Tag: Sakina Yazid

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ƙarshe

    Mijin Marigayiya Babi Na Ƙarshe

    EPILOGUE

    Bayan shekaru 3. An yi auren Afaf an kai ta gidanta, yaron da ta aura ƙanin abokin Abbanta ne, da kanta ta je ta kai wa Khadeeja katin bikin nata wanda ta karɓa cike da girmamawa. Ta yi mata magiya a kan ta je amma duk da haka ba ta je ba, domin ba ta son abinda zai haɗa ta da Naja da dangin Mustapha a cikin taro.

    Kuma duk yanda Mustapha ya so ya saka ta a cikin shawarar bikin Afaf ɗin da inda zai sayi furniture haka ta zame da wayo da dabara har ya gaji ya rabu da ita. Yana nan dai yana bibiya da kuma addu’ar ta yarda su mayar da aurensu. Yana zaune a ɗakinsa a kan dadduma yana hutawa bayan sallar la’asar kwana biyu bayan auren Afaf haka kawai ya ɗauki waya ya kirawo Khadeeja.

    Ya gyara zama ya jingina da bangon da ƙofar ɗakin take jiki ta yanda idan aka buɗo kofar aka shigo zai zama yana bayan ƙofar kenan. Bayan ta amsa suka gaisa suka shiga hirarrakinsu, tana tambayarsa labarin biki. A haka har yace ‘Kin ga da kin yarda ai da tare da namu za a ɗaura.’

    Ta yi dariya tace ‘Kai kuwa ka ƙi ka bar maganar nan. ‘Ba zan bari ba Khadija, har sai kin amince. Ko na tsufa ma sai na dawo da ke ko da takaba ne kya yi min sai mu haɗu a aljannah. Dariya kawai ta yi don ba ta da amsar da za ta ba shi. Suka yi shiru na ɗan lokaci sannan yace ‘Duk wani condition da kike so Khadeeja ki saka na yi miki alƙawarin zan cika in dai za ki zama mata ta.

    Just one more chance Khadeeja, ki daina wahalar da zuciyata haka. Ta yi murmushi mai sauti ba tare da ta ce masa komai ba; tabbas yana nema ya gamsar da ita ta sake amincewa da aurensa, amma a halin yanzu ba ta san amsar da za ta ba shi ba. Ya gaji da shirun kuma yana ji a jikinsa cewa kalamansa sun fara yi mata tasiri.

    Ya katse shirun yace ‘Gobe da safe zan shigo, ok? ‘Ok, Allah ya kai mu. Amma ina da programme da safe so ka bari sai bayan azahar. ‘Ok, I will take you out to lunch then. No execuses. Ta yi dariya ‘Ka dai san ba zan je ba ko? Kada ma ka fara wata rigimar daban.’ ‘In dai rigima ce ai a wajenki na koya. I will see you tomorrow at lunch.’ Ya ajiye wayar ba tare da ya bari tace wani abu ba.

    Ko da ba za ta yarda ya fita da ita lunch ɗin ba ya fi so ta bar shi ya kwana da murnan zai fita da Khadeeja gobe, in ya so idan ya je office ɗin su yi faɗan da suka saba. Tana tsaye a jikin ƙofar ɗakin tana jinsa, duk abinda ya faɗa tana ji. Sai da ya ajiye wayar sannan ta banka ɗakin ta shiga a fusace.

    Firgigit ya juyo ya kalli ƙofar da aka mako, yace ‘Ya haka kamar za ki fizge ƙofar? Me ya faru ne? Ko wani abun ya biyo ki? Ta tsaya tana masa kallon raini tana jijjiga, sai da gaji da kallon nasa sannan a fusace tace ‘Mustapha na gaji da wulaƙancin da kake mina a kan matar nan, shekara huɗu ana abu ɗaya saboda tsohon naci. Wallahi babu ruwan Allah da kun taɓa aure alaƙarku haramtacciya ce.

    Kuma idan ma zina kuke Allah zai kama ku. Faɗan nata bai harzuƙa shi don ya saba ji, idan ma ba ta ji yana waya da Khadeejan ba kullum cikin duba masa waya take. Ba sa magana ta whatsapp don haka kullum cikin duba calls take, da zarar ta ga call ɗin Khadeeja to sai ta yi wannan masifar. Ya miƙee ya naɗe daddumar yana cewa ‘Kada ki kuskura ki jefi khadeeja da wannan kalmar yanzu ranki zai ɓaci, kuma kin sani.’

    Ta riƙe ƙugu tana dan zare ido tana cewa ‘Ohh! Yanzu kai ka fi son Khadeeja kenan dan kanka, kai na jefe ka da koma menene amm kada na jefi Khadeeja ko? To wallahi da kai da ita baku isa ba…. ‘Ke kika sani.’ Ya faɗa tun kafin ta ƙarasa faɗin abinda take faɗa, ya ajiye daddumar ya kewayeta ya fice daga ɗakin.

    Ta juyo ta bi bayansa da kallo cike da takaici sannan ta wuce ta zauna a gefen gado ta zuba fuskarta a tafukan hannunta ta fashe da kuka. Wannan wane irin wulaƙanci ne, tana murna ya saki kishiyarta amma kullum suna tare, ita kuma tana nan ya kulle ta a gida. Wannan wace irin musiba ce? So take ta ware rana ta je ta sami Khadeejan a office ɗin nata ta tara mata mutane amma dai tana tsoron kada Mustapha ya sake ta a kan hakan; don yanzu ta ga kamar ma ba a haiyacinsa yake ba.

    To yanzu babu aure a tsakaninsu yana mata wannan tsohon nacin idan kuma ta dawo ya za a yi? Ita menene makomarta ya dawo da rabin ransa me ƙaunar ‘yayansa. Ta ɗora hannu a ka ta sake rushewa da kuka.

    END

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Dole tana ji tana gani ya kafa mata doka idan dai har zai ci abinci to parlor ɗin kasa zai ci. Babu yanda ba ta yi da shi ba yaran su dinga hawowa sama amma yace ba za su hau ba tunda ita saman take so a bar mata, haka ta haƙura ta saka masa ido saboda abun yana nema ya zama matsala a tsakaninsu.

    Duk wani taimako da aiki da malamai za su yi mata tana kan yi sai dai abun ya ƙi yi, idan ya yi kamar zai kama sai kuma ya sake botsare mata. Idan dai tana son ganin walwalarsa to ta yi wa yaran nan yanda suke so kuma ba tare da ta yi masa wani ƙorafi ba. Burinta ɗaya yanzu a aurar da Afaf domin haka ne kawai take ganin za ta sami natsuwa a gidan nan.

    Don a halin da ake ciki komai zai yi da Afaf yake shawara, wasu lokutan ko ta ba shi list ɗin cefanen gidan sai ya tambayi Afaf abinda take buƙata ita da kannenta ya siyo musu. Idan kuma ya kawo kayan sai ya tsaya a ƙasa Afaf ɗin ta ware nasu kayan sannan ya hau mata sama da sauran. Haka dai take haƙuri, musamman da yake ya iya lallaɓa ta ya tsara ta kawai dai ya nuna mata yaran nan nasa ba za su taɓu ba.

    Haka rayuwarsu ta cigaba.

    Duk yanda yake jin zai samu Khadeeja ta saurare shi ya gagara, ga shi kuma sai a yanzu Allah ya jarrabe shi da ƙaunarta. Kusan kullum sai ya yi mata waya, idan ta ga dama ta ɗauka idan kuma ba ta ga dama ba ta ƙi ɗauka. Ya mayarwa kansa duk Juma’a da yamma sai ya je gidan duba Hammad, sai dai hakan bai ba shi damar ganinta ba.

    Domin idan ya je ko da ya yi mata waya haka za ta saka a buɗe masa parlor ɗin baƙi ta turo masa Hammad, har ya gama hirarsa da Hammad ya tafi ba za ta fito ba. Don haka wasu lokutan sai kawai ya rutsa ta a office inda dole ta zauna su gaisa har su ɗan yi hira. Abu ɗaya ne yake hana shi zaƙewa a kan maganarta saboda har yanzu yana jin kunyar Baffanta, bai san da wane bakin zai je yace masa ya sake ba shi auren Khadeeja ba.

    Shi yasa ya dage yake ƙoƙarin ganin ya gamsar da Khadeejan ta je wa Baffan da maganar da kanta. Kwanci tashi har shekara ta zagayo. Tun da ya gama haɗa takardun yake cike da farin ciki, haka ya kwana cike da zaƙuwa sabodan yanda yake son gari ya waye ya je ya sami Khadeeja ya yi mata albishir.

    Yana fita office ɗinta ya fara tsayawa, ya yi sa’a kuwa ta riga ta zo. Kamar yanda ya saba a cikin office ɗin ya same ta tana zaune tana editing script ɗin da za ta yi amfani da shi wajen gabatar da show ɗinta. Yana shiga ya tura ƙofar sannan ya yi wa kansa mazauni a kujerar gabanta cike da walwala. Bayan sun gaisa yace ‘Kina jin daɗinki fa, kin ga yanda kike sheƙi kuwa.

    Ta yi dariya tace ‘Don Allah ka bari, haba. Ko waya ma ba ka yi min ba kace min za ka zo to da ka zo na riga na shiga studio fa? Shi ma dariyar ya yi yace ‘Sai na jira ki mana. Ai idan kina son na daina zuwa wajen nan to ki yarda mu mayar da auren mu mu huta, in ba haka ba dole kullum na zo nan na yi attendance don duk masu shirin yi min shigar sauri su ganni su san ina nan ba fashi.’

    Ta sunkuyar da kai don ba ta san me zata ce masa ba, amma dai yawan zuwan nashi office ɗin ya fara gundurarta. Ba wai don ba ta so a gan shi ba ne kuma ba wai tana jin ya isa ya hana ta kula wanda take son kulawa ba; kawai dai tana so ya ɗan ba ta space tunda ita dai ta gama magana a kan lallai ba za ta koma gidansa ba kuma har yanzu hakane a ranta.

    Muryarsa ce ta katse mata tunanin da ya kirawo sunanta, ta ɗago ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta kawar da kai. Yace ‘Ki sauwaƙe mana wahala ki yarda mu mayar da aurenmu, duk wani abu da ya ɓata miki rai a baya na yi miki alƙawarin ba za ki sake gamuwa da shi ba a zamanmu.’

    Ta jijjiga kai ‘Na fahimce ka Mustapha, amma dai ka yi haƙuri. Ba wai kai ne ba zan aura ba, auren ne gaba ɗaya ba zan yi ba. Don Allah ka daina wannan maganar, ka mayar da hankali wajen kula da iyalinka. Ka ga yanzu ni babu aurenka a kaina, idan ta ji kana zuwa wajena zaku iya samun matsala. Ka zo kai ba ka sami natsuwa da ta gidan ba kuma ni ba aurenka zan sake yi ba.’

    Ya jijjiga kai don ba ya son wannan maganar, shi yana ji a jikinsa Khadeeja matarsa ce shi kaɗai don haka duk tsawon lokacin da za ta ɗauka tana yi masa yanda zai jure. Ya zaro envelope daga aljihunsa ya ɗora a kan tebur ɗin ya tura mata gabanta yana murmushi yana cewa ‘Wannan na zo kawo miki daman. Ta ɗauko tana dubawa tana cewa ‘Me na samu?’

    Ta zaro takardun daga envelop ta fara dubawa; kujerar Hajji Mustapha ya ba ta. Tana dubawa tana murmushi saboda yanda tunanin za ta je Hajji ya faranta mata zuciya. Ta ninke takardu ta fara mayarwa cikin envelop ɗin a daidai lokacin da murmushinta ya ragu. Ta tura masa gabansa tace ‘Na ji daɗi Abban Hammad, na gode Allah ya ƙara arziki da rufin asiri.

    Amma ka yi haƙuri ba zan iya karɓa ba, ba wai don na raina ba ko wani abu. Na gaya maka ba zan sake aurenka ba so ka ga babu wani dalili da zai sa na karɓar maka kujerar Hajji. Kuma ko na karɓa ma Baffa ba zai taɓa barina na je ba sai dai a ɗaura mana aure kafin na tafi; kuma wannan ba zai yiwu ba. Please ka yi haƙuri! Amma na gode sosai.’

    Kafin ta gama bayanin fuskarsa ta canza gaba ɗaya, ba tare da ya ɗauki takardun ba yace ‘To ki karɓa mana Khadeeja ki bari a ɗaura mana auren, please ki daina guduna haka. Ta sunkuyar da kanta cikin damuwa tace ‘Ba gudunka nake ba, amma dai ba zan iya ƙara aure ba.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci. Jimawa kaɗan yace ‘To yanzu ya kike so a yi? Ni da sunanki na biya wannan kujera. Ka yi hakuri ba zan iya karɓa ba. Suka sake yin shiru na ɗan lokaci. Kafin su yi magana aka ƙwanƙwasa ƙofar, ta amsa ta ba da izini aka shiga. Wata mace ce abokiyar aikinta ta ɗan leƙo tace ‘Anti Khadeeja yallaɓai yace ke ake jira a studio za a fara.’

    ‘Yanzu zan shigo.’ Ta faɗa tana shirin miƙewa. Ta dubu Mustapha tace ‘Bari na je kada ka sa a kore ni aiki. Ya yi dariya shi ma ya miƙe, sai dai tana kula da shi bai ɗauki takardun ba. Ta miƙa hannu ta ɗauka sannan ta zagayo ta tsaya a gabanshi, ta miƙa masa takardun tana murmushi tana cewa ‘Ka yi haƙuri ka tafi da wannan, wallahi ba zan iya karɓa ba.

    Idan na karɓa ba zan iya da rigimar Baffa ba tunda na san ba zan aure ka ba. Ka yi haƙuri please. Ya miƙa hannu ya karɓi takardun yana tsare ta da ido kamar mai binciken wani abun a idonta, har sai da ta kawar da nata idon. Ta wuce ya biyo ta a baya suka fito daga office ɗin, suka jero har zuwa reception sannan ta yi masa sallama ya fice ita kuma ta miƙe ta nufi studio ɗin.

    Tana fatan Allah ya sa dai kada ta kwafsa saboda yanda Mustapha ya jagula mata lissafi; me za ta yi da kujerar makansa? Wato ma shi har yanzu tunani yake saboda kujerar Makka yasa ta ƙi komawa gidansa? Bai ma san wacece ita ba kenan, zaman da suka yi tare bai sa ya fahimce ta ba.

    Ba ta buƙatar kujerarsa kuma ta san tabbas idan ba aurensa ta kuma yi ba ko kashi ta kai gida tace shi ya ba ta sai sun yi rigima da Baffa, kuma ba ta shirya ƙarya ba saboda Mustapha wanda take so ya rabu da ita ya daina damun rayuwarta.

    Tana tashi daga waje aiki ta wuce gidan Yaya Mama, ta yi sa’a yaran duk sun tafi islamiyya don haka ta sami Yaya Mama ita kaɗai. Bayan sun gaisa Yaya Mama tace ‘Bari na samo miki ruwa ko lemo. Ta dafe cinyarta tace ‘Bar shi kawai sai da na tsaya na ci abinci sannan na ƙaraso.’

    Ba tare da ɓata lokaci ba ta fara ba ta labarin kujerar Makkan da Mustapha ya kawo mata ɗazu. Sai da ta gama ba ta labarin suka sheƙe da dariya a lokaci guda sannan tace ‘Wai ni zai saya da kujerar Makka ɗan rainin hankali. Yaya Mama tace ‘Ai kuwa ɗan rainin hankali lamba ɗaya, wato tunda kin ce ya sake ki saboda kujerar Makka bari ya biya ki sai ki yarda ya mayar da aurenku.’

    ‘Ashe kin gane. Suka cigaba da hira suna tuna abubuwan da Mustaphan ya yi a baya. Sai da Magriba ta fara kawo jiki sannan Khadeeja ta fara shirin tafiya. Bari na wuce kada magriba ta yi min a nan. ’Yaya Mama ta dafa hannunta tace ‘Khadeeja, idan fa za ki koma gidan Mustapha kin san babu wanda zai hana ki ko? Don ni ina ganin ma gara ki koma can ɗin tunda kin ga ko babu komai ga Hammad.

    Kuma na ga har yanzu ba ki da wani manemin; duk da ma duk wanda za ki aura mijn wata ne don haka kin ga dole ki zauna da kishiya. Ni ina ga gara gidan Mustaphan tunda dai ya yi nadama har yana ƙoƙarin ya faranta miki. Nan take ta ɓata rai, ta zare hannunta ta ɗan matsa daga kusa da ita sannan tace ‘Ba zan taɓa komawa gidan Mustapha ba, aure kuma ba ya gabana balle na fara damuwa da rashin manemi.

    Idan Allah ya saka ina da rabon aure a gaba to duk wanda Allah ya sa shi ne mijina zan aura amma fa in sha Allahu ba zan sake auren Mustapha ba. Mutumin da ya ɗauke ni ne kawai a matsayin solution to his problem. Ko yanzun ma da yake ta ƙoƙarin na koma gani ya yi ƙiriƙiri matar tasa ta kasa kula masa da gidan da yara kamar yanda na yi.

    Shi yasa ya lallaɓo ya mayar da ni cikin wahalar da Allah ya raba ni da ita. Ba zan koma na, can su ƙarata. Ta miƙe ta ɗauki jakarta, don haka ita ma Yaya Maman ta miƙe. Ta san idan ta fiya takurawa da maganar yanzu za su yi faɗa don haka sai ta ƙyale ta suka yi sallama ta kama hanya.

    Wunin ranar gaba ɗaya bai yi masa daɗi ba. Ko da dai bai sa ran Khadeeja za ta karɓi kujerar ba tare da an kai ruwa rana ba amma kuma bai sa ran za ta ƙi karɓa haka gaba ɗaya ba ba tare da wata ƙofa ta sulhu ba. Haka ya wuni a office ɗin babu walwala. Sai da yamma ta yi sannan ya kwashi kayansa ya koma gida.

    Yana shiga ɗakinsa ya ajiye takardun hannunsa a kan mudubi; takardar kujerar da ya ba wa Khadeeja ce a sama tare da wasu takardun na office. Tunda ya je sallar magriba masallaci ya dawo ya yi zamansa a ƙasa shi da yara. Da farko ta ɗan zauna a wajensu ana hira gaba ɗaya, daga baya kuma sai ta tashi ta haye sama ta bar su.

    Ɗakinsa ta shiga don ta samu ta huta domin nan ne kawai idan ta rufo ƙofar Rukayya ba za ta so ta buga ta tashe ta ba. Har ta wuce mudubin sai kuma ta koma da baya, ta sa hannu ta ɗauki envelope ɗin da ta ja hankalinta. A buɗe take don haka sai kawai ta zaro takardun ta fara karantawa.

    Nan da nan kanta ya kulle; tabbas wannan sunan Khadeeja ne. To me hakan yake nufi?Suna tare kenan yanzu ta zama bazawararsa ko me? Tunda idan ba wata alaƙa ce tsakaninsu ba me zai saka har ya biya mata kujerar Makka? Kenan ma ita Mustapha zai rainawa hankali, ya saki matar sannan ya koma yana bin ta? Gaskiya ba za ta yarda ba.

    Ta ɗaga kanta ta hango wayarsa tana chaji a kan bedside durowa; nan da nan ta ajiye takardun ta ƙarasa ta ɗauki wayar. Ta riga ta san PIN ɗin don haka kai tsaye ta buɗe ta fara duba whatsapp; sai dai har ta gama dubawa ba ta ga sunan Khadeeja ba. Tana duba calls ta ga sunan ‘Sweetheart’ shi ne sunan da ya yi saving lambarta tun yana zuwa zance kuma bai taɓa canzawa ba.

    Bayan rabuwarsu Najan ta goge ta saka maman Hammad amma ba ta san yanda aka yi ya mayar ba. Ta mayar da wayar ta ajiye cike da damuwa da takaici. Ta tashi ta dawo ɗaya gefen gadon ta zauna ta zuba tagumi; tabbas za su yi rigima da Mustapha don ba zai yiwu ba ya dinga zagayawa wajen tsohuwar matarsa suna raina mata hankali.

    Sai wajen ƙarfe tara na dare ya hawo saman, lokacin ya je sallar isha’i ya dawo kuma sun gama cin abinci da yara. Zuwa lokacin ita ma ta gama duk abinda take yi ta kwantar da yara tana kwance a kan gadon ɗakinsa sanye da rigar bacci ta miƙe kafa tana kallo a waya ya shiga ɗaki. Bayan ta amsa sallamarsa ta mayar da hankali kan wayar hannunta.

    Kai tsaye ya wuce ciki ya canza kayansa sannan ya zauna a kan carpet ɗin da ke gaban gadon ya miƙe ƙafa ya janyo computer ɗinsa ya kunna ya kama aiki. Yawanci idan dai har yana da aiki to ya kan kai dare sosai a zaune yana aikin, ita kuma ba za ta iya jira ba. Don haka ta miƙe ta zauna ta ajiye wayar da take hannunta ta yi gyaran murya sannan tace ‘Uhm, na ga wata takarda, wai Maman Hammad ka biyawa Makka?’

    Bai yi mamakin jin tambayar daga gareta ba duk da bai sa rai da ita ba, amma dai ya san ya manta ya ajiye takardun a kan mudubinsa. Ba tare da ya bar aikinsa ba yace ‘Eh ita na biyawa, akwai matsala ne. Cike da neman rigima tace ‘To kuma a yanzu meye tsakaninka da ita tunda na ga dai babu aure. Ko kuma kun mayar da auren ne ni ce ban sani ba.’

    Har yanzu hankalinsa yana kan aikin yace ‘Ba mu mayar ba muna dai kan hanya. To shi ne kuma ka biya mata Hajji. Ya ɗago ya dube ta yace ‘Eh, akwai matsala ne? ‘Gani dai na yi bai dace ba tunda babu aure a tsakaninku. ‘Wannan ra’ayinki kenan. Ta kula so yake ya yi mata wulaƙanci don haka ta miƙe ta zauna sosai tace ‘Ina fatan dai ka san yanzu ita ɗin ba muharramarka ba ce.

    Kuma ina fatan ka san ba zai yiwu ina nan gida ina maka biyayya wai ni matar aure ba ka dinga zagayewa wajen tsohuwar matarka wadda ka saka da hannunka, ba zan ɗauka ba gaskiya.’

    Ya ɗago ya kalle ta rai a ɓace yace ‘Sai ki ɗau mataki a kai. Ta kula kamar haushinta yake ji sai dai ba ta san dalili ba, don lafiya ƙalau suka rabu da safe ya ajiye ta a office sannan ya fice; to meye ya harzuƙoshi hakan daga yin magana? Kada fa ka gaya min magana daga tambaya, na dai gaya maka ba zai yiwu ba ina nan ka kulle ni a gidanka a dinga ganinka a gari kana yawo da wata matar banzan.

    Ta faɗa tana miƙewa tsaye. A fusace yace ‘Khadeejan kike cewa matar banza saboda wulaƙanci? Sai dai kafin ya rufe bakinsa ta fice daga ɗakin ta rufe masa ƙofar; wanda wannan ɗabi’arta ce idan dai ya ɓata mata rai sai ta gaya masa magana mai zafi sannan take fita daga inda yake. Ya yi tsaki ya cigaba da aikinsa don so yake ya gama aikin kafin ya kwanta.

    Haka rayuwarsu ta cigaba. Khadeeja ta ƙi yarda a mayar da aurensu sannan shi kuma ya kasa tunkarar Baffanta da maganar don ya san ba za a yi mata auren dole ba. Amma kuma ya ƙi ya daina bibiyarta; har ta kai ba ya iya sati bai neme ta yaganta ba. Idan ya je gidansu wajen Hammad ta ƙi fitowa to tabbas zai same ta a office. Waya kuwa daman ba ta yankewa don idan ma ta ƙi ɗauka haka zai yi ta kiranta har sai ta gaji ta ɗauka.

    Duk wata kalma da zai yi amfani da ita wajen ganar da ita ta yarda su mayar da aurensu ya yi amma ta sanar da shi ba za ta iya komawa ba. Duk lokacin da ta ji kamar za ta haƙura su koma idan ta tuna yanda yake banzatar da ita a gidan kuma ta tuna yanzun ma sai da ya rasa yanda zai yi da gidan sannan ya fara nemanta sai kawai ta ji ta fasa.

    Tana sane da duk wata rigima da ta faru a gidan tunda kusan duk Asabar a wajenta Habib yake wuni, duk abinda ya dame shi sai ya je ya same ta ya gaya mata. Lokaci zuwa lokaci tana samun masu nuna sha’awar aurenta sai dai auren gaba ɗaya ya fice mata daga rai; don haka yawancinsu ba ta ma bari su zo gidansu.

    Kuma duk inda ta je idan dai ba an santa a wajen ba to tana gabatar da kanta ne a matsayin matar aure don ma kada wani ya zo mata da wata magana; don haka mutanen da suka santa sai suka kasu kashi biyu, wasu suna ganin tana da aure wasu kuma suna ganin ba ta da aure. Amma kuma yawancin mutane kasa tambayarta suke yi.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Uku

    Kansa a cike yake saboda rashin bacci ga damuwa, don haka yana shiga office ɗin ya rufo ƙofar ya kwanta a kan 3-seater ɗin da take wajen. Yana rufe ido ya fara nadama; ya aka yi ya saki Khadeeja? Ya aka yi ya bari har ta gama idda bai mayar da ita ba? Tunda dai ai da ya mayar da ita ya san ba ta da wani zaɓi dole ta zauna da shi tunda ba za ta saki kanta ba.

    Tunda yake da Khadeeja bai taɓa ganin wata damuwa game da yaransa ba, ga shi wata takwas kacal da ta bar su gidan yana neman ya gagare shi. A da ya yi zaton Naja za ta fi ta kulawa da su musamman yanda ya ga tana nuna ƙauna garesu kafin ya aureta.

    To me ya canza mata ra’ayi har aka kai inda ba su da damar da za su ci abinda suke so a gidan ubansu? Lallai dole ya ɗau mataki. Haka ya wuni a office ɗin cikin rashin sukuni; yana tunani halin da yaransa suke ciki a gida sannan kuma ga shi zuciyarsa taƙki ta ƙyale shi da tunanin Khadeeja.

    Tabbas da Khadeeja tana nan da babu yanda za a yi ya wuni a office yana tunanin halin da yaran suke ciki. Domin ya tabbatar duk halin da suke ciki to ita ma tana cikin wannan halin a tare da su. Ya tuno lokacin da tace ba za ta yi musu girki ba yanda suka gaya masa gari suka sha kuma garin ma tare da ita suka sha.

    Ya yi dariya a fili; tabbas Khadeeja tana da rigima amma ta iya rigimarta. Ya tabbatar babu yanda za a yi ta ci kaza ta bar yara da baƙin shayi. Haka ya zauna yana aiki yana tuno rigimarsu da Khadeeja yana murmushi shi kaɗai. Bai taɓa zaton zai yi kewar rigimar Khadeeja ba amma yanzu tabbas kewar rigimar tata yake yi.

    Ƙarfe ɗaya da rabi daidai suka idar da sallah a farfajiyar office ɗin su. Yana shiga office ɗinsa ya zauna a kan kujerarsa ya tura ta baya kaɗan yana juyawa ya ɗauki wayarsa wadda take kan tebur ɗin ya lalubo lambarta ya dannan mata kira, ya kara a kunnensa bayan da ta amsa yace ‘Hello.’

    Bayan sun gama gaisawa yace ‘Kina ina ne? Da mamaki a muryarta tace ‘Ina office mana, akwai wata matsala ne? Murya a sanyaye yace ‘No, babu matsala kawai dai ina son ganinki. Zan iya zuwa office ɗin yanzu? ‘Umm! Akwai matsala ne? Ta sake tambaya. Ya yi ‘yar dariya ‘Babu matasala fa, akwai dai maganar da nake so mu yi. Zan iya zuwa, minti talatin kawai ya isa. ‘Ok, ina jiranka duk da dai na kusa tashi.’

    Ya ajiye wayar ya miƙe ya ɗauki mukullan motarsa ya kama hanya. Yana sane ya ƙi ya kirawo ta da ya isa don so yake ya shiga ya same ta a office ɗin nata, don haka bayan ya ajiye motarsa sai ya fito ya shiga gidan talabijin ya tambaya. Ba tare da ɓata lokaci ba aka nuna masa office ɗin nata.

    A hankali ya ƙwanƙwasa ƙofar, daga ciki muryarta ta ba shi amsa ‘Shigo a buɗe ƙofar take. Ya tura ƙofar ya shiga da sallama. Tana zaune a kan kujerar zaman mutum ɗaya wadda take gefe guda, da jakarta a gefenta tana ta danna waya; da alama ta gama shirin tafiya gida. Bayan ta amsa sallamarsa ya mayar da ƙofar ya rufe sannan ya ƙarasa ya yi wa kansa mazauni a kujerar da take kusa da wadda take zaune a kai.

    Bai san dalilin da yasa ganinta ya saka shi jin daɗi ba amma dai ya san ya ji daɗin ganinta. Cikin girmamawa ta gaishe shi kamar babu wata damuwa a tsakaninsu. Bayan ya amsa tace ‘Allah ya sa dai ba wata matsala don tunda kace za ka zo nake ta tunani.’ Ya yi murmushi yace ‘Babu wata matsala, kawai dai ina son ganinki ne.’

    Ta ɗan yi gajeren murmushi tace ‘Uhm, to gani. Ya yi dariya yace ‘Kamar dai kina kora ta. Ba korarka nake ba, kawai dai ina son na tafi gida don wallahi na gaji. Ya gyara zama; ya rasa ma ta inda zai fara domin ganinta ya goge masa duk zantukan da ya tsaro zai zo ya gaya mata. ‘Yara suna kewarki.’ Ya faɗa bayan ya gama nazarin ta inda zai fara.

    Nan da nan murmushinta ya ƙara faɗi, tace ‘Allah sarki ni da Hammad ma muna kewarsu. Don ma Yaya Habib yana zuwa gidan Mommy yana gaishe mu. Ya girgiza kai domin Habib bai taɓa gaya masa yana zuwa wajen Khadeeja ba, bai ma taɓa yi masa maganar Khadeejan ba tun bayan da suka rabu.

    ‘Ya Hammad? Ba ya kukan makaranta?’ Ya tambaya. ‘Baya yi, ka san ya haɗa wayon yayyinsa gaba ɗaya.’ Ta faɗa tana dariya. Suka yi shiru na ɗan lokaci; ita duk ta ƙosa domin so take ta tafi gida yayin da shi kuma ya gyara zama yana kwaso hira. Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan yace ‘Khadeeja. ‘Na’am.’ Ta amsa tana kallonshi.

    ‘Wai me yasa kika ce na sake ki? Ya tambaya yana tsare ta da ido. Ta sunkuyar da kai tana murmushi, ta ɗago ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta sake yi masa wannan murmushin nata wanda yake ɗauke da ma’anoni daban daban tace ‘Right question at the wrong time; amma dai zan ba ka amsa.’

    Ta sunkuyar da kai a daidai lokacin da murmushin fuskarta ya gushe, ta ɗago suka sake haɗa ido sannan ta gyara zama tace ‘Gajiya na yi Musatapha. Ka san idan mutum wanda bai iya swimming ba ya faɗa ruwa to zai yi ta ƙoƙarin ganin ya fita da rai ko, amma duk daɗewa zai gaji. To haka ce ta faru da ni.

    Soyayya ce ta saka na aure ka, amma idan dai ba na manta lissafin ba tun a shekarar farko na rasa soyayyarka. Haka na dinga kokawar janyo attention ɗinka ko za ka fahimce ni amma ba ka ko kalli inda nake ba; kai dai abinda kake so kawai shi kake so. Na haƙura ina zama da kai a haka saboda I was ok with just sleeping beside you every night; sai kuma ka ɗauko aure.

    Duk wani abu da nake so daga wajenka a lokacin ka ɗauka ka ba ta ina kallo. Haka na cigaba da kokawar samun attention ɗinka, ina ƙoƙarin ganin ka yi mana adalci amma hakan bai samu ba. Na tuna tun ina ni kaɗai ma ka fara kasa yi min adalci to balle yanzu mun zama mu biyu; ni da rabin ranka. So I gave up, ba zan iya ba, na gaji da faɗan da ba shi da ranar ƙarewa don na gane bana ma gabanka.

    Shi yasa na nemi saki kuma Allah ya taimake ni ka ba ni kuma ka bar ni har na gama idda. Idanuwansa suna kan fuskarta har ta gama ta yi shiru, ya cije leɓe yace ‘Kuma ba ki gaya min ba Khadeeja? How did I not see all this? Ta yi dariya tace ‘Da wanne yaren zan gaya maka?’

    Suka sake yin shiru na ɗan lokaci. Ta danna wayarta ta kalli agogo sannan tace ‘Time yana tafiya, wallahi so nake na tafi gida don na gaji. ‘Oh, sorry Suka sake yin shiru na ɗan lokaci sannan yace ‘Khadeeja yi haƙuri mu mayar da aurenmu, in sha Allahu haka ba za ta sake faruwa ba.’

    Ta miƙe tsaye tana dariya tace ‘Ka yi haƙuri Mustapha amma aure ba zan sake yi da kai ba, babu wannan zance don Allah kada ka sake yinsa. Shekarun da muka yi Allah ya amfana su kuma Allah ya sa kaffara ne amma kada Allah ya maimaita mana. Ya dafe kansa da hannuwansa biyu na ɗan lokaci sannan ya sauke hannuwan ya miƙe tsaye.

    Ta buɗe ƙofar ya fice sannan ta biyo bayansa suka fito daga office ɗin. Suka jero suka fito harabar office ɗin. Nan suka tsaya yana ta faman lallaɓata ta bari ya kai ta gida amma ta ƙi; yana ji yana gani ta tare taxi ta hau. Sai da ya tabbatar ta zauna a bayan motar sannan ya zagaya ya ba wa direban taxi ɗin kuɗinta. Suka ja mota shi ma ya koma ya shiga motarsa ya kama hanya.

    Ya dai ji tace ba za ta taɓa sake aurensa ba amma tabbas bai yarda ba, yana ji a jikinsa in sha Allahu za ta yarda su mayar da aurensu. Yanda zai yi da baffa ne ma yafi damunsa domin ya san tabbas Baffa ba zai saurara masa ba. Haka har ya isa gida yana wannan tunanin, sai dai yana saka ƙafarsa cikin gidan ransa ya ƙara ɓaci. Bai san a yanda zai je ya sami yaran ba sannan kuma ita kanta Najan yana jin haushinta do ba zai taɓa ba ta dama ta wulaƙanta masa yara ba.

    Ana cikin kiran sallar magriba ya shiga gidan, don haka ko zama bai yi ba ya ɗaura alwala ya ja Habin suka wuce masallaci. Ko da aka idar da sallar a can ya tsaya wajen magidantan unguwar suna hira, har sai da suka yi sallar isha’i sannan suka tashi daga hirar kowa ya koma gida.

    A parlor ɗin kasa ya sami yaran suna harkokinsu, ya wuce ya haye sama. Tana zaune a parlor tana jiransa saboda ba ta son yanda tun da safe ya ƙi ya ko kalli inda take. Ita idan ana faɗa ta fi so a yi hayaniya kowa ya faɗi abinda yake ransa, amma ya ma ƙi ya tambaye ta me yasa ta yi wa yaran haka balle ta samu ta yi masa bayani.

    Ba ta jin ya amsa sannu da zuwan da ta yi masa, idan kuma har ya amsa to tabbas ita dai ba ta ji ba. Ba tare da ya kalli inda take ba ya shige ɗakinsa. A fusace ta miƙe ta bi bayanshi. Yana tsaye a gaban mudubi yana rufe durowa ta shiga ta turo ƙofar, ta tsaya a bayan ƙofar ta rungume hannu tace ‘Ga abinci can a dining table.’

    Ba tare da ya kalle ta ba yace ‘Ki sauka da shi ƙasa a can zan ci ni da yara. Ta sunkuyar da kai ‘To bari nace su hawo sai ku ci a nan, duk da su ma na zuba musu nasu abincin kuma duk tuwon ne dai. ‘Ba sai sun hawo ba ni zan sauka, ki ɗauka ki kai can.’ Ya faɗa sannan ya juya ya zauna a gefen gado.

    Ta ƙarasa ta zauna a kusa da shi, ta dafa gwiwarsa ta dan marairaice tace ‘Don Allah ka ba wa Hajia haƙuri, wallahi abinda ta gani ba haka ba ne. Kai ma ka san babu yanda za a yi na ci wani abu na hana yara. Hawowa ne ba su yi ba na ajiye musu nasu a kitchen kuma da ka shiga za ka gani.’

    Ya kalle ta sheƙeƙe yace ‘Ai ba yau kika fara ba, kuma ba yau na fara yi miki magana ba. Babu wani haƙuri da zan ba ta idan kin gyara halinki su yaran za su gaya mata ai. Mugun halin da kike nuna musu kuma ki cigaba kada ki fasa. Ya miƙe zai fita, ta kama hannunsa ita ma ta miƙe tana cewa ‘Don Allah ka yi hakuri, yaran da nake hidimarsu tun kafin na aure ka kuma yanzu ribar me zan ci idan na yi musu mugunta?’

    ‘Ni ma shi ne abinda nake mamaki, wataƙila daman ba don Allah kike yi ba ko kuma zuga ki aka yi kika canza hali ni ban sani ba. Abinda na sani kawai shi ne kusan tun da Khadeeja ta bar gidan nan kika dage sai kin raba rayuwarki da ta yaran nan, ina kula da yanda kike ƙoƙarin ganin ba su hawo benen nan ba saboda tsabar samun waje…’

    ‘Don Allah ka dai wannan maganar, wallahi kai ma ka san ba haka ba ne. Na ga dai ko gidan waye akwai part ɗin mai gida inda ba a bari yara su shiga, amma in sha Allahu ba zan sake hakan ba tunda na ga kai ba haka ne tsarinka ba.’ Ta katse shi cikin ƙosawa. Ya zare hannunsa da ta riƙe ya miƙe yana cewa ‘Ki kawo min abincin parlor ɗin ƙasa yanzu.’

    Ya fice ba tare da ya saurari amsarta ba. Haka ta gama zumɓura baki ta sauko ta kawo masa abincin nan parlor ɗin ƙasa inda ya zauna suka ci da yaran; duk da sun nuna masa su ma tuwo aka ba su irin nashi. Haka ya kafa mata dokar idan dai yana gidan to a parlor ɗin ƙasa zai dinga cin abinci wajen yara, babu roƙon da ba ta yi masa ba a kan ya bari yaran su dinga hawowa saman ana cin abincin tare amma ya ƙi ya saurare ta.

    Ya kula cewa ganin saman bene take kamar wani abu na musamman don haka ya yanke shawarar bar mata saman benen ita kaɗai. Ya yanke shawarar a ƙasa zai dinga zama hira kuma a nan zai dinga kallo yana cin abinci, in ya so idan zai yi bacci ya dinga hawa saman ya kwanta. Ta yi yanda take so da saman ita kaɗai.

    Yana sane ya ƙi zuwa gidan Hajia a ranan sai washegari; ya san idan ya je zancen nan bai huce ba Hajia da Alaji haɗuwa za su yi a kansa har sai ya rasa abinda yake masa daɗi. Don haka washegari yana tashi daga office ya wuce gidan Hajia. Bayan sun gaggaisa ya sami Alhaji a parlor, yana gama amsa gaisuwarsa yace ‘Mustapha me yake faruwa ne a gidan naka? Ban ji daɗin bayanan da na samu daga wajen Habib ba kuma sai ga Hajia ta je ta gani da idonta. Me yake faruwa ne?’

    Ya gyara zama ya shafa kansa sannan yace ‘Wallahi Alhaji ‘yar matsala ce aka samu kuma na ma yi mata magana in sha Allahu hakan ba za ta sake faruwa ba. Ya tashi daga kashingiɗar da yake yana cewa ‘Yar matsala? ‘Yar matsala fa kace Mustapha? An bar yara a ƙasa kamar masu zaman kansu amma kana cewa ‘yar matsala? Gidan naka har ya kai an raba tukunya, ta marayun yaranka daban ta matar gida daban.

    Anya kuwa Mustapha? Rashin uwa ai ba hauka ba ne da za ka wulaƙanta su saboda Allah ya ɗauki ran mahaifiyarsu. Ya sake shafa kansa ‘Wallahi Alhaji akasi aka samu kuma in sha Allahu hakan ba za ta sake faruwa ba. Ya kawar da kai cike da damuwa ya yi shiru, jimawa kaɗan ya cigaba ‘Ita Khadeeja ya wajen nata da Muhamadun? Kana zuwa dai?’

    Ya gyara zama yana murmushi ‘Eh, ina zuwa. Jiya ma na je. ‘To ya kamata dai ka san yanda za a yi ku daidaita tsakaninku tunda dai ka ga ita ba a taɓa samun wata matsala tsakaninta da yaran nan ba, haɗawa ta yi ta riƙe su tun kafin ma ta sami nata. Kuma da ta sami natan ma babu abinda ya canza. Ka ga ita ce ta zama uwa ta gari a wajensu tunda ga su ƙalau da tarbiyyarsu.’

    ‘Haka ne Alhaji, in sha Allahu za mu daidaita. ‘Ya kamata dai ka san abun yi tunda ka san dai yanzu a kasuwa take, idan ba ka maida hankali ba wani zai iya yi maka shigar sauri. Suka ƙarasa hirarrakinsu sannan ya yi musu sallama ya wuce office.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Biyu

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Biyu

    Ba a fi sati ɗaya da kwashe kayan Khadeeja ba Naja ta saka Mustapha a gaba sai da ya sake fentin saman aka gyara ta kwashe kayanta ta koma. Yaran kuma gaba ɗaya ta tattaro su ta dawo da su ƙasa tare da masu aikinta guda biyu. Ɗakinta da parlor ɗinta nan ta mayar ɗakinsu Afaf, suna ji suna gani babu yanda suka iya.

    Shi kanshi Mustapha abun bai yi masa daɗi ba amma ya kasa magana; yana matuƙar mamakin abinda yasa ba ya iya hana Naja abinda take so a ‘yan kwanakin nan. Cikinta yana cika wata tara ta sake haifar ‘yarta mace, haka ta dage ta shirya taron suna fiye ma da wanda ta shirya a haihuwar Rukayya. Aka sakawa yarinyar suna Maryam.

    Washegarin suna su Anti Wiyya da sauran dangi suka soye naman suna suka gyara komai, sannan suka tafi suka bar Anti Wiyya ita kaɗai wadda za ta ƙara kwana biyu saboda taya ta jego. Tana zaune a parlor ɗin sama Anti Wiyya ta shigo da sallama, bayan ta amsa ta ƙarasa ta zauna a kusa da ita sannan tace ‘Wannan mai wankin naki gaskiya ya iya wulaƙanci, sai da ya fuskanci ana taro sannan ya gudu.

    Ni dai wallahi ko kayan sakawa gobe ba ni da su duk sun yi datti, ga shi duk jikina ciwo yake balle na zage na wanke kuma ‘yar aikinki ma dai ta fi ni gajiya. ‘Ai mai wankin nan ya yi wa kansa, in sha Allahu gobe Abban Rukayya zai samo mana wani mai wankin kowa ya huta.’ Ta faɗa tana gyara zama.

    Anti Wiyya tace ‘Don ma dai ‘yayanki ba sa moruwa ne in banda haka ga Habib can a ƙasa yana wanki ai da ko kala ɗaya ne ya wanke min. Ta gyara zama ‘Au ai ban san ma yana gidan ba kwaso kayan duka bari na kirawo shi zai wanke miki yanzu. Ba tare da ɓata lokaci ba ta juya ta koma ƙasa inda ta kwaso kayan nata yayin da ita kuma Naja ta ƙwalawa Afaf kira ta saka ta ta turo Habib.

    Kusan a lokaci guda suka isa parlor ɗin, shi ya tsaya daga a bakin ƙofa yayin da ita kuma ta ƙarasa ta zube kayan a gaban Naja. Yana daga tsaye a bakin ƙofa yace ‘Anti ga ni.’ Tace ‘Mai wanki ya kwana biyu ba ya zuwa, ka kwashi kayan nan ka wankewa Anti. Ya kalli kayan ya kalle ta yanda take muzurai; ba wai ba ta saba yi masa hakan ba ne, ta riga ta saba musamman tun bayan da Khadeeja ta bar gidan.

    Kawai dai ya kan yi mata abinda zai iya wanda ba zai yi ba kuma ya bar mata kayanta. Ya sake kallon kayan yace ‘Ah ku bar shi dai yanzu zan fita sai na samo muku wanda zai wanke ku biya shi. Har ya juya ya fara tafiya tace ‘Kana nufin ba za ka wanke ba ko me.’ Ya dan dawo ya kalle ta ya kalli kayan, har ya buɗe baki zai yi magana kuma sai ya fasa, ya fice ya barta nan a zaune da kayan.

    A fusace ta miƙe tana huci, kafin ta yi magana Anti Wiyya tace ‘Ai na gaya miki waɗannan yaran ba sa moruwa. ‘Ni ka tafi ka bari ina magana ko Habib? Saboda ka ga ni ba uwarka ba ce kuma ba khadeeja ba ce ko? Saboda ba a isa a saka aiki ka yi ba ko? To wallahi bari Abban naku ya dawo, sai dai ko ni ko kai a gidan nan don idan dai ba zan more ka ba sai dai ka bar gidan wallahi.’

    Wiyya tace ‘Ah to, yaron da bana jin ya haura sha takwas ya dinga yi miki irin wannan rainin, wannan nan da ‘yan shekaru ai sai ya kai miki duka. ‘Wallahi bari ubanshi ya dawo, dole ya bar min gidan nan idan ba haka ba ni na bar masa gidan. Idan ma Khadeejan ce take zuga shi ta janyo masa. Haka Wiyya ta sakata a gaba ta ƙara zuge ta kafin ya dawo.

    Ana idar da sallar Magriba ya shiga gidan, Habib ne ya buɗe masa gate tare da Baba maigadi ya yi masa sannu da zuwa sai dai bai raka shi har cikin gidan ba. Kamar yanda ya saba a parlor ɗin ƙasa ya sami yaran suna zaune suna kallon TV, bayan ya amsa sannu da zuwansu ya wuce sama.

    Da da ne Nasreen da Shukra sai sun raka shi har ɗakinsa, sai dai yanzu saboda yanda Naja take yawan korarsu tana nuna musu su dinga tsayawa a ƙasa ya sa sun haƙura, haka ya haye shi kaɗai zuciyarsa babu daɗi; saboda shi ma yana kewar wannan rakiyar. A ɗakinsa ya same ta tana ta cika tana batsewa, domin ko sannu da zuwa haka ta yi masa tana ta faman zumɓura baki.

    Bayan ya amsa yace ‘Me ya faru ne naga kina ta wani ɓata rai? Ta sake haɗe rai sannan tace ‘Ya za a yi a gidan nan a ce ban isa na saka Habib aiki ya yi ba? A gaban kowa zan ce Habib ya yi aiki amma kai tsaye ya ce min ba zai yi ba? Ai ba haka yake yi wa Maman Hammad ba, ko da yake na ji suna cewa yana zuwa wajenta ban sani ba ko ita ce take zuga shi ya dinga yi min rashin kunya.’

    Ya ajiye jakarsa ya zauna a kan kujerar gaba mudubi ya fara cire takalmansa yana cewa ‘Kada ki saka Khadeeja a cikin wannan maganar, da za ta sa wani ya yi miki rashin kunya da tun tana nan za ta saka su. Habib ɗin me kika ce ya yi ya ƙi yi? ‘Wankin kayansa yake yi shi ne na kirawo shi na ba shi kayan Anti Wiyya kala ɗaya nace ya taimaka ya wanke mata amma yaron nan ya ƙi, kuma yana kallo mai wankin namu ya gudu.

    Ita ce ta ke ta fama kula da gidan kayanta duk sun yi datti amma a gabanta Habib ya ce ba zai wanke mata kala ɗaya ba don wulaƙanci don ya nuna mata ban isa ba. Ya miƙe ya cire kayansa yana cewa ‘Ki ɗauko kayan idan na fito zan ba shi ya wanke in ya so zan gayawa Baba Maigadi ya zagaya nan makarantar almajirai ya samo yaro a wajen malaminsu wanda zai dinga zuwa yana wankin.’

    Kafin tace wani abu ya shige banɗaki. Ta zumɓura baki ta ja tsaki don ba haka ta so ba, so take a yi masifa ta sami damar da za a ce Habib ya bar gidan. In ya so sai ta san yanda za ta yi da Afaf, tana gamawa da waɗannan biyun ta san gidan ya zama nata, musamman da yake Shukra ita matsoraciya ce duk yanda ma aka juya ta haka take yi.

    Jimawa kaɗan ya fito ya sake kaya sannan ya wuce ya zauna a dining table ya fara cin abinci. Yana cikin cin abincin ya ɗauki waya ya kirawo Habib, ba tare da ɓata lokaci ba ya hawo ya same shi. ‘Abba gani.’ Ya faɗa yana tsaye daga gefe. Ya ajiye cokalin da yake hannunsa sannan yace ‘Habib me yasa Antinka ta saka ka wanki ka ƙi yi?’

    Yace ‘Abba ba ƙin yi na yi ba, wankin ne da yawa kuma nace gobe zan samo musu yaro ya wanke a biya shi. ‘Kala ɗayan ne da yawa? Kayan ma da ba nawa ba ne.’ Ta faɗa tana wasu muzurai. Yace ‘Ni dai kayan da aka ba ni za su kai kamar kala biyar ko fiye, ban sani ba ko ba su aka nuna maka ba.’

    Abbansu yace ‘Ka ga Malam, ba na son wani ƙarin bayani. An ce kaya kala ɗaya ne kuma gobe ake so a yi amfani da su. Ka je a ba ka kayan ka wanke yanzu in ba so kake ranka ya ɓaci ba, kuma daga yau ba na son a saka ka aiki ka dinga ƙin yi. Ba zan ɗauki taurin kai da rashin kunya ba. Ya buɗe baki zai yi magana sai kuma ya fasa, ya juya ya fice.

    Ya dubi Najan yace ‘Ki je ki ce mata ta ba shi kayan ya wanke. Ta tashi ta fice. Yana zaune a tsakar gida wajen Baba maigadi Shukra ta je ta kirawo shi. Yana shigowa ya ci karo da wankin a zube a bakin ƙofa; tabbas wankin sun fi kala biyar. Yana shiga cikin parlor ɗin kafin ya yi magana Naja da take tsaye tace ‘Gasu nan ka je ka wanke, kuma wallahi idan ba su fita ba sakewa za ka yi har sai sun fita.’

    Ta juya ta haye sama ta bar su a nan shi da ƙannensa. Ya juya ya dawo ya tsaya a kan wankin yana ƙare musu kallo yana tunani; tabbas ba zai yi wankin nan ba, ko da kuwa kala ɗayan ta bayar kamar yanda tace. Kuma yanda ya ga a gaban Abban tace kala ɗaya ne kuma ta ɗauko kaya da yawa haka ta ba shi ya san ta shirya wata maƙarƙashiyar.

    Ya san ba lallai Abbanshi ya saurare shi ba saboda tana gabansa tana tsara masa zance, kuma ya san idan har ya yi wannan wankin to ta sami damar da za ta mayar da shi ɗan aikin gida kuma ba zai yi ba. Haka ya kewaye ya fice ya bar wankin a nan inda ta ajiye su. Suna sama ita da maigidan suna ta hirarsu cikin kwanciyar hankali, sai waje ƙarfe tara sannan Anti Wiyya ta fito daga ɗakin baƙi ta ga wankin.

    Ta yi matuƙar mamaki musamman da ta tambayi Afaf ta tabbatar mata Habib ɗin ya fice bai ɗauki wankin ba. Nan ta koma ɗaki ta kirawo Naja a waya wadda ta sauko, ta nuna mata wankin sannan ta yi mata bayanin cewa a nan ya fice ya bar su.Yaran suna kallo ta tsuguna ta tsince kayan ta bar kala ɗaya da hijab guda ɗaya sannan Anti Wiyyan ta koma ɗaki ita kuma ta haye sama.

    Jimawa kaɗan Mustapha ya sauko yana tambayar Afaf ina ƙaninta. ‘Abba ban ganshi ba, ficewa kawai ya yi ba tare da yace komai ba.’ Ta ba shi amsa. A fusace ya murɗa ƙofar ɗakin Habib ɗin ya shiga yana kiransa, sai dai ga mamakinsa Habib ɗin ba ya cikin ɗakin. Ya fice wajen Baba Maigadi inda ya tabbatar masa bai san inda Habib yake ba, ya ƙara da cewa ‘Bana jin ma fita ya yi, don tun da aka ce ya zo kana kiransa ban sake ganin gilmawarsa ba.

    Sai dai ko da ina sallah ne ya fice ban sani ba. Ya koma cikin gidan ba tare da yace komai ba. Yana shiga parlor ɗin ya dubi kayan yace ‘Nasreen zo ki kwashi kayan nan ki mayar mata, yayan naki zai zo ya same ni. Ya haye saman inda ya tarar da Naja a zaune a parlor ita da Rukayya, ya sami waje ya zauna sannan ya ɗauki wayarsa ya dannawa Habib kira.

    Ba ƙaramin mamaki ya yi ba da ya ji wayar Habib ɗin a kashe, sai dai ya yi tunanin kashe wayar Habib ɗin ya yi don ya san ba shi da gaskiya. Don haka sai kawai ya sauko ya sanar da Baba Maigadi cewa idan Habib ya shigo gidan ya yi masa waya. Tun yana sa ran shigowar Habib har abun ya fara ba shi tsoro; yaran duk sun tafi sun kwanta har sha biyun dare ta yi amma Habib bai shigo gidan ba, ga shi sai kiran wayarsa ake yi a kashe.

    Yana son ya kirawo Hajia ko Habib ɗin ya je can amma kuma ba ya son ya ɗaga musu hankali. To ina Habib zai shiga? A karo na babu iyaka motsin shigarsa ɗakin ne ya farkar da ita daga bacci, ta gyarawa Baby Maryam kwanciyarta sannan ta dube shi tace ‘Wai bai dawo ba. A jigace yace ‘Eh, wallahi har abun ya fara ba ni tsoro. To ina Habib zai tafi?

    Ina ma ya sani a garin nan shi da ba wani yawo yake ba? Tace ‘Ya za ka ce ina ya sani yaron da yake level 1, kuma yake tafiya makaranta da kansa. Ai yanzu ba kamar da ba ne, tsaf ya san ko ina. To ina zai tafi a wannan daren? Ga shi Baba Maigadi ma yace ko fitarsa bai gani ba kuma gidan nan babu inda ba mu duba ba baya nan.’

    Tace ‘To ka dai yi hakuri ka zo ka kwanta tunda ka ga yanzu ɗayan dare ta kusa, zuwa wayewar gari sai a nemo shi a ba shi haƙuri a gaya masa ya bar wankin. ‘Mtseww! Wai kin san me kike faɗa kuwa? Na zo na kwanta saboda ke kin kwanta ko? Ya sake jan tsaki sannan ya fice daga ɗakin ya rufe mata ƙofar da ƙarfi, rufe ƙofar da sai da ya farkar mata da Baby daga barci.

    Ta juya a fusace tana gunguni ta ɗauki yarinyarta ta saka mata nono. Yanda ya ga rana haka ya ga dare, yana zaune a parlor shi kaɗai. Sai dai idan bacci ya ɗauke shi ya yi firgigit ya farka, ya sake buga lambar Habib amma a kashe. Yana fara jin kiran sallar asuba ya kirawo Alhaji ya sanar da shi ba a ga Habib ba.

    A shirye ya fice masallaci, bayan an idar da sallar asuba ya sanar da su ɓacewar habib. Yana dawowa gidan ya ɗauki mukullin motarsa ya fice ya nufi gidan Hajia. Su ma a tsaye ya same su cikin tashin hankali, nan suka zauna suna jira gari ya ƙara wayewa su je police station su sanar. Suna zaune a parlor ɗin Alhaji cikin tashin hankali Hajia ta dubi Mustapha tace ‘Kuma ka tuntubi kakanninsa, can gidan su Ma’u da ma ita Khadeejan ko wajensu ya tafi?’

    Ya gyara zama yana cewa ‘Khadeeja dai na tambaye ta ita ma ba ta ganshi ba, amma gidan mama ma ni na manta da su. Bari na kirawo su na ji. Kafin ya gama laluben lambar suka jiyo bugun ƙofa, gaba ɗayansu suka nufi ƙofar saboda Alhaji ya ba da sanarwa a masallaci ya yi zaton ko an sami wani labari ne. Ga mamakinsu Kawu Auwal ne wato ƙanin Ma’u tare da Habib ɗin.

    Suna haɗa ido Mustapha ya kai masa duka yana cewa ‘Shi ne za ka fice ba tare da ka gayawa mutane ba saboda raini ko? Alhaji yace ‘Ka bar shi mana ya zauna ya yi bayani.’ Suka ƙarasa cikin gidan suka zauna a parlor ɗin Alhaji. Bayan sun gaggaisa Kawu Auwalu yace ‘Wallahi ni ma da asuba Mama ta kirawo ni tace na zo na dawo da shi, ita ma ta yi zaton an san yana gidan shi yasa ma ba ta nemi kowa ba.

    Sai ɗazu bayan sallar asuba Antinsa Khadeeja ta kirawo ta tana cigiyarsa. Shi ne ta kirawo ni tace na kawo shi nan na yi bayani. Alhaji ya yi masa godiya sannan ya dubu Habib yace ‘Mutumina ya haka kuma? Me suka yi maka a gidan da za ka bi dare ka gudu? Kuma madadin ka zo ka gaya min sai ka tafi ka ɗagawa Mama hankali.’

    A nan ne ya sami dama ya gayawa Alhaji abinda ya faru, sannan ya sanar da shi irin zaman da ake yi a gidan. Hajia tace ‘Dama Aminan Jidda ta faɗa, tace wancan zuwan da suka yi gidan ba su ma ga Najan ba. Kamar yaran suna ƙasa su da mai aiki suna rayuwarsu ita kuma tana sama ita da nata yaran, kuma yanda ya faɗa haka Aminan ta faɗa tace shi kanshi Mustaphan yaran ba sa ganinshi sai dai idan ya sauko.’

    Shi ma Auwalu ya tabbatar musu da cewa duk waɗannan maganganu yaran sun daɗe da yi wa Mama bayani, sai dai da yake ta ɗauka ba huruminta ba ne shi yasa ma ba ta ce komai ba. Amma dai gaskiya da akwai matsala, tunda ai da ba a taɓa samun matsala irin wannan ba. ‘Haka ne, in sha Allahu za a duba kuma a ɗauki mataki.’ Alhaji ya faɗa.

    Suka ƙarasa tattaunawa Auwalu ya yi musu sallama ya tafi. Shi ma Mustapha ya miƙe ya sa Habib a gaba don su tafi, sai dai shi Habib ɗin ya nuna ba zai koma don ya fi so ya zauna a nan wajen Hajia. Alhaji ne ya saka shi a gaba da nasiha yana nuna masa gara ya zauna saboda ƙannensa, kada ya tafi ya barsu su kuma bai san me zai faru da su ba.

    Sai wajen ƙarfe tara sannan Hajia ta shirya suka kama hanya tare da Habib ɗin da Mustapha suka koma gidan. A cikin tashin hankali suka sami yaran, Nasreen da Shukra suna sanye da uniform ɗinsu; don sai da suka fara shirin makaranta sannan Naja ta sauko ta sanar da su ba za su makaranta ba Habib ya ɓata Abbansu kuma ya tafi nemansa.

    Babu wanda ya ji shigowarsu gidan saboda Mustapha a waje ya ajiye motarsa saboda Hajia tace yanzu za ta fito ya mayar da ita. Da sallama suka shiga parlor ɗin, Nasreen ce da Shukra suna zaune a parlor ɗin da flask ɗin shayi a gabansu da ƙaton bread. Sai dai sun kasa shan shayin sun yi tsuru-tsuru. Da gudu suka miƙe, Shukra ta faɗa jikin Habib tana dariya yayin da Nasreen ta matsa kusa da Hajia. Suka ƙarasa ciki suka zauna.

    Hajia tace ‘Ina Afaf? Nasreen tace ‘Tana ɗakinmu. ‘Antin fa da Rukayya? Nasreen ce ta sake sunkuyar da kai tace ‘Ba su sauko ba. Hajia tace ‘To ki je ki kirawo min ita ki ce ta zo. Shukra tace ‘Yanzu fa ta leƙo kuma tace kada wanda ya hau mata sama ya dame ta, ko menene a jira sai ta sauko. Hajia ta jijjiga kai, ta kalli Mustapha.

    Ya ɗan diririce sannan yace ‘Hajia tasowa za ki yi mu je saman ai. Ba tare da wani musu ba ta miƙe ta tasa Nasreen da Shukra a gaba tana biye da su yayin da Mustapha da Habib suke biye da ita. Anti Wiyya ce a zaune a kan kafet da kwanuka a gabanta suna cin abinci ita da Rukayya, yayin da Naja take zaune a kan kujera tana cin nata abincin suna hira.

    Da yake kicin a buɗe yake ana hango mai aikinta da goyon baby tana goge-goge. Shukra ce ta fara shiga tana surutu don haka a fusace Anti Wiyya tace ‘To sarkin tsurku, ba cewa aka yi ku zauna a ƙasan ba shi ne kika shigo kina….’ A lokaci guda kuma Naja tace ‘Ai sai na yi maganin wannan yar… Sallamar Hajia ce ta katse musu zantukan, ta ƙarasa ciki yayin da Shukra ta zagaye ta koma bayan Abbanta.

    Suka ƙarasa ciki suka zauna yayin da Naja da Wiyya suka diririce. Naja ta yi wuf ta miƙe ta kwashi kwanukanta tana cewa ‘Bari na wanko hannu.’ Ta nufi kicin cikin sauri. Ita ma Wiyya ta kwashi nata kwanukan ta miƙe tana cewa ‘Sannu da zuwa Hajia, bari na kawo miki abinci. Rukayya tace ‘Anti ban ƙoshi da naman ba.’ Ba ta ko saurare ta ba ta wuce kichin yayin da ita kuma ta tashi ta bi bayanta da sauri.

    Sai dai duk saurinsu kowa ya riga ya ga abinda yake cikin kwanukan nasu; farfesun kaji ne wanda suke haɗawa da burodi da shayi suna ci. Bayan sun zauna Hajia ta dubi Mustapha sannan ta dubi Nasreen tace ‘Nas ku ina naku naman na ga kuna cin gayan burodin. Ta yi darya tace ‘Ba a bamu ba, dama kullum abincin sama daban da na ƙasa har gara ma idan Abban yana nan.’

    Hajia ta sake kallo shi tace ‘Allah ya sauwaƙe. Naja ce ta dawo parlor ɗin ta zauna a kan kafet ta gaida Hajia, bayan ta amsa ta dubi Nasreen tace ‘Je ki kicin ki taya Anti Wiyya ta ɗauko wa su Hajia abinci. Hajia ta ɗaga hannu tace ‘Ki ce ta bar shi, ku bar shi ma, abincin da na ga bai isa an raba da yara ba ai ba zai isa har a ba wa baƙo ba. Ni na ci abincina ku bar shi na ƙoshi.’

    ‘A a Hajia ai akwai, su ma hawowa ne ba su yi ba nake jira Jummai ta gama wanke-wanke ta miƙa musu. ‘To me za su shigo su yi, su da za ki yi maganinsu. Ai sai dai kawai a cigaba da addua kada a wayi gari kin koro su daga gidan kamar yanda kika koro ɗan uwansu cikin dare.’ Hajia ta ba ta amsa.

    ‘Wallahi Hajia babu wanda ya koro shi. ‘Allah ne kawai zai gane gaskiya, amma dai ke ki ji tsoron Allah. Kin ba ni kunya, wallahi kin ba ni kunya! Ban taɓa zaton haka daga gareki ba. Gaba ɗaya mun zata zuwanki gidan nan zai sa yaran nan su sami kulawa ta musamman ashe ba haka ba ne. Ke da ‘yauwarki da ‘yayanki kuna sama kuna cin kaji yaran suna ƙasa suna fama da burodi.

    Kuma ma har sharaɗi aka kafa musu cewa kada su hawo su dame ki. Kamar dai ba gidan ubansu ba. Suka yi shiru kamar ruwa ya cinye su. Hajia ce ta karya shirun ta dubi Mustapha tace ‘Kai dai ba ka kyauta ba, yanzu rayuwar da kuke yi kenan? Su waɗannan da uwarsu ta mutu kun bar su a ƙasa kuna sama kuna jin dadi. To ka ji tsoron Allah. Ke ma kuma ki ji tsoron Allah.

    Bana jin sun taɓa ganin haka a wajen Khadeeja, ashe dama jira kike ku kore ta daga gidan ki cuzgunawa marayun Allah. Ta sunkuyar da kai kamar wadda za ta dungura. Habib yace ‘Ai tunda suka dawo daga Saudiyya aka hana su hawowa nan, ɗakinsu ma da komai nasu ya koma ƙasa.’

    Hajia ta dubi Mustapha duba na takaici har sai da ya sunkuyar da kansa cike da kunya. Ta miƙe tana cewa ‘Ai shikenan, amma tabbas ba zan bar wannan zaluncin ba. Kuma ko da kin ga kamar kin yi nasara to Allah yana kallonku gaban ɗaya. Yaran su ma suka miƙe, Hajia ta dubi Mustapha wanda kunya ta hana shi miƙewa tace ‘Za ka samu ka mayar da ni gida ko sai ta ba ka izini?’

    Ya miƙe kamar wanda aka tsikara. Naja tace ‘Don Allah Hajia ki yi haƙuri. Wallahi ba haka abubuwan suke ba rashin fahimta kawai aka samu wallahi ana kula da su. Ta dube ta tace ‘Allah ya sa, ai ni ma haka nake so. Sai dai kowa yayi don Allah ai ya sani ko, Allah kuma yana sane. Ta wuce yaran da Mustapha suka bi ta a baya suka fice.

    Har suka isa gida tana faman caccakar Mustapha a kan yanayin da ta gani a gidansa kuma tana tuna masa girman haƙƙin yaran nan a wuyansa da shi da matarsa. Ba shi da abinda zai gaya mata sai haƙuri kawai yake ba ta; shi ma ba ya jin daɗin yanda gidan ya koma tun bayan rabuwarsa da Khadeeja. Ba da son ranshi ba ta mayar da yara ƙasa kuma wannan raba abincin ya sha yin magana a kai.

    Amma ta iya abun ganin ido ne kawai, idan yana nan sai ta yi kamar komai normal amma da zarar ya fita sai ta tsawatarwa yaran kowa ya shiga hankalinsa. Abinci kuwa dama idan dai ba a gidan zai ci ba tabbas abincin da ake dafawa a sama daban kuma abincin da take ba wa mai aiki ta dafawa yaran daban ne. Duk wani daɗi a sama suke ci ita da yaranta da ‘yan uwanta su kansu yaran har sun saba.

    Ga shi ta hana su kula ubansu sosai, domin in dai yana saman nan ba ta barinsu su ganshi. Har sun gaji da yanda take musu sun haƙura sun ma daina cewa suna son magana da shi. Haka ya ƙarasa gidan ya ajiye Hajia a bakin gate ya dawo saboda ba ya son ya shiga ciki saboda ya san ba zai ji da daɗi ba a wajen Alhaji.

    Suna fita Anti Wiyya ta fito daga kitchen jiki a sanyaye, ta zauna kusa da Naja ta kama haɓa tana cewa ‘Ikon Allah, kin ji mutane ko? Ko motsin shigowarsu ba mu ji ba sai kace shiri. Ta taɓe baki ‘Hmmn! Su suka sani. Dama tafiya ya yi ya kai rahoto shi yasa ya bi dare su kuma ba su yi tunanin su kirawo mutane su sanar cewa ya isa can ba saboda sun shirya tsiya. A kansu zata ƙare in sha Allahu.’

    Ta miƙe kamar an tsikare ta tana cewa ‘Bari ki gani na haɗa kayana na bar gidan nan kafin ya dawo ya kore ni da kansa. ‘Haba Anti, saura sati biyu dama fa ki tafi tunda kin ce ba za ki yi min arba’in ba. Ki yi zamanki babu abinda zai yi.’ Ta faɗa tana gyara zama. Wallahi tafiya zan yi, da wanne idon zan kalle shi ya riga ya gama raina ni. Ina nan ina yagar kaza na bar masa yara suna fama da gayan burodi.’

    Ta marairaice ‘Anti idan kika tafi ma in ya dawo ai sai yace ba ni da gaskiya. Ta nufo ƙasa don haɗa kayanta tana cewa ‘Ku kwashe ƙalau amma ni da mijinki ba za mu sake haɗuwa ba in sha Allahu, ko a kwararo balle ma a gidansa. Tana ji tana gani Anti Wiyya ta fice ta bar mata gidan. Ba ta daɗe da fita ba Mustapha ya dawo.

    Yana shiga parlor ɗin ƙasa ya tarar da Afaf ta fito tana shan baƙin shayi da burodi yayinda sauran yaran suke zaune suna kallon TV. Bayan ya amsa sannu da zuwansu ya ƙarasa ya zauna a kusa da Shukra, ya kalli kofin shayin Afaf wanda ta ajiye a kusa da ita tana ƙoƙarin sake yago burodi. Yace ‘Ya kike shan baƙin shayi Yaya?’

    Tace ‘Um, babu madara a nan dama idan na yi canjin kuɗin makaranta ne nake siyo mana kuma yanzu ka ga ina hutu shi yasa ba ni da kuɗi. Takaici ya cika shi, yanzu da ransa da lafiyarsa madarar shayi a ce sai Afaf ta tara kuɗin makarantar da yake ba ta ta siya sannan za su sha. To wai ina kansa ya shiga hakan take faruwa a gidansa? Tunda yake a rayuwarsa bai taɓa ganin Khadeeja ta hana yaranshi wani abu da ya siyo ba, sai dai ma ya san lokutan da take sayen abu da kuɗinta su ci ita da yaran.

    To wai yaushe ma Khadeeja ta bar gidan? Ba a fi wata takwas ba fa da rabuwarsa da Khadeeja amma gidan duk ya zama haka? Ita da take zama cin abinci a tsakiyar yaran balle a ce ta ɓoye wani abu ta hana su. Ya bi fuskar yaran da kallo gaba ɗayansu babu wadda take da cikakkiyar walwala, tabbas yanzu ne za su ji nauyin maraicinsu.

    Shi kanshi sai ya ji ƙwalla tana neman kwace masa, sai da ya yi da gaske sannan ya mayar da ƙwallar. Ya dubi Nasreen yace ‘Nas ɗauko min kofi ni ma na sha shayin.’ Ta tashi ta shiga nan kichin ɗin ƙasan ta ɗauko masa tsohon kofin tangaran ta kawo masa da sugar a ‘yar roba. Ya kalli kofin duk ya dafe ya dubi Nasreen ɗin da ta ajiye kofin yace ‘Ki je sama ki dauko min wani kofin mai kyau.’

    Tace ‘Abba Anti Naja fa tace kada mu hau kuma wallahi idan na hau zagina za ta yi in na yi magana tace na mata rashin kunya, sai dai ko yaya Afaf ta je ta ɗauko. Haka ya karɓi kofin ba don ya so ba ya haɗa banƙin shayi ya sha tare da ragowar burodin da suke ci. Sai da ya gama sannan ya tashi ya haye sama domin ya shiryo ya fita aiki.

    Ta ji dawowarsa tunda ya shigo da motarsa, sai dai da ta ji shiru ta saka rai ya tsaya a wajen yaransa don ya ƙara jin abubuwan da za su gaya masa a game da ita. Don haka a parlor ya same ta tana ta cika tana batsewa ita a dole kada ya yi mata faɗa. A gajiye yake sannan ba shi da karsashin hayaniya da ita, don haka ko inda take bai kalla ba ya shige ɗaki ya fara shirinsa.

    A shirye tsaf ya fito ɗauke da jakarsa, tana nan zaune a inda ya bar ta. Ya ɗauke kai ya nufi ƙofa bayan ya amsa a dawo lafiyar da Rukayya ta yi masa. Ta miƙe ta nufo shi fuska babu walwala tana cewa ‘Ga abincinka can za ka fita ba ka yi breakfast ɗin ba. Ya kalle ta a fusace ba tare da ya daina tafiya ba yace ‘Abincin da kike hana yarana? Ni na ƙoshi ki kirawo ragowar ‘yan uwanki ku cinye.’

    Ta buɗe baki za ta yi magana sai dai kafin ta ce wani abu ya ci rabin ƙafar benen, tana nan tsaye kamar za ta haɗiyi zuciya ta jiyo ficewar motarsa daga gidan. Dole ita ma ta shirya ta fice ta tafi wajen aiki domin a hakan ma ta san sai an harare ta tunda ta makara.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Ɗaya

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Ɗaya

    Suna daga cikin na farko-farkon dawowa a alhazai. Tun kafin su baro masaukinsu ta gama magana da shi a kan ba za a ɗauko yara ba sai ta yi kwana biyar tana hutawa, don Rukayya ma tace kada a dawo da ita sai bayan sati biyu. Abokinsa ne ya ɗauko su daga airport ya kai su har gida, da yake ya saka Habib ya buɗe gidan an gyara tsaf suka sami ko ina.

    Da safe suka sauka don haka kafin su shiga gidan sai da suka yi order ɗin abincin rana. Sai can da yamma bayan sun gama hutawa sannan ya shirya ya wuce gidan Hajia. Nan ya zauna suka yita hira a wajen Hajia. Duk da ya gaya musu ba yau zai tafi da su ba amma Shukra ta kafe a kan ita a ranar take son ta bi su, don haka yace su shirya tare da su zai tafi.

    Sai bayan sallar magriba sannan Alhaji ya dawo, bayan sun gaisa suka cigaba da hirarrakinsu. Alhaji yace ‘Yauwa, ya wajen Khadeeja kuwa? Kun yi magana ne? Yace ‘A a ni ban neme ta ba kuma ba zan neme ta ba Allhaji, ita ce fa tace na sake ta kuma na saketan, ta je ta ɗana zaman gidan.’

    Alhaji ya ɗan ɓata rai yace ‘Kai! Ba a yi wa mata haka, idan jira kake ta neme ka to ba lallai ta neme ka ba gara ma ka je idan da wani abu ka yi wa iyayenta bayani su yi mata faɗa ka mayar da aurenta. Ya jijjiga kai ‘Alhaji ni ba inda zan je, idan tana son auren nata za ta neme ni tunda ai da kanta ta nemi sakin.’

    Haka Alhaji ya saka shi a gaba ya yi ta yi masa nasiha, daga baya ya yi musu sallama ya kwashi yaransa suka wuce. Ba shi kaɗai ba hatta yaran ma sai da suka gane ba ta ji daɗin dawowarsu a ranar ba, haka dai suka gaggaisa suka yi mata sannu zuwa kowa ya shiga harkarsa. Inda Allah ya taimake ta ma shi ne ya siyo musu abincin dare.

    Ta riga shi kwanciya saboda gaba ɗaya ba ta ma jin daɗin jikinta, sai da suka gama hira shi da yaransa sanan ya rufe gidan kowa ya tafi ya kwanta. Motsin shigarsa ɗaki shi ya tashe ta daga bacci, sai da ta bari ya gama shirinsa ya kwanta sannan ta gyara kwanciya tace ‘Kai da muka yi da kai ka bar yara sai mun huta shi ne ka taho da su?

    Ya gyara kwanciyarsa yace ‘To sun ce za su taho, su ma fa ba daɗin zaman suke ji ba a wani wajen kin san kowanne yaro ya fi son gidansu. Ta kula idan dai a kan yaransa ne ba zai saurare ta ba don haka ba tare da ta ce komai ba ta juya masa baya ta cigaba da baccinta; amma dai ta san tabbas dole ta ɗauki mataki don babu yanda za a yi ta bari ya kori kishiyarta kuma ya mayar da yaransa kishiyarta.

    Dole ta ɗauki mataki. Sai da ta yi sati da dawowa sanna ta je gidansu ta taho da Rukayya, don ko ‘yan gidan nasu ma da za su zo musu sannu da zuwa cewa ta yi kada a zo da ita don idan ta zo ba za ta yadda ta koma ba. Bayan ta gama hirarta a gidan ta wuce gidan Anti Wiyya.

    Nan suka zauna ta yi mata bayanin ayyukan da aka yi mata, sannan ta ba ta wasu layu guda biyu tace ‘Gasu nan hatimi ne aka rubuta da ayoyin Allah, ki sami waje ki ƙone su ƙurmus sai ki zuba masa tokar a miya. In dai ya sha miyar nan to ba zai sake yi miki musu ba. Wannan aikin bana haufinsa kamar yankan wuƙa ne sai dai idan ba ki aikata ba.

    Ta karɓa ta mayar cikin ledarsu ta kulle ta jefa a jaka tana cewa ‘Ai dai kin ce ayoyi ne ko? Tace ‘Wallahi ayoyi ne, ke malamin fa har almajirai gare shi suna karatun allo. Ai idan kin haihu za mu je ki gani da kanki idan har kina da wata matsala. ‘Hmm! Ai dole ma na yi Anti Wiyya, daga dawowarmu ya fara neman ya nuna min iyakata a kan yaransa, ga shi su baka isa ka saka su aikin komai ba sai dai kai ka ƙare a hidimarsu.

    Ai yau ɗin nan zan aikata wannan layun kowa ya shiga hankalinsa. Ko nan ma fa da zan taho shi so ya yi na taho da su wai saboda kada na bar su su kaɗai, ki ji don Allah sai kace wasu jarirai. ‘Ya zata ke ma Khadeejan ce. Suka yi dariya gaba ɗaya. Sai gefin magriba sannan ta ɗauko Rukayya suka dawo gidan. Tana zuwa ta ɗora abincin dare inda ta dafa tuwo miyar kuka.

    Tsaf ta haɗe tokar layun nan ta juye masa a miya ta juya komai ya shige, ta yi sa’a kuma ya sami tuwon nan ya yi masa cin ƙoshi. A hankali ta fara ganin kyawun aikin da Anti Wiyya ta yi mata. Cikin wata ɗaya da dawowarsu ta tattare kayanta ta koma sama part ɗinshi, ba ta son ta yi maganar part ɗin Khadeeja sai ta bari wata uku ya cika saboda kada ma ta tuna masa ya je ya dawo da ita.

    Yanzu ta samu idan suna sama shi da ita ta hana yaran hawa kuma ya kasa yi mata magana. Ta san bai ji daɗi ba don yana nuna mata a fuska amma wannan ba damuwarta ba ce, kuma idan shi ya zauna a ƙasan da zarar ta kirawo shi haka zai tashi ya bi bayanta su koma saman da shi da ita da Rukayya, sauran yaran suna ƙasa.

    Sai dare ya yi idan za su kwanta ne suke hawa saman da yake ɗakinsu yana can. Suna hawa sai ta kaɗa su su wuce ɗaki su kwanta. Tun ranar da ta koma gida take lissafi, duk da dai tana jini a lokacin amma dai sai da ta lissafa jini uku, kuma jiya ne ranar da ta fita daga jini na uku bayan rabuwarsu da Mustafa.

    Tana zaune a gefen ƙaramin gadonta wanda shi ne dai gadonta tun kafin ta auri Mustapha, ta rufe fuskarta da tafukan hannunta tana tunanin yanda rayuwarta za ta cigaba; tabbas ta ji daɗin rabuwa da Mustapha, ba ta yi nadama ba kuma ba za ta koma ba. Domin ko babu komai yanzu ne ta tabbatar tana cikin nutsuwa.

    Duk wani abu na kulawa da Hammad yake buƙata za ta iya yi masa don haka ba zama ta nemi Mustaphan da maganar Hammad ɗin ba saboda ma kada yace ta ba shi yaronsa. Fatan ta ɗaya Allah ya tabbatar mata da alkahiri a cikin rayuwarta ta nan gaba; duk da ba ta tunanin akwai namijin da za ta sake aure.

    Ba za ta yarda a sake yi mata yanda Mustapha yai mata ba kuma ba ta fatan ta zama dalilin da zai saka wani namijin ya mayar da matarsa kamar yanda Mustapha ya mayar da ita bayan ya ƙara aure. A hankali ta miƙe ta fito daga ɗakin. Ta ji daɗi da ta sami Baffa da Mommy a parlor suna zaune suna cin abinci. Bayan ta gaishe su ta dubi Baffa tace ‘Baffa ina so a debo min kayana na gidansu Hammad.’

    Ya ajiye cokalinsa yace ‘Ikon Allah, bai neme ki ba kenan? ‘Eh Baffa, duk da ma ko ya neme nin ba zan koma ba. Jiya ne na gama iddata ka ga auren ma ya ƙare kenan. ‘Haka ne, Allah ya sa haka ne ya fiye muku alkhairi gaba ɗayanku. Gobe sai ƙaninki ya shirya su je a kwaso miki kayan, ki yi masa bayanin abubuwan da za su kwaso. ‘To Baffa.’

    Mommy tace ‘To ya za a yi da Hammad? Ai dai ya kamata a yi magana da Mustaphan ya dinga turo abinda za a kula masa da yaron ko? Tace ‘Eh ba mu dai yi magana da shi ba, amma da bari na yi sai zai shiga makaranta tukunna. Baffa yace ‘A a tun yanzu zai ɗauki nauyin ɗan sa, ni zan neme shi in sha Allahu.’

    Mommy tace ‘Haka ne kam, ba sai daga baya ba a zo ana sa toka sa katsi. Suka ƙarasa hirarrakinsu sanna Khadeeja ta yi musu sallama ta tafi office. A mota suke tafe yana tuƙa su, zai sauke Naja a wajen aikinta sannan ya wuce. Wayarsa ce ta fara ringing, kusan a lokaci guda suka kalli screen ɗin wayar “Babe” shi ne sunan da ya yi saving lambar Khadeeja da shi tun kafin aurensu kuma rabuwarsu ma ba ta saka ya goge ba.

    To me ya mantar da shi Khadeeja ma da bai ko da kirawo ta a waya ba tun bayan dawowarsa daga aikin Hajji? Ko da yake ba mantawa ya yi ba jira yake ta kirawo shi ta ba shi hakuri idan ba haka ba ma ya ƙyale ta ta ɗanɗana zawarcin daga baya ya koma a sake ɗaura musu aure idan ta gane shayi ruwa ne. To menene take kiransa yanzun?

    Ko har zawarcin ya ishe ta ne? Wataƙila kuma ta ga tana daf da gama idda ne bai neme ta ba shi ne ita take nemansa ya zo a daidaita. Ya ɗauki wayar ya amsa sannan ya kara a kunnensa a daidai lokacin da ya kaucewa haɗa ido da Naja wadda take ta faman bin shi da kallo saboda ta san lambar wacece ya yi saving da sunan Babe.

    Babu wata alamar nadama ko kuma damuwa a muryarta, cike da walwalarta suka gaisa kamar babu wani abu na rashin daɗi da ya taɓa haɗa su. Bayan sun gaisa tace ‘Na gama idda jiya, so in sha Allahu idan babu damuwa gobe zan turo Ahmada za su zo su ɗebar min kaya na. kayan da suke bedroom ɗin kawai za a ɗauka tunda dama duk na sabon gida ne ka saka.

    Amma akwai food flasks ɗina a kitchen guda uku da kuma tea flask da za su haɗo min da su shikenan. Ina fatan babu wata damuwa. Sai da ya buɗe baki da niyyar ba ta amsa sannan ya gane yawun bakinsa ya riga ya ƙafe, ya kifta ido ya ɗan lalubo yawun bakin nasa sannan ya kalli Naja wadda take ta faman binsa da kallo kamar wata mayunwaciyar kura a yayin da ta hango nama yace ‘Ehhm, babu matsala. Um kin gama idda kenan?’

    ‘Eh, na gama jini uku a jiya. Idan ma an haɗa da jinin ɓarin da na yi jini huɗu kenan duka da shi kwana biyu ya yi ya ɗauke tun kafin sakin. ‘Oh haka ne, Allah ya kai mu, sai sun zo ɗin.’ Ya amsa. Da yake ranar aiki ce za su zo da wuri domin su same ka a gidan in sha Allahu.’ Ta faɗa sannan ta yi masa sallama ta ajiye wayarta.

    Ya mayar da tashi wayar ya ajiye a inda ya ɗauka ya mayar da hankalinsa ga hanya. Naja wadda take ta kallonsa tana jiran ya ba ta labarin abinda aka faɗa wayar ta gaji da kallonsa kuma bai yi alamar zai yi magana ba tace ‘Maman Hammad ce? A gajarce yace ‘Eh.’ Ba iya wannan amsar take son ji ba don haka tace ‘Wai menene?’

    Cikin yanayi na ƙosawa yace ‘Ta gama idda ne take so gobe da safe za a zo a kwasar mata kayanta. Ta gyara zama ta ɓata rai tana cewa ‘Ai na zata furnitures ɗin naka ne? A fusace yace ‘Eh, iya nata za a kwasar mata ai ko akwai naki a ciki ne kuma. Ta taɓe baki tace ‘A a, me ya yi zafi.’

    Daga haka har suka ƙarasa ya sauke ta babu wanda ya sake magana. Duk yanda ya so ya mayar da hankali a kan aikinsa hakan bai samu ba; zai iya cewa ba ya nadamar rabuwa da Khadeeja amma tabbas yau da ta gaya masa ta gama idda jikinsa ya yi sanyi. Zai yi kewarta, kuma ya ma ji a jikinsa kamar a gutsure wata tsoka daga jikinsa.

    Bai ma taɓa tunanin zai yi kewar Khadeeja haka ba amma ga shi kayanta kawai aka ce za a kwasa amma ya ji babu daɗi. Bai daɗe da shiga office ɗin ba ya lalubo wayarsa ya danna mata kira, kamar ɗazu yanzu ma muryarta cike take da walwala. Sosai ya kasa kunne yana ƙoƙarin ko gano wata alama ta damuwa a muryarta amma ji yake kamar ma an ƙarawa muryarta zaƙi.

    Bayan ta amsa sallamarsa tace ‘Um ka yi mantuwa ne? Kamar wanda aka farkar daga barci yace ‘No. Umm! Hammad fa? Ya kamata ya dawo cikin ‘yan uwanasa ai ko? A nutse tace ‘Eh haka ne, amma ka ga bai ƙarasa shekaru huɗu ba ma. Ina ganin nan da zuwa ya gama primary in sha Allahu sai ya dawo cikin ‘yan uwansa tunda tabbas ni na san kula da yaro akwai wahala, musamman da yake ka ga Antinsu ba zama take ba tana aikinta.

    Ina ganin ka bar min shi duk wani abu da yake buƙata in sha Allahu zan sanar maka, idan ya iya kula da kansa sai ya dawo gida. So yake ya ce mata hakan ba zai yiwu ba ko don ma ya ɓata mata rai, amma ya kasa. Tabbas yana son ganin yaronsa a kusa da shi cikin ‘yanuwansa amma kuma idan ya karɓe shi ba ya jin Naja za ta iya haɗawa da shi ta riƙe, don yanzun ma kullum cikin ƙorafi take a kan yara suna gajiyar da ita.

    Gara ma ya bari ta riƙe shi in Allah ya yi da ragowar zaman sa koma tare. ‘Um haka ne, to babu damuwa. Sai goben kenan. ‘Ok, Allah ya kai mu goben. Ba ta taɓa tsammanin Mustapha zai bar mata Hammad da sauƙi ba, don haka ma da ya yi saurin amincewa da maganarta sai ta ji wani daɗi marar misaltuwa; domin ta hango wahalar da zai sha idan ya koma gidan; zama zai yi kamar maraya.

    Tunda su Shukra su huɗu ne, Rukayya kuma uwarta tana gidan sai shi kaɗai wanda ba shi da uwa ba shi da ɗan uwa a gidan. A hankali ta mayar da wayar tata ta ajiye a kan teburinta. Ta sunkuyar da kanta ta share ƙwallar da ta taru a kwarmin idonta sannan ta zuba fuskarta a tafukan hannunta; ta tuno lokacin da suna soyayya da Mustapha kafin suyi aure. Wai ina soyayyar nan ta tafi ne?

    Ya barta ita kaɗai tana ta dakon soyayyarsa har tsawon shekaru takwas? Tabbas ta sha wahala a gidan Mustapha; ba wai wahalar jiki ba don wahalar jiki ta san abinda ta yi bai wuce abinda matar aure za ta yi ba. Sai dai wahalar zuciya da ta sha; kulawa da tausaya tare da ƙauna da zuciyarta take buƙata daga wajen Mustapha su ne ba ta samu ba.

    Ko su ɗin ma ta haƙra da su tana zama haka tunda ko babu komai tana kallonsa a matsayin mijinta kuma suna kwana tare. Amma daga lokacin da ya auro wata kuma ya ke ba ta kulawa da ƙauna wanda ita ya kasa ba ta daga lokacin ta yanke ƙauna daga zaman gidan Mustapha.

    Ba za ta ce ba ta jin zafin rabuwa da shi ba domin tabbas ta san ko babu ƙauna akwai sabo, amma tabbas ba za ta sake komawa gidan Mustapha ba. Domin ta yi sujjada ta roƙi Allah kada ya sake haɗa ta zaman aure da Mustapha. Da farko ta fara jin haushnsa amma daga baya sai ta ga jin haushin babu wani amfani; ko babu komai dole ta yi wa Hammad kara ta girmama mahaifinsa.

    Ta sake share ƙwallar da ta taru a kwarmin idonta, ta kalli ruwan hawayen da ta lakata a hannun nata; to kukan me take a halin yanzu? Ta zata ta gama kuka a kan Mustapha. Ta yi murmushi ta sake goge ƙwallarta; ta san ba za ta iya goge Mustapha daga cikin tarihin rayuwarta ba amma tabbas ba ta fatan sake rayuwa irin wadda ta yi a gidansa. Ta goge fuskarta ta fice ta nufi cikin studio inda za ta gabatar da labarai.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin

    Ba ƙaramin mamaki Hajia da Alhaji suka yi ba da Mustapha ya gaya musu ya saki Khadeeja. Shi kaɗai ya shiga da yaran don ita Naja ma cewa ya yi ta zauna a mota saboda kada taɓbata musu lokaci. Suna shiga yaran suka wuce cikin gida shi da Hajia da Alhaji suka tsaya a parlor yana musu bayanin abinda ya faru.

    Alhaji yace ‘To kai wane irin rashin hankali ne wannan? Ai don mace tace a sake ta ba a sakin nata. Zuciya ce ta kwashe ta kuma sai daga baya za ta zo tana nadama. Da ka sani ka ba rta da aurenta idan ma tafiyar za ta yi ta tafi idan ka dawo ƙalau za ka ga ta dawo.’

    A fusace yace ‘Alhaji yarinyar ce ta ƙure ni, ita kullum sai dai a yi mata yanda take so amma ita ba za ta yi yanda ake so ba? Ta je idan mutuwar aure daɗi ne ai ta samu sai ta ɗana ta fi shiga hankalinta. Hajiya tace ‘Ai shikenan tunda haka ta zaɓa. To yanzu ina Hammad ɗin da Rukayya? Ban gansu tare da ‘yan uwansu ba.’

    ‘Shi Hammad dama yana gidansu, ita kuma Rukayya gidansu ta kai ta. Ai shikenan, Allah ya sauwaƙe. Idan ka dawo a san yanda za a yi domin dai aure bai kamata ya mutu saboda kujerar hajji ba.’ Alhaji ya faɗa cike da nadama. Mustapha ya dubi Hajia yace ‘Mukullin gida yana hannun Habib in an jima Baba Sani abokina zai zo ya kai su shi da Afaf su ɗebo kayansu su rufo gidan.

    Idan sun dawo sai ya ba wa Alhaji mukullin gidan ya ajiye min. Akwai ATM card ɗina hannun Afaf idan ana buƙatar wani abu na kuɗi sai ta je ta ciro ta bayar. Ya yi musu sallama ya fice zuciyarsa cike da damuwa.

    Zuciyarta fayau ta fito daga gidan tana addu’ar Allah ya sa iyakar zamanta kenan da Mustapha tunda ta san saki ɗaya ya yi mata. Suna tsaye a bakin titi ita da Hafsa suna jiran mota ya zo ya wuce su a guje a tashi motar. Ta bi bayan motar da kallo tana murmushi; ta tuna lokutan da yake zuwa ya wuce ta a titi za ta tafi makaranta amma ba zai iya rage mata hanya ba.

    Ta yi murmushi ta kawar da kai. Jimawa kaɗan da wucewarsu ta sami mota, suka hau suka nufi gidan Mommy. Tana tura gate ɗin gidan Baffa ne a tsaye yake rufe motarsa, da alama dawowarsa kenan. Suna haɗa ido da shi hawayen da ta kasa fitarwa ya ƙwace, ta saki akwatin da take ja.

    Ahmad wanda yake tsaye a kusa da shi ya ƙarasa ya riƙe akwatin yayin da ita kuma ta ƙarasa ta faɗa jikin Baffa wanda yake bin ta da kallon mamaki. Ya rungume ta sannan ya dafa kanta wanda ta kwantar a ƙirjinsa yana cewa ‘Subhanallahi! Me ya faru da ku Khadeeja? Ta kasa magana sai kuka kawai take har da shessheƙa.

    Baffa ya fara shafa bayanta yana cewa ‘Ya isa haka, ya isa, ki gaya min me ya faru? ‘Ya sake ni.’ Ta faɗa a cikin shessheƙar kuka kamar mai raɗa. Take fuskar Baffa ta canza, ranshi ya yi matuƙar ɓaci. Yace ‘Mustaphan ya sake ki? Ta ɗaga masa kai. Ya sake shafa kanta cikin yanayi na lallashi yana cewa ‘To shikenan, ya isa haka.’

    Ya ja hannunta suka shige gidan; da yake Mommy tana ɗakinsa kai tsaye can ya wuce da Khadeeja. Mommy tana ƙoƙarin yi masa sannu da zuwa ta kula da Khadeeja, tace ‘A a, Baffa a ina ka samo wannan? Ya zaunar da ita a gefen gadonsa yace ‘Mustapha ya sake ta. ‘Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un! Saki kuma? A yau ɗin? Na ɗauka ce min kika yi yau jirginsu zai tashi?’

    Ta share ragowar hawayenta ta ajiye jakar hannunta sannan tace ‘Eh, kafin su tafi airport ɗin ne ya sake ni saki ɗaya. Lallai Mustapha, to me kika yi masa ya sake ki? Ko kuwa dai tsabar wulaƙanci ne ya ga gara ya sake ki kafin ya wuce ya yi ibada?’ Mommy ta tambaya tana daga tsaye.

    Ba ta yi tunanin wata amsa da za ta bayar idan an yi mata wannan tambayar ba, amma dai tana jin gara ta faɗi gaskiya don ma kada ya zo shi ya ba da amsa da ta bambanta da tata. Ta ɗaga fuskarta suka haɗa ido da Mommy sannan ta sunkuyar da kai. Murya kasa-kasa tace ‘Ni nace ya sake ni.’

    Saura kaɗan wayar da take hannun Mommy ta kufce ta faɗi, ta riƙe wayar sannan tace ‘Kika ce ya sake ki Khadeeja? Saboda rashin hankali ko saboda me? Baffa da yake tsaye a gaban wardrobe ɗinsa yana rataye babbar rigarsa ya zagayo ya zauna a kusa da ita yana kallonta yace ‘Dije me yasa kika ce mijinki ya sake ki?’

    Kafin ta yi magana Mommy tace ‘Saboda wulaƙanci mana, ko kuma saboda yace ba zai je da ita aikin Hajji ba sai ya je da amaryarsa. Kallonta kawai Baffa ya yi ta yi shiru, ta gyara tsayuwarta tana binsu da kallo. Ya dubi Khadeejan ya sake cewa ‘Deeje me yasa kika ce mijinki ya sake ki?’

    Ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta sake sunkuyar da kai tace ‘Baffa na gaji, wallahi Baffa ba ka ga zaman da muke yi a gidan nan ba. Tun kafin ya auri matarsa Baffa dama haƙuri nake, matsayina a gidan da kaɗan ya wuce matsayin ‘yar aiki. Kuma bayan ya auro ta ma ya kara tabbatar min da hakan; duk wani abu na walwala da jin daɗi da ita ake yi amma wallahi idan aiki ne da wahala Baffa ni zai kawowa kuma dole na yi.

    Ita kanta matar tasa haka yake saka ni na yi mata aiki babu sannu bare na gode. Shi yasa kwanaki da nace ba zan yi ba ya zo ya kawo maka ƙarata. Wallahi Baffa a lokacin sai da na yi wata takwas ina mata aikin gida da girki da komai kuma kullum shi a wajenta yake kwana.’Ta sake sunkuyar da kai ‘Na gaji Baffa, ba ya sona, wulaƙancin da yake min suna da yawa, gara na haƙura kawai shi yasa nace ya sake ni.’

    Ya kama hannunta wanda take wasa da shi a kan cinyarta ya kalle ta suka haɗa ido yace ‘To ya isa, kuka ya isa haka. Ki je ki kai kayanki ɗaki ki huta ma yi magana wani lokacin.’ Ta gyaɗa kai ta miƙe ta fice daga ɗakin. A fusace Mommy ta bi bayanta, cikin sauri Baffa yace ‘Zo mana.’

    Ta juyo a daidai lokacin da Khadeejan ta rufe ƙofa, ya nuna mata inda Khadeejan ta tashi ta zauna. Sai da ya ɗauki lokaci yana kallonta sannan yace ‘Ki bi ta a hankali tunda dai kin ji bayaninta. Ni da na ba shi aurenta ai ba ‘yar aiki na ba shi ba ko? In ya dawo ya zo ya yi bayani in ya so sai a san matakin da za a ɗauka.

    Shi a zaman aure ma wani lokacin hutu kawai mutum yake buƙata; kada ki je ki ɗaga mata hankali. Ki barta ta huta ƙarshenta in ya dawo sai dai ki ji da kanta tana gaya miki ya mayar da ita za ta koma. Da-Allah kada ki ɗaga mata hankali tunda dai ita ta kawo mutumin nan tace tana so ai ba laifi ba ne idan ta dawo tace bata son shi.

    Ki ba ta lokaci ta sami nutsuwa tukunna. Ta sauke numfashi sannan tace ‘To. Ta tashi ta fice ta bar shi a ɗakin. A nan gidan Hajia ya ajiye motarsa ya samar musu taxi wadda za ta kai su airport, ya shiga gaban mota ita kuma ta shiga baya. Suna kama hanya ta zaro wayarta ta lalubo lambar Anti Wiyya ta tura mata sako ta wahtsapp tana sanar da ita an saki Khadeeja.

    Bayan sun gama hirarrakinsu na murna da nuna jin daɗi Anti Wiyya ta turo mata saƙo kamar haka “Kije ki yi ta addu’a Allah ya sa kada kuna dawowa ya dawo da ita. Nan ma in sha Allah akwai wani malami da zan kai wa abin sadaka ya yi miki aikin da ba za ta taɓa dawowa gidan ba, kin ga kin ci gida se yanda kika yi.”

    Ta turo mata emoji na dariya ta rufe wayar, ta mayar da hankalinta kan hanya zuciyarta fes cike da fatan Allah ya sa kada ya dawo da Khadeeja tunda ya ce saki ɗaya ne; in ya so sai ta ji da yaran kawai. A hankali Khadeeja ta ba je kayanta a gida; ta sanar da Baffa ko da ya dawo ma ba za ta koma ba domin ko ya mayar da aurenta to kotu za ta kai shi ya sake ta.

    A haka dai aka bar maganar domin shi Baffa gani yake kamar idan aka ba ta lokaci ta huce za su yi wa kansu sulhu ita da shi. Tun Baffa yana sa rai zai ji kira daga wajen iyayen Mustapha sun biyo sawu har ya fitar da rai. Saura kwana biyu babbar sallah suna zaune a parlor shi da Mommy suna hira yace ‘Mutanen nan dai shiru, babu wanda ya biyo sawun Dije.

    Na san dai babu yanda za a yi su ce ba su san ya sake ta ba tunda ai za su ga ba ita ya barwa yaransa ko? ‘Uhm, ni abun har ya ishe ni ma wallahi. To amma ko tuntuɓarsu za ka yi ka ji, tunda ai ba za mu taru mu zama ɗaya ba ko?’ Mommy ta ba shi amsa. Ya yi ‘yar dariya yace ‘Babu wanda zan tuntuɓa tunda ai da zan ba su aurenta ba ni na tuntuɓe su ba su suka zo har gida suka tuntuɓe ni.

    Idan na tuntuɓe su haƙuri zan ba su ko me? Ni aka yi wa wulaƙanci aka saki ‘yata ko ma don wanne dalili ne amma kuma ni ake jira na yi magana? To su cigaba da zamansu kada ma su zo inda nake. A haka suka bar zance domin Mommy ta san in dai Baffa ne yanda ya kafe ba zai yi magana ba to tabbas ba zai yin ba.

    Su ma daga can gidansu Mustapha a tunaninsu Baffan Khadeeja ne ya kamata ya neme su don ya kamata idan ta je gida a bincika a ji, sai dai har aka shiga hidimar bikin sallah babu wanda ya neme su. Sai suka bar maganar kawai suna jiran Mustaphan ya dawo su ji ko shi ya yi magana da iyayen nata.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Tara

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Tara

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Tara

    Shirye-shiryen tafiya aikin Hajji sun kankama domin ana maganar saura sati uku alhazai su fara tashi. Duk wani abu da suke buƙata na kula da gida Mustapha ya tanada ya kawo musu, kuma ya yi mata bayanin abokinsa wanda dama ta san shi; shi ne zai kawo musu raguna kuma ya tsaya a yanka.

    Yanzu kullum sai yamma ta yi sai ya ɗauki Najan a mota su fice wai sun tafi bita, haka ta zuba musu ido tana ta ba wa kanta haƙuri. Gaba ɗaya maganar tafiyar ta fita daga ran Khadeeja, kuma Mustaphan ma gaba ɗaya ya fice mata daga rai; ji take yi kamar matsayinta a wajensa bai wuce na mai aiki ba.

    Zuwa yanzu ta san wanda ma bai san halin da suke ciki ba ya san Naja tana da ciki domin tara yawunta ya ƙaru kuma ta yi fari tas irin na masu ciki. Sai dai har yanzu ita Khadeejan ba ta sanar da Mustapha cewa ta san Najan tana da ciki ba. Sai shirye-shiryensa yake yi yana zuwa sallama da mutane domin Hajia ta gama gayawa kaf dangi Mustapha zai tafi Hajji da matarsa.

    Danginsa da na Naja sai zuwa suke sallama, duk wanda ya zo sai ya cewa Khadeeja Allah ya kirawo ‘yan baya. Wannan kalmar ba ƙaramin ɓata mata rai take yi ba, amma haka ta share ta kawar da kai. Tun jiya ba ta jin daɗi sai dai ba ta gane me yake damunta ba, haka take ta fama. Da yake ba ita ce da aiki ba kuma Hammad baya nan haka ta wuni a kwance.

    Daf da magriba ta fara gane abinda yake damunta; mararta ce take ciwo ga wani amai da yake taso mata amma ya ƙi fitowa. Haka ta sha panadol ta shige ɗakinta ta kwanta. Wajen 9pm Mustaphan ya shigo ɗakin domin sanar da ita ya dawo kamar yanda ya saba. Har ya juya zai fita ya ɗan tsaya yace ‘Wai ya na ganki a kwance ne? kamar ba ki da lafiya.’

    ‘Uhm, mara tace take ɗan ciwo.’ Ta amsa a gajiye. ‘Ok, Allah ya sauwaƙe. Ko kina buƙatar wani abu? Tace ‘No ina jin zai daina don na ma sha panadol. Ya sake yi mata sannu sannan ya juya ya fice. Can wajen 10:30pm ciwon ya matsa mata, tun tana daurewa har ta kasa. Ta lalubi wayarta ta kirawo shi, ba tare da ɓata lokaci ba ya shigo ɗakin nata.

    Kafin ya shigo ma ta riga ta shige banɗaki saboda yanda take jin kamar za ta yi kashi, kafin ta ƙarasa toilet ɗin abinda yake shirin fitowa daga jikinta ya riga ya fito sai jini da ya biyo baya gaba ɗaya da aman da ya tokare mata ƙirji. A tsugune ya same ta a banɗakin, ya ƙarasa da sauri ya duba halin da take ciki. Ya kama ta ta miƙe sannan ta ƙarasa ta zauna a kan toilet.

    Tace ya jira ta ta wanke jikinta sai su je asibiti. Nan da nan ta wanke jiki ta gyara sannan ta tattare zanin nata da bainda ya fita daga cikin nata gaba ɗaya ta saka a leda sannan ta fito ta shirya suka kama hanyar asibiti. Babu wanda ya yi magana sai shi da yake mata sannu lokaci zuwa lokaci; a haka har suka isa asibitin.

    Ba tare da ɓata lokaci ba likita ya duba ta kuma ya tabbatar da cewa cikin jikinta ya fice gaba ɗaya, don ko wankin ciki ma ba sai an yi mata saboda komai ya fice. Aka rubuta mata magunguna aka sallame su. Tun a mota ta gane Mustapha bai ji daɗin zubewar cikin ba, duk da ita ta fi shishiga damuwa da zubewar cikin; amma dai ta kula ba haka ya yi ba wancan lokacin da ta yi ɓari.

    Har yanzu tana jin ciwon mara don haka ba za ta iya surutu ba. Bayan sun dawo gida ta haye samanta ta sake yin wanka sannan ta sha magungunanta ta saka Hafsa ta haɗa mata indomie da shayi mai kauri ta zauna ta ci. Sai da ta ci ta ƙoshi sannan ta kirawo Mommy da Yaya Mama ta sanar da su.

    A daren Momy ta so zuwa sai da Khadeejan ta hana ta ta sanar da ita cewa ta sami lafiya su bari da safe sa zo; don haka suka haƙura. Can wajen ɗaya saura ya same ta a ɗakin; tana kwance a gefen gado tana shirin yin bacci. Ya zauna a gefenta yace ‘Sannu. ‘Yauwa. Ta amsa tana daga kwance.

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, ta san da zance a bakinsa don haka ta yi kasaƙe tana jiran ta ji me zai ce. Jimawa kaɗan ya gyara zama kamar wani mara gaskiya yace ‘Um wai ni me ya faru ne? Me ya kawo wannan miscarriage ɗin? Ko wani abun kika sha ne? Ta yi ‘yar dariya tace ‘Babu abinda na sha, Allah ne dai ya kawo kamar yanda ya kawo wancan.’

    Ya ɗan yi jim yace ‘Allah ya sauwaƙe. Ya sake yi mata sannu sannan bayan ya tabbatar babu abinda take buƙata sannan ya fice ya bar ta. Washe gari tun da safe Mommy da Yaya Mama suka zo, nan suka zauna suka zube mata kayan dubiyar da Baffa ya aiko mata. Mommy ta ji daɗi yanda ta ganta ta riga ta miƙe kamar ma ba daren jiya ta yi ɓari ba, sai kai wa da kawowarta take yi ana hira da ita.

    Har sun fara shirin tafiya suna zaune Yaya Mama tace ‘Kin ga idan dai ciki ne zai sa a fasa tafiya da ke ai yanzu sai a ba ki kujerarki ko. Ta yi dariya tace ‘Dama kujera ba tawa ba ce, babu ruwan ciki niyyar ba ni ne ba a yi ba. Mommy ta dafa ta tana ɗan zare ido tace ‘Khadeeja in ce ko dai ba wani abu kika sha kika fitar da cikin nan ba saboda kujerar Makka.’

    Ta ɗan zaro ido ta kalle ta suka haɗa ido tace ‘Mommy! Me ya yi min zafi? Wallahi babu abinda na sha, sai kace wata marar hankali? Ai na gaya miki fa ba ciki ne ya sa ba zai ba ni kujerar ba kawai haka ya yi niyya, yanzu kuma ɓarewar cikin ba za ta sa ya fasa tafiya da ita ba. Ni ce kawai ba za shi da ni ba. Yaya Mama tace ‘Haba Mommy, a kan wata kujera za ta ɓarar da ciki?

    Ta gyara zama ‘To ai abun naku ne sai a hankali. Suka ƙarasa hirarrakinsu suka yi mata sallama suka kama hanya. Ta zauna tana tunanin dalilin da yasa Momy za ta yi wannan tunanin; to ko tunanin da Mustapha ma ya yi kenan yake tambayarta me ya faru bayan sun dawo daga asibiti? Allah ya gani babu abinda ta sha, cikin nan ma ba ta taɓa kawo masa zubewa ba kuma ko da wasa ba ta so hakan ba.

    Kawai dai Allah ya yi ikonsa ne kamar yanda ya yi a wancan karon, kuma ta san shi ne zai fitar da ita daga duk wani zargi da zai iya tasowa. Kujerar Makka ma idan dai Mustapha ne zai ba ta kam ba ta so ta san Allah zai hore mata ta je tunda ita ma tana kan neman kudinta.

    Can da yamma su Hajia suka shigo ita da Yaya Jidda da ‘yan matanta. Ba ta san da Hajia suka shigo ba don haka ta yi banza da su tunda ta jiyo su a wajen Naja. Jimawa kaɗan suka hawo saman gaba ɗaya; ta sauke su a nan parlor ɗinta ta kawo musu ruwa da lemo, suka zauna suka yi mata dubiya da jaje. Suna cikin hirarrakinsu Mustaphan shi ma ya shigo ya zauna aka cigaba da hirar yana sa musu baki lokaci zuwa lokaci.

    Yaya Jidda ta dube ta tace ‘Alhazai dai sun kusa tashi balle ma a ce za a canza a ba ki kujera tunda cikin da ya hana ya fice, ko ka canza ne Mustapha? Ya kalle ta sannan ya kalli Khadeejan yace ‘A a ai an gama wannan maganar, ita za ta zauna da yara idan Allah ya kai mu shekara mai zuwa sai a je da ita. Hajia tace ‘E ai an gama wannan maganar.

    Allah ya ba ki lafiya ya kawo wasu yaran masu albarka. Ita Najan sai su je kamar yanda aka tsara. Ita dai tana zaune a tsakiyarsu amma ba ta iya ce musu komai ba; to kenan su ma zarginta suke yi da zubar da cikin ko me? To me Mustaphan ya gaya musu har suke mata wannan zargin? Sai da suka gama hirarrakinsu sannan suka yi mata sallama suka tashi suka fice.

    Bayan sallar Magriba Mustaphan ya same ta a ɗakinta tana zaune a gefen gado, bayan ta amsa sallamarsa ya karasa ya zauna a gefenta. Ta yi masa sannu da zuwa ya amsa suka zauna suka ɗan yi shiru, jimawa kaɗan ya kirawo sunanta. Bayan ta amsa ya kakkafe ta da ido sannan yace ‘Wai ni me kika yi ne cikin nan ya zube, ko wani abun kika sha saboda ya zube mu tafi da ke aikin Hajji.’

    Ta yi ‘yar dariyar takaici sannan tace ‘Mustapha ban zubar da ciki ba, domin kujerarka ta maka ba ta isa ta saka ni na zubar da ciki ba. Kamar yanda Allah ya kawo wancan cikin ya zube ba tare da na yi wani abu ba wannan ɗinma hakan ce ta kasance. Yace ‘To ai kin ce wancan wahala ce da aiyuka suka yi miki yawa ya sa ya zube, ko ba haka kika ce ba? Wanna kuma na ga babu wannan ko?

    Ta gyara zama ita ma ta kakkafe shi da ido tace cikin zafin rai tace ‘Mustapha wai ba ka ji me nace ba; ban zubar da ciki ba kuma kujerar Makka ba ta isa ta sa ni na aikata hakan ba. Na riga na san ba ka yi niyyar zuwa da ni Hajj ba domin lokacin da kake cewa ina da ciki ba za ka je da ni ba ita ma Najan cikin ne da ita. Ka dai zaɓi matarka wadda kake so ka tafi da ita ni kuma ‘yar aikin gidanka ka bar ni na kular maka da gida da yara kamar yanda ka saba.

    Idan ma kai ne ka gayawa ‘yan uwanka wannan maganar har suke yar min da magana to ka koma ka gaya musu ƙarya ne. Ya miƙe a fusace ‘Daga an tambaye ki kuma shi ne za ki yi min rashi kunya kamar yanda kika saba saboda ke ba a gaya miki gaskiya ko? Wannene rashin kunyar a ciki; ganewa da na yi cewa ka yi rashin adalci wajen zaɓar matar da za ka je da ita hajji ko kuwa gaskiyar da na gaya maka?’

    ‘Mtsewwwww!’ Ya ja dogon tsaki ya miƙe a fusace ya fice daga ɗakin. Ta zuba fuskarta a tafukan hannayenta, so take hawayenta ya fita ko za ta samu ta ji sanyi a ranta amma hawayen ya bushe ƙyamas. Ƙirjinta har zafi yake saboda yanda zuciyarta take turiri; Mommy ce ta fara yi mata wannan zargin ga shi yanzu Mustaphan ma da shi da ‘yanuwansa suna zargin ta zubar da cikin ne don ya je da ita Hajji.

    Tabbas Allah sai ya bi mata haƙƙinta. Haka ta kwanta zuciyarta na mata zafi saboda takaici; ta so ta kirawo Mommy ta gaya mata ko za ta sami salama a ranta, to amma hakan ba zai yi mata wani amfani ba. Tunda Mommy ɗin ce ta fara yi mata wannan zargin. Ta sake fashewa da kukan takaici ta gyara kwanciyarta; yau ita ce da kwana amma ta san yanda Mustapha ya fice daga ɗakin nan wataƙila sai dai idan ya dawo daga aikin hajji sannan ya waiwaye ta.

    Ranar Laraba aka kirawo su Mustapha, jirginsu zai tashi ƙarfe biyar na yamma don haka aka ba su shawara su kasance a cikin airport ɗin tun kafin azahar. Sun gama haɗa kayansu shi da Najan kuma ya riga ya sanar da Khadeeja, ya danƙa mata duk wani abu da take buƙata don kula da gidan. Wajen ƙarfe sha ɗaya yana zaune a parlor ɗinsa shi da yara Khadeeja ta fito daga ɗakinta ta shige kitcen don ɗora abincin rana.

    Ya tsallake yaran ya bi bayanta ya tsaya daga ƙofar kitchen ɗin ya rungume hannuwansa a ƙirji sannan yace ‘Kada fa ki dafa abincin da ni yanzu za mu wuce airport, ki dafa ke da yara kawai. ‘To.’ Ta amsa murya ƙasa-ƙasa. Ya kula tunda suka yi maganar zubewar cikinta take son ta-da masa fitina shi kuma ba zai saurare ta ba, fata yake kawai Naja ta gama haɗa kayanta su fice su bar mata gidan kafin ta takalo rigima. Don haka ya juya ya koma cikin yara ya zauna.

    Har ta ɗauko tukunya za ta ɗora shinkafa sai kuma ta fasa, ta ajiye tukunyar ta fito daga kitchen ɗin ta koma ɗakinta. Tana shiga ta wuce gaban mudubi ta ja kujerar ta zauna; ba ta san me ya sa ta fasa ɗora girkin ta zo ta zauna ba. Kamar dai tana buƙatar wani wanda za su yi magana ne amma ta rasa wanda za ta gayawa damuwarta ya fahimce ta.

    Ta ɗaga fuskarta ta kalli kanta a cikin mudubin, ta yi wa kanta murmushi sannan ta sake sunkuyar da idanuwanta. Yanzu haka za ta cigaba da rayuwa a gidan nan a matsayin ‘yar aiki? Tunda matsayinta bai wuce hakan ba, duk wasu alamu sun nuna. Mustapha ya tabbatar mata ba zai taɓa iya yi mata adalci ba tun ma tana ita kaɗai matarsa balle yanzu da ya haɗata da wadda yake ƙauna.

    Ta sake daga ido ta kalli kanta a mudubin; to wai zaman me take a gidan Mustapha ne? Shi dai ya gama nuna mata ba zai taɓa canzawaba; duk wani abu da yake yi mata a halin yanzu za ta iya yi wa kanta. Buƙatar aure ce kawai wadda dama sai ya gama dama yake zuwa wajenta tunda ta daina bin shi ɗakinsa. Ta yanke ƙauna daga samun adalci a wajen Mustapha komai yawan ƙaunar da za ta nuna masa da kulawarta ga ‘yayansa.

    Ta tabbatar shi ba zai iya nuna mata ƙauna da kulawa ba; wataƙila sai dai idan ana ƙwatan soyayya ta ƙwata ta ƙarfin tsiya daga wajen Mustapha; to idan sai an ƙwata kuma ya koma ba so ba. Ta ja gwauron numfashi, ta zuba fuskarta a tafukan hannayenta, ɗumin hawayenta ne ya sa ta ɗaga fuskar tata ta kalli hawayen da ya ɗiga a hannuwanta.

    Ta jijjiga kai tana murmushi a lokacin da hawaye yake gangarewa a kumatunta; ta gaji, ba za ta iya ba, ta gaji da wannan kokawar, ta gaji da kokawar ƙwatowa kanta mutunci da so a wajen Mustapha, ta gaji ba za ta iya cigaba ba. Ta miƙe kamar wadda aka tsikara ta nufi gaban wardrobe, ta sauke akwati ta fara zuba kayanta. Ba za ta iya cigaba da wannan rayuwar ba, gara kawai a yi ta ta ƙare.

    A hankali ya turo ƙofar ɗakin ya shigo da sallama, fuskarta fayau kamar ma farinciki take. Ta dube shi ta amsa sallamarsa ta cigaba da jera kayanta a cikin akwatin. Ya dube ta da mamaki yace ‘Ya na ga kina haɗa kaya, ko wardrobe ɗin kike gyarawa? Ta ɗan tsaya da zuba kayan ta kalle shi tace ‘No ba gyarawa zan yi ba, gidan mu zan tafi.’

    Mamakinsa ya ƙaru, ya kasa matsawa kusa da ita ‘Ban gane gidanku za ki tafi ba bayan yanzu za mu tafi, shigowa ma na yi na gaya miki ki fito ku yi sallama da Naja za mu wuce. Ta rufe akwatin ta zuge sannan ta juya cikin wardrobe ɗin ta ɗauko jakarta ta sake ajiyewa a kan gadon. Ta kalle shi tace ‘Ka ba ni minti biyar na ƙarasa haɗa kayana na fita sai ka rufe gidan gaba ɗaya don ni ma gidanmu zan tafi.’

    Ya ɗan fara fusata ya matsa ya sha gabanta yana cewa ‘Ba na son wulaƙanci Khadeeja, wai ke me yasa ne duk lokacin da mutum yake cikin uzuri yake so ki yi masa wani abu sai kin yi fitina ne? An gama magana da ke amma yanzu saboda kina so ki sa mu yi missing flight za ki fara maganar za ki tafi gida. Ta yi murmushi ta ɗaga kai ta kalle shi tana cewa ‘In sha Allahu wannan ita ce fitina ta ƙarshe da zan yi maka Mustapha, daga ita ba zan sake ba.

    Gidanmu zan tafi Mustapha saboda na gaji da aurenka, kuma na gama aurenka daga yau. Za ka iya sakina yanzu ko kuma duk lokacin da ka sami natsuwa ka rubuta min takardar sakin ka aiko gida; amma ba zan sake zama a matsayin matarka ba. Gaba ɗaya yawun bakinsa ƙafewa ya yi saboda bai taɓa zaton Khadeeja za ta iya faɗa masa haka ba.

    Ya sake ta! Kuma a wannan lokacin; ya kalle ta ya sunkuyar da kai, jimawa kaɗan ya sake kallonta sannan yace ‘Saboda kujerar Makka kike so ki kashe aurenki Khadeeja? Kujerar da na gaya miki next year da ke za a tafi. Tukunna ma kin san hukuncin matar da ta nemi saki a wajen maigidanta ba tare da wani dalili ba?

    Ta jijjiga kai tana murmushi a daidai lokacin da ƙwalla ta faɗo daga idonta, ta share ƙwallar sannan tace ‘Ko ɗaya, kujerarka ba ta kai ta ɗaga min hankali ba tunda dai ƙasar Makka ta Allah ce ba taka ba. Alhamdulillahi ma kace wadda ta nemi saki ba tare da dalili ba; don ni ina da dalili kuma Allan da ya halicce ni ya fi ni sanin dalilin. Amma tabbas yau zan bar gidanka da aurenka Mustapha.

    Ya ja baya ya sake ƙare mata kallo, yace ‘Kin san me kike faɗa kuwa Khadeeja? Please idan wasa kike ki bari kada ki saka mu yi missing flight. Ta yi ‘yar dariya yayin da ta ware hijabinta ta saka tana cewa ‘Ba wasa nake ba, amma dai kana da zaɓi. Ka sake ni yanzu ko kuma ka tafi idan ka dawo ka rubuta min takardar ka aiko min gida.’

    Ta kewaye shi ta ɗauko jakarta daga kan gadon ta nufi gaban mudubi. Yana tsaye mamaki ya hana shi magana. Yana ɗaga kai idonsa ya sauka a kan agogon bangon yake kafe a saman ɗakin; 12:52pm agogon ya nuna; shi da aka cewa su zama suna cikin airport kafin azahar. ‘Mtseww!’ ya ja ɗan gajeran tsaki sannan ya fesar da iska daga bakinsa.

    ‘Khadeeja yanzu ya kike so na yi da yaran bayan mun gama magana da ke? Kuma me na yi miki da har za ki riƙe a matsayin hujjar da ta saka za ki ce na sake ki? Yara kam ai yanzu ba matsalata ba ne, duk yanda ka yi da su daidai ne. Ni dai zan tafi, yanzu in sha Allah. Ta sauke akwatinta ta fara ja tana nufin ƙofar ɗakin. Ya bi bayanta da kallo; to me ya yi mata da har za ta ce ya sake ta a wannan lokacin?

    Anya kuwa ta san menene zawarci? Kawai saboda baƙin cikin ba da ita zai fara tafiya aikin Hajji ba? Ko ma me take nufi ya kamata ya cika mata burinta, wataƙila kafin ya dawo ta dawo hayyacinta kuma ta gane mahimmancin aure a rayuwarta. In ya so idan ya dawo da ita sai ta haƙura ta zauna tunda dai shi bai ga wani abu da ya yi mata ba.

    Tana daf da ƙarasawa bakin ƙofar yace ‘Khadeeja. Ta juyo ta ɗan tsaya ‘Ki je na sake ki saki ɗaya. Ta yi sauri ta juya fuskarta saboda kaucewa haɗa ido da shi; duk da ita nema kuma da yaƙinin zai aikata haka amma sai da fitar kalmar ta yi mata ciwo. Ta sake juyowa cikin murya ƙasa-ƙasa tace ‘Nagode.’

    ‘Za ki yi nadamar rabuwa da ni Khadeeja.’ Ya faɗa a gajarce. Ta kalle shi ta yi murmushi sannan ta kawar da kanta ta faki idonsa ta goge ƙwallar da ta taru a kwarmin idonta. Bugun ƙofa ne ya katse su da Shukra tana cewa ‘Abba Anti tace za ku makara fa. ‘Um, gani nan zuwa.’ Ya amsa daga cikin ɗakin.

    Ya wuce Khadeejan ya buɗe ƙofar ya fice. Ta bi bayansa janye da akwatinta. Shukra ta tsaya a gefenta tace ‘Anti ke ma har da ke za a tafi? Ta kama hannunta tace ‘A a ni gidanmu zan tafi ba da ni za a tafi ba. Gidan Mommy? To da mu za ki tafi? Ta tambaya da mamaki.‘Eh, gidan Mommy zan tafi amma ba da ku zan tafi ba. Abbanku zai gaya muku wadda zata zauna da ku.’

    Gaba ɗaya yaran suka zuba mata ido suna ƙoƙarin gane me take faɗa. Ta ƙwalawa Hafsa kira ta ba ta umarni ta haɗa kayanta su tafi gida. Ba tare da ɓata lokaci ba ta juya. Ta dubi Naja wadda take zaune tana binsu da kallon mamaki tace ‘Maman Rukayya sai kun dawo, Allah ya amsa ibada Alah ya maimaita mana. ‘Amin.’ Ta amsa a gajarce sannan ta dubi Mustapha tace ‘Ban fa gane ba, me yake faruwa ne?’

    Kafin ya ba ta amsa tuni Khadeeja ta ja akwatinta ta fice daga parlor ɗin. Shukra wadda ta ƙarasa ta faɗa jikin Abbanta ta rushe da kuka; saboda ta kasa fahimtar me yake faruwa su da aka ce za a yi tafiya har Abbansu a bar su da Anti kuma Antin ta fara tafiya. Ya dubi Naja yace ‘Cewa ta yi na sake ta kuma na sake ta, tunda ita ta nema.’

    Ta ɗan firgita ta dafe ƙirji, ba ta san lokacin da yawun da yake bakinta ya wuce ba tace Saboda me? Kai kuma ka biye mata? Saboda baƙin cikin zan tafi dake Hajji ban tafi da ita ba.’ Ya faɗa cike da ɗacin rai. Ya ƙarasa ya zauna a kan kujera a jigace kamar wanda aka tura. Sukayi cirko cirko suna kallon shi. Habib ya shigo a guje ko sallama bai yi ba, yana cewa ‘Abba na ga Anti tafi. Me yake faruwa ne? Waye zai zauna da mu?’

    Ya miƙe a jigace yana cewa ‘Maza kowa ya ɗebo kaya ko kala ɗaya ne mu wuce, sai na ajiyeku gidan Hajia. In ya so ko gobe sai ku dawo da Yaya Jidda ku ɗebi kaya. Antin ta tafi. Ya fice ba tare da ya saurare su ba Naja ta rufa masa baya. Nasreen ta kalli Habib ta kare gefen bakinta kamar me raɗa tace ‘Ya sake ta. Ya zaro ido zai yi magana suka jiyo muryar Abbansu daga ƙafar bene yana cewa ‘Maza fa ku sauko. Suka miƙe gaba ɗaya suka shirya suka fice.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Takwas

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Takwas

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Takwas

    Kwanci tashi sai da Khadeeja ta kwashe shekaru biyu tana aiki a gidan rediyon nan a matakin internship sannan aka sami gurbi aka ɗauke ta cikakken aiki, aka saka mata albashinta Naira dubu saba’in.

    Ba ƙaramin daɗi ta ji ba da samun wannan ci gaban domin tun da ta fara service ya zama wasu hidimomin nata ita take yi wa kanta kamar kayan shafe-shafe, turare wani lokacin ma har da sutura. Ba ta sani ba ko haka yake yi wa Najan ma tunda ita ma tana da albashi ko kuma ita kaɗai yake yi wa hakan.

    Sai dai ba ta da lokacin da za ta bincika ko kuma ta tambaya don haka take rayuwarta yanda ta ga za ta iya. Afaf ta shiga Jami’ar Bayero ta Kano inda take karantar Computer Science yayin da Habib yake SS3 yayin da Nasreen take JSS3 ita kuma Shukra tana primary 5.

    Zuwa yanzu duk baƙon da ya yi kwana ɗaya a gidan zai gane cewa gidan ya kasu kashi biyu; Shukra da Halifa waɗanda su ‘yan ɗakin Khadeeja ne da kuma Afaf da Nasreen waɗanda su ‘yan ɗakin Naja ne. Ko a wajen tarbiyya ‘ya’yan ɗakin Khadeeja sun fita daban da ‘yayan ɗakin Naja.

    Domin ita Khadeeja tarbiyyar take ba su da kulawa saboda Allah kamar yanda take yi wa Hammad, ita kuma Naja hankalinta yana kan yanda za ta ƙwace gida ta mallake maigidan don haka duk abinda zai saka shi farin ciki shi da yaransa shi take yi; ko da kuwa abun ba daidai ba ne.

    Lokuta da dama idan ta je wajen malamanta tana samu ta fara juya Mustapha, sai dai abun bai fiya daɗewa ba. Da zarar ta fara samun yanda take so sai kuma ta sake rasa kan maigidan nata. Ta yi iya bakin ƙoƙarinta ganin ta inda za ta samu ta haɗa shi faɗa da Afaf amma ta gagara; saboda son da yake yi wa Afaf ba kaɗan ba ne. Kuma kusan duk wani abu da zai yi to da Afaf yake shawara.

    Haka aka yi a farkon shekarar nan da zai canza mota; da kansa yake faɗa Afaf ce ta zaɓar masa motar bayan ita ba ta ma san zai canza motar ba sai da aka kawo motar gidan. Haka kuma aka yi da zai canza fentin gidan; Afaf ce ta zaɓi wanda take so aka yi, sai daga baya matan gidan suka ji labari.

    Lokuta da dama Naja ta so su haɗe kai da Khadeeja ko da su samu su ƙwaci Mustapha daga hannun ‘yayan ne, amma ba ta sami haɗin kai ba. Domin har yanzu zaman nasu dai babu yabo babu fallasa. Shi yasa ma Najan take wa Khadeeja kallon ba ta san me take yi ba saboda yanda ta bari yara suke controlling miji.

    Ita kuwa Khadeeja ba ta taɓa ɗaukan alaƙarsa da yaransa a matsayin matsalarta ba, matsalarta ɗaya da shi rashin adalcin da yake nuna mata tsakaninta da Naja. Idan dai abun a nuna kulawa ne da ƙauna to Naja yake nunawa, amma idan abu ne wanda za a yi masa hidima shi da yaransa to sai yace a kai wa Khadeeja.

    Duk wani ƙoƙari da za ta yi ta ga ya nuna mata so da ƙauna ta yi amma abun ya ci tura; har ta gaji ta zuba masa ido. Lokuta da dama idan ta yi magana sai dai ya dinga ƙoƙarin nuna mata cewa ya fi sonta kuma ya fi trusting ɗinta shi yasa yake saka ta hidimarsa da ta yaransa. Ta gaji da jin wannan tatsuniyar shi yasa ma ta haƙura ta daina ƙorafi; kawai dai duk abinda za ta yi za ta yi, abinda ba za ta yi ba kuma haka za ta zuba masa ido ya ƙaraci barazanarsa amma ba ta yi.

    Haka rayuwarsu ta cigaba.——–

    Tun kafin ta yaye Hammad al’adarta ta dawo, don haka kai tsaye ta tafi asibiti ta karɓo ƙwayoyin family planning; ko Mustaphan ma ba ta gayawa ba sai da ta karɓo. Ba wai haihuwar ce bata so ba, kawai dai ba ta da tabbas ɗin zaman auren.

    Kullum Mustapha nuna mata yake ita ce jakar gida yayin da Naja ita ce matar gida; don haka duk da yana kula da yaransa sosai kuma yana son su amma ba ta jin za ta iya tara masa wasu yaran balle ma a zo inda za ta yi magana a ce ta yi haƙuri ta zauna don yaranta.

    Tunda ta karɓi ƙwayar nan ba ta taɓa yin fashi ba kamar yanda likita ya sanar da ita, ko da kuwa ba ita ce da kwana ba haka take shan ƙwayarta. Amma a ‘yan kwanakin nan gaba ɗaya ta rasa gane kan jikin nata; wasu abubuwa take ji kamar na mai laulayi.

    A hanyarta ta dawowa daga office ta tsaya a chemist ta siyo pregnacy test strip, har ta zo gida tana fargaba saboda duk wasu alamu na ciki sun gama bayyana a tare da ita. Sai da ta bari ta yi baccin dare sannan ta ɗauki fitsarinta na sassafe ta gwada da shi; kafin sakamakon ya bayyana a jikin ‘yar takardar gaba ɗaya ta gama ruɗewa.

    Ko da ta ga layukan guda biyu sun bayyana ba tare da wata matsala ba sai da zuciyarta ta kusan bugawa, ta muttsike ido ta sake kalla amma har yanzu layukan suna nan guda biyu. Haka ta haƙura ta miƙe ta ɗauro alwala sannan ta fito daga banɗakin ta tayar da sallar asuba.

    Bayan ta idar da sallar ta zauna a kan daddumar ta yi shiru; ta daga hannu za ta yi addu’a amma ta rasa ta inda za ta soma. Gaba ɗaya ma ba ta san me take ji ba. ‘Alhamdulillah. Ta faɗa a fili kamar me yin raɗa. Haka ta ƙarasa azkar ɗinta sannan ta miƙe ta shiga hidimarta.

    Dole ta haƙura ta daina shan ƙwayar family planning ɗin da take sha saboda kada ta je ta cutar da abinda yake cikinta. Sai bayan kwana biyu ta ɗan sami natsuwa sannan ta je asibiti aka sake yi mata gwajin, aka tabbatar mata tana ɗauke da ciki na sati shida. Bayan ta dawo daga asibitin sannan ta sanar da Mustaphan.

    Wannan gwajin da ta yi kuma sai ya zama kamar ta kunno laulayin gaba ɗaya. Babu inda yake mata ciwo amma tana fama da kasala sosai sannan kuma ga rashin son cin abinci. Haka dai ta cigaba da lallaɓawa.

    Ranar kwananta ne don haka Mustapha a ɗakinta zai kwana. Yaran duk sun kwanta a ɗakinsu yayin da Hammad da Shukra suke kwance a ɗakin baƙinta wajen Hafsa. Yana zaune a gaban mudubinta yana aiki a computer ɗinsa yayinda ita kuma take kwance a kan gado tana game a waya. Ya bar aikin ya juyo yana kallonta ya kirawo sunanta, ta bar game ɗin ta mayar da hankalinta kanshi sannan ta amsa.

    Yace ‘Umm! Ina so dama na sanar da ke bana za mu je aikin Hajji da Naja. Da da ke za mu je amma kin ga ke laulayi ya saka ki a gaba don haka na cire sunanki na saka nata sunan. Ta ɗan yi shiru saboda yanda maganar ta zo mata a ba-zata; idan dai ba wai ba ta ga dai-dai ba ma kamar dai ganin da ta yi wa Najan shekaran jiya ta ga kamar ita ma tana ɗauke da yaron ciki; ko da bai fito ba dai amma ita Khadeejan ta ga wasu alamu.

    Domin a lokacin har ta ji kunya tana fatan Allah ya sa ba ganewa Najan ta yi ita tana ɗauke da ciki ba ta je ita ma ta yi. Kallon da ya kafe ta da shi ya sa ta yi firgigit ta dawo hayyacinta tana cewa ‘Masha Allahu, Allah ya nuna mana. Amma ai ana zuwa da masu ciki kuma zan iya; in dai an yi niyyar kai ni to a ba ni kujerata zan je.’

    Ya yi dariya ‘Haba aikin hajin fa ba wasa ba ne kuma ba a kwance ake yi ba, ko so kike mu je wahala ta sa ki sami miscarriage? Kuma ya za a yi na ɗauke ku mu tafi saudiyya gaba ɗayanmu? Mu bar yaran a wajen wa? Kin san Hajia yanzu ba lafiya ce da ita ba.’ ‘Haka ne, to ai sai Najan ta zauna ni na je tunda ni ka fara yin niyyar biyawa.’

    ‘To ai na gaya miki ke ga ciki, da a ce ba ki sami ciki yanzun ba da ke za mu je amma ki yi haƙuri sai shekara mai zuwa in Allah ya nuna mana. Ta tashi zaune ta ƙara marairaicewa tace ‘Idan na mutu a haihuwa fa? Ya harare ta yace ‘Ka faɗi alkhairi ko ka yi shuru.’

    Ta sunkuyar da kai tana murmushin yaƙe; yayin da ya juya ya cigaba da aikinsa. Ta zame ta koma ta kwanta; tabbas ba kuskure ta yi ba ciki ne da Naja, ko da kuwa bai kai sati shida ba. Kuma tabbas ta san ba ita Mustapha ya yi niyyar biya wa Hajji ba, Najan ya so biyawa. Kawai dai cikin ya zo masa ne a matsayin uzuri da kariya. Ya wanke kansa daga zargi.

    A hankali ta zame ta gyara kwanciyarta ta janyo abun rufa ta rufe jikinta sannan ta rufe idonta kamar mai bacci; haka ta kwana zuciyarta tana ƙuna. Me Mustapha ya mayar da ita ne; shikenan idan dai abun ƙaruwa ne ba zai iya sakata a ciki ba sai bayan ya saka Naja amma idan dai wahala ce ita ce a kan gaba? Yanzu yana nufin yace da matarsa zai tafi aikin Hajji; wadda ita ma cikin ne da ita sannan ita kuma ya barta ta kular masa da yara da gida duk da ita ma cikin ne da ita.

    Za ta iya wahalar kula da gida amma ba za ta iya wahalar ibada ba kenan? Sai yau ta gane girman rainin da Mustapha ya yi mata da kuma yanda ya ɗauke ta. Tun ranar da Mustapha ya sanar da ita zai tafi Saudiyya da Naja ta so ta je gida wajen Mommy, amma saboda kada abun ya yi kama da za ta yi reporting ɗinsa sai ta haƙura.

    Tun dare ta sanar da shi za ta je gida kuma ya ba ta izini, don haka gari yana wayewa da yake ba ita ce da girki ba ta shirya. Hafsa ta kama hannun Hammad suka sauko, suka fice tsakar gida suna jiranta yayin da ita kuma take rufo part ɗinta. Ta saba duk lokacin da za ta fita idan Naja tana nan sai ta leƙa ta sanar da ita ta fita, don haka yau ɗin ma tana saukowa ta shige parlor ɗin Naja.

    Tun kafin ta hango fuskokinsu ta ɗauki muryar Yaya Jidda, ba ta yi mamaki ba tunda yanzu sun saba zuwa gidan su wuni a wajen Naja idan ba ta sauko ba babu mai hawa nemanta kuma ko yara ba za a tura a ce ta zo ba. Ta ƙarasa ta zauna a kan hannun kujera ta gaida Yaya Jidda cike da girmamawa sannan suka gaisa da Naja.

    Har ta miƙe za ta fice Yaya Jidda ce ‘Sai muka ji abun arziki kuma, Mustapha yace da shi da Naja za su je aikin Hajji. Ta ɗan koma ta zauna tana murmushi tace ‘Eh, haka yace. To Allah ya sa su je a sa’a, muma ‘yan baya Allah ya kirawo mu. ‘Amin ya Allah.’ Ta amsa sannan ta miƙe ta yi musu sallama ta fice.

    Har ta je gida abun yana yi mata ciwo a rai; wato har ma ya gayawa ‘yan uwansa da Naja zai tafi Hajji kenan an fara zuwar mata murna ta kuma ana yi mata Allah ya kawo na ‘yan baya. Kuma wannan ganin da ta yi wa Naja ya ƙara tabbatar mata da cewa Najan tana dauke da ciki domin yawu ne a bakinta irin wanda masu ciki suke tarawa.

    Tun da ta shiga gidan Mommy ta san da matsala, amma dai ba ta tambaye ta ba saboda bata son ganin kukanta. Ta san yanzu da ta tambaye ta damuwarta sai ta yi kuka mai isarta sannan za ta gaya mata damuwar. Suna zaune a parlor ɗin Mommy bayan sun gama cin abincin rana suna hira yayin da Hammad yake ta kai wa da kawowarsa, Mommy ta dube ta tace ‘Ki bar min Hammad a nan ya kwana biyu ki samu ki ɗan huta, na ga duk kin yi wani zuru-zuru.’

    Ta yi gajeran murmushi tace ‘Ga shi nan Mommy an bar miki, idan na shirya sai Ahmad ya mayar da ni gida ya karɓo masa kayansa. Ta yi dariya ‘Dama neman kai ake da shi.’ Jimawa kaɗan tace ‘Momy wai Abbansu ne zai tafi Hajji shi da Naja. Nan da nan fara’arta ta ƙaru, tace ‘Kai ma sha Allahu, Allah ya amsa ibada.’ Ta kalli Khadijan suka haɗu kuma kamar wadda aka tunawa wani abu tace ‘Ah, to ke me yasa ba za a haɗa da ke ba ko kuma a fara kai ki, ko kin yi halin naki ne ya ɓata miki rai kin ce ba kya son kujerar?

    Ta sa yatsanta ta goge ƙwallar da ta faɗo a kwarmin idonta, ta kawar da kai sannan tace ‘Haka ya zaɓa ya fara tafiya da ita. Da mamaki ta zaro ido tana tambaya ‘To ke me kika yi masa, tunda dai ai kece babba ke ya kamata ya fara tafiya da ke ko kuma ya tafi da ku dukanku a lokaci guda.’

    ‘Yace wai ciki ne da ni don haka ba zai tafi da ni ba sai dai ko wata shekarar zuwa lokacin na haihu. Ta kalli cikinta sannan ta kalli fuskarta ‘Ciki? To ai ƙarami ne kuma na ga har yanzu ana zuwa da masu ciki sai dai idan basu da lafiya. Ni ban ma san kina da cikin ba ai. ‘Ni ma bai fi last week na gane ba, ban ma sa rai da shi ba kawai na gan shi.’

    Mommy ta dafa hannunta tace ‘To ai shikenan tunda ya zo sai mu ce Allah ya raya, amma dai masu ciki suna zuwa aikin Hajji har yanzu. Ana ta dai cewa za a hana amma ba a hana ɗin ba tukunna. Kawai da yace bai so zuwa da ke ba. Ta sake share ƙwalla tace ‘Tabbas Mommy bai so ba, don ita ma Najan ai ciki ne da ita.

    Kawai dai ya zata ban san tana da cikin ba ne shi yasa yake so ya raina min hankali kamar yanda ya saba. Ikon Allah. ’Suka yi shiru na ɗan lokaci; ita ma Mommy abun ya ɗaure mata kai. Duk gidajen da ta sani na mata biyu ko sama to idan irin wannan damar ta samu babba ake fara kai wa. Tabbas abun ya sosa mata rai to amma babu yanda za ta yi.

    Ta dafa hannun Khadeejan wadda ita ma ta yi nisa a nata tunanin tace ‘Kuma ba ki gaya masa Najan ma ciki ne da ita ba? Ban gaya masa ba Mommy, kuma ba zan gaya masa ba. Yana sane da abinda yake yi Mommy, tsaf ya san tana da ciki. Ita da take tara yawu idan tana laulayi, kuma ko yau ma da na shiga wajenta da yawun a bakinta.

    Kawai dai da ita ya yi niyyar zuwa, ko na gaya masa kuma ba canzawa zai yi ba sai dai kawai ya yi ta kawo hujjoji. ‘Uhm, to ai shikenan. Kin ga dama shi Hajji kiran Allah ne, ke ma in sha Allahu Allah zai kirawo ki nan ba da daɗewa ba ta hanyar da ya so. Kada ki sa wata damuwa a ranki balle ki illata ɗan da yake cikinki.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan ta gyara zama tace ‘Wallahi ni Mommy na ma gaji da auren nasa gaba ɗaya. Tabbas ko shekara nawa zan yi da Mustapha ba zai taɓa canzawa ba, ba zai iya yi min adalci ba. Wataƙila ya daina so na, wataƙila kuma iya son da yake min kenan. Amma dai gaskiya na gaji Mommy.’

    Ta dafa hannunta cike da kulawa tace ‘To ai haƙuri za ki yi, dama shi aure ya gaji haka kuma ribar aure ta me haƙuri ce. Ba ki sani ba ko ita abokiyar zaman naki wani abun take yi na biye-biyen malamai, ai duka ana yi. Ta yi murmushin yaƙe tace ‘Ai wallahi babu wani biye-biye Mommy, a hayyacinsa yake yi.

    Kawai dai idan hidima za a yi masa to ya fi so ni ya saka ni aiki, idan kuma morewa zai yi da harkar soyayya to wannan ita ta iya. Amma babu wani asiri haka ya tsarawa kansa. Ta sake kama hannunta ta riƙe tana kallon fuskarta tace ‘Ki dai yi haƙurin, in sha Allahu za ki ga ribarsa. Kuma idan dai Hajji ne da izinin Allah ke ma zai kirawo ki.’

    ‘Uhm.’ Nan suka ɗauki lokaci Mommy tana ba ta baki. Can zuwa yamma ta shirya Ahmad ya mayar da ita gida ta ba rwa Mommy Hammad.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

    Kamar yanda Khadeeja ta faɗa ba ta sake kula hidimar yaran a ranar da ba ita ce da kwana ba, sai dai ranar kwanata tana fitowa ta sallami kowa sanna ta cigaba da harkarta. Idan kuma dare ya yi ta shiga ɗakinta ta yi kwanciyarta don ta tabbatarwa Mustapha cewa ta ba shi kwanan.

    Ranar Asabar ce don haka yara babu makaranta duk suna gida, kamar yanda suka saba tunda Khadeeja ta ƙi hidimar yaran to duk ranar girkin Naja Anti Wiyya ce take abinci har yaran. Ita kuma Najan ita ce za ta tsaya a kansu su yi wanka su shirya, sai dai ranar da ba ta tashi ba dole haka Mustaphan yake tashi ya yi ta faman yi musu faɗa har ya samu su gama shiryawa a hankali.

    Afaf ce ita kaɗai a parlor ɗin Naja tana kallo saboda TV ɗin parlor ɗinsu Startimes ce ita kuma ta fi son DSTV wadda take parlor ɗin Naja; yayin da Anti Wiyya take ta kai wa da kawowa tana ƙoƙarin dora a bincin rana. Ta wuce Afaf a parlor ta shige ɗakin Naja inda ta same ta a kwance a gefen gado; bayan ta amsa sallamarta ta ƙarasa ta zauna a gefen kafarta kamar a fusace.

    Tace ‘Sannu Anti, kina ta hidima. Lallaɓa ta nake yi idan ta ƙoshi goya ta zan yi na fito na taya ki. Salaman ma ina jin yau ba za ta zo ba; ko wa take so ya yi mana wanke-wanke da sharar oho ga girki. Ta yi tsaki ta kawar da kai tace ‘Kin ganni a cike nake da haushinta, ga shi kamar ta shirya wulaƙanci tunda yau wanke-wanken ya fi na kullum yawa sannan ta ƙi zuwa.’

    ‘Hmm! Ai sai haƙuri masu aikin zuwa da dawowa ba su da kirki, ni ma da na gama jegon nan me kwanan zan ɗauka. Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan Anti Wiyya tace ‘Ita kuma wannan ‘yar taki wallahi ita ma ba ta da mutunci; yaushe za a ce budurwa kamarta ba za ta yi aiki ba komai ƙanƙantarsa?

    Sai dai ta dinga bin mutane da kallo suna mata aiki sai kace ubanta sayenmu ya yi. Gaskiya ku sake zama a gidan nan, haba! Idan banda ma rashin mutunci ya za a ce mace tana jego kuma a barta da kula da gida da yara bayan tana da kishiya? Ai kamata ya yi ta karɓar miki aikin. Ko da yake wannan ‘yar mulkin kishiyar taki na kula daga ke har maigidan tsoronta kuke yi.’

    Ta tashi zaune ta kwantar da Rukayya wadda ta riga ta yi bacci, ta kama haɓa ta dubi Antin tata tace ‘A a shi dai yake tsoron matarsa, duk abinda ta ga dama tace ba za ta yi ba haka zai yi ta kame-kame saboda ita ba a iya yi mata dole. Ta kalle ta sheƙeƙe tana cewa ‘Kece karkatacciyar kukarsa mai daɗin hawa ko? Shi yasa kina jego amma aka lafta miki aiki?

    Ita ko kunya ba ta ji? Sai ta sauko ta ishi mutane da gaishe-gaishe kamar wata musulmar ƙwarai. Cikin damuwa tace ‘Haka take fa, da an haɗu ta yi ta haba-haba da mutum amma mugun halinta yana nan fal cikinta sai mu da muke zaune da ita muka san halinta. Anti Wiyya ta ɗan yi ƙasa da muryarta tace ‘To gaskiya dai dole a yi aiki a kan wannan matar, yanda ta kama maigidan nan tana juya shi ai ba fin mu iyawa ta yi ba.

    Kema idan kika zo yawon arba’in da kaina zan kai ki inda za a taimaka miki a ƙwato miki daraja. Wannan kwarjinin da take da shi take yi wa kowa har maigidan ke ma a samo miki shi. Taimako ne da ayar Allah ina da malamina a hannu kuɗi kawai za ki bayar. Har yaran ma don ubansu ko su bi ki su zauna lafiya ko kuma su koma ‘yan kallo.’

    Tana ta jijjiga kai saboda gamsuwa tana cewa ‘Babu komai Anti, in sha Allahu za mu je. Don ni ma wallahi zaman haka ya ishe ni. Kuma dama Yaya ma tace za mu je ban san me ya ɗauki hankalinta ba. Nan suka zauna suka gama ƙulla yanda za a yi sannan suka fito suka kama hidimar gidan.

    Haka suka cigaba da yi har Naja ta yi arba’in; duk wata kalma da Mustapha zai yi amfani da ita ya sa Khadeeja ta karɓi hidimar nan ba ta yi amfani ba har ya gaji ya sakawa sarautar Allah ido. Sai da Naja ta yi arba’in sanna suka cigaba da rabon kwana. Idan Khadeeja ce da kwana sai Mustaphan ya je ɗakinta yayin da ita kuma Naja take zuwa ɗkinsa.

    Kwanci tashi har ya zama ta mayar da saman nasa kamar nata, ya zama kullum tana ciki ko parlor ɗinsa ko ɗakinsa. Ba ta daɗe da yin arba’in ɗin ba kuma Khadeeja ta gama bautar ƙasa; sai dai duk yanda ita da Baffanta suke ƙoƙarin samar mata aiki bai samu ba. Inda ta yi bautar ƙasar ma ta so su riƙe ta amma suka nuna mata ba sa buƙatar ma’aikata.

    Ba ta son zaman gidanta, domin ta san in dai ya zama Naja za ta tafi aiki ta barta a gidan da yara to dole Mustapha zai yi duk yanda zai yi ya tursasa ta ta dinga kula da yara. Ya zama shi da matarsa suna yawon neman kuɗi ita tana musu hidimar gida da ta yara. Don haka ta sanar da manager za ta dinga zuwa Litinin zuwa Juma’a tana yi musu aiki kyauta.

    Da ya ji haka sai ya sa aka ɗora ta a kan tsarin internship da suke da shi; inda duk wata za a dinga ba ta naira dubu goma sha biyar har zuwa lokacin da za a sami wani gurbi a gidan rediyon kawai sai a ɗauke ta. Sosai hakan ya yi mata daɗi, kuma ba tare da wata fargaba ba ta sanarwa Mustapha sun riƙe ta aiki, ta cigaba da zuwa.

    Kusan wata takwas kenan da haihuwar da Naja ta yi; kuma kamar yanda suka tsara an kai ta wajen malami. Bayan malamin ya ji bayaninsu ya ba ta wani abu mai kama da gishiri yace ta yi sati tana zuba musu a abnci duk gidan kowa ya ci har Khadeeja. Haka ta dage ta yi amfani da abun nan sai dai ba ta da tabbcin Khadeeja ta ci abun marmarin da take girkawa tana aika mata, shi ma Habib ba ta da tabbacin cinsa domin ya fi cin abinci a wajen Khadeeja.

    A hankali ta fara ganin sauyi, kamar dai duk yaran da Mustaphan suna saurararta; tunda wasu lokutan idan ta sa Afaf aiki haka za ta tashi ta yi ko ba ta so kuma Mustaphan ya daina hanata.

    Sun gama magana da ita a kan zai siya mata mota, amma ga shi lokaci yana ta ƙurewa yanzu ya ma ce mata shi ba alkawari ya yi mata ba; shi kawai ce mata ya yi zai yi tunani. Cikin damuwa suke waya ta sanar da Anti Wiyya halin da ake ciki; tace ‘Wallahi Anti nema yake ya canza maganar.

    Kuma dama na gaya miki aikin malamin nan ba kullum yake ci ba, tunda ko Mustaphan ya fara saurarar maganata da an kwana biyu sai ya sake komawa kamar da. Gani ma nake kamar duk lokacin da matarsa ta karɓi kwana sai ta warware min aiki, shi yasa nake ta fama da shi. Daga ɗaya ɓangaren Anti Wiyya tace ‘Au haka ne? To bar ni da su, ai ba mu za a yi wa bariki ba.

    Akwai wani malamin aikinsa yana da zafi sosai, in kin sami lokaci kiyi min waya sai mu je wajensa. Ke kanki sai kin yi mamakin aikinsa. Suka ƙarasa hirarrakinsu suka yi sallama. Ta jefa wayarta a kan gadonta cike da ƙwarin gwiwa; ta san Mustapha yana ƙoƙari wajen kyautata mata amma ita gani take kamar tsoron khadeeja yake yi. Kuma ma ita so take ya zama gaba ɗaya gidan sai abinda ta faɗa za a yi.

    Tana ganin yanda maza suke yi wa matansu kyauta ta burgewa, ita ma haka take so ya dinga yi mata, duk abinda ta nema ya ba ta kawai tunda ta san yana da kuɗin. Idan ma ta sami yanda take so to ko ganin Mustapha yaran ba su isa su yi ba sai da izininta, domin ta kula da yanda yake saurararsu yana bin ra’ayinsu kamar su suka haife shi.

    Sai an yi magana yace su marayu ne. Tabbas dole gidan nan gaba ɗaya ya dawo tafin ƙafarta don ta gaji da wannan mulkin da ake mata ana kasa mata hankalin miji tsakanin uwargidansa da yaransa.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

    Tun wajen 12pm ta nemi izini a wajen aikin nata ta fice, kai tsaye gidansu ta nufa. Ta ci sa’a ta sami Mommy da Yaya Mama suna zaune a parlor suna hirarrakinsu. Bayan sun gaisa Khadeeja ta dubi Yaya Mama tace ‘A nan kika kwana Yaya. Ta yi dariya tace ‘Ga jakata a kusa da ni kina kallo amma kike min wannan tambayar, to ni yanzu ma zan tashi saboda 2pm zan ɗauko yara a makaranta sannan mu wuce gidan.’

    Ita ma ta yi dariyar, ta umurci Hafsa da ta shiga ɗakin Nabila ko ta je kitchen wajen masu aikin gidan ta zauna. Tun kafin tace wani abu Mommy ta dube ta tace ‘Lafiya dai na ganki kamar a fusace, sarkin rigima. Ta zumɓura baki ta sunkyar da kai tana kallon hannunta kamar me ƙunƙuni, sai da ta gama zumɓura bakin sannan cike da takaici tana ƙoƙarin danne hawayen da ya taso mata tace ‘Mommy ni Mustapha zai mayar ‘yar aiki, kuma Baffa ya goya masa baya.’

    Mommy ta gyara zama ta fuskance ta sosai tana kallon fuskarta da mamaki sannan tace ‘Ban gane ba, kuma me kawo Baffanki a cikin mayar da ke ‘yar aiki? Shi Mustaphan me ya yi miki? Tana buɗe baki za ta yi magana hawaye ya ƙwace mata, ta sa bayan hannunta ta goge sannan ta labartawa Mommy abinda ya faru.

    Zuwa lokacin hawayenta ya gama ƙwacewa yana zuba kamar ana zubar da ruwan famfo, Mommy ce ma take ƙoƙarin goge mata. Tace ‘Mommy yanzu shikenan haka zan yi wata tara ina mata hidimar gida tana kwana da miji, bayan ni haka na yi nawa laulayin ko tausayina ba ya ji. Ko haihuwar Hammad fa ana gama suna dole na miƙe na koma hidimar gidan saboda ban ma ga fuskar cewa ba zan iya ba.

    Amma yanzu saboda ya auro ‘yar gwal shi ne zan karɓar mata aiki ita kuma ta yi laulayi. Yaya Mama tace ‘Ni fa gaba ɗaya ban gane ba. To ke me yasa ba kya zuwa ɗakin kike barinta ta je, ai da sai ki je ki yi kwanciyarki a can ki ga ta inda marasa kunya za su kwana tare.’

    Kafin ta yi magana Mommy tace ‘Gaskiya ni ma dai ban gane dabarar yin hakan ba, ai ɗakin ya kamata ki gyara ki tare har sai kin gama kwananki. Ta sa bayan hannunta ta goge hawayenta sannan tace ‘Mommy ba zan iya ba, ya kwana da wata matar a kan gadon sannan ni ma ya kwana da ni a kan wannan gadon.

    Wataƙila ma da ya yi aurensa ba tare da ya ci min mutunci ba abubuwa da dama za su zo min da sauƙi, amma gaskiya ba zan iya ba. Tunda ko bayan ta tare ranar da zan karɓi girki bayan da ta gama kwana takwas ɗinta na shirya tsaf zan shiga ɗakin, amma har magriba ba ta fito daga ciki ba. Lokacin shi kuma ya riga ya fita.

    Don haka na ƙyale ta na shirya masa abincin dare tunda na gama kintsawa. Amma yana dawowa ko kallon abincin bai yi ba ya same ni wai tunda ina jego na ba shi kwanakin ya kai wa amaryarsa in ya so idan na yi arba’in sai a fara rabon kwanan. Kin ga kenan ita ta riga ta san ba zai ba ni kwanan ba shi yasa ta ƙi fita ma daga ɗakinsa.

    Daga wannan lokacin ɗakin da me ɗakin suka ƙarasa fice min daga rai gaskiya. Idan yana buƙata ta ya same ni a ɗakina, kuma yana zuwa ɗin. ’Mommy wadda take binta da kallo tana jijjiga kai tace ‘Lallai Mustapha, ni na rasa ma me zan ce. Ni fa mamakin da nake Baffanki ko gaya min bai yi zai je ba balle da ya dawo ya gaya min, wataƙila jiya bayan ya fita da magriba Mustaphan ya yi sa’a ya same shi a gate suka gama magana.’

    Yaya Mama tace ‘Hmm! Ai komai daɗinki da miji idan dai wata macen ta gifta to sai abinda kika gani. Watan haƙurinki ne ya kama har ya gama yayinta. Mommy tace ‘To yanzu ya za a yi? Kin ga Baffanki ya riga ya sa baki a maganar ba tare da kin gaya masa ainahin abinda yake faruwa ba.

    ‘To Mommy ya za ayi na yi masa duk wannan bayanin ya gane, ai ban ga alamar zai ma gane ba tunda ko a lokacin ma yace amfanin mata biyu kenan ɗaya ta taimakawa ɗaya. Kuma ya za a yi na zauna ina gaya masa Mustapha yana satar min kwana saboda na ƙi zuwa ɗakinsa? Umm, haka ne kuma. To Allah ya kyauta.

    Yanzu kam sai dai ki yi haƙuri a ga abinda hali zai yi tunda dai babu wanda zai je ya kwance maganar Baffanki. Ina ga kula da yaran wanda kika yi a baya bai kashe ki ba ba na jin na wata tara nan gaba zai dame ki. Haka suka zauna suka yi ta ba ta hakuri; sai daga ƙarshe Yaya Mama tace ‘Kuma ke ma idan kin gaji kawai ki yi pretending ki kwanta masa, wallahi da kaina zan zo na taho da ke na kawowa Mommy ta yi jinyarki idan kin huta kya koma.’

    Mommy ta kai mata duka tana cewa ‘Allah ya shirye ki yayar kwabo. Suna nan zaune wajen 1:30pm Baffa ya shigo gidan da sallama, bayan ya amsa gaisuwarsu da sannu da zuwa ya dubi Mommy tana zaune a tsakiyar su Khadeeja yace ‘Gulmar wa kuke yi suka saka ki a tsakiya haka. Ita ma dariyar ta yi tace ‘Ba dai gulmarka muke yi ba.’

    Yaya Mama ta yi musu sallama ta fice yayin da Khadeeja ta miƙe ta nufi ɗakin Mommy ba tare da tace komai ba. Baffa ya bi bayanta da kallo sannan ya yi dariya ya dubi Mommy yace ‘Wannan iya rigimar ƙarata ta kawo ko? Ta harare shi tace ‘Ashe ka san ka yi mata laifi? Ya yi dariya yace ‘Rabu da ita da-Allah, ya za a yi a ce mutum yana da mata biyu a ce ɗaya ba za ta karɓi ɗaya aiki ba idan ba ta da lafiya? Ai ita ma ba ta so a zauna lafiya ba.’

    Nan ta ƙara yi masa bayanin yanda zaman nasu yake, sai dai ta kasa gaya masa cewa Mustaphan yana ba wa Naja kwanan Khadeeja saboda Khadeejan ba ta yarda ta je ɗakinsa. Yanda ta san shi ta san tabbas ba zai ɗauki wanna ba, tunda shi ma tashi uwar har ta koma ga Allah turaka take zuwa ranar kwananta.

    Haka dole Khadeeja ta haƙura ta cigaba da hidimar gida da ta yara. Shi ma Mustapha da ya gama zagaye-zagayen haka ya same ta a ɗakinta yana nuna mata jin daɗinsa ganin yanda take kula da yaran sai dai baya jin daɗin yanda idan ta jera abinci take komawa ɗaki ta bar su shi da ‘yayansa.

    Duk yanda ya so ta ba shi haɗin kai su tattauna maganar ta ƙi, da ya dame ta da zance ma sai tace ‘Don Allah ka bari! Kai dai ba so kake na cigaba da hidimar gidanka da yaranka ba amaryarka tana hutawa? To ai ina yi ko? Ina ga duk a inda na zauna na ci abinci ma wannan bai kamata ya zama damuwa ba tunda dai ku kun ci naku.’

    Kafin ya ba ta amsa ta fice ta bar masa ɗakin. Dole ya haƙura ya zuba mata ido tunda dai tana yin abinda yake so kuma duk ranar da ya kai mata kwananta ba ta hana shi buƙatarsa.

    Da fari lokacin da Mustapha ya ƙara aure Khadeeja ta ga ‘yan uwansa ba sa wani damunta ta yi zaton tunda an mata kishiya sun fita harkarta. Sai dai tunda suka ji labarin Naja tana da ciki sai suka kama zarya gidan; babu yanda za a yi Yaya Jidda ta yi sati ba ta zo gidan ba. Haka za ta taho da girki a flask wai Hajia ce tace a kawo wa Naja saboda kwaɗayin mai ciki.

    Ga shi idan ta zo a wajen Najan za ta sauka, sai dai idan Khadeejan tana nan ta shiga su gaisa sai ta koma wajen Najan. Sai kuma ta yi ta aiko yara; a ba ta abinci. Idan ta cinye kuma tace a ba ta wani ɗan abun taɓawa. Ranar da ba ta zo ba kuma sai a turo yaranta da abincin; haka za su zo ta wuni surutu da hidima da su ba ta taɓa jin wani yace Hajia tana gaisheta ba.

    Kuma shi ma Mustaphan yana kallo ana yi amma bai taɓa cewa komai ba; sai dai yawan godiya da za ta ji shi yana yi wa mutan gidan nasu. Haka ta kawar da kai ta cigaba da duk wannan hidimar tana ganin rawar kai kala-kala. Haka ta cigaba da dagewa har Allah ya sauki Naja lafiya, aka sami yarinya mace wadda tun ranar da aka haihu Mustapha ya yi mata huɗuba da suna Rukayya.

    Ba su tsara za ta tafi gida ba don haka sai aka kawo ƙanwar mahaifiyarta Alawiyya wadda suke kira da Anti Wiyya ta zo yi mata zaman daɓaro. Tun Khadeeja tana saka ran za ta ji Mustapha yace zai haɗe mata kwanan saboda Naja tana jego har dai ta fitar da rai. Ranar da aka kwana takwas da haihuwa ranar ta kama kwanan khadeeja ne sai dai a daren ranar za ta fita daga girki.

    Da yake a ɗakinta suka kwana a nan yake shirin fita office; musamman tunda banɗakin ɗakinsa ya kwana biyu rabon da a wanke saboda Naja ba za ta iya wanke wa ba kuma Khadeeja ta ƙi ma shiga ɗakin; ga shi kuma yana ƙyashin ya saka Afaf ta wanke tunda ba ya son damuwarta. Yana zaune a gaban mudubinta yana shafa mai ta fito daga wanka, ta ɗauki kayan shafawarta ta koma gefen gado, suna yi suna taɓa hira.

    Jimawa kaɗan tace ‘Yauwa, tazarce za mu yi ko? Sai na haɗe kwanakin tunda Naja tana jego har zuwa ta yi arba’in ko? Ya ɗan yi dum, alamar maganar ta shammace shi; tun ranar da Naja ta haihu ta gaya masa ba za ta bayar da kwananta ba saboda ko ba za ta iya biya masa buƙatarsa ba tana so ya kwana da su ita da Baby, in ya so kwana biyu sai su haƙura.

    Ya riga ya amsa mata hakan domin shi ma hakan ya yi masa; duk da dai shi ba mutum ne mai son jarirai ba domin ko ɗaukan yaro ba ya son yi har sai yaro ya iya zama sosai. To amma dai tunda ta nuna tana so shi ma sai ya ji hakan ya yi masa ko hira ce sa yi, musamman da yake bai taɓa tsammanin Khadeeja za ta nemi wani ƙarin kwana ba duk da ita ta ba da nata kwanan an ba wa Najan.

    ‘Um, no ina ga ba haka za a yi ba. Na riga na yi magana da ita amma ba ta ba da kwanan nata ba, tunda kin ga ke ma tambayarki na yi kika bayar ba tare da na yi miki dole ba. To ita ba ta bayar ba, don haka sai a cigaba da kwana bibbiyun kawai.’ Ya faɗa cikin in-ina yana satar kallon Khadeejan ta cikin mudubi.

    Sai da ta yi da gaske sannan ta haɗiya malolon da ya tokare mata maƙogoro; duk da dama hakan ta sa rai zai faɗa amma sai da abun ya yi mata ciwo. Ita ba ta ma yarda Naja ce ba za ta ba da kwananta ba, ta fi yarda shi ne dai ba zai iya ba ta kwana arba’in ba ba tare da ya ji ɗumin rabin ransa ba.

    Ta daure ta yi murmushin yaƙe sannan tace ‘Allah sarki haka ne kam, to babu damuwa Allah ya raya mana Rukayya ita kuma mai jego Allah ya ƙara mata lafiya. Shikenan ai tunda ta haihu lafiya idan ta karɓi kwana yau to ta haɗa da sauran hidimar gida da yara da nake yi ni ma na samu na huta.

    Ya yi shiru da bakinsa a buɗe yana kallon Khadeejan ta cikin mudubi; to a gaban Antin tata zai sakar mata aikin gida da na yara bayan ga ɗanyen jego sannan kuma ga Khadeejan tana kallo? Kuma a ce ita ce za ta tashi ta shirya masa yara, duk da dai kusan sun iya shirya kansu amma dai idan ba a tsaya a kansu ba haka za su yi ta shiririta har su makara.

    Ga shi Afaf ta shiga SS 3 yanzu tun 7:15 am ake tare su makara. Ya san idan dai ba a tsaya a kansu ba to kullum sai dai ya dawo da Afaf. Ya rasa ma me zai ce mata, domin ya san kusan ko me yace tana da amsar ba shi kuma ya tabbatar fitinar da ba ta yi ba ce a lokacin da Baffanta yace ta dinga taya Naja aiki take shirin biyan bashinta yanzu. Ta miƙe ta kwashi mayukanta da ta gama shafawa ta ƙarasa gaban mudubin ta ajiye.

    Ta ɗan tsaya daga gefensa tana kallonshi fuskarta cike da walwala kamar ba yanzu ta haɗiye ɓacin rai ba, tace ‘Kuma ni na yafe nawa kwanan ka haɗa mata, idan kuka yi arba’in sai mu cigaba da rabon. Ka ga ita da Baby suna buƙatar lokacinka da kulawarka sosai a waɗannan kwanakin. Ta wuce ta nufi gaban wardrobe domin saka kaya.

    Yana nan zaune a gaban mudubin ta shirya ta fice ta bar shi a ɗakin; nan da nan ta haɗa masa breakfast ta jera a kan table sannan ta dawo ɗakin ta same shi ya riga ya gama saka kaya. Tana tsaye daga bakin ƙofa tace ‘Na yi serving breakfast. ‘Ok.’ Ya amsa. Ta juya ta fice ya biyo bayanta. Suka zauna tare suna cin abincin. Har suka ci kusan rabin abincin babu wanda yace wani abu; kowa da abinda yake ransa.

    Ya ajiye kofin shayinsa bayan da ya kurɓa sannan ya ɗauki fork ɗinsa ya tsikari dankalin baturen da yake gabansa, ya ɗan ajiye fork ɗin ya kirawo sunanta a hankali kamar ma ba ya so ta ji kiran. Ta ɗaga kanta daga kallon kwanon abincinta ta amsa tana kallonsa. Ya yi gyaran murya sannan yace ‘Um, da-Allah ki yi haƙuri ki cigaba da girki a ƙalla har zuwa lokacin da Antin Naja zata gama yi mata wanka ta tafi.

    Tunda kin ga ga Hafsa nan tana taimaka miki kuma na san Afaf ɗin ma yanzu duk abinda kika gwada mata za ta iya taya ki da shi. Saura kaɗan dariya ta ƙwace mata; wato yanzu Afaf ta kai ta taimaka wajen girki kenan tunda ya auro matar so? Ashe ma ya san kunya tunda ga shi ba ya so ya ji kunyar iyayen Naja.

    Ta ajiye cokalinta ta kurɓi shayinta sannan tace ‘Don Allah Abban Afaf mu bar wannan maganar, hidimar gidannan ta wata takwas na karɓar mata. Ai na yi ko? Yanzu sai ta cigaba daga inda ta tsaya. Kwanan kuma da nace na ba ta da gaske nake, ku je ku yi jegonku na masoya kwana arba’in; wataƙila dai a kwankin da suka kama nawa ne na yi aikin gidan idan ina nan in ya so ita sai ta kwana da angonta.’

    Cike da jin zafin abinda ta faɗa yace ‘Khadeeja ni kike gayawa wannan maganar? A cikin abinda ta faɗa ba ta san menene ya ɓata masa rai haka ba tunda ita dai a iya saninta ba rashin kunya ta yi masa ba, amma ta ga ya fusata yana faman yi mata muzurai. Ita da ya kamata a ce ita ce ranta ya ɓaci haka saboda nauye-nauyen da yake nema ya ɗora mata waɗanda ƙarara suke nuna rashin adalci.

    Ta kalle shi ta kawar da kai tace ‘Allah ya ba ka haƙuri. Ta kurɓe ragowar shayinta ta miƙe da kofin da kwanonta ta wuce kitchen. Tana ajiye kwanukan ta fito ta wuce ɗakinta, tana turo ƙofar ɗakin hawayen da take riƙewa suka ƙwace mata, ta ƙarasa ta zauna a kan kujerar gaban mudubi. Ta zubawa mudubin ido tana kallon yanda hawaye suke fita daga idanuwanta suna gangarewa ta kan kumatunta.

    Wai me Mustapha ya ɗauke ta ne? Mai aikin Naja? To da me yasa ya aure ta ne? ko dama haka ake soyayya? Ba ta sami amsar tambayoyinta ba ƙarar fitar motarsa daga gidan ta katse mata tunani, ta tuna ita ma aiki za ta tafi. Don haka ta miƙe ta wanke fuskarta ta ƙarasa shiryawa ta fice daga gidan zuciyarta cike da damuwa.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyar

    Edita@rumasau-kallamu