.

    Ta yi cak ta ɗauke farantin da take niyyar ajiyewa ta dubi Habib tace ‘Yaya ka je kitchen ka ɗauko naka abincin ke kuma Afaf ungo wannan ni sai na ɗauko wani. Cike da fara’a Naja tace ‘Ina kwana Umman Hammad. Ita ma nan da nan ta saki fara’a ‘Lafiya ƙalau amarya ba kya laifi, ya gajiya? ‘Alhamdulillah. Sannu da aiki. ‘Yauwa.’

    Har cikin ransa ya ji daɗin yanda suka gaisa, haka yake son iyalansa ko da dai idan ba ya nan ba za su haɗu su yi hira ba to idan yana nan a zauna duka kamar haka a ci abinci tare; ya dubi Khadeeja yace ‘Yauwa ita ma ki taho mata da abincin ko? ‘Ok.’ Ta amsa a gajarce sanna ta juya ta nufi kitchen ɗinta. Kafin ta ƙarasa kitchen ɗin zuciyarta ta gama tunzura; Mustapha so yake ya yi mata dole kenan?

    Ta gaya masa ba za ta yi abinci da matarsa ba amma shi ne zai saka a kirawo ta har da zama a kujerarta. Lokacin da ita Najan take girki ai bai taɓa kiran Khadeejan yace ta zo su ci abinci ba shi ne sai yanzu don ya tabbatar mata Naja ita ce matar da yake ƙauna shi ne zai ce ta ba ta abinci. Nan take ta juye ragowar dankalin wanda dama ba yawa ne da shi ba ta ajiye ne saboda Shukra, ta haɗa da wanda da ta zuba wa Afaf ta zuba sauce da ƙwai.

    Ta haɗa shayinta mai kauri ta ɗauka ta wuce ɗakinta ta bar Hafsa a kitchen tana cin nata abincin. Shiru Khadeeja ba ta fito ba, kowa yana ta cin abinci yayin da Naja take shan shayinta wanda ta haɗa. Shirun ya yi yawa ya dubi Habib yace ‘Je ka dubo ko Antinka dankalin ta tsaya soyawa? Bai daɗe da shiga ba ya dawo yace ‘Abba ba ta kitchen ɗin, tana ɗakinta kuma ta kulle ƙofar.

    Ya zauna ya cigaba da cin abincinsa ba tare da wata damuwa ba. Ajiye fork ɗin da ke hannunsa ya yi, ya yi shiru saboda takaici; mantawa ma ya yi ya ba wa Khadeeja mukullin ɗakinta saboda a da ya yi alƙawarin ba zai sake ba ta mukullin ɗakinta ba saboda yanda take kulle kanta a ciki ta yi burus da kowa. Ya ture kwanonsa ya miƙe, ita ma Naja ta miƙe a lokacin.

    Ya kalli plate ɗinsa; ya riga ya ci da yawa sannan kuma sauran duk ya dame da sauce. Cike da damuwa ya cewa Naja ‘Ko wannan za ki ci naje na dubo. ‘No, kada ka damu. Ku ci abincinku akwai bread a ƙasa zan je na ci.’ Ta juya ta fice daga parlor ɗin ba tare da ta surare shi ba. A fusace ya nufi ɗakin Khadija, tun kafin ya fara buga ƙofar ya kirawo sunanta.

    Ba tare da ɓata lokacin ba ta amsa sannan ta taso ta buɗe masa ƙofar, ko a fuska ba ta nuna masa ta san ta yi laifi ba. Ya shige cikin ɗaki ya kalli abincin da take ci a gefen dadduma yace ‘Ya za ki taho nan ki kama cin abinci ki bar mutane? Kuma kina ji nace ki ba ta abincin ita ma. Duk yanda ta so ta bi maganar a hankali bai samu ba, domin yanda ya yi mata wannan tambayar da isa da gadara take ta ji duk wata kara da za ta iya yi masa ta bushe.

    Ta kalle shi ta kawar da kai sanna ta wuce shi ta koma ta zauna a gaban abincinta inda ta taso sannan tace ‘Gani na yi kun cike table ɗin, abincin kuma babu tunda ni ban soya dankali da ita ba. Me kake so na ba ta? ‘Ai tun jiya nace ki dinga saka abincin a can don kowa ya ci kuma kika amsa ko? Me yasa ne kike so ki dinga raina ni a gaban mutane? Saboda me nace ki ba ta abinci ba za ki ba ta ba zaki shigo nan ki bar mutane?’

    Ta kula dai duk wani zille-zille ba zai yi mata ba, ta kalle shi suka haɗa ido ta yi murmushin yaƙe mai ɗauke da takaici sannan tace ‘Kwana kusan talatin ta yi a gidan nan tana girki ba ta taɓa ba ni ba, kuma tare kuke cin abinci kai da ita da yara ba ka taɓa cewa a kirawo ni na ci abinci ba; ko da yake ko ka kirawo ni ma ba ci zan yi ba tunda ni ma na iya girkawa.

    Ka yi haƙuri ba zan haɗa girki da matarka ba ita ma kar ta haɗa da ni, duk wanda ya girka yaci shi da maigida da yara kawai. Ta miƙa hannunta ta ɗauki fork a kan plate ɗin da yake gabanta ta fara wasa da shi tana ƙoƙarin tokare takaicin da yake taso mata yana neman ya saka ta kuka.

    ‘Wai ke me yasa ban isa na gaya miki magana ki ji ba ne Khadija? Ko.. ‘Ita da ka gaya mata ai ta ji har ta ba ni abincin, ko da yake ita ka ɗauka mutum shi yasa kake nema mata abinda za ta ci. Ni da babu wanda ya damu da rayuwata ina nan kake fita ka siyo muku abinci ka saka ta a gaba ita da yaranka ku cinye ba tare da ko rabona an ba ni ba. Ban yi magana ba, shi ne kuma yanzu za a ce ni zan ba ta abinci; to ta cigaba da jira na ta ga idan za ta ci abinci.

    Ta gyara zama ta jingina da bango ta kawar da kai. Ya rasa abinda zai gaya mata saboda tabbas ya san duk abinda ta faɗa gaskiya ne, sai dai a wancan lokacin ai laifi ta yi masa na ƙin amincewa ta kula da yara don haka bai ga dalilin da zai sa ya ba ta abincin da ya siyo ba bayan ta ƙi ta girka. Ba tare ya ce mata komai ba ya fice daga ɗakin don a yanda ya san Khadija da taurin kai sai dai ya datse igiyar auren nan amma ba za ta yi abinda yake so ba.

    Sai dai tabbas idan ta cigaba da gwada masa taurin kai irin wannan zai datse igiyar auren ya huta, ta je can gidansu ta cigaba da taurin kan. Haka ya ƙarasa shiryawa zuciyarsa babu daɗi, don ko ɗakin Najan ma bai shiga ba suka fice tare da Habib suka tafi ɗaurin aure. Yana ficewa ita ma ta gama shiryawa, ta kulle ɗakinta da parlor ɗinta gaba ɗaya.

    Ta haɗa mukullanta da wanda ta cire daga jikin nashi keys ɗin duka ta jefa a jaka don ba ta so ko shi ya buɗe mata waje idan ba ta nan. Ta goya Hammad ta tasa Hafsa a gaba, suna saukowa ƙasa ta shiga parlor ɗin Naja inda ta jiyo hayaniyar yaran, ta dube ta da fara’a tace ‘To Anti ni na fita, zan je gidanmu ne in sha Allahu zan kwana biyu. Sai ranar Litnin zan dawo.’

    Ta juyo ta yi mata wani kallo na raini sanna tace ‘A dawo lafiya. Shukra ta tashi da gudu ta kama hannunta tace ‘Anti gidan Mommy za ki je? Ta shafa kanta ‘Can zan je Shukra, sai ranar Monday zan dawo. Ta langaɓe kai tana cewa ‘Kai Anti ina son zuwa fa, kwana biyu ban je wajen Anti Nabila ba fa.’

    ‘Ai kin ga Monday akwai school ko? Shi yasa ba zan tafi da ke ba. Amma idan zan koma ranar da babu makaranta zan tafi da ke kin ji. Haka ta tsaya ta lallaɓa ta sannan ta wuce.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Uku

    Sai bayan la’asar suka dawo tare kamar yanda suka fita, a lokacin yara suna islamiyya. Don haka cikin walwala ya ƙarasa ciki don ya san Khadeeja ta kular masa da yaran. Sai da ya leƙa parlor ɗinta ya gaya mata ya dawo sannan ya wuce ɗakinsa. Yara suna dawowa daga islamiyya suka wuce parlor ɗin Naja inda suka jiyo su ita da Abbansu.

    Kafin wani ya yi magana Shukra ta faɗa jikin Naja tace ‘Yauwa Anti kin dafa mana abinci ko? Wallahi yau gari muka sha mu da Anti, tace idan kin dawo za ki dafa mana abinci. Ta kalli Mustapha sanna ta sake kallon Shukran, kafin tace wani abu Mustaphan ya janyo Shukra jikinsa yace ‘Gari kuka ci Shukra?’

    Ta ɗaga masa kai. Nan take ragowar yara suka tabbatar masa da haka aka yi. Ya kalli Afaf wadda shigowarta kenan tana ƙoƙarin zama yace ‘Ke ba sai ki dafa muku ko indomie ba ce? Ta zumɓura baki ta kawar da kai ba tare da tace komai ba. Ya yi gajeren tsaki sannan ya dubi Nasreen yace ‘Ina Hafsa? Ita ba sai ta dafa muku ba?’

    ‘Ita ma garin ta ci ai, Anti ba ta ce ta dafa komai ba haka tace mu jira Anti Naja ta dawo ita ce da girki. Ya kalli Najan wadda take ta faman cika tana batsewa, ya miƙe a fusace ya fice daga parlor ɗin. Tana zaune a parlor ɗinta tana shan kunun alkama ya same ta.

    Kafin ta gama amsa sallamarsa ya fara magana a fusace ‘Khadeeja wane irin raini da wulaƙanci ne zai saka ki ba wa yara gari, ke ba za ki girka musu abinci ba kuma ba za ki saka yarinyarki ta girka musu ba. Ta ajiye kofin kununta ta kalle shi tana jijjiga kai sannan cikin halin ko in kula tace ‘To ai mai girkin ba ta bar musu abinci ba kuma ba ta barwa yarinyar tawa wani abu tace ta dafa musu ba, shi yasa da aka ji yunwa na haɗa mana gari duka muka sha. Ina laifi?’

    Ya fesar da iska mai zafi saboda yanda takaici ya kama shi, ba ya son yanda idan Khadeeja za ta yi masa fitina take zama da nutsuwarta shi kuma tana saka shi yana yin spark. ‘Khadeeja, don Allah me kike so ne kike min wannan wulaƙancin? ‘Ba wulaƙanci nake maka ba. Abu ɗaya kawai nake so shi ne ka yi adalci.

    Yanda nake buƙatar hutu daga kwana saboda jego haka nake buƙatar hutu daga hidimar gida da ta yara, don dama wallahi dagewa nake yi. Idan kuka gama arba’in ɗin muka fara rabon kwana sai na dinga haɗawa ina karɓa. Ya ja dogon tsaki ya yarfar da hannu, har ya buɗe baki zai yi magana kuma sai ya fasa. Ya juya ya fice daga parlor ɗin.……..

    Duk yanda yake tunanin Khadeeja za ta saurara masa hakan bai samu ba. Yana so ya mayar mata da kwananta da ya karɓa ya ba wa Naja amma kuma yana son ƙarin lokaci don ya ƙara sabawa da Najan. Haka dole ya haƙura ya zuba musu ido; sai dai duk wani jin daɗi da yake sa ran zai samu daga wajen Najan ba ya samuwa saboda yanda take wuni a gajiye saboda hidima.

    Suna kwanciya bacci yake kwashe ta; ga shi kullum cikin yi masa mita take a kan ita ya mayar da hidimar yara wajen Khadeeja. Duk da kusan Khadeejan ta sallama musu Hafsa tana taya ta. Ita kuwa Khadeeja gaba ɗaya haushinta yake ji don gaba ɗaya ya daina kula ta, a yanda yake ji yanzu ma ba ya jin zai kula ta koda ta yi arba’in ɗin idan dai ba itace ta kawo kanta ta ba shi haƙuri ba.

    Duk yanda Naja ta za ta kula da yaran nan zai yi mata sauƙi abun ba haka ba ne, domin da ƙyar take kai wa yamma saboda gajiya. Ga shi Khadeeja ta sallama musu Hafsa kullum cikin taimaka mata take; abu ɗaya da Khadeeja ta hana Hafsa yi mata shi ne girki. Ta so ƙwarai a ce ta dinga bar wa Hafsa tana yi musu girki idan ta fita, amma Khadeeja ta ƙi bari.

    Don haka kullum kafin ta fita aiki sai ta dafa musu abincin rana kuma idan ta dawo sai ta yi na dare. Ga shi duk da suna shiri da Afaf ta gane Afaf ta fita son jiki, don duk yanda take jin za su taya ta aiki hakan ma bai samu ba.

    Yau satinta biyu da tarewa; yana zaune a parlor ɗinta shi da yaransa kamar yanda suka saba suna kallon TV bayan sallar isha’i. Ita kaɗai ce a tsaye tana ƙoƙarin jera abincin dare a dining. Tana jerawa tana mita a ranta yanda yaran ba sa taya ta aiki, ko da za ta ce su taya ta to fa idan dai yana nan ba za su taya ta ba; sai dai ta yi aikinta ita kaɗai.

    Gashi kuma ba ya son Hafsa ta dinga yi masa girki. Bayan ta gama jera abincin suka taso gaba ɗayansu suka zauna har da ita suna cin abinci. Jollof sphagetti ce da kifi; ana cikin cin abincin Shukra ta ɗaga kifin da yake kwanonta tace ‘Abba a cire min ƙaya. Har ta buɗe baki za ta ce Afaf ta cire mata ya yi sauri yace ‘Ki miƙowa Antinki ta cire miki.’

    Haka Afaf wadda take zaune a tsakanin Najan da Shukran ta ɗauki plate ɗin da yake gaban Shukran ta miƙawa Naja. Ba tare da ta ce komai ba ta sa hannu ta ɓara kifin gida biyu ta cire ƙayar sannan ta miƙawa Afaf wadda ta sake miƙawa Shukra. Haka har suka gama cin abincinsu babu wanda Naja ta sake yi wa magana.

    Tana zaune a gefen gado tana shirin kwantawa bacci ya tura ƙofar ya shigo da sallama, da ƙyar ta amsa sallamarsa saboda yanda take jin haushinsa. Gani take kamar da gayya ya bari matarsa ta sallama mata yaran sannan kuma sun kai su kula da kansu amma komai sai yace sai ta yi musu.

    Ya ƙarasa ya hau gadon ta bayanta ya kwanta, tana kwanciya ya janyo ta jikinsa. Ta ɗan ture shi tana cewa ‘Bacci fa nake ji Habibi, wallahi na gaji. Kuma ka ga gobe yara za su makaranta kuma zan je aiki. Ya ƙara ƙanƙame ta yana laluba jikinta yana cewa ‘Sannu, bari na yi miki massage yanzu gajiya za ta sauka.’Ta dage ta janye jikinta ta zauna a kan gadon, hakan ya sa shi ma ya tashi ya zauna a kusa da ita yana kallon fuskarta kamar mai neman amsa a fuskar tata.

    Kafin ya yi magana ta langaɓe kai tace ‘Habibi ni dai don Allah ka mayarwa da maman Hammad kwananta, in ya so mu cigaba da yi kwana bibbiyu yanda tsarin yake. Da mamaki ya kalle ta suka haɗa ido sannan yace ‘Kin gaji da ni kenan Baby. Ta miƙa hannu ta shafi gefen fuskarsa tana murmushin yaƙe sannan tace ‘Ya za a yi na gaji da kai, ni kam ai ban ƙi ba a ce ni kaɗai ce matarka kullum muna tare.

    Amma ka ga aiki yana yi min yawa sosai, yi wa yara abinci kaɗai ya ishe ni da shirya su makaranta. Kullum a gajiye nake kai kanka ba ka samun yanda kake so a wajena. Amma ka ga idan zan dinga samun kwana biyu a tsakani na huta ai ina ga hakan zai fi mana sauƙi ko?

    Tunda nace a ɗaukar min mai aiki ka ce Hafsa ta ishe mu; ita kuma wannan yarinyar wallahi ƙarin aiki ce saboda ta fi su wasa da son jiki. Ni ban ma san yanda aka yi Khadeejan take zama da ita ba. Kawai dai kace ta karɓi kwananta. Har ta gama maganar yana bin ta da kallo ba tare da yace komai ba, sai da ta gama ta numfasa sannan yace ‘Um haka ne, amma dai ai kin ga kula da yaran yanzu fa ba wani aiki ba ne tunda gaba ɗayansu kowa ya iya kula da kansa.

    Kusan za a iya cewa abinci ne kawai sai an dafa musu. Ta kalle shi suka haɗa ido. Har ta buɗe baki za ta yi magana kuma sai ta fasa; ta kula ba so yake ya karɓi uzurinta ba. Yaran da hatta kula da kan nasu ma da yake cewa sun iya idan dai ba ta tsaya a kansu ba babu wanda zai yi, idan kuma aka bar su haka yace zai yi wa mutane fada.

    Ta ja numfashi sannan tace ‘To ka dai mayar mata da kwananta don Allah, a fara rabon haka tunda ka ga yanzu saura kusan sati uku ta cika arba’in ɗin. Ya numfasa ya zame sannan ya janyo ta jikinsa ta gyara mata kwanciya yana shafa bayanta sanna yace ‘Kada ki damu, in sha Allahu da safe zan yi mata magana. Ai na san kina ƙoƙari wajen kula da yaran nan kuma suma za ki ga suna jin daɗin zama a wajenki, nagode sosai da kike kula min da su.’

    A haka dai ya samu ya lallaɓata suka kwanta. Ya san wulaƙancin Khadeeja, tabbas idan ya je yace mata za a fara rabon kwana yanzu ba lallai ta saurare shi ba. Baya jin ma zai iya tunkararta da wannan maganar idan dai ba so yake ta yi masa dariya ba. Haka ya cigaba da lallaɓar Naja don ba ya ma son ya tayar da maganar mayarwa da Khadeeja kwananta da ya ƙwace.

    Tunda ta kwana ashirin da bakwai da haihuwa ta yada wankan jego, kuma da yake ita ɗin mace ce wadda ta damu ta fatarta sai ta mayar da hankali wajen gyaran fata da gashin kanta waɗanda ruwan zafi ya ɓata. A zaman da suke yi da Mustapha ta san yana jin haushinta saboda ta ƙi ta cigaba da kula da yara shi da amarya su yi amarci, ta san ba lallai ya ba ta wasu kuɗi ba.

    Don haka ‘yan kuɗaɗenta da ta samu a barkan Hammad su ta fito da su ta nemi Baffanta ya ƙara mata dubu goma sannan ta haɗo kayan gyaran fata. Nan da nan cikin sati guda haske da santsin fatarta ya fara dawowa. Kamar yanda ya saba kullum da safe zai leƙa su gaisa kafin ya fita. Yau ɗin ma haka ya shigo parlor ɗin da sallama.

    Suna zaune a parlor ɗin ita da Habib suna cin abinci; ita tana zaune ta miƙe ƙafa da Hammad a kan cinyarta yayin da shi kuma Habib yake zaune daga gefenta yana cin nasa abincin. Funkaso ne ta soya da zafinsa tare da parpesun kaza suke karyawa da shi; don kanta ta dafa farfesunta amma ta riga ta saba shi Habib idan dai tana nan ba ya cin abinci a wajen Naja.

    Don haka idan dai ya shigo ba ta hana shi, domin wani lokacin ma ajiyewa take yi don ta san zai zo nema. Ya ƙarasa ya zana a kan kujera daga kusa da Khadeejan, bayan ya amsa gaisuwarsu yace ‘Nan kuka ƙule kuna cin daɗi ashe shi yasa na ji shiru. Ta yi dariya kawai ba tare da tace komai ba, Habib ne yace ‘To ai Abba Anti Naja tuwo ta dafa jiya na san ɗumame za a ci shi yasa na gudo.’

    Suka yi dariya gaba ɗaya. Ta san so yake yace zai ci domin yana son funkaso, ita kuma ba ta so yace zai ci saboda dafawa ta yi har abincin rana tunda so take ta fita idan ta dawo kawai sai ta ci abunta. Ya dube ta tana cinye funkason ƙarshen yace ‘Idan akwai funkason ki zuba min na ɗan ci, duk da dai na yi breakfast amma ya ba ni sha’awa.’

    Ji ta yi kamar tace masa babu, amma Allah ya sa ba ta iya rowar abinci ba, musamman ga mutumin da shi ya kawo cefanen. Don haka bayan ta cinye nata ta miƙe ta kwashi kwanukan ta shige kitchen bayan ta miƙawa Mustaphan Hammad; Habib shi ma ya kwashi nashi kwanukan ya bi bayanta.

    Jimawa kaɗan suka fito tare, ta kawo tray ɗin da ta riƙo ta ajiye a gaban Mustaphan sanna ta sa hannu ta karɓi Hammad; shi kuma Habib ya fice daga parlor ɗin.Ya sauka ƙasa ya fara cin abincin sannan ya dube ta yace ‘Shi ne kin yi funkaso ko ki kirawo ni. Ta yi ‘yar dariya tace ‘Ai na san ka riga ka ci better ka cika cikinka shi yasa na sa yarona a gaba muna ci mu kaɗai.

    Ya yi dariya ya mayar da hankali wajen cin abincinsa. Jimawa kaɗan ta tashi ta shige ɗaki, ba ta daɗe ba ta fito tana riƙe da takarda a hannunta. Sai da ta zauna sannan ta miƙa hannu ta ajiye takardar a gafensa tana cewa ‘Ga posting letter ɗina, jiya na karɓo. An yi posting ɗina gidan talabijin na ARTV.’

    Nan da nan ya ɓata rai, bai ce mata komai ba sai da ya ƙarasa cinye abincin sanna ya dube ta yace ‘Kin san dai ba na son aikin jaridar nan ko, sai da nace ki saka a yi posting ɗinki makaranta amma shi ne kika je kika saka aka kai ki gidan talabijin don ki dinga fitowa a TV.’

    Ta kawar da kai tana mamakin Mustapha. Tana karatunta na aikin jarida ya ganta ya auro ta amma tunda ya ga ta kusa gamawa yake ta faman gaya mata aiki ɗaya zai bari ta yi shi ne koyarwa. Wataƙila ma da a ce bai ƙara aure ba da ta haƙura ta yi koyarwar amma yanzu kam babu yanda za a yi ya auro amaryarsa tana aikin office duk da dai ba na TV ba ne; sannan ita yace koyarwa za ta yi.

    Tace ‘Ni ba ni nace su kai ni can ba, sun duba abinda na karanta ne kawai. Kuma idan nace a kaini makaranta na je na koyar da su me? Ni da na karanci aikin jarida.’Cikin halin ko in kula yace ‘Ko Hausa ba sai ki koyar ba ko English, amma kin san babu yanda za a yi na barki kina fitowa a gidan TV duk duniya suna kallonki kina iyayi ko?’

    ‘To yanzu ya kake so a yi? Ki je kawai su canza miki, idan kuma ba haka ba ni zan je a canza amma ba za ki yi aikin TV ba matuƙar da aurena a kanki ba na so. Ta ɗan gyara zama tace ‘To ai ko na je gidan ARTV ɗin ma ba lallai na dinga fitowa a TV ba tunda aiyukan suna da yawa kuma ba duk ma’aikatan ne suke fitowa a TV ba.’

    Ni dai ba na son ki je wajen kwata-kwata tunda idan dai kana wajen wata rana za a saka ki a wani shirin kuma babu yanda za ka yi. Kawai ki je su mayar da ke makaranta ko kuma ki ba ni takardun ni na je.’ Ya faɗa yana miƙewa tsaye. Ba ta ce komai ba yace ‘Ni na tafi gidan Hajia.’

    ‘A dawo lafiya, ka gaishe min da su.’ Ta faɗa ba tare da ta kalle shi ba, kuma da yake shi ma ba kallon nata yake yi ba bai ma san yanayin da take ciki ba. Ta bi bayansa da kallo bayan da ya fice daga parlor ɗin; ta ma rasa me za ta ce masa. Koyon aikin jarida ya ganta tana yi ya auro ta, kuma sau da dama ta sha gaya masa cewa babu abinda take so take buri kamar a ce yau ga ta a gidan talabijin tana karanta labarai ko kuma gabatar da wani shiri.

    Sai da ta kusan gama karatun sannan yake sanar da ita shi ba ya son matarsa ta dinga fitowa a TV, kuma duk lokacin da ya gaya mata ana gaya masa cewa ita kuma burinta ɗaya kenan a duniya. Daga baya ne ma ta fahimci cewa da ba don ya auro Naja a ma’aikaciya ba to da tabbas ba zai bar ta ta yi aiki ba ma gaba ɗaya.

    Yanzu kam ma sai ta ga kamar yana dai so ya takura ta ne saboda ba ta yi masa yanda yake so ba, amma za ta san yanda za ta ɓullo wa lamarin. Sai da ta bari dare ya yi lokacin ta san Baffa yana zaune a gida sannan ta kirawo shi, bayan sun gaisa ta sanar da shi abinda Mustapha ɗin yace game da inda aka kai ta bautar ƙasa.

    Bayan a saurari bayaninta yace ‘To ke ki je makarantar mana, ai ba shi ne aikinki ba tunda bautar ƙasa shekara ɗaya ne kawai. Tace ‘To ai Baffa idan na je ina fatan ne su riƙe ni su ba ni permanent aiki, kuma ka ga Baffa gaskiya ba zan iya aikin koyarwa ba don za a dinga samun matsala da ni.’

    ‘Um haka ne, to bari mu gani. To ko gidan rediyo za ki je a mayar da ke? In ya so sai na yi wa Mustaphan bayani. Baffa ni dai da ka yi masa magana ya bar ni na je gidan TV ɗin. Yace ‘A a, ki yi haƙuri ki yi a gidan rediyo tunda dai yace ba ya son a dinga nuna matarsa a TV kin ga kuma hakan ya nuna yana kishinki. Ki je ki yi a gidan rediyo ta yanda ko da an saka ki a wani shiri to muryarki kawai za a ji ba za a ganki ba.’

    Ta so ƙwarai a ce Baffa ya goya mata baya ta tafi gidan TV domin shi ya san tun tana yarinya burinta kenan, amma ta san tunda yace haka ba zai goya mata baya ba; sai dai idan ta matsa ranta ya ɓaci. Don haka sai kawai ta haƙura. Suka yi sallama da Baffa suka ajiye wayar.

    Sati yana zagayowa ta fara bautar ƙasa a gidan radio na Freedom Radio bayan da Baffa ya kirawo Mustaphan ya yi masa bayani sannan ya ba shi haƙuri a kan ya bar ta ta yi a nan ɗin. Haka ya bari ba don ya so ba.

    Tunda ta fara zuwa aiki kuma sai aikin gida da na yara suka ƙara taruwa suka yi wa Naja yawa. Domin sai ya zama kullum idan Khadeeja za ta fita da Hafsa take fita saboda riƙe mata Hammad a wajen aiki. Ganin haka ya sa Naja ta saka Mustapha a gaba sai da ya bari ta ɗauki mai aiki wadda take zuwa kullum tana tafiya da yamma; tunda ya ce ba za ta raba wa su Afaf wanke-wanke da gyaran gidan su dinga yi idan sun dawo daga makaranta ba.

    Babu yanda ba ta yi da shi ya mayar wa da Khadeeja kwananta ba amma ya ƙi; saboda ƙi-faɗi. Duk da shi ɗin ma yanzu zai so a ce sun fara kwana bibbiyun tunda yanzu yana son shiga harkar Khadeejan; amma dai ya san Khadeeja ba za ta karɓi kwanakin nan da ta bayar ba tare da son ranta ba sai ta saka masa ciwon kai. Ita kuma ta so ta yi wa Khadeejan magana amma ba za ta yi ba.

    Saboda kusan tunda ta zo gidan ba wata magana da take haɗasu da Khadeejan bayan gaisuwa; da yake ma Khadeejan ba mai son fitowa ba ce sai ya zama idan dai ba aiki za ta je ba to za su iya kwana biyu ma ba su haɗu ba. Haka suka cigaba da rayuwarsu.

    Ranar Juma’a ce ta kama ranar da Khadeeja ta cika arba’in. Duk wani shiri ta gama yinsa, ta gama gyaran jikinta kamar yanda duk wata maijego take yi. Sai dai ba ta sa rai zai ba ta kwanan ba kuma ta ci alwashin ba za ta taɓa kai masa kanta ba sai dai shi ya kawo kansa. Bayan ta idar da sallar asuba sai ta sake bin gado ta kwanta tunda ta san Hammad ba zai taɓa wuce ƙarfe takwas yana bacci ba zai tashe ta.

    Ba ta san iya tsawon lokacin da ta ɗauka tana bacci ba bugun ƙofar da ake mata ne ya tashe ta, a tare suka farka da Hammad wanda ya sa kuka. Ta lalubo wayarta ta duba lokaci inda ta ga 8:30am; nan da nan ta mutssike ido don ya kamata a ce kafin ƙarfe tara ta fita ta tafi gidan rediyo. Sai da ta ɗauki Hammad sannan ta miƙe ta buɗe ƙofar. Hafsa ta gani a tsaye; bayan ta gaishe ta tace ‘Anti na gama aikin gaba ɗaya na ga ba ki fito ba kuma jiya kin ce min na shirya da wuri za mu fita.’

    ‘Hmm! Bacci ne ya kwashe ni. Zauna ki jira ni na shirya Hammad na miƙo miki shi ni ma na shirya mu tafi. Nan da nan ta shirya Hammad ta miƙa shi wajen Hafsa suka zauna a parlor sannan ta koma ɗakin ta shiga wanka. A gurguje ta yi wankan ta fito ɗaure da ƙaramin farin tawul ɗinta, tana riƙe da wani tawul ɗin tana goge jiki. Mustapha ta hango yana zaune a gefen gadonta ya miƙe kafa yana kallo a waya.

    Ba ƙaramin mamaki ta yi ba domin gaba ɗaya ta kasa tuna me yake jira. Ba wai ba ya shiga ɗakin ba ne amma dai tunda Naja ta tare bai zauna a ɗakin ba sai dai ya shiga ya gaya mata abinda zai gaya mata yana daga tsaye ya fice. Ta ɗan tsaya kaɗan ta kalle shi sannan tace ‘Ina kwana. Ya ajiye wayar ya amsa gaisuwar tata da fara’a. Ta ƙarasa gaban mudubi tana goge jiki yayin da shi kuma Mustaphan ya miƙe tsaye ya nufo ta.

    Ya ƙarasa ya tsaya a bayanta ya rungumo ta ta baya, ta kalle shi ta cikin mudubin suka haɗa ido tace ‘Fita fa zan yi ka ga ma na makara. Ya yi murmushi ya saka bakinsa a kan kunnenta yace ‘Ni ma fita zan yi, amma dai kin san yau kin yi arba’in ko? Ta ɗan motsa saboda yanda yake ƙara shigewa jikinta tace ‘Um. ‘Ok, ki karɓi kwananki yau sai ki ajiye min dinner.’

    Murya ƙasa-ƙasa tace ‘Toh. Ya sumbaci gefen wuyanta sannan ya sake ta ya juya. Har ya kusa zuwa bakin ƙofa kuma sai ya juya ya dawo, kafin ya ƙarasa inda take ita ma ta juyo don haka ya tsaya a gabanta. Cike da damuwa ya kirawo sunanta, bayan ta amsa yace ‘Bana jin daɗin yanda kuke zama da Naja kamar kuna gaba, please ki dinga ɗan zama a parlor ɗin kasa saboda ku saba.

    Ta dan yi murmushi tace ‘Ba wata gaba da muke yi tunda muna gaisawa, kuma duk abinda ya kama na magana ai muna yi. Ya kalleta suka haɗa ido sannan ya riƙe ƙwayar idonta yana cewa ‘Duk da haka dai ki dinga dan zama a can kuna hira. Kin ga idan kina nan ba za ta shigo ba ita ma sai ta yi ta zama a parlor ɗinta inda ke ba kya shiga.’

    Ba ta son ta ja zancen saboda ba ta son ta makara, don haka tace ‘To shikenan. Ya sake tsattsare ta da ido sannan yace ‘Please! Ta yi gajeren murmushi ta ɗaga kai. Ya fice bayan tayi masa a dawo lafiya. Ta ja tsaki bayan da ya fice; ba ta jin za ta iya raɓar Naja, ta tsaneta.

    Wataƙila hakan yana da alaƙa da yanda Mustaphan ya ɓata mata rai a kan Najan tun kafin aurensu da kuma maganganun da ta gani a wayar Afaf da suna chatting da Naja. Gaskiya ba za ta iya hira da wata Naja ba, gashi kuma ba ta iya munafurci ba balle ta je ta yi na ƙarya. Shi dai da ya ga Naja yana so ya auro ta suje can su ƙarata. Cikin sauri ta karasa shiryawa suka fice ita da yaranta.

    Tun kafin Magriba ta gama abincin dare, don haka Habib yana shigowa daga masallaci sallar magriba ta tura shi ya kirawo ƙannensa a wajen Naja. Nan suka zauna a parlor ɗinta suka ci abinci inda ta dafa macaroni da miyar hanta da salad. Suna gama cin abinci Afaf wadda dama bayan sallama ba ta ce mata komai ba ta tashi ta fice daga parlor ɗin. Sauran yaran kuma suka zauna a nan aka cigaba da hira ana kallon TV.

    Wajen 8:30pm duk suka fara jin bacci don haka da kanta ta tashi ta raka su ɗakinsu, ta shirya shukra sannan ta tsaya Nasreen ma ta shirya suka yi brush suka kwanta sanna ta koma nata ɗakin. Shi ma Habib ya yi mata sai da safe sannan ya wuce nashi ɗakin. Har zuwa lokacin Mustapha bai dawo ba, sai dai ya yi mata waya ya sanar da ita sun fita da Alhaji don haka sai ta gan shi.

    Don haka bayan ta yi wanka ta yi shirinta na bacci sai ta koma ta jera masa abincinsa a table ɗin parlor ɗinta sannan ta wuce ɗakinta ta kwanta. Sai wajen 9:30pm sannan ya shiga gidan. Kai tsaye bayan ya kulle gidan parlor ɗin Naja ya shige tunda ita ce a ƙasa. Tana zaune a kan kujera tana shan cornflakes ranta a ɓace. Ya ƙarasa bayan ta amsa sallamarsa ya sumbaci kumatunta sanna ya zauna a kusa da ita yana cewa ‘Cornflakes kike sha a daren nan?’

    ‘Um. To me gidan ce da girki kuma ba ta ba ni nawa abincin ba shi ne na haɗa cornfakes nake sha tunda ban saba zama da yunwa ba.’ Ta faɗa tana ƙara shan kunu. Ya ɗan shiga duhu, yace ‘Umm, Khadeeja ba ta yi abinci ba ne? Ta yi, amma nan ta turo aka kirawo yara suka je samanta suka ci abinci. Da suka gama cin abincin ma a can suka yi zamansu Afaf ce kawai ta sauko ta taya ni hira.’

    ‘Um! To ai na zata kowaccenku dama girkinta za ta dinga yi ko? Ta harare shi sannan tace ‘A ina ake haka? Tunda wadda take da girki ita ce za ta dinga kula da yara ai girkin ma gaba ɗaya za ta dinga yi. Shi yasa ni ma idan na yi abinci nake fito wa da shi nan parlor ɗin inda kowa zai iya ɗiba, ita ce ba ta fitowa ta ɗiba saboda ba ta son ganina.’

    ‘Wa ya gaya miki? Ba haka ba ne. Bari zan yi mata magana in ya so sai ta dinga yi da ke, ke ma ranar naki girkin sai ki dinga yi da ita kun ma ragewa kanku aiki. Ta zumɓura baki ‘Ah to don ni dai haka na san duk masu mace sama da ɗaya suna yi. Ya yi mata sallama ya wuce sama. Bata taɓa sanin idan Khadeeja ta karɓi kwana abun zai sosa mata rai ba sai a wannan lokacin.

    Gaba ɗaya zucuyarta ta yi ƙunci, haka ta bi bayansa da kallo har ya fice daga parlor ɗin ya rufe mata ƙofa. Nan take hawaye ya wanke mata fuska; ta ajiye kofin da yake hannunta a kan tebur ta haɗa kai da gwiwa ta sa kukan da ta kasa gane me ya kawo shi. Haushin Khadeeja ta karɓi kwana ko kuwa haushin an barta da yunwa?

    Yana ƙarasa shiga parlor ɗinsa ya kalli dining table, bai ga alamar abinci ba. Kamar ma ko taɓa wajen ba a yi ba tunda ya fita da safe. To me Khadeeja take nufi? Duk wannan ɗokin da yake na zuwa wajenta ita ashe ba ta gama fushin ba kuma ba ta gaya masa ba? Cikin sanyin jiki ya ƙarasa ya shiga ɗakinsa. Ga mamakinsa ɗakin ma ba a gyara ba.

    Yanda Naja ta fita ta bar shi da safe yana nan a haka, babu ma alamar da take nuna mutum ya shiga ɗakin bayan fitarsa. Khadeejan ma da yake sa ran zai gani a ɗakin ba ta ciki. To ina take? Me take nufi bayan ya sanar da ita yau ita ce da kwana?

    Gaba ɗaya  ranshi ya gama baci; ba ya son fitinar Khadeeja don ita rigima da ita ba ta ƙarewa, musamman a yanzu da yake da buƙatarta. Har ya juya zai fita kuma ya fasa, ya tsaya ya canza kaya ya shirya sannan ya ɗauki wayarsa ya fito ya nufi ɗakin Khadeejan.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyu

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyu

    Ta yi zaton ranar da kwana zai dawo kanta za ta ji tana cikin yanayin murna, sai dai ba hakan ya kasance ba. Yau ne za ta karɓi kwana amma sai ta ji kamar ma ba za ta iya bari ya kusance ta ba saboda kamar dai har yanzu ƙoƙari take ta saba da cewa su biyu ne matansa.

    Haka dai ta tashi ta gama duk wata hidima da take yi. Ya riga ya sanar da su cewa da daddare za a dinga karɓar kwanan don haka tun yamma ta shirya abincin dare; duk da ba ta cikin walwala amma haka ta girka abincin da ta tabbatar yana so; tuwo miyar kuɓewa danya. Ta haɗa komai ta jera a table ɗin sama.

    Sai dai ga mamakinta har wannan lokaci Naja tana ɗakinsa na sama, don haka ma ba ta ko je kusa da ɗakin ba tana jiran ya dawo ta ji ko shi ne zai biyo ta ɗakinta tunda dai kwananta ne. Da yake bayan ya ci abincin rana ya sake fita sai wajen 8pm ya shigo gidan.

    A ɗakinta ya same ta tana miƙe a kan gado da Hammad a kwance a kan cikinta yana wutsil-wutsil ɗinsa. Bayan ya amsa sannu da zuwanta ya ƙarasa ya zauna gefen gadon ya sa hannu ya ɗauki Hammad yana masa wasa. Suka ɗan taɓa hira sanna tace ‘Um ga abinci can a dinin fa, idan ka shirya sai mu je mu ci.

    Yara dai sun ci nasu don yau tun magriba Nas ta fara jin yunwa. ‘Oh,Ok.’ Ya amsa kamar mara gaskiya. Tace ‘Kuma na ga amarya har yanzu tana ɗakin naka fa, ko a nan za mu kwana ne? Kamar wanda aka tayar daga bacci yace ‘Umm. No, umm kin gane? Dama ina so na yi miki magana don da na san za ki dafa abincin daren zan ce ki dakata.’

    Ta kalle shi da mamaki tana jira ta ji ƙarashen bayanin, suka haɗa ido ya yi sauri ya kawar da idonsa. Suka ɗan yi jim sannan ya cigaba ‘Ina ga ya kamata tunda ke kina jego ki bar mata kwanakin naki zuwa lokacin da za ki cika arba’in ko? Ta tashi zaune tana ƙarewa Mustapha kallo ko zai sauya maganarsa, kamar bai fahimci saƙon ba don sai ya ƙara haɗe rai yana wasu muzurai.

    Ta yi murmushin yaƙe tace ‘Oh, yanzu kenan kwanan gaba ɗaya na amarya ne har sai na cika arba’in da haihuwar Hammad? ‘Eh, to ai kinga kina jego. Menene amfanin kwanan? Ta sunkuyar da kai, ta ɗago ta kalle shi sanna ta yi gajeran murmushi tace ‘Haka ne, Allah ya kai mu arba’in ɗin.’

    Kamar wanda aka tsikara ya miƙe yana yage baki yana cewa ‘Yauwa, to bari na je sai da safe ko. Cikin sauri ya miƙa mata Hammad fice daga ɗakin kamar wanda yake tsoron kada ta riƙe shi tace ta fasa. Ta bi ƙofar da kallo bayan ya fice; wasu hawaye masu zafi suka gangaro kan fuskarta a daidai lokacin da wani malolo ya taso ya tokare mata maƙogoro take neman kasa numfashi.

    Sautin rufe ƙofar ya dawo da tunaninta cikin ɗakin bayan da ta kifta idonta; ta yi murmushi mai ciwo tare da sunkuyar da kai. Wato dai yanzu Mustapha ya yi sabuwar amarya har ya fara gudunta, tunda ai lokacin da ta yi ɓari sai da ya nuna ɓacin ransa a kan tafiyar da ta yi gida. To me yake nufi da ita?

    Wato idan wahala ce ta je ita kaɗai ta yi ta sha kenan, lokacin da zai iya morarta shi ne lokacin da zai ba ta kwana. Lallai akwai aiki amma dai ba za ta fasa addu’a duk da zuwa yanzu duk dan wani karsashin kyautatawa Mustapha da take so ta yi ya zirare. Sai da Hammad ya fara kuka sannan ta yi ajiyar zuciya ta sa bayan hannunta ta share hawayenta sannan ta miƙa hannu ta ɗauko shi daga inda yake kwance ta saka masa nono.

    Har ya gama shan nonon ya saki tana ajiyar zuciya, ta shirya shi ta goya shi sannan ta fice daga ɗakin. Da yake dare ya yi tana jiyo muryarsu ƙasa-ƙasa sun hira tunda ɗakin nasa yana jikin nata ɗakin. Haka ta wuce da yake a parlor ɗinta ta jera musu abincin daren can ta wuce ta je ta kwashe ta mayar kitchen tana ƙwafa. Ta dawo suka kwanta ita da Hammad.

    Duk yanda take jin bacci a wannan daren kasawa ta yi, sai dai da yake bacci ɓarawo ne sai da ya faki idonta ya sace ta; sai ji kawai ta yi ana assalatu. Duk da ba sallah za ta yi ba sai da ta tashi ta wanke fuska sanna ta zauna ta yi azkar ɗinta sannan ta koma ta kwanta.

    Tun kafin a ɗaura aurensa da Naja ya riga ya gaya mata amarci za su yi na kusan kwana talatin domin lokacin da za ta tare zai yi daidai da kwanan Khadeeja goma sha biyu da haihuwa. Don haka ya sanar da ita gaba ɗaya kwanan nata ne har sai Khadeeja ta gama jego kwana arba’in. Ita Khadeejan ce bai gayawa ba shi yasa ma ta zata za a yi yanda aka saba ne ta karɓi kwananta bayan kwana bakwai.

    Ba ƙaramin daɗi ya ji ba da Khadeeja ta amsa masa ko da yake dama bai sa ran za ta ba shi matsala ba tunda dai ta san ba za ta biya masa buƙatarsa ba wadda a wannan lokacin ko Allah ma bai haramta masa ya kai wa ɗaya matar tasa buƙatar ba. Cikin walwala suka kwana shi da amaryarsa, ko da ya fito da asuba zai tafi masallaci ya hango fitila ta kasan kofar ɗakin Khadeeja don haka ma ya san ta riga ta tashi.

    Da sallama ya shigo parlor ɗin bayan ya dawo daga masallaci, kai tsaye ya nufi kitchen ɗin don ya jiyo motsinta a can. Tana tsaye da goyon Hammad tana zuba ruwan zafi a flask. Bayan ta amsa sallamarsa ta gaishe shi; yana ta wani kau da kai yana muzurai kamar yanda ya saba idan yana so ya gwada mata son kai haka ya amsa gaisuwar tata.

    Ta mayar da kettle ɗin inda take sanna ta buɗe fridge don ta ɗauko ragowar peppersoup ɗinta. Yace ‘Ina yaran? Ba su taso ba. ‘Eh.’ Ta amsa a gajarce ba tare da ta bar abinda take yi ba. Ya kula da yanayinta idan ya takura ta za ta iya birkice masa a safiyar don haka yace ‘Ok, idan sun shirya ki ce su buga min ƙofa please.’

    ‘Ok.’ Ta sake ba shi amsa a gajarce. Ya juya ya fice daga kitchen ɗin. Ta ƙarasa ɗumama soup ɗinta ta juye a flask, ta ɗauki ruwan zafinta ta haɗa ta kai ɗaki sannan ta dawo ta ɗauki kayan shayi duka ta shigar ɗaki. Ta zauna ta ci burodi da soup ta sha shayinta mai kauri sannan ta koma ta kwantar da Hammad ita ma ta kwanta.

    Ba ta daɗe da kwanciya ba kuwa bacci ya ɗauke ta saboda dama na jiya ba isar ta ya yi ba. Kamar a mafarki ta ji ana buga mata ƙofa, ta yi firgigit ta buɗe ido. Ko ba a gaya mata ba ta san wannan bugun Habib ne don haka ta tashi zaune ta janyo wayarta ta duba lokaci; 8:25am. Ta janyo zanin goyon Hammad da ke kusa ta rufe jikinta sanna tace ‘Shigo Habib.’

    Ya turo ƙofar ya shigo da sallama, tun kafin ta gama amsa sallamar tasa yace ‘Anti yau makara kika yi ne? Yanzu har past 8 fa kin ga ba mu tafi makaranta ba. To me yasa ba ku tafi ba? Ni ai na zata kun tafi tuni. Ya ƙarasa ya zauna a bakin gadon da mamaki a fuskarsa yana cewa ‘Anti ba ki tashe mu ba fa; ni ma bayan mun dawo daga masallaci da Abba har na yi wanka fa na ɗan kwanta don na san za ki tashe ni shi ne bacci ya kwashe ni.

    Su Afaf ma ga su can ko sallah ma ba su yi ba sai yanzu na taso su har Hafsan. Ta kama haɓa tana cewa ‘Ikon Allah. To ai ba ni ce da girki ba Habib, Antin ku ce. Ita ce za ta tashi kowa ta shirya shi yasa ma ka ga ban fito ba. Ya taɓe baki yana zare ido ‘Tab, to ai kuwa daga ita har Abban babu wanda ya fito.’

    ‘To Allah ya sa dai lafiya, ka je ka buga musu ƙofa. Ka murɗa kofar parlor ɗin a buɗe take sai ka ƙwanƙwasa ɗakin ka ji. Ya miƙe ya fice daga ɗakin yayin da ita kuma ta zame ta gyara kwanciyarta da niyyar komawa bacci.

    A tsakiyar parlor ɗin Habib ya ci karo da Abban nashi yana fitowa da gaggawa, suka haɗu a tsakiya suka yi cirko-cirko. Abban nasu yace ‘Kai Habib meye haka? Na cewa Anti ku taso ni idan kun shirya me yasa ba ku taso ni ba? Kai ko uniform ma ba ka saka ba. Yace ‘Abba ai makara muka yi, Anti Najan ba ta tashe mu mun shirya ba.”

    Kafin ya ba shi amsa sauran yaran suka shigo kowa da kayan bacci, ya kalle su sannan ya mayar da hankalinsa kan Habib din yana cewa ‘Wace Anti Naja kuma, ko dai Anti Khadeeja? ‘To ai ita ma Antin bacci take yi yanzu na je tashinta tace min ba ita ce da girki ba Anti Naja ce za ta shirya mu.’

    Mamaki ya kama shi; ya za a yi Khadeeja ta gayawa yaro wannan maganar? Wane irin wulaƙanci ne bayan ita ce ta saba shirya yaran kawai kuma yanzu sai tace Naja ce za ta shirya su? Ba tare da yace komai ba ya wuce yaran ya nufi ɗakin Khadeejan. Habib ya dubi ‘yanuwansa yace ‘Yau dai mun yi mising school, ni yunwa nake ji ma ku zo mu je ƙasa bread yana can ko shayi sai mu haɗa.’

    Ya wuce suka bi shi suka sauka ƙasa. Kusan a fusace ya tura ƙofar, hango ta da ya yi a kwance tana bacci ya ƙara harzuƙa shi. Sautin buɗe ƙofar ne ya farkar da Hammad daga bacci. Ta tashi zaune tana mittsike ido sanna ta miƙa hannu ta ɗauke shi. Ta dubi Mustapha cikin halin ko in kula tace ‘Ohhh! Abba ka tayar min da yaro yanzu babu sauran bacci.

    Ta ɗaga shi ya yi miƙa sannan ta saka masa nono yayin da Mustaphan yake cewa ‘Me ya faru na ga ba ki tashi kin shirya yara ba bayan yau akwai makaranta, kuma fa ko da asuba sai da na ce miki idan sun shirya ki ce su yi min magana? Tace ‘Oh! Ai ba su zo sun ce min sun shirya ba na zata ma sun gaya maka kun wuce sai da Habib ya gaya min yanzu sannan na sani.’

    ‘Ban gane ba, wai wace magana kike yi ne? To me yasa ba ki tashi kin shirya su ba? ‘Oh to ai wadda take da kwana ita ce da gida musamman ma da yake ni ina jego. Na zata da ka kai mata kwanan ka gaya mata abinda aka saba yi na running gidan. Mamakin da yake fuskarsa ya ƙaru ya haɗe da takaicin Khadeeja, yace ‘Ban gane wadda take da kwana ita ce take da gida ba Khadeeja.

    Ke kika saba shirya yaran nan kullum kuma kin san haka, shi ne yau saboda ganin ido za ki ce ita za ta shirya su? Idan kina jin haushina ai sai ki gaya min tunda ba dole na yi miki kika bar mata kwanan ba ko? Za ki fara wulaƙancin naki ko Khadeeja? Ta yi dariyar yaƙe tace ‘Wallahi ni duk ban gane ba.

    Ai ni a yanda na sani duk matar da take da kwana da girki ita ce take duk wata harka ta kula da gida, ni ma idan na karɓi girki sai na haɗa gaba ɗaya na yi. ‘Khadeeja, ba na son wulaƙanci. Yaran nan a hannunki suke kuma da ke suka saba, ya za a yi tana zuwa ki ɗora mata kula da su ita da yau za ta koma aiki ma.’

    ‘Amma dai ba da su na zo ba a nan na same su ko? Kuma idan ban manta ba ni ma daga zuwana aka haɗa ni da su, kamar ma ita an ɗaga mata ƙafa. Hidimarsu ta makaranta ma wadda ta riga ta saba yi tun ma kafin ta auri ubansu balle yanzu da ta aure ka, ai ina ga wannan ma ƙaramin abu ne.’

    Ya gama ƙulewa har wani huci yake, ya cije leɓe sannan yace ‘Khadeeja ba na son wulaƙancinki fa, yanzu me kike nufi da yaran nan? ‘Alkhairi nake nufi da kowa, kawai dai duk wadda take da kwana ta haɗa duk har gidan da yaran ta kula da su. Shikenan. Har ya juya zai fita ya juyo ya nuna ta da yatsa yana cewa ‘Yanzu shikenan kin tura mata yara har tsawon sati huɗu?

    Ta ɗago ta kalle shi cikin halin ko in kula tana cewa ‘Na tura mata mijin ma? ‘Mtsewww!’ ya ja dogon tsaki ya fice ya maka mata ƙofar. Ta yi ‘yar dariya ta cigaba da wasa da Hammad. Har ya koma ɗakin tana kwance tana baccinta domin office ɗin da za ta ta riga tace sai wajen sha ɗaya za ta tafi saboda an canza mata branch sakamakon aurensu da Mustapha; ta san tunda yau za ta fara reporting tana da damar makara.

    A hankali ya buɗe ƙofar ya shiga saboda kada ya tashe ta daga bacci, ya ƙarasa ya zauna a gefen gadon. Ya zuba fuskarsa a tafukan hannunsa yana shafa fuskar, gaba ɗaya kansa ya kulle. Ya yi zaton yaran nan tunda suna wajen Khadeeja shikenan a wajenta za su cigaba da zamansu ko da ya ƙara aure.

    Gaba ɗaya ma shi bai taɓa zama sun yi maganar yara da Naja ba, kawai dai yana saka ta hidimarsu idan ta kama kuma yana nuna mata cewa yana so su sami kulawar da yake jin sun rasa daga wajenta. Baya jin za ta ba shi matsala saboda yanda ya ga tana kulawa da su tun ma kafin ta aure shi balle yanzu da za ta yi da hujja. Ya juya ya ɗan taɓa ta. Ta buɗe ido ta kalle shi ta yi murmushi sannan ta yi miƙa.

    Tace ‘Honey har ka dawo? Ya ɗan kawar da kai sanna yace ‘Daga ina? ‘Umm! Na zata ‘yan makaranta ka kai. ‘No, ban kai su ba sun riga sun makara sosai sai gobe. ‘Ok, Allah ya kai mu. Ta zuro ƙafafunta ƙasan gadon ta kwanta a kafaɗarsa tana cewa ‘Bari na je na yi wanka sai na fito na haɗa mana breakfast. Ina jin ma kawai sai na shirya ka ba ni lift.’

    Yace ‘Ai kuwa sai ki yi sauri don ga yara can ma ke suke jira ki zo ki ba mu abincin gaba ɗaya. Ta ɗaga kafaɗarsa ta ɗan kalli fuskarsa da mamaki ‘Antin ba ta nan ne? Ya kawar da kai daga kallon da ta kafe shi da shi, yace ‘Tana nan. To ai kin ga kece da kwana don haka ke ce za ki dinga yin abincin duka gida kina kula da yara, in ya so idan ta karɓi kwana sai ta cigaba.

    Duk wadda take da kwana ita ce da gida. Ta sake leƙa fuskarsa da mamaki a kan fuskarta tace ‘Ban gane ba, ai ni ban karɓi girki ba, kwana ne kace ka tambaye ta ta ba mu har ta yi arba’in. kuma yara ai na zata tunda a wajenta suke sai su yi zamansu duk abinda ya kama ai zan saka hannu.’

    ‘A a, wadda take da kwana ita ce za ta dinga haɗawa ta yi komai kawai. Ki yi sauri ki yi wankan ki zo ki ba mu abinci. Shiru ta yi kawai tana bin shi da kallo. Jimawa kaɗan ya kalle ta suka haɗa ido, ya gyara zama ya kama hannuwanta duka biyun ya riƙe sannan yace ‘Kin ga wannan fa ba wani abun damuwa ba ne, ai dama kin san duk inda ake da mace sama da ɗaya ai dama duk wata hidima rabawa ake yi.

    Idan yanzu kika ki yin wani abu ai sai ki janyo kwanan amarcin ya ƙare tunda kin ga dole ne na koma kan tsarin kwana bibbiyu don tabbatarwa an yi adalci ko? Ta sunkuyar da kai tana kallon ƙasa don gaskiya ita ba ta zata haka ba; ba wai ba za ta kular masa da yara ba amma dai ta sa rai za su yi zamansu a wajen uwarsu ita ce za ta dinga hidimarsu ta kullum in ya so ita duk wanda ya zo inda take a cikinsu za ta yi masa duk wani abu da ya kama.

    Ta ɗago ta kalle shi tace ‘To yanzu kenan duk wadda take da kwana ita ce za ta dinga tashi tana yi wa yara komai? Ya ɗaga mata kai alamar e. ‘To idan za ni aiki fa. Ya kama haɓarta ya ɗago fuskarta, suka haɗa ido ya yi mata murmushi sannan yace ‘Ki bari wannan a hankali za mu ga yanda za a yi.’

    Ta ɗan ja baya za ta tashi, ya riƙe fukarta ya sake tsare ta da ido har sai da ta yi murmushi, ya sumbaci leɓenta sannan ya miƙe yana cewa ‘Muna ƙasa muna jiranki ni da yara. ‘Ok.’ Ta amsa sannan ta shige banɗaki. Ya tashi yafito daga ɗakin. A parlor ya tarar da yaran suna zaune suna shan shayi da burodi wanda Hafsa ta dafa musu ruwan zafin. Ya nemi waje ya zauna ya ɗauki remote ya canza channel.

    Ya fi minti talatin da zama shi da yaran suna ta hira sannan ta sauko, ta sha kwalliya sai ƙamshi take yi. Bayan ta amsa gaisuwar yaran kai tsaye ta wuce part ɗinta, nan da nan ya tashi ya bi bayanta yayin da Nasreen da Shukra suka rufa masa baya. Nan da nan ta soya ƙwai ta haɗa musu da shayi suka zauna shi da ita a dining table suka karya.

    Suna gama karyawa shi ma Mustaphan ya shirya suka fito tare. Har za su sauka daga bene sai kuma ya ba ta mukullin motar yace ta fito ta jira shi zai yi sallama da Khadeeja. A parlor ɗinta ya same ta tana kwance a kan doguwar kujera da remote a hannunta yayin da Hammad yake cikin baby rocker ɗinsa yana ta wutsil-wutsil.

    Tana daga kwance ta amsa sallamarsa, ya ƙarasa kusa da kanta yace ‘Za mu fita ni da Naja, ita ma yau za ta koma aiki. Tace ‘Ok, a dawo lafiya. Har ya juya zai fita tace ‘Ta dai bar wa yara abincinsu ko? Ga shi za su je islamiyya ko da yake na san sun yi wanka in lokacin ya yi ko Hafsa sai ta taya su shiryawa su wuce.’

    Ya juyo ya tsaya ya zuba mata ido na ɗan lokaci; ya ma rasa ta ina zai fara. Ya kan rasa yaren da zai yi wa Khadeeja magana da shi idan ta fara wannan taurin kan nata, lokuta da dama ya kan ɗauka cewa tana jin tsoronsa amma fitinar da yake gani a ƙwayar idonta idan tana wannan taurin kan tana ba shi tsoro. Ya cije leɓensa sanna yace ‘Fita fa nace miki za mu yi, ya kike so ta yi da abincin ranansu?’

    Ta tashi zaune ta gyara zamanta sannan tace ‘Yanda nake yi idan zan tafi makaranta ko? Ya jijjiga kai sanna yace ‘Khadeeja please kada ki saka min ciwon kai da safen nan, ga yara nan ki ba su abinci in ya so idan mun dawo ta ba su na dare. Idan kuma kin ga dama ki bar su da yunwa. Ta kalle shi suka haɗa ido ta yi masa gajeran murmushin yaƙe ta zame ta kwanta ba tare da ta ce masa komai.

    Haka shi ma ya juya ya fice zuciyarsa cike da wasi-wasi saboda ya san wannan murmushin nata ba wai yana nufin za ta kula da su ba ne, amma dai ya tafi yana addu’ar Allah ya sa ta kula masa da su.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Ɗaya

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Ɗaya

    Cike da ɗoki ya shiga ɗakin amaryarsa riƙe da ledarsa ta kayan ciye-ciye; tana zaune a can a ƙuryar gado. Ko da a ce ta amsa sallamarsa to shi dai bai ji ba, amma ya riga ya san yanda amare suke. Har inda take ya ƙarasa ya same ta bayan ya ajiye ledar hannunsa a kan mudubi.

    Ga mamakinsa bayan ya ɗaga fuskarta kuka take yi sosai da hawaye kamar wadda aka yi wa auren dole, don haka nan take ya shiga aikin lallashi. Sai da suka kusan minti talatin sanna ya samu ta goge hawayen ta saurare shi. ‘Wai me ya faru ne kike ta faman kuka haka sai kace wadda aka yi wa auren dole?’

    Ta ɓalla masa harara ta ɗauke kai sannan tace ‘Ni da ka kawo na zaɓi ɗakin da nake so a sama kusa da naka ɗakin shi ne za a kawo ni a ajiye ni a nan, ka sa ina nema na yi musu da masu kawo ni. Ya yi murmushin yaƙe ya sake kamo hannunta wanda ta riga ta fizge yana cewa ‘Haba ke kuwa? Ai na zata da suka zo kafi sun gaya miki.’

    Ta zumɓura baki ‘Ni babu wanda ya gaya min, sai da aka kawo ni kawai na ga an ajiye ni a ƙofar gida kamar wata wadda ba a so zuwanta ba. Nan ya shiga faman ba ta haƙuri da bayani tana faman fizgewa har dai ya samu ta sauko. Ta kalle shi tace ‘Amma gaskiya ni fa ba zan zauna a nan ba, matarka da yaranka da kai kuna sama.

    Kenan fa duk ranar da ba kwana na ba ni kaɗai ce a ƙasa bakin ƙofa. Gaskiya wannan tsarin bai yi min ba, ko dai a ba ni sama ko kuma gaskiya ka nema min wani gidan. Wannan ai duk wanda ma ya zo ya san matsayina. Ya ƙara matsawa ya janyo ta jikinsa ‘Kin ga, kada wannan ya dame ki. Ko da ban kama wani gidan ba za ki iya komawa saman in ya so ko ni sai na dawo ƙasan ku kuma gaba ɗaya ku yi zamanku a saman.’

    ‘Ni dai ba haka nace ba, amma gaskiya ka cika min alƙawari don ba zan yarda wata tana sama ni ina ƙasa ba. Haka ya yi ta lallaɓa ta har ya samu ta amince masa. Ya tattara musu kayansu suka wuce sama ɗakinsa wanda da farko ta so ta ƙi zuwa, sai kuma ta tuna gara ita ma ta hau saman ta ga yanda Khadeejan za ta yi.

    Da yake dama Hammad bai saba barinta baccin safe ba yau ɗin ma tun wajen 6am ya tashe su, ba ta buɗe ɗakin ba sai da ta yi wanka shi ma ta shirya shi. Ta riga ta ji motsinsu tun dare don haka ta san a ɗakin Mustaphan suka kwana. Tana fitowa ta taso Hafsa suka shiga kitchen.

    Ya siyo burodi kamar yanda ya saba duk dare, don haka nan da nan ta soyawa kowa ƙwai ta haɗa kayan shayi tsaf ta ba wa hafsa ta sauko da shi ƙasa. Kafin ƙarfe takwas ta jera komai da suke buƙata ita da yara na breakfast a parlor ɗin ƙasa. Tana shirin hawowa bene Hafsa ta biyo ta da wayarta ta miƙa mata tana ringing. Tana dubawa ta ga Baffa ne.

    Bayan sun gaisa ya ƙara yi mata nasiha sanna yace mata nan da awa ɗaya Nabeela ta shirya Ahmad zai zo ya ɗauke ta.Ba ta ji wata damuwa ba saboda dama ta san halin Baffa, ba tare da ɓata lokaci ba ta taso Nabila ta sanar da ita. Nan da nan ta haɗa kayanta don ko wanka cewa ta yi idan ta je gida ta yi abunta, haka ma breakfast cewa ta yi idan ta je gida ta ci kosai don tabbatar yau Lahadi ƙosai Mommy ta yi.

    Wajen 9am suna zaune a dining table ita da yara in banda Afaf wadda ba ta tashi ba ko kuma ba ta fito daga ɗakinsu ba. Breakfast suke yi suna ta hirarrakinsu Shukra sai labari take ba su suna dariya gaba ɗaya. Da sallama ya sauko daga benen ya ƙarasa gaban table ɗin yana cewa ‘Ina can ina nemanki a ɗakinki ashe kina nan ke da yara kuna ta jin daɗinku.’

    Ta yi murmushi ta kawar da kai. Ita da yaran duka suka gaishe shi, bayan ya amsa ya dube ta yace ‘Idan kun gama cin abincin ki zo ki ba ni nawa breakfast ɗin ni da ƙanwarki. Ta yi murmushin yaƙe tace ‘Da yake mu ma bread da shayi muka sha ba wani abu ba,  amma dama na ga bread ɗin da yawa ka siyo ga shi can mun bar muku guda ɗaya ka ɗauka ka haye muku da shi.

    Ko a nan za ku yi breakfast ɗin? Ya kalle ta da ɗan mamaki ya cije leɓe don ba ya son ya ja zancen a gaban yara yace ‘Um, idan kin gama dai kya hawo da shi.’ ‘Ok.’ Ta amsa cigaba da cin abincinta. Sai da suka gama cin abincinsu tsaf sannan ta ɗauki bread ɗin ta haye sama, tana shiga babu kowa a parlor ɗin don haka ta ƙarasa kan dining table ta ajiye bread ɗin ta shige ɗakinta.

    Kamar tare suka shiga ɗakin don ko zama ba ta yi ba ya shigo ya tura ƙofar, yana daga tsaye a jikin kofar yace ‘Wai ya na ganki a nan ina breakfast ɗin namu ni da ƙanwarki? Ta ƙarasa ta zauna a kan gadon ta jingine ta miƙe ƙafarta tana cewa ‘Oh, ga bread ɗin can na ajiye muku ai ko akwai wani abun ne?’

    Da mamaki yace ‘Ai na zata za ki ɗan dafa wani abu ko don saboda ganin ga baƙuwa kin kwana da ita a gidan. Ba ta san lokacin da dariya ta ƙwace mata ba, haka kawai maganar tashi sai ta ba ta dariya musamman da ta kalle shi kuma yana cewa wai “kin kwana da baƙuwa”

    Ta ɗan gintse tana ƙoƙarin saita fuskarta sanna tace ‘Na kawana da baƙuwa ko ka kwana da ita? Tea and bread muka ci fa kuma ga shi can na ajiye mata ita baƙuwar tawa, ina ga kamar ai dafa ruwan zafi bai kamata ya zama matsala ba ga wanda aka ba wa burodi ko? Ya ɓata rai saboda kwata-kwata bai zata haka ba; a iya saninsa sai sun kwana bakwai da amarya Khadeeja tana yi musu girki sannan sai a raba kwana amma ga shi tana nema ta kawo masa raini.

    ‘Ba fa na son raini Khadeeja, duk wanda ya ƙara aure matarsa ta gidan ita ce take yi wa amarya girki har sai ta kwana bakwai amma zan zo ina miki magana kina min wani zancen banza. Ai ko bazawara na aura kin san ya kamata ki yi mata abinci na kwana uku balle budurwa. Ta kalle shi ta kawar da kai; babu yanda za a yi ta yi wa Naja girki sai dai duk abinda zai yi ya yi; ta tsani Naja ta tsani jin sunanta.

    Wataƙila da a ce ya biyo ta hanyar da ta dace wajen sanar da ita zai ƙara aure da wadda zai aura da haushin da take ji bai kai haka ba, amma gaskiya babu abinda zai sa ta yi wa wata Naja girki. Ya auro matarsa ya gama more kwanan amarci sanna ita kuma bayan bacci da ba ta yi cikin nutsuwa ba kuma ita yake so ta tashi da sassafe ta haɗa musu breakfast na warware gajiya, bata taɓa ganin rainin hankali irin wannan ba.

    Ta ɓata rai sannan tace ‘Ba a biya mana wannan hadisin ba a islamiyya. Mamaki ya kama shi ya buɗe baki amma ya rasa abinda zai gaya mata. Yana kallo ta zame ta gyara kwanciyarta ta juya masa baya. Bai shirya da wannan mahaukacin taurin kan nata ba wanda idan ta fara shi sai duk garin kowa ya ji.

    Ya ɗan tausa muryarsa yace Bana son wasa Khadeeja, don Allah ki tashi ki samarwa yarinyar nan abinci. Next week ai za ku raba girkin kowa ta dinga yin nata, amma for now ki tashi ki ba mu breakfast. Ta sake gyara kwanciya ba tare da tace masa komai ba. Ya kalli kasa yana jijjiga kai don ya san ta gama magana; takaici ya kama shi.

    To yanzu ya za a yi tana amarya ya ba ta bread ruwan zafin ma a ce sai ta dafa. Haka ya fice daga ɗakin yana wasi-wasi. Yana ficewa ta juyo ta harari ƙofar kamar yana wajen ta ja dogon tsaki tace ‘Ɗan rainin hankali!’

    Yana shiga ya tarar da ita ta fito daga wanka tana shiryawa. Tun kafin ya gama shiga ɗakin tace ‘Allah ya sa dai an gama abinci don wallahi yunwa nake ji kamar an min sata a ciki. ‘Akwai dai bread, sai dai idan kin fito ki dafa ruwan zafi da ƙwai haka sai mu karya.’

    Da mamaki ta kalle shi tana cewa ‘Ruwan zafin ma sai na dafa? Yau ne fa kwanana na farko a gidan, haba! Kitchen ɗin ma ban san inda yake ba. Cikin damuwa yace ‘To ko order za a yiwo? ‘Ni ban gane ba, wai ita matar gidan ba ta girki ne? Ya ƙarasa kusa da ita yana ƙoƙarin kama dogon gashinta da take tajewa yana cewa ‘Ki bar wannan maganar, ki zo mu je na nuna miki kitchen ɗinki sai ki samar mana ruwan zafi mu karya.

    Idan kuma akwai inda za ki iya yiwo mana order a kawo nan da awa ɗaya haka to sai na tura kuɗin. Ta jijjiga kai ‘Gaskiya babu, sai dai ko na rana don wallahi kwana bakwai ɗin nan sai na yi su ba tare da na ɗora tukunya ba. Don ni abinda na sani matar gida ko ‘yar gwal ce idan aka yi amarya ita take girki kafin a zauna a raba.

    Haka ya yi ta ba ta haƙuri yana lallaɓa ta, daga ƙarshe ta shirya suka sauko parlor ɗinta ta dafa musu ruwan zafi sanna ya ɗebo ƙwai ta soya musu. Wajen 12pm ya haɗa su a parlor ɗinsa ya yi musu introduction; ita Naja amarya sai muzurai take yi tana wata yanga, ita kuwa khadeeja cike da walwala ta yi mata maraba suka gaisa babu laifi.

    Ya sanar da su idan an kwana bakwai za su raba kwana kowacce kwana biyu. Ba ƙaramin mamakin Khadeeja ta yi ba, ko da yake wannan ba baƙon abu ba ne a wajensa. Ta yi masa rashin kunya mintuna kaɗan kuma ta koma kamar ba ita ba. Shi yasa a lokuta da dama yake kasa fassara ta.

    Ganin walwalarta ya saka ya sa rai cewa za ta yi abincin rana da su, amma gudun kada a kuma ya sa ya bi ta don ya tabbatar. Sai dai ta tabbatar masa da cewa ta riga ta dafa abincin rana tun da safe kuma nasu ne ita da yara, sauce ne kawai a fridge za ta ɗumama ta haɗa musu salad su ci. Ko amsa bai ba ta ba ya fice ya bar ta a ɗakin, ta bi bayansa da harara tana dariya.

    Don haka da rana ta yi sai kawai ya yiwo order ɗin abinci aka kawo musu har gida, haka ya kirawo yaransa gaba ɗaya suka haɗu da Naja suka ci suka ƙoshi. Ita kuma Khadeeja ko damunta abun bai yi ba, ta ci abincinta ta zuba wa Hafsu sannan ta bayar da ragowar. A haka aka ƙarasa wannan amarcin. Kullum Khadeeja za ta dafa abincinta shi kuma zai yiwo order su ci su ƙoshi tare da amarya da yaransa. Babu wanda ya taɓa yiwa Khadeeja tayi ita kuma ba ta taɓa tambayarsa nata kason ba.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin

    Ranar ɗaurin aure tun da sassafe baƙi suka fara zuwa gidan, zuwan nasu ma sai ya fi mata sauƙi tunda ya ba ta dama ta baro Mustapha a sama ta taho wajen baƙin. Ba za ta iya tsayawa a inda yake ba yana ta faman walwala yana kai wa da kawowa yana kwalliya, sai ta ga kamar yana yi ne don ya ba ta haushi.

    Don haka ta ji daɗi sosai da aka ce mata Yaya Jidda ta zo da mutane. Nan ta sauko suka gaisa, ta buɗe musu ɗakin baki tunda dama a ɗaya parlor din suka sauka wanda ba na amarya ba. Sosai Yaya Jiddan ta so su hau sama amma sam Khadeeja ta ƙi ba da fuska, don haka suka haƙura suka baje zugarsu a nan ƙasan.

    Duk wani abu da suke buƙata na cefanensu sun taho da shi da manyan tukwanensu, shi kansa Mustaphan bai san a nan za su yi girkin ba da ya biya an girka musu don ba ya son a ɓata gidan nan. Amma haka yana ji yana gani kafin ma ya sauko an sauke kayan aiki an hau ƙoƙarin hura wuta; a cewar Yaya Jidda sun bayar a yi musu tuwon shinkafa da masa da shinkafa amma masu yi miyarsu ba ta daɗi don haka su za su girka tasu miyar.

    Nan da nan ya ja motarsa ya fice daga gidan suka tafi ɗaurin aure. Tunda Mustapha ya fita ta ɗauki Hammad ta haye sama, suka zauna da Nabila wadda dama ba ta sauko ba ma balle ta ga kalarsu. Hafsa mai aikinta dai ita dole ta zauna ana komai da ita, sannan ga su Afaf waɗanda tuni suka shiga cikin dangi ana ta rawar kai.

    Can kusan la’asar su Yaya Mama suka zo ita da cousins ɗinsu mutum biyu da kuma ƙannen Mommy su biyu. Bayan sun gaisa da Yaya Jidda a parlor ɗin ƙasa kai tsaye suka haye sama. Ba su daɗe da hayewa ba kuma Hajia mahaifiyar Mustaphan ta iso da tata zugar, nan da nan gida ya cika ana ta kai wa da kawowa.

    Bayan an gaggaisa Hajia ta dubi Yaya Jidda tace ‘Ina Khadeejan ne? Ban ganta ba. Inna Ramla ta yi sauri ta amsa kafin Yaya Jidan tace wani abu ‘A a suna saman benen nan fa ita da ‘yanuwanta, benen da ‘yan gidan ma ban ga suna hawansa ba tunda duk ga su nan tare da mu.’

    Ta sake duban Yaya Jidda tace ‘Ban gane tana sama ba. Ta taɓe baki ‘Toh haka muka gani, tana saman ita da ‘yan uwanta. Kafin tace wani abu Khadeejan ta sauko parlor ɗin da sallama; Shukra ce ta hau ta gaya mata zuwan Hajia shi ne ta yi sauri ta sauko saboda kada ta yi laifi.

    Ta ratsa mutanen har gaban Hajia ta tsuguna ta gaishe ta cikin girmamawa sannan ta yi mata Allah ya sanya alkhairi. Ta dubi mutanen duk suka gaggaisa tana kama sunan waɗanda ta sani. Har ta miƙe Hajia tace ‘Ina Mommyn naki, ba ta zo ba? Tace ‘Eh, ba ta zo ba, su Yaya Mama ne kawai suka zo.’

    ‘To madalla.’Ta miƙe ta fice tsakar gidan suka gaggaisa da mutanen da ke zazzaune, ta kalli wajen da su Yaya Jidda suka yi aikinsu yanda ya yi kace-kace ta ɗauke kai. Har ta juya za ta koma ciki Habib ya turo gate ya shiga, daga inda yake ya kirawo sunanta ‘Anti.’ Ta tsaya ta juyo ‘Yaya Habib, ina ka shiga ne tun ɗazu Shukra take nemanka.’

    ‘Ina nan Anti, wajen abokina na je. Yanzu ma wallahi yunwa nake ji, abinci za ki ba mu. Tace ‘To ai Anti Jidda za ka yi wa magana ga abinci nan an dafa. Ya shafa kai yana cewa ‘Anti ai na gaya mata, tuwo ne fa da masa Anti don Allah ni dai ki ba ni abinci. Ta yi dariya don ta san tabbas Habib ba ya cin tuwo da masa da ma abincin gargajiya da yawa, tace ‘Kaje sama wajen Anti Nabeela ta zuba maka.’

    Har ya wuce yace ‘Ni da abokaina Anti? ‘Eh, ka gaya mata ko ku nawa ne. Bai jima da hayewa ba ita ma ta bi bayansa, kafin ta je ya ɗauko flask Nabeela ta zuba masa shinkafa da kaza ga coleslaw da sauce ɗin dankalin bature wanda duk a nan saman suka dafa shi tunda ba su da yawa. Ya ɗauko kwanukan ya sauko ya fice.

    Haka aka yi ta hada-hada ana kai wa da kawowa. Sai dai zuwan Hajia ya sa babu yanda Khadeeja za ta yi dole ta zauna a ƙasa a yi da ita, don haka Yaya Mama da kuma Anti Innani suka sauko suka gaida Hajia suma suka zauna don taya ta zama. Bin mutane kawai take yi da kallo zuciyarta tana ƙuna; ji take a ranta kamar da za a buɗe zuciyarta to da za a tarar tana turiri saboda zafin da take ji.

    Fuskokinsu take kallo ɗaya bayan ɗaya, musamman Hajia wadda ake ta yi mata Allah ya sanya alkhairi ana barka da arziƙi tana amsawa kamar wadda aka yi wa bushara da kujerar Makka. Haka tacigaba da zama a cikinsu tana jin kamar ta ruga da gudu; sai dai lokaci zuwa lokaci ta kan tashi kamar mai duba wani abu ta haye sama, idan ta ja numfashi ta share ƙwalla sai ta dawo.

    Haka suka yi ta yi har gefin magriba; abokan ango suka zo da motaci suka ɗebi yan ɗauko amarya sannan suka tafi ɗauko amarya. Har ta yi sallar magriba zuciyarta tana dukan uku-uku; ta rasa ma abinda yake ɓata mata ran. Tabbas tana kishi to amma ta fi tsoron rashin adalcin da take ji a jikinta Mustapha zai shimfiɗa; amma tana addu’a kuma ba za ta fasa ba don ta san tabbas Allah ne gatanta.

    Wajen 8:30pm aka shigo da amarya, nan da nan gida ya ɗau guda mata na ta shewa. A lokaci guda kuma bugun zuciyar Khadeeja ya ƙara gudu. Tana zaune a kan kafet kusa da Hajia; duk su Yaya Jidda suka miƙe suna tarbar amaya, aka buɗawa waɗanda suka riƙo amarya suka ƙarasa gaban Hajia wadda take hakimce a kan 3-seater. Aka zaunar da amarya a gaban Hajia, mata suka cigaba da zabga guɗa.

    Sai da hayaniya ta lafa sannan aka gaisa da masu kawo amarya, suka miƙa ta hannun Hajia. Hajia tace ‘Masha Allah, Allah ya sa wannan aure har aljannah. Wannan ai ‘yar uwarta za a ba wa ita ba ni ba, ina Khadeejan ne da fa tana nan zaune kusa da ni. Wadda take zaune kusa da Khadeejan tace ‘Gata nan fa.’

    Mutane ne suka zauna a gabanta suka kare ta da aka shigo da amaryar; nan da nan aka buɗa. Hajiya ta miƙa hannu yayin da Khadeejan ta matso tana cewa ‘Zo Khadeeja ga ƙanwarki an kawo miki. Ta sunkuyar da kanta tana duban cinyarta domin tana tsoron kada idanuwanta su ba da ita ta hanyar tunkuɗa hawaye a daidai wannan lokacin.

    Hajia ta kama hannunta sanna ta kamo hannun Naja ta ɗora ta haɗa ta riƙe tana kallon Khadeejan tana cewa ‘Ga amanar ƙanwarki nan, ki riƙe ta amana ku zauna lafiya ku samarwa da mijinku nutsuwa. Allah ya haɗa kayuwanku. Mata suka kaure da amshi ‘Amin. Amin.’

    Wata cikin iyayen amaryar ta karɓe ta cigaba ‘Eh gata nan amana, a yi haƙuri uwargida sarautar mata ku zauna cikin amincin Allah domin kayan Allah na annabi ne. Aka sake kaurewa da guda. So take ta zare hannunta amma Hajia ba ta ba su dama ba; bugun zucuyarta ƙara sauri yake yayin da take jin hanunta kamar ta riƙe wuta.

    ƘoƘari take ta dafe bakinta saboda kada abinda yake zuciyarta ya fito; Amana! Ita za a ba wa amanar matar Mustapha? Ina ruwanta da ita? Ko sun yi mantuwa ne? Shi da ya ga zai iya da amanar ai ya yi gammo ya ɗauko. Don me za su ce ita aka ba wa amana? Tabbas wanna amana ce da ba ta karɓa ba kuma ba za ta taɓa iya karɓa ba.

    Sai da aka gama addu’oi sannan Hajia ta saki hannuwansu, cikin dabara Khadeeja ta faki ido ta goge ƙwallar da ta taru a kwarmin idonta. Ba daɗewa kuma aka fara miƙewa aka kama hannun amarya aka nufi ɗakinta, a haka ne Khadeeja ta samu ta sulale ta haye sama, yayin da su kuma matan suka bi bayan amarya.

    Haka ta koma cikin su Yaya Mama ta cigaba da dagewa, su kuma suna ta ba ta baki da nasiha. Wajen 9pm gayya ta fara watsewa, aka kirawo ta ta yi sallama da Hajia, ba daɗewa kuma su Yaya Mama suma suka yi mata sallama suka bar ta ita da Nabeela. Tana zaune a gefen gadonta tana jiyo yara wajen 11pm suka hawo saman, gaba ɗayansu sai da suka leƙa ɗakinta suka yi mata sai da safe amma banda Afaf, suka wuce ɗakinsu inda suke kwana tare da Hafsa.

    Ba su daɗe ba kuma Nabila ta fito daga ɗakin baƙin da yake saman ta turo ƙofar ɗakin a hankali ta shiga, ta wuce Khadeejan a gefen gadon ta zagaya ta kwantar da Hammad a gafe ta lullube shi. Ta zagayo ta zauna a kusa da Khadeejan, ba ta motsa ba kamar ma ba ta san an zauna a kusa da ita ba. Ta mika hannu ta dafa nata hannun da yake kan cinyarta tana kallon fuskarta tana cewa ‘Yaya Khadeeja ga Hammad fa na kwantar miki da shi.’

    Ta kalle ta suka haɗa ido, ba tare da tace komai ba ta sake kawar da idonta saboda ta tokare hawayen da suke neman ƙwace mata. Nabila ta ɗan matsa hannunta tana cewa ‘Ya Khadeeja. Kafin tace wani abu hawayen ya fara bin idonta, gaba ɗaya ta sake su saboda yanda take faman riƙe su tana jin kamar an ɗora mata dakon wani kaya mai nauyi.

    Gaba ɗaya ta faɗa jikin Nabeela wadda ta rungume ta gaba ɗaya suka sa kuka. Ita Nabeela auren ma gaba ɗaya ya ƙara ba ta tsoro, kuma ta tabbatar ko da wanne lokaci za a iya ɗaura nata auren; tunda da ba don Ahmad ya tafi UK ƙaro karatu ba da tuni ta shekara a ɗaki. Ita kuma Khadeeja gaba ɗaya komai ma ya tsaya mata; tana dai fatan Allah ya sa Mustapha ya zama mai adalci.

    A hankali suka fara lafawa, Khadeeja ta zare jikinta ta kalli Nabeela. Suna haɗa ido suka tuntsire da dariya duk da hawayen da suke fuskokinsu. Suka riƙe hannun juna suna murmushi. Khadeeja ta dube ta tace ‘Sorry. Itama murmushin tayi mata tana cewa ‘Its’s ok, you will be fine in sha allah. Komai zai wuce kamar ba ayi ba.’

    Murmushi ta sake mayar mata sanna tace ‘Ki je ki kwanta, na san yanzu Abbansu zai shigo. Ta sake rungume ta sannan ta yi mata sallama ta fice ta rufe mata ƙofa. Ba tare da ɓata lokaci ba ta miƙe ta shiga banɗaki inda ta yiwo wanka sannan ta fito da alwala, ta shirya ta sa kayan baccinta sannan ta kabbara sallar isha’i.

    A nan ya shigo ya same ta tana zaune a kan dadduma tana gyangyaɗi; kallo ɗaya ta yi masa ta ji zuciyarta ta sake komawa cikin damuwa wadda ta fi ta da. Sai wani faman yage baki yake yana muzurai a lokaci guda; a sanin da ta yi masa ta san murna ce da ɗoki yake yi na amarya kuma yana ƙoƙarin tabbatarwa ita ɗin ba ta kawo masa cikas ba.

    Nan da nan ta danne duk wata damuwa da take ranta ta ƙaƙalo murmushi ta yi masa sannu da zuwa. A tsaye ya amsa ya yi mata bangajiyar biki sannan yace ‘Um ni bari na je, na ga ke ma bacci kike ji. In ya so da safe na shigo da ƙanwar taki ku gaisa. ‘To Allah ya kai mu. Ya juya ya fice ya rufo mata ƙofa.

    Ta ji daɗi sosai da ya sanar da ita ba zai shigo da matarsa a wannan daren ba, domin gaba ɗaya a gajiye take. Ba jikinta ba har ruhinta ma ji take ya gaji, fatanta kawai waɗannan kwanakin su wuce ko kuma ma ta farka ta ga mafarki take yi.

    Ta ga rayuwarsu ta dawo kamar yanda take a farkon aurensu; ko da yake a farkon auren ma babu wani abun kirki da za ta ɗorar; kamar dai gara ma tace rayuwarsu ta dawo yanda ake kafin aure. Sai da bacci ya fara ɗibanta sannan ta tashi ta kwanta a kan ganto ta kashe fitila.

    Edita@rumasau-kallamu

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Tara

     

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Tara

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Tara

    Duk yanda take cikin damuwa da zarar Mustapha yana waje to sai ta shiga walwalarta da yara, yayin da shi kuma duk wasu shirye-shiryensa na tarbar amarya ne. Har ta kai ba ya iya ɓoye murnarsa; shi da yara kullum hirarsu ta Anti Naja ce. Musamman Afaf wadda zuwa yanzu kusan gaisuwa ce kawai take haɗa ta da Khadeeja.

    Lafiya suka tare a sabon gida kuma kamar yanda ta zaɓi ɗakin sama haka ya haƙura ya ba ta ɗakin saman; duk da daga baya ya yi nadamar hakan. Domin da a ce ya san ta riga ta san da maganar aurensa to da tabbas zai gaya mata amarya zai saka a sama. Sai dai a lokacin tunaninsa ba ta san da maganar auren ba kuma ɓoye mata yake son ya cigaba da yi.

    Tsaf ta gyara ɗakinta da parlor, ɗakin su Afaf kuwa tunda ta ga ra’ayoyinta suna cin karo na da Afaf kuma tana nema ta yi mata rashin kunya sai ta haƙura. Sosai ɗakinta ya yi kyau, ta tsara musu komai nasu ita da Hammad, don Baffanta ma da Mommy sai da suka ƙara mata kuɗi ta yi sayayya.

    Sati yana zagayowa kuma aka shiga hidimar bikinsa. Babu yanda ba ta yi da Mustapha ba a kan ita ba ta so a yi mata taro amma ya ƙi amincewa; domin yace Hajia tace dangi ba su san sabon gida ba don haka za su zo su karɓi amarya sannan su ga gida.

    Tun dare ta sanar da shi cewa idan gari ya waye za ta bi ‘yan makaranta ta je gida wajen Mommy, kuma ba tare da wani musu ba ya amsa. Bayan ya kai ‘yan makaranta ya dawo suka zauna tare a parlor ɗin sama suna cin abinci yayin da Hammad yake hannun Rashida. Shiru suke cin abincin babu wanda yake magana, kamar ma dai ba sa cikin walwala.

    Ya ajiye cokalin da ke hannunsa yace ‘Kin ce babu wani abu da kuke buƙata saboda taryar baƙi ko? Ba tare da ta daina cin abincinta ba tace ‘Eh. Ni kam ma ai don dai ka hana ne da sai na yi tafiyata wajen Mommy idan aka kawo ta aka tafi sai na dawo da daddare ko ma da safe.’

    ‘No, don Allah ki bar wannan maganar. Ai ya kamata dai a ce a samu a karɓi baƙin nan cikin mutunci. ‘Um. Suka cigaba da cin abincinsu, jimawa kaɗan yace ‘Hajia ma tace a nan za su zo su yi biki ranar Lahadin, in ya so sai su tsaya su karɓi amarya sannan su tafi.’

    Ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta kawar da kanta, wani malolo ya zo ya tokare mata maƙogoro; su Hajia za su yi biki a nan? Saboda suna murna za a yi mata kishiya ko me?Ta ɗauki kofin shayinta mai zafi ta kurɓa da fatan zafin shayin zai tafiyar mata da abinda ya tokare mata maƙogoro amma hakan bai samu ba.

    Ta kalle shi a jigace tace ‘Ka ga shikenan sai na tafi gidan Mommy ko? Tunda ka ga masu karɓar amarya za su zo.’Ya ɗan zaro ido yana cewa ‘Haba dai! Hakan kuma ai bai yi tsari ba, kina matar gida kuma a zo biki gidan ba kya nan. Ko ba haka ba ma kin san Hajia za ta ga kamar kin raina ta ne shi yasa za ki tafi ki bar su su kaɗai su yi bikin. Please ki yi haƙuri kawai saboda kada abun ya zama wata fitina kuma. Kin ji?’

    Ta ɗaga kai tana cewa ‘Uh. Yauwa, please ki yi haƙuri a gama taron nan ba tare da wata matsala ba. Ta yi gajeran murmushi tace ‘In sha Allah. Ya ture kwanon bayan ya kurɓe ɗan ragowar shayinsa sannan yace ‘Zan saka miki kuɗi a account ɗinki saboda na san za ki iya buƙatar wani abun ko don baƙi.

    Akwai ruwa da lemo wanda zan kawo, abincin kuma dama tunda kika ce ba za ki yi a nan ba na bayar da kuɗin don haka su Hajia za su taho da shi. ‘Ok. ‘Idan kuma da buƙata za ki iya yin wani abincin a nan ko da kaɗan ne. ‘Ok, babu damuwa. Ya miƙe ya shige ɗakin domin ya ƙarasa shiryawa.

    Nan take ita ma ta ture kwanon indomie ɗin ta miƙe ta haye sama. Kuka take son ta yi ko za ta ji sanyi a ranta, amma ba ta so ta ɓata lokaci musamman da yake yana jiranta kuma tare za su fita. Haka ta yi sauri ta shirya suka sauko tare, ta karɓi Hammad a wajen Anti Binta suka fice suka bar Anti Binta da Hafsu wadda ƙanwar Rashida ce aka kawo mata bayan an yi auren Rashidan tun kafin ta haifi Hammad.

    Haka suka zauna a mota babu wanda yake magana da ɗan uwansa; ya riga ya kula da yanda take nema ta tayar masa da fitina a wajen bikin nan amma ba zai bar ta ba. Sosai ya ji daɗi da Hajia tace za su zo nan su yi biki don ba ya so ta bayar da matsala idan an kawo amarya, amma ya san tunda Hajia tana nan babu wata matsala da za ta ba su. Haka ya je ya ajiye ta a gidansu sannan ya wuce.

    Tana shiga gidan ta sami Ahmad a parlor yana shan shayi; nan da nan ya miƙe ya karɓi Hammad daga hannunta. ‘Ina Mommy?’ ta tambaya bayan ta amsa gaisuwar da yake mata. ‘Tana ɗakin Baffa. Ba tare da ta ba shi amsa ba ta bar masa Hammad ta wuce ta nufi ɗakin.

    A zaune ta hango Mommy a kan dadduma ta miƙe ƙafa da waya a hannunta, ta jefar da mayafinta ta ƙarasa gaba daya ta faɗa jikin Mommy ta rushe da kuka. ‘Inna lillahi wa Inna ilaihi raji’un! Khadeeja me ya faru? Ina Hammad ɗin?’ Mommy ta tambaya cikin tashin hankali.Da ƙyar ta buɗe baki tace ‘Yana hannun Ahmad.’

    Ita kanta sai da ta ji ajiyar zuciyar da Mommy ɗin ta yi, sanna ta cigaba ‘To me ya faru kike wannan kukan haka? Ko Mustaphan sakinki ya yi ne? Ta jijjiga kai alamar a a ba tare da ta ɗago ba, ta cigaba da kukanta. Kawai sai Mommy ta haƙura da tambayar ta zuba mata ido, a hankali ta ɗaga hannunta tana shafa kanta; ta dai san da maganar saura kwana uku a ɗaurawa Mustapha aure don haka wataƙila wani abun ya yi mata wanda ya sosa mata rai shi ne ta taho nan tazo tana wannan kukan.

    Sai da ta ɗauki loakci tana wannan kukan sannan ta ɗan numfasa ta ɗago ta kalli Mommy, suna haɗa ido kuma sai ta sake fashewa da kuka. Cikin sheshekar kuka tace ‘Mommy ba zan iya ba, ba zan iya ba Mommy. Ta ɗago fuskarta tana share mata hawayen tace ‘Menene ba za ki iya ba Khadeeja?’

    Ta tsagaita da kukan sai dai hawayenta ya kasa daina fita; ta sa bayan hannunta ta goge hawayen ta kalli Mommy suka haɗa ido na ɗan lokaci. Ta kawar da kanta tace ‘Mommy ban san me Mustapha yake so da ni ba. Bayan ya gama raina min hankali lokacin da yana neman aure yanzu kuma duk da ban ba shi matsala ba amma ba zai bar ni na zauna lafiya ba.

    Ta share mata hawaye tana cewa ‘Me ya yi miki kuma? Mommy nace masa ina so ranar da za a kawo amarya na taho nan idan sun gama kai ta sai na koma ya hana ni, na haƙura nace zan zauna amma ba zan yi taro ba; su kawo amaryarsu kawai su tafi. Da farko har ya yarda amma yau yake gaya min wai babarsa tace za ta zo a nan gidan namu za ta yi biki, kuma yace ba zan tafi na bar su ba.

    Mommy so suke baƙin ciki ya kashe ni? Ɗansu zai yi min kishiya kuma su zo suna celabrating a gaba na? Da mamaki Mommy tace ‘Ikon Allah, ita mahaifiyar tasa ce za ta yi biki saboda zai ƙara aure? Ta sa hannu ta goge ragowar hawayen da yake kan fuskarta sannan tace ‘Eh Mommy, wai za su zo suyi biki. Kin ga kenan na ce ba zan karɓi amarya ba amma za su yi min dole.’

    Mommy ta kama hannunta ta kalle ta sannan tace ‘Ki yi haƙuri kin ji, za ki iya. Kishiya ba ta kashe kowa ba in sha Allahu ke ma ba za ta kashe ki ba. Ki bi su a hankali, dare ɗaya ne a yi ya wuce. Da an kwana biyu ita ma za ta zama kamar ke kuma yanda ya yi miki haka zai yi mata.

    Ta jijjiga kai tana murmushi mai ɗauke da ma’anoni tana cewa ‘Hmm! Mommy ba zai taɓa yi mana adalci ba. Kina ganin yanda tun kafin ta shigo shi da yaransa da ‘yanuwansa suka karkata wajenta. Gaskiya ban saka rai Mustapha zai iya yi min adalci ni da matarsa ba, sai dai kawai nace Allah ya ba ni haƙuri ko kuma ya kawo min mafita mafi alkhairi.’

    ‘Kada ki damu, ai ba shi ya yi kansa ba, in sha Allahu Allah ba zai bari ya cutar da ke ba daga shi har ‘yanuwan nasa gaba ɗaya.’‘Hmmm!’ ta sunkuyar da kai tana kallon yatsunta da take wasa da su. Jimawa kaɗan tace ‘Mommy ba na son a yi min biki a gida, bana son a kawo min amaryarsa a ce za a ba ni amanarta ko a yi mana faɗa tare. Amma kinga duk sun shirya hakan za su yi.’

    Mommy ta sake kamo hannuwanta duka biyun ta kalle ta suka haɗa ido sannan tace ‘Kada ki damu, kamar yanda na gaya miki na ranar ne kawai. Kuma ke ma ‘yan uwanki za su zo, duk da kin ce kada a zo da yawa toh yayarki za su zo da kamar mutum huɗu haka. Nabila kuma tace gobe za ta taho ta taya ki kwana zuwa lokacin da za su gama bikin. Kada ki damu in sha Allahu komai zai wuce.’

    Haka suka zauna Mommy ta yi ta ba ta baki har zuwa yamma. Ta samu zuciyarta ta yi sanyi amma dai ba ta da tabbacin ko za ta iya ɗauka, ta dai haƙura ta ga yanda za ta kaya kamar yanda Mommy tace. Sai da yamma sanna ta shirya ta koma gidan zuciyarta cike da wasi-wasi.

    Washegari ‘yan uwan amarya suka zo suka yi kafi. Ba su ja fitina ba don haka lafiya aka rabu, ta sa Hafsa ta miƙa musu kuloloin abincin da ta bayar aka dafa musu; don ita tunda suka shigo gidan ta haye sama kuma har suka gama ba ta sauko sun haɗu ba. Sun tura Hafsa ta je ta kirawo ta sau ba iyaka amma haka Hafsan take dawowa tace musu saman a rufe yake.

    Haka suka gama kafinsu suna ta rangaɗa guda, ga turare da suka baɗe gidan da shi. Sai da suka kusan gamawa sannan yara suka dawo daga makaranta, nan da nan suka shige cikinsu da yake sun saba da ƙannenta saboda yawan zuwa gidansu da suke yi.

    Dawowarsu daga gidan kafi ya yi daidai da dawowarta daga wajen lalle, a zaune ta same su a farfajiyar gidan ana ta hirarraki. Ta dubi yayarta Ummi tace ‘Yaya har kun dawo daga kafin? Ta taɓe baki tace ‘Hmmm! Mun dawo. Ta ɗan kalle ta da alamar tambaya tace ‘Ya na ga kina yatsina fuska? Komai dai ya tafi dai-dai ko?’

    Salma wadda cousin ɗinta ce tace ‘Um babu laifi. Amma fa mu a ƙasa Mustaphan ya nuna mana ɗaki guda biyu da parlor yace nan ne naki kuma a nan muka yi kafi. Saman gidan nan ma dai ‘yar mulkin uwargidan taki ba ta ko bari mun hau ba ta ja ƙofa ta rufe don ba mu ko isa ta sauko mu gaisa ba ta aiko mana da kulolin abinci kamar wasu mayunwata.’

    Ta zumɓuri baki ‘Ban gane a ƙasa ya ba ku ɗaki ba? Ai ni sama muka yi da shi kuma ya amsa min a kan haka. ‘To ai kuwa dai bai isa ba don Hajia Babba ta haye sama, ba ta ko saukowa idan ba ta ba wa baƙo mahimmanci ba. Nan da nan idonta ya kawo ƙwalla, ta miƙe ta ɗaga waya ta nufi cikin gidan. Ba tare da ɓata lokaci ba Yaya Ummi ta miƙe ta bi bayanta.

    A ɗaki ta same ta har ta lalubo lambar Mustapha za ta buga. Ta dafe wayar tace ‘Ba sai kin kirawo shi ba domin ƙarya kawai zai yi miki ya sake ɓata miki rai, alamu dai sun nuna ita ce mai gidan. Kada ma ki ɗaga hankalinki a kan wannan maganar balle ki hana ku morar satin amarcinku, don in kika hana muku wannan kwanakin to kin yi mata alfarma ne don ita za ta so haka.

    Ko da ma kun yi magana da shi ɗin ki nuna masa babu komai. Ta kalle ta tana zumɓura baki tace ‘Yaya babu komai fa kika ce? Ai ba haka muka yi da shi ba. Tun lokacin da ya sayi gidan fa muka je da shi nace sama nake so kuma ya amince, shi ne zai je kuma ya canja magana.’

    Ta yi murmushi tace ‘Kika san me aka yi masa ya canza? Wannan mata duk da ban ganta ba amma na san a shirye take, idan ba mu dage ba zuwa za ki yi ki zama ‘yar kallo don da alama tana shimfiɗa mulki yanda ranta yake so. ‘To yanzu ya za a yi?’

    Ta yi murmushi ‘Kada ki damu zan yi magana da Inna, dama kin ga tunda aka fara maganar bikin nan take faman nemar miki taimako. Kin ga yanzu sai a mayar da hankali a yi aikin da za ki haɗa kan gidan ki mallake a sauke miki ita daga benen kuma a cire ta daga zuciyarsa gaba ɗaya.’

    ‘Anti dama fa ba ta zuciyarsa gaskiya, don gaskiya haƙuri kawai yake yi da ita ba tun yau ba. Da bakinsa ya gaya min babu ragowar ƙaunarta a zuciyarsa…..’ ‘Ke rabu da shi, namiji ai munafiki ne. Za dai mu yi maganinsa tunda mun ga kamun ludayinta.’ Ta katse ta tana yarfe hannuwa.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Takwas

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Takwas

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Takwas

    Duk yanda take cikin damuwa da yanda take so ta yi wa Mustapha tijara game da yanda ya ɓoye mata maganar aurensa da Naja haka ta haƙura ta danne zuciyarta. Domin ita kanta ta kasa ganin maslahar yi masa maganar; tunda dai ita ce ba ya so ta sani gara ta rabu da shi ta gani ko za a ɗauro auren ne a kai amarya sama jannati saboda kada ta sani.

    Cikin da take ɗauke da shi ma kasa gaya masa ta yi, domin ba ta ga alamar yana farin cikin kasancewarta matarsa ba. Gaba ɗaya ma cikin ya zo mata a wani lokaci ne da take jin cewa da ba ta same shi ba za ta iya haƙura da haihuwa a gidan Mustapha har sai ta fahimci inda auren nasu ya sa gaba.

    Ko da yake dai ta san ana cewa idan namiji zai ƙara aure matarsa da take gidan sai ta yi matuƙar haƙuri; to tabbasa ta ji a jikinta cewa lokacin nata haƙurin ne ya kama yanzun. Da kansa ya kula da yanda take mu’amalarta kwana biyu cikin kasala ga shi ba ta ma son magana, don haka ya tasa ta a gaba ya kai ta asibiti.

    A nan aka tabbatar masa da cewa tana ɗauke da ciki sati shida. Suna zaune a mota yana tuƙo su a hanyarsu ta dawowa ya dube ta yace ‘Kin gani ko, kin sami cikin a kwanciyar hankali ba tare da kin je nemansa a asibiti ba ko? Allah ya sa dai ba mai wahala ba ne? Ta ɗan yi gajeran murmushi tace ‘Amin ya Allah.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, ya dube ta yace ‘Wai ya na ga duk kin yi wani shiru ne? kamar ba abin nema ne ya samu ba? Ta kawar da kai tana murmushin yaƙe tace ‘Bana jin daɗi ne, bacci ma nake ji. Ta kwantar da kanta a jikin kujerar motar ta rufe ido, don haka shi ma ya ƙyale ta ya mayar da hankali a wajen tuƙinsa.

    A haka Khadeeja ta dage ta cigaba da mu’amalarta tana yin duk wata hidima da ta saba. Ko a wanne yanayi ta tashi haka take daurewa ta yi duk wata hidimarta don ba ta shirya drama da Mustapha ba. Ta riga ta san idan dai tana numfashi a gidan nan to duk wata hidima da matar gida take yi ba yafe mata zai yi ba; don haka ta daure ta cigaba da dagewa tana yi.

    Musamman da yake duk wani aiki da ta saba yi a gidan ta riga ta koyawa Rashida kuma ta iya sosai, ga shi yarinyar ba ta da ƙyashi ko ɗaya, don haka abubuwa suka zo mata da sauƙi sosai. Sai dai fargabarta ɗaya iyayen Rashida suna maganar ko da wane lokaci za a iya zuwa a ɗauki Rashida saboda aurenta ya kusa; duk da dai an ce za a kawo mata ƙanwarta to amma ta san akwai aiki.

    Haka ta cigaba da rayuwarta tana goyon cikinta. A hankali ta fahimci lokutan da yake zuwa zance wajen Naja, kuma da yake shi yake kai ta makaranta da ta shiga motar take gane Naja ta fita a motar ko kuma sun fita tare. Daidai lokacin da za su fara jarrabawar ƙarshe a lokacin cikinta ya shiga wata na takwas; ga hidimar gida, ga karatu kuma ga shi tana ƙoƙarin haɗa project ɗinta.

    A dai-dai lokacin ne kuma Mustapha ya gama gyara gidansa wanda yake fatan da zarar sun koma za a yi bikinsa da Naja. Sau biyu yana kai su gidan ita da yara, kuma duka zuwa biyun sai ta tambaye shi ko aure zai yi ne yake yin gidan kamar da zubin mata biyu. Amma duk lokacin da ta tambaya sai yace mata ko da zai yi auren to ba yanzu ba; ta rasa gane dalilin da yasa yake son ɓoye mata aurensa da Naja.

    Don haka ma ta daina tambayarsa gaba ɗaya. Ranar Asabar ce kuma tun dare ya sanar da ita da safe yara su shirya zai fita da su, don haka tun wajen tara na safe bayan da suka ci abinci ta sallame su ta koma ta kwanta. Ya dai ce mata gidan Hajia za su je kuma su ma yaran haka suka gaya mata; amma a ‘yan kwanakin nan yana yawan fita da yaran ranar da babu aiki yace wajen Hajia zai kai su.

    Ta riga ta gane wajen Naja yake kai su, sai dai ba ta ga dalilin da zai sa ta yi masa magana ba tunda ‘yayansa ne sannan kuma gaya musu da yake su ce mata gidan Hajia suka je su yake cutarwa ta hanyar koya musu ƙarya. Gaba ɗayansu suka fice banda Habib, wanda dama ya riga ya saba duk lokacin da za su yi wannan fitar shi baya bin su.

    A gida yake zama tare da Khadeejan da Rashida. Sai wajen ƙarfe biyar na yamma sannan suka dawo, lokacin ta riga ta gama abincin dare ta zuba a flask tana kwance a ɗaki. A ɗakinta yaran suka same ta tana kwance tana hutawa, suka sanar da ita sun dawo. Shukra kuwa sai ta wuce ta haye gadon ta kwanta kusa da ita tana cewa ‘Bacci kike yi Anti?’

    Tace ‘A a, hutawa nake yi. Ta ɗan matsa jikinta tana gyara kwanciya, Khadeejan ta ɗan gyara kwanciyarta tana kawar da Shukran daga cikinta. Ta yi dariya tana cewa ‘Na matsa ko Anti, kada na lotsewa ƙanina hanci. Ta yi dariya saboda ita ce ta saba gaya mata hakan a duk lokacin da take son kwanciya a jikinta tunda cikin ya fara girma; domin Shukra yarinya ce mai son jikin tsiya kuma ta samu Khadeejan ba ta ture ta.

    Tace ‘Yauwa, ashe dai kin gane. Kada a dinga ce miki yayar mai lotsattsen hanci. Suka yi dariya gaba ɗaya; Shukra ta ci gaba da wasa da hannun Khadeejan guda ɗaya yayin da Khadeejan take riƙe da waya a ɗaya hannun tana chatting. Jimawa kaɗan cike da damuwa tace ‘Anti.’

    ‘Umm.’ Ta amsa ba tare da ta bar abinda take yi ba. Tace ‘Gaskiya ni ba zan koma wajen Anti Naja ba, a wajenki zan zauna ko? Ta ajiye wayar tace ‘To wa yace za ki koma wajen Anti Naja kuma? Ai muna nan tare, ko ba gamu ba a gidanmu. Cike da damuwa tace ‘Ai ita ma tace auro ta Abbanmu zai yi ta dawo gidanmu. Amma sai mun koma sabon gida.

    Shi ne yau da muka je wajenta take cewa Yaya Afaf idan ta tare duk wajenta za mu koma. Gaskiya ni dai ba zan koma ba ko? Ta ɗan yi shiru tunani yana nema ya birkita ƙwaƙwalwarta; duk da bai gaya mata ba ta san yana kai yaransa wajen Naja, amma maganganun da Najan take gayawa yaran ba sa kama da maganganun da ya dace a gaya musu a daidai wannan lokacin.

    Sai dai ta san babu yanda za ta yi tunda shi ya ba ta dama. ‘Anti.’ Muryar Shukra ta katse ta tana kiran sunanta. Bayan ta amsa Shukran ta cigaba cikin damuwa ‘Tace saura wata biyu ta tare, gaskiya idan ta zo ki gaya mata ni a wajenki zan zauna ba a wajenta ba. Kuma ma na ji tana gayawa Yaya Afaf idan an koma sabon gida sama take so ke ce a ƙasa, na gayawa Yaya Afaf mu ne a sama mu da ke tace min wai da Allah can.

    Gaskiya ki gaya musu mu ne a sama. ‘Hmm! Zan faɗa musu Shukra, ai mu ne a sama kada ki damu. Ta cigaba da surututa tana ba wa Khadeeja labarin irin abubuwan da suke yi idan suka je gidan Naja. Duk da Khadeeja ba ta yi mamakin jin cewa Naja ta san da sabon gida ba amma ta yi mamaki da ta ji cewa har Naja ta zaɓi part ɗin da take so yayin da ita kuma har yanzu bai ma gaya mata ita da wata matar za su zauna a gidan ba.

    Ta kasa gane dabarar da Mustapha yake jin ya yi da ya ƙi gaya mata zai yi aure; amma dai za ta cigaba da binsa ta ga ƙarshen wulaƙancinsa. Ko da yake a ‘yan kwanakin nan ma yanda yake ƙara tubure mata ta tabbatar da tana biye masa da kullum sai sun yi faɗa.

    To sai dai ba ta da wannan lokacin tunda ga project ɗinta wanda take so ta gama kafin su fara jarrabawa wanda tana fatan Allah ya sa kada haihuwa ta zo mata har sai tayi final paper. Haka ta ajiye wannan ma a ranta tana jiran ranar da za ta titsiye Mustapha tunda haka ya zaɓa.

    Tun kafin su fara jarabawa ya sanar da ita idan ta haihu aka yi suna aka gama zuwa barka za su koma sabon gida, saboda ba ya so a je a ɓata masa gida. Ita ma tsarin ya yi mata don haka ba tare da wata matsala ba ta amsa. Kuma kamar yanda ya ba ta umarni ta fara haɗa kayanta da za ta tafi da su duk da cewa ya gaya mata ya saka sabbin furniture a gidan.

    Ranar da za ta yi jarrabawar ƙarshe ya kama yara suna hutun makaranta, kuma sai 2pm za su shiga paper. Don haka yace idan babu matsala yana so ta shirya da wuri su tsaya a sabon gida ta ga furniture ɗin da ya siyo in ya so sai ya ajiye ta a makaranta shi da yara su wuce wajen Hajia. Ta riga ta gama karatunta don haka tun wajen sha ɗaya ta shirya suka shiga mota gaba dayansu suka kama hanya.

    Saman gidan yana ɗauke da parlor guda biyu ƙarami da babba da kuma ɗakuna guda uku sannan da kitchen, ɗaki daya da parlor suna tare da juna wanda dama ya sanar da ita nan ne nashi part ɗin. Ƙasan kuma parlor ne guda daya me haɗe da ɗakuna biyu da kicin kamar na saman, sai wani babban parlor ɗin kuma da ɗakuna guda biyu waɗanda suke kusa da juna.

    Parlor ɗin ƙasan duk a nan aka sauke furniture ɗin; duk da kusan kowanne yana cikin kwalinsa. Suna shiga suka ɗan yayyage kwalin ita da yara suka gani. Ya dube ta yana nuna ɗakunan ƙasan yana cewa ‘Sai ki zaɓi a wane dakin za a saka miki gadon, in ya so ɗaya dakin kuma sai a ɗauko gadonki na tsohon gida a saka.’

    Ta kama hanyar sama tana cewa ‘Eh hakan ma ya yi; ɗakin wanda yake jikin nakan sai saka min sabon gadon a nan in ya so na kusa da shi sai a gyarawa ‘yan mata na ko? Shi kuma Yaya Habib sai a ba shi ɗaya daga cikin wannan na ƙasan. Shukra ce kawai ta biyo ta shi yana tsaye a inda yake. Ta dan juyo tana cewa ‘To ka zo mu je mana ka gani.’Ya yi ‘yar dariya yace ‘Na zata za ki fi son waɗannan ɗakunan na ƙasa ai, kin ga sun fi girma.

    Kuma ai ina ga zai fi min privacy a ce ɗakin ki yana nan ƙasa a madadin yana kusa da nawa idan kin yi baƙi ina jiyo ku. Ta yi dariya tace ‘Haba dai, kuma don ni ce duk faɗin gidan nan sai na rasa wajen sauke baƙi sai bedroom? Ai dama sama ba wajen saukan baƙi ba ne tunda nan ƙasan ma da parlor.

    Amma dai can ne ɗakina, in ya so idan ma ba ka so yaran su hau sama za a iya barinsu a ƙasa. Shukra tace ‘Gaskiya Abba mu ne a sama mu da Anti, in ya so ita Anti N…’ Kafin ta ƙarasa Afaf ta katse ta cikin ɗaga murya tana cewa ‘To ba ki ji me Abban yace ba, ƙasan ya fi girma ne da space. Khadeeja tace ‘To mu dai ba ma son ƙasa, muna sama abin mu.’

    Ta ja hannun Shukra suka haye saman. Habib wanda yake tsaye a kusa da Abban nasu ya dube shi yace ‘Haba Abba, dama ai sama na Anti Khadija ne.’ Kallon da Abban ya yi masa ya sa ya kawar da idonsa da sauri ya waske yana cewa ‘Bari na je na taya su zaɓen ɗakin. Haka ya haƙura shi ma ya bi su saman inda khadeeja ta nuna masa ɗakin da yake jikin nasa tace shi take so, ɗayan kuma wanda yake gefe ɗaya sai a bar wa yara.

    Ba shi da wata hujja da zai ba ta a kan hana ta ɗaukan ɗakin sama, kuma har yanzu ba ya jin ya shirya gaya mata cewa zai ƙara aure, ya fi so sai ta haihu tukunna saboda kada ma ya ji tausayinta idan tace za ta tayar masa da hankali. Haka suka gama zagayensu a cikin gidan sannan suka shiga mota suka nufi BUK don su kai ta.

    Har suka isa makarantar ba ta daina mamakin Mustapha ba; ta kasa gane sai yaushe zai daina yi mata wannan ƙaryar. Kuma ta kasa gane dalilin da yasa yake fifita buƙatar Naja da son zuciyarta a kan tata, amma dai haka za ta cigaba da biye masa ta ga gudun ruwansa.

    Kwanansu biyu da gama jarrabawa Khadeeja ta haifi yaronta, don haka ko kwana ba ta yi a asibiti ba aka wuce da ita gidanta. Sai daga baya aka kawo mata Anti Binta wadda kanwa ce a wajen Mommy. Tun a asibiti Mustapha ya sanar da su ya sakawa yaro suna Muhammad; sunan Baffan Khadeeja. Daga baya Nabila ta yi masa laƙabi da Hammad.

    Nan da nan aka shiga hada-hadar shirya bikin suna; kuma a lokacin Mustapha ya sanar da ita idan an yi suna da sati biyu za su koma sabon gida. Ranar kwana biyu da haihuwa Mustapha ya sameta a dakinta da daddare, tana zaune a gefen gado da baby a cinyarta tana kallonsa tana murmushi. Ya ajiye shopping bag ɗin da ke hannunsa sannan ya zauna a kusa da ita ya shafa kan baby yace ‘Shikenan kuma kin mayar min da yaro abun kallo kamar wata TV ko?’

    Ta yi ‘yar dariya tace ‘To ina laifi, ina yaba halittar Allah ne. Ya matsar da ledar kusa da ita yana cewa ‘Ga wannan ‘yan office ɗinmu ne suka bayar a kawowa Baby. Ta karɓa ta ɗan buɗa ta leƙa sannan ta mayar ta ajiye tana cewa ‘Mun gode, Allah ya saka da alkhairi. Ai dole Muhammad ya kawo tukuici tunda an yi masa takwara.’

    Ya yi dariya. ‘Wannan ma ba na Muhammad ba ne, sauran ma’aikatana ne dai. Shi yace sai gobe za su zo da matarsa. ‘Allah sarki mun gode, Allah ya bar zumunci. Suka ɗan taɓa hira sannan ya fita. Yana fita ta ɗauki ledar ta zazzage kayan; rigunan Baby ne masu kyau da tsada guda biyu, sai set ɗin kayan sanyi guda ɗaya, set ɗin huluna da kuma set ɗin kayan wasa.

    Ta taɓe baki ta mayar da kayan cikin ledar, jikinta ya ba ta wannan kayan Naja ce ta bayar don haka ko burge ta ba su yi ba. Rawar kan da yake yi da ya shigo da kayan kaɗai ta isa ta sa ta san cewa daga wajen Naja kayan suka fito. Ta tsani yarinyar gaba ɗaya ta tsani ta tuna ta, ba ta ko son jin sunanta. Haka ta ajiye kayan da niyyar da zarar an gaya mata haihuwa ita ma za ta yi barka da su.

    Lafiya ƙalau aka gama taron suna; musamman da yake Khadeeja ta kawar da kanta daga abubuwa da yawa. Domin hatta abincin sunan Yaya Jidda cewa ta yi ya ba su za su yiwo su zo da shi, shi kuma ya hau kai ya zauna. Tunda ta ga haka ta gayawa Mommy kada su yiwo gayya da yawa, sannan Baffa ya ba su kuɗi suka shirya nasu abincin wanda suka taho da shi.

    Ko da Yaya Jidda ta gansu da kulolin abincinsu sai ta soke duk wani wulaƙanci da ta shirya yi musu, haka aka gama taro kowa ya watse lafiya. Bayan kwana biyu tana kwance a ɗakinta tana hutawa da daddare wayar Mustapha ta shigo; ta riga ta san yana cikin gidan don haka ta san kiranta yake yi. Haka yake yi tunda Anti Binta ta zo; baya shiga ɗakinta sai dai ya yi mata waya ita ta same shi a ɗakinsa.

    Ba tare da ɓata lokaci ba ta miƙe ta nufi ɗakin. Ta ƙarasa ta zauna a gefen guda kusa da shi tace ‘Gani. To sannunki da zuwa.’ Ya faɗa yana bin idonta da kallo yana ƙoƙarin karanto yanayinta. Ta yi murmushi tace ‘Godiya nake, a ba ni abinda aka kawo min. Suka haɗa ido na dan lokaci, ya ɗauke nashi idon ya ɗan cije leɓe sannan yace ‘Ya shirin tashi, saura kwana biyar fa.’

    ‘Ai ni na gama shiri, maƙota ma duk na gama sallama da su. Sai mun tare zan yi musu kwatance su zo ganin gida. To da kyau. Suka yi shiru na ɗan lokaci; ita tana sauraronsa don ta kula da magana a bakinsa yayin da shi kuma yake ta sake tauna maganar bakin nasa yana tunanin ta inda zai fara. Ya kalle ta suka haɗa ido ya yi gajeran murmushi, ita ma ta mayar masa da murmushin. Cikin sanyin murya yace ‘Um ki yi haƙuri ki saurare ni kuma ki fahimci maganar da zan gaya miki.’

    Ta kalle shi na ɗan lokaci da mamaki a fuskarta tace ‘In sha Allah.’Ya sake gyaran murya sannan yace ‘Um Khadeeja aure zan yi, don maganar da nake miki ma saura sati biyu a ɗaura auren. Idan mun tare a sabon gida da sati ɗaya ita ma za ta tare. Suka haɗa ido, ta yi murmushi sosai sannan ta zare hannunta daga nashi tana cewa ‘Allah sarki, abun ya zo kenan. Toh Allah ya sanya alkhairi.’

    Buɗe baki ya yi yana kallonta saboda tsabar mamakin yanda ta nuna halin ko in kula da maganar tasa kamar dai wadda yake cewa gobe Litinin a ranar Lahadi. Ta miƙe za ta fice ya riƙe hannunta yana cewa ‘Um wani abun kike yi ne kike saurin tashi. Ta koma ta zauna tana cewa ‘A a, na zata ka gama maganar da za ka faɗa ɗin.’

    Ya ɗan sunkuyar da kai saboda gaba ɗaya ya kasa haɗa ido da ita, wannan halin ko in kula ɗin da ta nuna yasa duk ya firgice; gaba ɗaya ta goge masa haddar kalaman da ya tsaro don ya ba ta haƙuri. Cikin sanyin murya yace ‘Um baki ma tambayi wacece wadda zan aura ba. Ta ɗan yi dariya tace ‘Oh, Naja ce mana. Ko ka fasa auren nata ne?’

    A jigace ya amsa ‘Ita ce. Ta daga gira cikin halin ko in kula tana shirin miƙewa tace ‘Allah ya sanya alkhairi. ‘Um, wai dama kin san zan yi auren ne ko na ga kamar kin sani tun tuni. Ta yi ‘yar dariya ta koma ta zauna tace ‘Na sani mana, ko bai kamata na sani ba? Ya jiijiga kai ‘No, ina dai mamaki ne. Suka yi shiru na ɗan lokaci.

    ‘To don Allah wa ya gaya miki?’ Muryarsa ta katse mata tunani yana tambaya. Ta yi ‘yar dariya tace ‘Oh, ka san fa na ɗauka kai ka gaya min; ashe ba kai ba ne. Ina jin dai a cikin waɗanda ka gayawa ne kace kada su gaya min aka sami wani ya gaya min. Ya sunkuyar da kai domin ya kasa haɗa ido da ita; wato duk wannan tsawon lokacin ashe kallonshi kawai take yi duk abinda yake ɓoyewa ta sani.

    Ba ƙaramin mamaki ya yi ba. Kafin yace wani abu suka jiyo kukan Hammad daga cikin gidan, don haka ta dube shi tace ‘Ka ji yarona can yana kuka, bari na je na gani. Ta fice ba tare da ta saurari amsar shi ba. Tana fitowa daga ɗakin Mustaphan ta tarar da Anti Binta a parlor tana ta jijjiga Hammad, tun kafin ta ƙarasa wajensu tace ‘Yunwa yake ji, zo ki ba shi ya sha.’

    Ta karbe shi ta shige ɗakinta Anti Binta tana biye da ita. Haka ta daure ta haɗiye malolon da ya tokare mata maƙogoro har ta gama ba shi nono suna hira da Anti Binta. Sai da ya sha ya ƙoshi sannan ta miƙawa Anti Binta shi tana cewa ‘Ga shi Anti Binta, banɗaki nake son shiga. Ta karɓe shi ta miƙe tana cewa ‘To muna can ɗakin yara muna hira da mutuniyata.’

    Ta fice ta ja mata ƙofa sannan ta miƙe ta shige banɗakin don ta san idan dai tana cikin ɗakin nan wani sai ya zo nemanta, idan kuma ta rufe da mukulli za a yi ta faman tambaya. Tana shiga banɗakin ta turo ƙofar ta jingina a jikin kofar, take hawayen da take riƙewa suka ƙwace kamar an kunna famfo. Ta haɗa tafukan hannayenta ta rufe fuskarta tana jijjiga kai, saboda tsabar takurar da zuciyarta ta yi har wani ɗaci take ji a bakinta.

    Yaushe Mustapha ya raina ta haka? Wannan ma ya fi ƙarfin raini ya koma wulaƙanci. To me yasa ya yi mata haka? Daman can ba ya sonta ne ko kuwa son da yake mata ne ya ƙare? Ba ta taɓa tunanin za ta auri miji ta zauna ita kaɗai ba amma dai ta ɗauka idan ka auri mutum zai cigaba da girmama ka yana ganin mutuncinka har ƙarshen tarayyarku.

    A halin yanzu ta rasa wanne za ta yi; murna ta haihu ita ma ta sami yaro ko kuwa jaje za ta yi wa kanta tunda ko babu komai wannan yaron da ta haifa zai ƙarawa alaƙarta da Mustapha tsawon rai. Ba ta san tsawon lokacin da za ta iya ɗauka tana jure wulaƙanci irin wannan da Mustapha yake mata ba, amma dai ta san tabbas ba za ta iya jurewa har abada ba.

    Ga shi shi ba dukanta yake ko zagi ba, wani irin wulaƙanci ne yake mata yana nuna cewa komai normal ne, kuma a mafi yawancin lokuta ma idan ta yi magana sai a dinga nuna mata haka maza suke. Domin kowa ce mata kawai yake idan dai namiji ne ba ta ga komai ba. Ta bar wa Allah al’amarinta kuma za ta jira su tare ta ga yanda yanayin zaman zai kama; amma tabbas idan aka cigaba a haka ba ta jin za ta iya zama da Mustapha.

    Zuwa yanzu kuma duk wasu alamu sun nuna mata cewa ba zai taɓa yi mata adalci ba ita da Naja, kamar ma dai yanzu ne ya yi aure na soyayya wanda yake sa ran zai more rayuwarsa a ciki; tunda ta gama yi musu wahala ta raini yaransa lokacin da suke tsananin buƙatar uwa. Yanzu sun girma sun zama mutane don haka sai ya aure wadda yake so ta zo su more rayuwarsu ita kuma a mayar da ita saniyar ware.

    A hankali ta zame a jikin ƙofar ta zauna ta sake fashewa da kuka. Sai da ta yi mai isarta sannan ta ba wa kanta haƙuri ta wanko fuskarta ta fito daga banɗakin.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Bakwai

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Bakwai

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Bakwai

    A zaune yake a parlor ɗin Alhaji, yayin da Hajia take zaune a kusa da Alhajin. Zuwa ya yi musu da labarin auren yana son ya ƙara don har ma yana gaya musu sati me zuwa yake so a je a kai kuɗin aure.

    Cikin walwala Alhaji yace ‘Ai kwanaki da muka yi magana da kai da na ji ka shiru na zata ka fasa. Ya yi ‘yar dariya ‘Ba fasawa na yi ba Alhaji, na dai ɗan tsaya ne na ƙara shiryawa, na gaya maka zan sayi gida ai.

    To dama tsayawa na yi a samo gidan, kuma yanzu an samo, cinikin ne ma bai faɗa ba saboda ina so su ɗan yi min ragi. Amma in sha Allahu ina sa ran za mu daidaita shi yasa nake son yanzu a kai kuɗin auren.’

    Murmushin Alhaji ya ƙara faɗi, ya dubi Hajia sannan ya dubi Mustapha yace ‘To ma sha Allahu. Wannan ai sai dai mu sa albarka kawai. Ka je ka sami babanka Safiyanu ka yi masa bayanin ita yarinyar idan ya gama bincikensa ya tabbatar gidan mutunci ne ai sai su je su kai kuɗin. Allah ya sa albarka, Allah ya ƙara buɗi.’

    Suka haɗa baki shi da Hajia suka ce ‘Amin. Hajia tace ‘To ka gayawa Khadeejan ko? Me tace? Ya shafa kai yana murmushi ‘Ban gaya mata ba tukunna, amma in sha Allahu zan gaya mata. So nake sai an gama magana tukunna idan ya zama saura kamar sati uku ko huɗu sai na gaya mata ko don saboda gudun fitina.

    Kafin nan na siya gidan mun koma. Alhaji yace ‘Eh, to hakan ma ya yi. Sai dai kuma Allah ya sa kada mata su riga ka gaya mata. Hajia tace ‘A a babu wanda zai gaya mata, ka yi abinka a hankali idan ka shirya ka gaya mata. Nan suka ƙare hirarrakinsu daga baya ya yi musu sallama ya kama hanya.

    Abu ɗaya ne yake ci wa Khadeeja tuwo a ƙwarya rashin haihuwa, domin har yanzu tun bayan cikin da ta samu ya ɓare ba ta sake ko da ɓatan wata ba. Ga shi yanzu har sun shiga final year amma babu wani labari.

    Duk lokacin da ta yi yunƙurin zuwa asibiti Mustapha sai ya nuna halin ko in kula ko kuma yace lafiyarta ƙalau za ta je ta fara neman fitina, don haka ta tattara ta haƙura. Sai dai ta yankewa kanta hukuncin cewa da zarar ta gama final exam za ta je asibiti a duba ta a tabbatar mata da abinda ya hana ta samun ciki; ko babu komai ita ma tana so ta ga ta haifi dan cikinta.

    Tunda idan ta gama karatu ba ta san lokacin da za ta sami aiki ba. Haka ta haƙura ta mayar da hankali a kan karatunta tana addu’a. Zamanta da yaran Mustapha kaɗai ya isa ya sa ta ji tana son haihuwa; domin yanzu yaran sun girma tunda Shukra auta ma tana primary 1 yayin da Afaf take SS.

    Kusan gaba ɗaya yaran yanzu ba daɗinsu take ji ba, domin abinda suka ga dama suke yi. Habib ne ma kawai wanda ya damu da rayuwarta kuma yake neman shawara a wajenta kamar uwa, amma Afaf da Nasreen ma ba ta san wanene yake ba su shawara ba.

    Ta dai san duk wani abu na wulaƙanci da suke yi mata da sa hannun Yaya Jidda. Ga wani mahimmanci da Musttapha yake ba wa Afaf ta yanda ko da sun gama magana da Khadeejan Afaf tana iya saka shi ya canza. Duk abinda ya shafi yaran kuma ko da Khadeeja ce ta gaya masa to a ƙarshe da Afaf ɗin zai yi shawara.

    Hatta kitchen ɗin gidan ya zama kamar na mata biyu; domin a lokuta da damam sai ta gama girka abinda kowa zai ci ta fita daga kitchen ɗin sai Afaf ta shiga ita ma ta dafa abinda ta ga dama tace ba ta cin wanda Khadeejan ta dafa. Ta yi magana har ta gaji, tunda Mustaphan ya fara nuna tana so ta takurawa Afaf ne saboda ba ita ta haife ta ba.

    Tana kwance a ɗakinta tana jiyo hayaniyar yaran a parlor; Afaf ta shigo ta same ta ta miƙa mata waya tana cewa ‘Anti Abba ne yake waya yace yana kiran wayarki ba ta shiga. Ta tashi zaune ta karɓa ta ɗan kalli wayar ta ga whatsapp call ne, sannan ta kara a kunnenta.

    Yace ‘Ina kika shiga ne nake kiran wayarki ana ta cewa not reachable? Ta yi ‘yar dariya tace ‘Sai dai ko idan network ne don ga wayar ma a hannuna. ‘Kin san Ali Ahmed ko? Abokina da muke zuwa zance tare. ‘Eh na san shi mana.’

    ‘Yauwa da Allah shi ne ya shigo gari nan da kamar awa ɗaya za mu zo gidan, me za ki iya dafa masa sai mu yi dinner tare. Yana dai son tuwo ‘Ok, to sai a yi tuwon ai. Amma dai ka bari na duba freezer tukunna na ga yawan kazarmu yadda za a samu a yi muku peppersoup ma ko?’

    ‘Eh, ƙwarai kuwa da zobo ma please. Duba idan babu kazar sai na bayar a kawo miki yanzu, riƙe wayar ki duba ki ba ni amsa. Ta miƙe ta dubi Afaf da take tsaye tana jiran wayarta ta nufi kitchen.

    Suna fitowa parlor Afaf ɗin ta ga Nasreen ta canza channel ta mayar Disney Junior, da sauri ta yi kanta tana cewa ‘Wane mara kunyan ne ya canza min channel ban gama kallo ba. Anti idan kin gama wayar ina nan.’

    Ta shige kitchen ta bar su. Tana shiga ta ƙarasa ta buɗe freezer ta duba sannan ta ce masa ‘Za ta isa ma, amma dai idan za ka dawo sai ka siyo wata don gaba ɗaya zan kwashe na dafa muku yanzun. Suka yi sallama ta katse wayar.

    Sunan da ta gani a jerin chats ɗin kan wayar shi ya ja hankalinta ta fasa fitowa daga kitchen ɗin tana ƙarewa sunan kallo; Anti Naja aka rubuta da alamar zuciya ta emoji. Daga haka da take kallon hoton da yake kan sunan kuma tabbas Naja ce sakatariyar Abbansu.

    Ba tare da ta yi wani tunani ba ta danna kan sunan ya buɗe mata chats ɗin, har za ta yi sama sai kuma wani saƙo da yake cikin jerin saƙunan da ke ƙasa ya ja hankalinta. Afaf ce ta turawa Naja saƙon kamar haka “Congrats Anti, Abba ya ce min an kawo kuɗin auren ko?”

    “Eh my girl, sun kawo har da sadaki ma. Saura kawai ya gama gyaran sabon gidan mu shikenan. “I can’t wait to have you here with us Anti.”“Soon my girl. Amma dai ta daina ba ki matsala ko? “Ta daina, tunda ta ga babu riba. Yanzu ba sosai ma take kula ni ba dama ni haka nake so. Habib ne kawai sarkin rawar kai ya manne mata.”

    “Kada ki damu kwanan nan zan zo na gyara mata zama. Motsin da Khadeejan ta jiyo ne ya sa ta yi sauri ta rufe saƙonnin ta dire wayar a kan teburin da yake kusa da freezer ɗin ta kama murfin freezer ɗin ta ɗaga kamar a lokacin ta rufe. ‘Anti ina wayar?’ Afaf ta faɗa bayan da ta ƙarasa shigowa kitchen ɗin.

    ‘Kin ganta nan a kan tebur, ɗauki. Ta ƙarasa ta ɗauki wayarta ta fice ta koma parlor ɗin. Cikin sanyin jiki Khadeeja ta tsaya a ta jigina da freezer ɗin ta kafa tagumi. Kusan wata takwas da suka wuce Mustapha ya kalli tsabar idon Baffa da Mommy yace musu ba auren Naja zai yi ba, amma ga shi daga waɗannan chats ɗin da ta karanta yanzu har an kai kuɗin aure da sadaki.

    Wato ma Afaf ta san komai ita ce kawai ba ta san mijinta zai ƙara aure ba kenan; kuma kamar dai ba shi ma da niyyar gaya mata. To me ta yi wa Mustapha ne? Me yake tunanin za ta yi a a kan ƙara aurensa da yake ɓoye mata?

    Ita dama da ya kai ta gidan da ya siya yanda ta ga gidan ta san sai ya ƙara aure, kawai dai ba ta zata Naja zai auro ba don kwata-kwata ba ta sake ganin wata alama da take nuna yana tare da Naja ba tun bayan da suka je wajen Baffa.

    Wato dama da take zargin Yaya Jidda ce take hure mata kunnen yara ashe Naja ce, tunda ga shi nan ta gani har tana gayawa Afaf cewa za ta shigo ta gyara mata zama. Ta jijjiga kai, ta goge gumin da ya fara tsattsafowa daga goshinta sannan ta tuna ce mata fa ya yi nan da awa ɗaya za su zo.

    Jikinta a sanyaye ta koma cikin gidan ta kirawo Rashida sannan suka fito suka kama aiki. Haka ta haɗiye duk wani ɓacin rai ta yi ta haba-haba da abokinsa, sai bayan sallar isha’i sannan ya yi musu sallama ya tafi.

    Ta san cewa ya kula da yanayinta yanda ya sauya, amma bai yi mata magana ba. Duk da dai ko da ya yi mata maganar ma za ta gaya masa gajiya ce kawai. Haka dai suka kwana shi yana baccinsa ita kuma Khadeeja duk lokacin da ta yi juyi sai ta kalle shi tana tambayar kanta wai me ta yi masa ne yake mata abubuwa kamar wata wadda aka aura ba don soyayya ba?

    Haka ta haƙura ta yi ta danne zuciyarta har gari ya waye. Sai ƙarfe biyu na rana take da lecture amma haka ta shirya da wuri lokacin da Mustapha ya shirya zai tafi office tace ya wuce da ita ya kai ta gidan Mommy, in ya so daga can sai ta wuce makarantar ta kuma dawo gida. Haka kuwa aka yi.

    Tunda ta shiga gidan Mommy ta karanta damuwa a fuskarta, ta dai kyale ta har Baffa da Nabila suka gama shirinsu suka fice. A nan parlor ɗin inda suka bar su Mommy ta zuba mata ido na ɗan lokaci, har ta ji a jikinta Mommy ɗin kallonta take. Tana juyowa kuwa suka haɗa ido; ta ɗan yi dariya tace ‘Mommyy.’

    Ita ma ta yi dariyar tace ‘Ya aka yi ne? Kamar dai kina da damuwa. Ko kuma ba kya jin daɗi ne? Ta jijjiga kai tace ‘Mommy Mustapha aure zai yi.’Ta ɗan zaro ido ‘Aure? Ikon Allah.’ Sai kuma ta saki fuskarta ta cigaba ‘Ko da yake wannan ba abin mamaki ba ne ai don haka kada ma ki saka wa kanki damuwa.’

    Ta sunkuyar da kai cikin damuwa tace ‘Mommy ni ma ba damuwa na yi ba, kawai dai yayanyin abun ne. Ban gane ba. Nan ta sanar da ita wadda zai aura sannan ta sanar da ita a inda ta ga labarin auren da kuma irin saƙonnin da Afaf take tura wa Najan da kuma yanda take fama da Afaf ɗin a ‘yan kwanakin nan.

    Duk da Mommy ba ta yi mamaki ba amma dai ta ji babu daɗi, musamman yanda Afaf ta zama ‘yar rahoton Naja. Tace ‘Ikon Allah, to shi me yasa yake ɓoye miki auren? Tace ‘Wallahi ban sani ba, ko da wasa bai taɓa gaya min ba kuma danginsa ma babu wanda ya gaya min.

    Amma kin ga yaran har sun sani, tunda ga shi har ana gaya musu za a zo a gyara min zama. Lallai mutum sai a bar shi. Dama na gaya miki Mommy tunda na ga gidan da ya saya nace miki gidan nan ba na mace ɗaya ba ne, kin ga maganata ta tabbata.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan Mommy tace ‘To da ce mata aka yi ba ki zauna daidai ba da take cewa za ta gyara miki zama ko me? Amma kafin ta gyara miki zama ke ce za ki bi dare ki gyara zama ta hanyar addu’a, idan gari ya waye kuma ki ɗora da sadaka.’

    Ta sunkuyar da kai tana ƙoƙarin ɓoye ƙwallar da ta gangaro a kwarmin idonta; wannan kalmar ta za a gyara mata zama ta tsaya mata a rai. Domin dai kalma ce da za ta iya ɗaukan kowacce ma’ana. Amma kamar yanda Mommy ta faɗa hakan za ta yi tunda ta san ba ta da gatan da ya wuce Allah.

    Haka suka cigaba da hira Mommy tana ta ba ta baki kuma tana yi mata alƙawarin daga nan ma za ta dinga yi mata addu’a kuma da sadaka, ta tabbatar mata ba za ta yi nasara a kanta ba.

    Da wuri Mommy ta sauke abinci saboda Khadija ta ci kafin ta tafi makaranta, tana daga kitchen ɗin ta ƙwalawa Khadeejan kira. Tana shiga kitchen ɗin ta fara gatsina fuska tana cewa ‘Mommy wannan wane irin kifi ne kika dafa me azabar ƙarni? Allah ya sa dai ba da shi kika yi abincin ba.’

    Mommy ta ƙare mata kallo na ɗan lokaci sannan tace ‘Wane kifi da aka dafa tun jiya da daddare aka cinye, ni shinkafa da wake ma na dafa. Nana da nan fara’arta ta ƙaru, ta ɗauki plate ta matsa tana miƙawa Mommy tana cewa ‘Yauwa Mommy zuba min na fice don wallahi kitchen ɗin nan ƙarni yake.’

    Ta karɓi plate ɗin tana cewa ‘Ciki ne da ke ko? Ta kalli Mommy da baki a buɗe, suka ɗan zuba wa juna ido sannan ta rufe bakin tace ‘Anya kuwa Mommy, tunda dai ni ban ji wani sauyi na a zo a gani ba.’Ta zuba mata abincin ta miƙa mata tana cewa ‘To ki dai bincika tukunna kafin ki yi saurin cewa a a, don tunda kika shigo nake kula da ke gaba ɗaya ma na dauka abinda ya kawo ki kenan.’

    ‘To ban sani ba gaskiya Mommy, amma zan duba yau ɗin nan kuwa. Bayan ta gama cin abincin ta yi sallah sanna ta fice ta kama hanyar makaranta. Sai da ta tsaya a chemist ta sayi abun pregnacy test sannan ta wuce. Ta riga ta san su Rahma suna jiranta a hostel don haka kai tsaye can ta wuce, tana ajiye jakarta a ɗakin ta fice ta faɗa toilet.

    Tana tsoma abin nan a fitsarinta ya nuna raɗau positive; wato tana ɗauke da ciki. Ta yi murmushi tana ji kamar ta daka tsalle saboda murna, nan da nan idonta suka ciko da ƙwalla saboda jin dadi. A take kuma jikinta ya yi sanyi da ta tuna cewa Mustapha ne ya yi mata ciki kuma shi ne yake shirin auro matar da ta ke ikirarin za ta shigo ta gyara mata zama.

    Ta sunkuyar da kai ta saki takardar a ƙasa sannan ta fito daga banɗakin cike da damuwa. Yanayin da ta shiga ɗakin ya tabbatar musu da akwai matsala, don haka tun kafin ta Zauna Farida ta miƙe ta tare ta tana cewa ‘Ya na ganki haka, lafiya dai ko?’

    Ta zauna a kan gado Rahma kamar wadda aka jefa, ta kalli Farida suka haɗa ido sannan ta saki murmushe wanda yake haɗe da takaici tace ‘I am pregnant Farida. Nan da nan su Rahma da Amina da ke zaune suka dako tsalle suka faɗa jikinta sun ihu.

    Sai da suka fahimci ita ba ta taya su ihun kamar yanda suka saba sannan suka tsaya suna kallonta. ‘Girl, wannan ai abun murna ne na ga kamar ke ba ki ji daɗi ba.’ Amina ta faɗa tana riƙe da hannun Khadeejan.

    Ta sunkuyar da kai ta zare hannunta ta goge ƙwallar da ta faɗo daga idanunta. Ta ba su labarin auren Mustapha da kuma abinda ta gani da ma yanda yake ɓoye mata. Tace ‘Ban ma san wanne zan yi ba; murna ko baƙin ciki? Ni da za a zo a gyarawa zama ina zan miƙe ƙafa na fara haihuwa; haihuwar da ni ban ma tabbatar zai yi murna da ita ba.

    A yanzu ma gaba daya kai na ya kulle. Mommy dai tace kada na kuskura na yi masa maganar ƙara aurensa, na bar shi har sai ya zo da kansa ya gaya min, a lokacin sai a yi duk wadda za a yi. Amma wallahi ban sani ba ko zan iya jurewa. Gaba ɗaya ma yanzu ban san matsayina a wajen Mustapha ba, kuma ga ciki.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci. Amina ce ta katse shirun nasu tana cewa ‘Gaskiya mutumin nan dan wulaƙanci ne, haba!’ Rahma tace ‘Amma gaskiya ina bayan Mommy, ki bar shi kawai kada ki yi masa magana in ya so idan ya zo zai gaya miki da kansa sai ki yi masa wankin bargo tunda dai babu abinda zai sa ya fasa wannan auren da yayi niyya.’

    Tace ‘Haka ne. Nan suka ɗauki lokaci suna ba ta baki, sannan daga baya Farida da Rahma suka fice suka tafi lecture ɗin suka bar su a ɗakin ita da Amina wadda ta tsaya ta taya ta zama don tace ba za ta iya zuwa lecture ɗin ba.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Shida

    Edita@rumasau-kallamu

  • Baɗi Ba Rai Kashi Na Ɗaya

    Baɗi Ba Rai Kashi Na Ɗaya

    A short story by
    Sakina Yazid (Innar su Amal)

    Kamar duk lokacin da irin wannan abun ya faru yau ɗin ma haka ta shiga gidan cike da tashin hankali; duk da dai ta daina kukan ta share hawayenta. Hawayen iya na fuskarta ne kawai ta share amma tabbas ta san ba za ta iya daina kukan zuciya ba, ko za ta daina to ba ta san lokacin da za ta daina ɗin ba.

    Parlor ɗin shiru, da alama Umma da kuma su Maimuna suna ɗaki; wataƙila suna sallar la’asar domin lokacin sallar ne. Kai tsaye ta wuce ɗakin Umman ta tura ƙofar ta shiga da sallama.

    A kan dadduma ta hango Umman tana zaune tana azkar. Kallon da Umman ta yi mata ya sa duk wani karsashi da ta taho da shi ya zube kafin ta ƙarasa gabanta. Ta riga ta san amsar da Umman za ta ba ta guda ɗaya ce; wato wadda ta saba bata. Zuwa yanzu ma gani take yi gaba ɗaya kamar Umman nata ta ƙosa kuma ta gundura da jin matsalolinta.

    To amma idan ba wajen Umman ba ina za ta? Da wa za ta yi magana ta ji sanyi a ranta? Duk da dai yin maganar bai taɓa samar mata mafita ba. An riga an hane ta da yin ƙawaye tun lokacin da aka yi mata aure, don haka ta fita harkar ƙawayen har su ma suka rabu da ita. Mutum biyu ne a rayuwarta iyayenta da kuma mijinta Misbahu; su suka fi mata kowa muhimmanci a rayuwarta kuma su ne suke neman tura cikin halaka.

    Cikin sanyin jiki ta ƙarasa gaban Umman ta sauke goyon Adnan ta zaunar da shi; nan da nan kuwa ya rarrafa yana dariya ya haye jikin Umman wadda ta ɗauke shi tana dariya.‘Umma ina wuni.’ Ta faɗa cikin sanyin murya. Ta harareta sannan ta amsa ‘Lafiya ƙalau. Yanzu kuma me aka yi na ganki fuska duk a koɗe?’

    Ta sunkuyar da kai ta yunƙura ta haɗiye malolon da ya tokare mata ƙirji, ta buɗe baki da ƙyar tace ‘Umma duka na ya yi, kuma ya gaya min maganganu na wulaƙanci fiye da yanda ya saba gaya min. Ga neman mata Umma, a gabana zai yi waya da budurwa ya saka a loudspeaker wai na ko yi soyayya.’

    Cikin damuwa Umman ta sauke Adnan wanda ya kama rarrafe a tsakar ɗakin, ta dube ta cikin natsuwa kamar me nazari sannan tace ‘To in dai maganganu ne menene ba ki ji ba a bakin Misbahu? Ai tuntuni nace ki fita harkarsa ki mayar da hankali wajen wannan yaron da Allah ya ba ki. Kuma yau ya aka yi kika biye masa har ya kai miki duka?’

    Ta share hawayen da ya gangaro a kan fuskarta, ta yi ajiyar zuciya a karo na babu iyaka sannan tace ‘Hayaniyarsa ya gama yi ya shiga ɗaki ya kwanta shi ne na shiga maƙota dubiya. Shi ne ina dawowa ya hau zagina, kuma na ce ya yi haƙuri shi ne ya mammare ni yace wai zuwa na yi maƙota na kai gulmarsa.’

    Nan da nan ta sake fusata tace ‘To ke me ya kai ki maƙota kin riga kin san halin mutumin nan? Na riga na gaya miki ki fita harkarsa ki bar shi da mugun halinsa. Idan ba ya son shiga maƙota to ai sai ki bari. Umma bai taɓa hana ni shiga ba wallahi. Kuma na gaya miki idan ya tashi wulaƙancinsa bana ma sanin me na yi masa, tunda ko na saba yin abu wataran sai kawai ya hau zagina a kai.’

    ‘To ai sai ki kiyaye, tunda kin ga dai mahaifinki da kansa ya yi masa magana kuma yace ya daina. Ki je ki cigaba da lallaɓa shi ki mayar da hankali kan ɗanki. Bawa ba ya wuce ƙaddararsa, wata ƙila ke taki ƙaddarar kenan.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci; Farida tana ta faman share hawaye yayin da Ummanta take faman hidima da Adnan. Jimawa kaɗan tace ‘Umma na gaji da auren mutumin nan wallahi, son shi ya fice min daga rai. Bana son zaman gidansa; idan ina cikin gidan ji nake kamar an saka zuciyata a keji kuma an kunna wuta a cikin kejin. Wallahi Umma wulaƙancin da yake min ya ishe ni.’

    Ta kawar da kai tare da haɗe fuska sannan tace ‘Haƙuri za ki je ki yi, tunda dai mutumin nan babu abinda ya rage ki da shi; ci, sha sutura da sauransu. Ko muma nan kullum cikin hidima yake da mu. Kina kallo ga ƙannenki can a gidajensu amma ke kullum kina tafe kawo ƙara. Ni kaina da kika gani idan da ban yi haƙuri da ubanku ba da yanzu wani zancen ake ba wannan ba.

    Kuma ma idan dai maza ne na yanzu duk haka suke kowanne da tashi matsalar musamman neman matan; idan kin fito ba ki san gidan wanda za ki koma ba. Idan ma kin sami mijin kenan.’

    Haka dai Umma ta ƙare mata faɗa da nasiha sannan ta tursasata ta koma gidan; domin a faɗarta ba ta ma so a ɗaga maganar balle mahaifinta ya ji don ita ma sai ya yi mata faɗa. Don haka cikin matsananciyar damuwa ta goya Adnan suka kama hanya.

    Ƙwaƙwalwarta ta cushe gaba ɗaya; wace irin rayuwa ce wannan? Auren soyayya suka yi da Misbahu amma yanzu ba shi da aiki sai cuzguna mata; duk da dai ba wai kullum ba ne yake mata hakan. Sai suna zamansu lafiya kamar kowanne ma’aurata laifi kaɗan sai ya gaya mata maganganu masu zafi watarana ma ya mammare ta.

    Ga shi ba ta sanin wanne laifi ne za ta yi ya haifar da hakan don haka kullum a ɗari-ɗari take a gidan. In dai haka maza suke to idan ta samu ta rabu da Misbahu ma babu wani auren da za ta sake balle a ce ba a san wa za ta aura ba; tana ji a jikinta zawarci zai fi mata sauƙi da wannan rayuwar da take yi yanzu.

    Tana hango gidan bugun zuciyarta ya ƙara sauri, wata sabuwar fargaba ta shige ta. To amma idan ba nan ba ina za ta? Gidansu ne kawai ragowar gatanta kuma can ta je aka koro ta. Haka ta ƙarasa ta shiga gidan tana fatan idan dai har mutuwa ce za ta raba ta da Misbahu to tabbas ta shirya mutuwa don tana da yaƙinin Allah zai ji tausayin ta.

    Yana kashingiɗe a parlor ɗin a kan 3-seater ta tura ƙofar ta shiga; ƙasa-ƙasa ta yi sallama ta shige ba tare da ta saurari amsa ba. Tana jin ƙwayar idonsa yana bin ta da kallo na wulaƙanci irin wanda ya saba. Sai da ta kai tsakiyar parlor ɗin tana daf da shiga ɗakinta ya daka mata tsawa.

    ‘Daga ina kike? Akuya sarkin yawo.’ Ta ɗan diririce tana shirin komawa da gudu sannan ta dage ta lalubo nutsuwarta cikin in-ina tace ‘Gidanmu na je. Ya sake ƙare mata harara yana jan dogon tsaki ‘Mtsewww!’ Ta bi bango ta shige ɗakin ta turo ƙofar tana fatan kada ya zo yace zai doke ta.

    Haka ta lallaɓa ta yi sallar magriba sannan ta fito ta ɗora abincin dare tun kafin ya nema ya ɗaga mata hankali. Ya riga ya san babu abinda za ayi duk da kai ƙarar tasa da ta yi, don haka da ya fita ma bai dawo gidan ba sai da sha biyun dare ta gota; lokacin ta daɗe da yin bacci.

    A hankali suka ɗan shirya kamar yanda suka saba, sai dai ita duk a firgice take. Zama take na ɗari-ɗari a gidan saboda ba ta san me za ta yi ta tsokano shi ba. A bayan layinsu aka yi haihuwa, kuma da yake ya san maigidan tun jiya ya ba ta izinin zuwa suna da ake yi yau Asabar.

    Wajen 12pm maƙociyarta ta yi mata sallama a kan ta zo su je sunan don ita daga can za ta wuce cikin gari. Nan suka haɗu su uku maƙota suka wuce. Tun da suka shiga layin gabanta yake faɗuwa; akwai gidaje na ƴan jami’a a layin inda wasu ƴan mata ne suke zaman kansu wasu kuma samari.

    Akwai wata yarinya Shahida wadda Misbahu yake nema; ba ta taɓa ganin yarinyar ba amma an tabbatar mata a nan layin gidan yarinyar yake. Don matan layinsu ma sun sha gaya mata sun gan shi da yarinyar ya sauke ta nesa da unguwar. Sun yi magana sau babu iyaka har ma ta gaji; tunda yanzu ma a yanda ake ya gaya mata idan ta ƙara yi masa maganar wata daga cikin ƴan matansa sai ya kora ta gida ya kawo matan gidan ya ga idan akwai wanda ya isa ya hana shi.

    Haka dai ta dafe zuciyarta suka ƙarasa cikin gidan sunan; nan da nan kuma da suka haɗu da matan unguwa ta manta da komai aka ci gaba da hira cikin walwala. Sun kai kimanin awa ɗaya, ‘ƴan matan suka shigo gidan; da yake ba wani sosai aka cika tsakar gidan ba sai da suka tsallake suka zo kusa da Farida sannan suka zauna.

    Suka gaggaisa da mutane da alama wasu daga cikin matan da suke zaune a wajen sun san su. Ita ma Farida ta waiga ta gaisa da su. Suka tambayi maijego aka ce musu yanzu ta shiga canza kaya don haka suka zauna nan aka cigaba da hira.

    Jimawa kaɗan suka jiyo muryar maijego daga parlor tana magana da wasu matan. Ɗaya daga cikin ‘ƴan matan nan wadda take zaune kusa da Farida ta buɗe baki ta ƙwala mata kira bayan ta amsa tace ‘Da Allah ki zo ki nuna min matar masoyina na yi mata kallon ala tsine uwar mai ƙarya; ko da yake dai ya gaya min kalarta.’

    Ta fito daga parlor ɗin tana dariya ta nuna yarinyar tana cewa ‘Shahida ba fa na son wulaƙanci, duka nan babu sa’anki ƴar rainin hankali.’ Aka sheƙe da dariya gaba ɗaya wajen. Farida tana jin an ambaci Shahida ta sha jinin jikinta; ta juya ta kalle ta suka haɗa ido yayin da yarinyar ta tintsire da dariya. Maƙociyarta wadda suka zo tare ta taɓa ta tace ‘Tashi mu tafi Maman Adnan.’

    Suka miƙe a tare, ita ma Shahida ta miƙe tana dariya da kallon raini tana cewa ‘Ashe ma kusa dake na zauna, sannu fa. Mai jego tace ‘Ke Shahida ba fa na son raini… A a ku fa uwayen gidan nan haka kuke wallahi, ba ku iya kula da miji ba sai ikon tsiya. To komai baƙin cikinku sai mun shigo.’ Ta faɗa da shaƙiyanci tana dariya.

    Farida ta ja tsaki, ta raɓa ta gefenta ta wuce, maƙociyarta Anti Amina tana biye da ita. Ta ƙyalƙyale da dariya tace ‘A a fa kada ki bangaje ni idan ba haka ba wallahi na sa a baki red card a daren nan ki kwana gidan father ɗinki. Farida ta shammaci mutanen da suke wajen ta juya ta yi taku ɗaya ta ƙarasa gaban Shahida ta sauke mata mari a kumatunta.

    Nan take wajen ya yi tsit yayinda Shahida ta dafe kumatunta tana fitar da hawaye. Farida ta nuna ta da yatsa tana cewa ‘Idan ke ‘ƴar halak ce ki ba shi umarni kada ya bar ni na kwana a gidan yau.’ Ta sauke yatsan sannan ta cigaba ‘Ko da yake ba zan yi mamaki ba idan ke ɗin ba ‘ƴar halaka ba ce tunda ga shi nan kin mayar da kanki kamar public toilet.

    Kowa ya tashi juyen ƙazantarsa sai ya zo ya haye kanki. Ki bashi umarni yau kada ya bari na kwana a duniyar ba ma a gidansa ba. Ta juya ta fice ba tare da ta saurari kowa ba Anti Amina tana biye da ita. Nan ragowar matan da ke tsakar gidan suka haɗu da maijego suka fara ba wa Shahida haƙuri.

    Ta share hawayenta ta zauna, ta zari wayarta tana cewa ‘Wallahi sai ta gane kurenta, sai na saka ya ci ubanta tunda ta mare ni. Kuma wallahi ita da zaman lafiya da Misbahu har abada, sai na yi ajalin wannan auren nata.’

    Suka cigaba da ba ta haƙuri maijego tana cewa ‘Ki dai yi haƙuri ki bar maganar nan tunda kin ga kece ba ki da gaskiya, Please ki fita harkar ta.’ Ta goge fuskarta ta dubi matan tace ‘Ku yi shiru zan yi waya da Allah.’ Nan da nan suka yi shiru saboda son jin gulma.

    Ta lalubi lambar Misbahu ta danna masa kira; bugu ɗaya kuwa ya amsa yana cewa ‘Ƴan matana ya aka yi ne, har kin…’ Nan take ta rushe da kuka; abinda ya saka shi ya ruɗe ya shiga jero mata tambayoyi ‘Babe me ya faru? Kina ina ne? Ko accident kika yi ne?’
    Ta sassauta da kukan tace ‘Matarka ce ta mareni kuma ta zazzage ni a cikin mutane.’

    Cikin ƙosawa yace ‘Ban gane ba, Farida? A ina kuka haɗu? Ko gidan kika je? Ta sheƙe majina irin na me kuka tace ‘A gidan suna muka haɗu nan kusa da gidanmu, shi ne ƙawarta ta nuna mata ni suka haɗu suka yi min wulaƙanci a cikin mutane kuma ta mammare ni.

    Dole sai fitowa muka yi ni da Ikram saboda kunya. Wai ni take kira public toilet har da cewa ni ba ƴar halaka ba ce. ‘Ya isa, ki daina kukan mana. Kina ina ne na zo yanzu? Sai na ji yanda aka yi, kema kin san ba zan ƙyale ta ba.’ ‘Ni kada ka zo inda nake, ai duk kai ka janyo tunda kai ne kake zuwa kana ba ta labari na har ta sami damar yi min wulaƙanci.’

    Ta tsinke wayar ba tare da ta saurari amsar shi ba, ta mayar da wayar cikin jakarta ta kama hannun ƙawarta suka fice.

    Cike da damuwa Farida ta koma gida; ba ta nadamar marin da ta yi wa Shahida, amma dai tana fargabar haɗuwarta da Misbahu. Don ta san tabbas idan bai mammare ta ba to sai ya yi mata zagi na ƙasƙanci; idan ba ta yi wasa ba ma to sai ya ba ta red card kamar yanda budurwar tasa ta faɗa.

    Haka Anti Amina ta ɗauki lokaci tana ba ta haƙuri sannan ta bar ta ita ma ta wuce nata gidan. Ba ta jima da shiga gidan ba Maryam yarinyar da take mata aiki ta shigo; tunda dama tace mata ta zo bayan 2pm. Ta ji daɗin shigowar tata saboda ta san ko da Misbahu zai shigo yanzun to zai ƙyale ta a ƙalla zuwa lokacin da Maryam ɗin za ta tafi; kafin nan ta samu ta shirya yanda za ta ƙwaci kanta.

    A fusace ya shigo gidan wajen 2:30pm; tunda sai da ya tsaya a wajen Shahida ya lallaɓa ta yayin da ita kuma ta ƙara yi masa fanfo sannan ya huto gidan. A lokacin da ya shiga gidan Maryam tana kitchen tana aikinta yayin da ita kuma Farida take ɗaki tana kwantar da Adnan wanda ya yi barci.

    Ba ta rufe ƙofar ɗakin sosai ba don haka bai ma kula da mutum a kitchen ba ya shige ɗakin. Tana ƙoƙarin yi masa sannu da zuwa ya kama hannunta ya janyo ta daga ɗakin tana turjewa tana tambaya ‘Abban Adnan lafiya kake ja na haka? Ka bari na gyara masa kwanciya mana.’

    Bai saurare ta ba kuma bai fasa jan nata ba, har sai da suka fito ƙofar ɗakin sannan ta samu ta fincike hannunta. Cikin ƙarfin hali tace ‘Wai meye haka Misbahu, ya za ka kama ja na kamar wata yarinya.’

    Ya ɗan ja baya yana mata kallo na takaici da mamaki saboda bai taɓa zaton za ta iya yi masa magana haka ba. Ita kanta ba ta san ina ta samu ƙwarin gwiwar ba amma tabbas tana jin yau ba za ta saurara masa ba.

    Cikin huci yace ‘Ni za ki yi wa rashin kunya saboda ba ki da mutunci ko? Saboda kin haɗu da ƴan iskan ƙawayenki sun hure miki kunne ko?’ Ta sun kunyar da kai tana ja da baya saboda yanda yake nufo ta, sai dai kafin ta yi wani yunƙuri ya kwaɗa mata mari. Tana ƙoƙarin dafe kumatun ya sake kwaɗa mata a ɗayan sannan yace ‘Wace shegiyar ce tace ki mari Shahida? Kuma sannan ki zage ta?’

    Nan da nan hawaye ya wanke mata fuska, cikin ƙunan rai tace ‘Ita ba ta gaya maka abinda ta yi min ba kafin na mare tan, ko kuwa nice wadda ba ni da gata da za ka zo kana mari na saboda karuwa? Ya yi wata ‘ƴar dariyar mugunta sannan yace ‘An mare ki ɗin, ko akwai abinda za ki iya yi a kai? Shashasha kawai.’

    Cikin kuka tace ‘Babu abinda zan iya yi amma zan cigaba da kai ƙara wajen Allah. Duk wanda ya zalunce ni Allah ya isa ba zan taɓa yafewa ba.’

    A fusace ya fara ƙoƙarin kwance belt ɗinsa yana cewa ‘Lallai yau za ki gane kurenki, ni kike yi wa Allah ya isa saboda ba ki da mutunci? Jikinki zai gaya miki. Kafin ta yi wani yunƙuri ya zabga mata belt ɗin wanda ya bi ta wuyanta ya sauka a saman bayanta. Ta gantsare ta saki wata ƴar ƙara tana ƙoƙarin sosa wajen dukan; wanda tuni ya riga ya yi ja zur ya tashi.

    Ya sake ɗaga belt ɗin ya zabga mata. Ta ja baya kamar za ta faɗi bango ya tare ta; ƙoƙari take ta shiga ɗakinta ta turo ƙofa amma sai da ta wuce ƙofar sannan bangon ya tare ta. A nan ta sulale ta zube saboda zafin dukan da kuma gigicewa. Ya gyara belt ɗin ya riƙe ƙasan yanda ƙarfen belt ɗin zai sauka a jikinta; a daidai lokacin kuma Adnan wanda ya riga ya tashi daga bacci har ya sauko daga kan gadon ya rarrafo ya nufi jikin mamansa yana kuka.

    A lokacin Misbahu ya riga ya ɗaga belt ɗin zai zuba mata; tana ƙoƙarin ɗauke Adnan belt ɗin ya sauka a ƙeyarsa. Nan take jini ya wanke mata jiki yayin da Adnan ɗin ya yi wata gajeriyar ƙara ya faɗa ƙirjinta kamar wanda aka jefa.

    Ta jijjiga shi cikin matsananciyar firgita tana kiran sunansa; a dai-dai lokacin Misbahu ya saki belt ɗin ya nufo kanta yana ƙoƙarin karɓar Adnan ɗin yana cewa ‘Me kika yi masa? Inna lillahi wa Inna ilaihi raji’un!’

    Maryam wadda take tsaye a bakin ƙofar kitchen tana kallon su tana share hawaye ita ma ta zuba ihu ‘Inna lillahi wa Inna ilaihi raji’un!’ Kafin su yi wani yunƙuri ta zura da gudu ta yi waje ta ƙofar kitchen tana faman ihu tana kiran mutane.

    Nan da nan jikin Misbahu ya hau rawa suka miƙe tare da Farida wadda ita ma jikinta yake rawa tana ta wani gunji ta ƙanƙame Adnan saboda yanda hawayenta ya bushe ta kasa kuka. Kai tsaye waje Farida ta nufo rungume da Adnan yayin da shi kuma Misbahu ya juya kan center table inda ya ajiye mukullin motarsa yana cewa ‘Ki tsaya na fito mu kai shi asibiti.’

    Kusan a lokaci guda suka ƙaraso tsakar gidan inda suka ci karo da Maryam mutum uku sune biye da ita; maƙocinsu Dr. Abdul da wani mutum tare da shi sannan kuma da maigadin gidan. Dr. ya sha gaban Farida wadda ko ɗankwali babu a kanta yana cewa ‘Subhanallah! Me ya sami Adnan ɗin?’

    Cikin rawar baki tana waigawa tana kallon Misbahu tace ‘Ya fasa masa kai da belt, ya kashe min yaro. Maryam wadda take share hawaye ta tsomi baki tana cewa ‘Dukanta yake yi da belt ɗinsa wallahi yana ɗagawa ya kwaɗawa yaron, dukansa ya yi da belt ɗin. Shi ne baban nasa.’

    Dr ya ja su suka koma kan baranda sannan ya ba ta umarni ta kwantar da Adnan. Nan ta shimfiɗe shi ta janyo gefen rigar ta ta fara goge fuska ba tare da ta damu da jinin da yake jikinta ba. Ya dudduba shi sannan ya juya ya dubi mutumin da suka zo tare da shi yace ‘Inna lillahi wa Inna ilaihi raji’un! Wannan sai dai a yi haƙuri Allah ya karɓi kayansa.’

    Nan take Farida ta juya ta cakume Misbahu tana cewa ‘Ka kashe min yaro, sai ka kashe ni ni ma. Da ƙyar ya samu ya haɗa hannuwanta ya riƙe tana faman kuka. A hankali kuma kamar wadda aka zarewa laka ta sulale ta zauna kamar me zaman tahiya ta haɗa hannuwanta guda biyu ta rike tana fitar da numfashi a hankali.

    Maryam ta ƙaraso ta zauna a kusa da ita suka yi jugum suna bin mutane da kallo. Mutumin da suka shigo da Dr ya dube shi yace ‘Ai sai an kirawo police tunda ya zama case ɗin accident kenan. Ba tare da ɓata lokaci ba ya fidda wayarsa ya kirawo ‘ƴan sanda, a lokacin ne kuma Misbahu ya sami dama ya koma gefe ya kirawo mahaifiyarsa.

    Jimawa kaɗan ita ma Maryam ta miƙe ta koma cikin gidan ta ɗaukowa Farida hijab ta zo ta saka mata sannan ta kama hannunta ta dangwala a wayarta ta buɗe ta lalubo lambar Ummanta ta kirawo ta. Abinda kawai ta iya gayawa Umman Farida shi ne Adnan ya rasu, ta katse wayar ta riƙe a hannunta suka cigaba da kallon ikon Allah.

    Kusan a lokaci ɗaya ƴan sandan suka iso da mutanen gidan su Adnan, kafin wani lokaci kuma mutanen gidansu Farida suka iso. Mahaifin Adnan shi ya ja ƴan sandan ya sallame su, kusan ma babu wanda ya kula da lokacin da suka sulale suka fice.

    Tunda Umman Farida ta iso take fama da Farida a kan ta shiga cikin gidan su zauna amma ta ƙi, kuma ta ƙi yi wa kowa magana. Don haka suna nan tsaye aka yi wa Adnan sutura aka yi masa sallah yayin da Umma da Maman Adnan suke tsaye sun saka Farida a tsakiya suna lallashinta.

    Ana fita da gawar mata suka fara shigowa gidan domin ta’aziyya, sai dai har zuwa lokacin Farida ta ƙi shiga cikin gidan ga shi magriba ta fara kawo kai. Da yake maƙabartar babu nisa nan da nan aka kai shi aka dawo. Babu wanda ya kula da lokacin da Farida ta sulale ta fice daga gidan ta kama bin hanya.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu