MOHAMMED BALA GARBA
1. Rabbana Sarki Ilahu,
Rabbi mai tayar da ruhu,
Rabbi ga baiwarka Hauwa.
2. Babu mai tsarki ya naka,
Babu mai rahama kamarka,
Rabbi kai rahama ga Hauwa.
3. Babu mai jin ƙai kamarka,
Babu mai tausai irin ka,
Don Rasulu ka dubi Hauwa.
4. Duk Karamci na wurinka,
Ragwame ita ce sifarka,
Rabbi rangwantawa Hauwa.
5. Yadda duk ka yi babu mita,
Ba mu jayayya da yin ka,
Rabbi kai rahama ga Hauwa.
6. Hauwa Ƙamshi jaruma ce,
Babu shakka malama ce,
Mai rubuce-rubuce Hauwa.
7. Rabbi duk an mata shaida,
Kamila ce mai ibada,
Sayyada laƙabi na Hauwa.
8. Rabbi ta yabi mai Madina,
Kuma ta yi riƙon amana,
Sa Rasulu ya san da Hauwa.
9. Rabbi kai rahama gare ta,
Rabbi kai jin ƙai wurin ta,
Rabbi don kakarmu Hauwa.
10. Rabbi sanyaya kabarinta,
Rabbi kyautata kwanciyarta,
Faɗaɗa shi saboda Hauwa.
11. Sa Rasulu ya zo gare ta,
Sa ya yo murnar zuwanta,
Har ya ce “sannunki Hauwa.”
12. Hauwa sai mun zo gare ki,
Wataran za mu biyo ki,
Za mu sadu ki ji ni Hauwa.
13. ‘Yan uwa nai ta’azziya,
Marubuta ga marsiyya,
Na ta’aziyya ta Hauwa.
14. Rabbana ka daɗo salati,
Gun Habibu da yai wafati,
Shi masoyi ne ga Hauwa.
15. Ɗanbala suna Mohammed,
In ka so ka kirani Ahmed,
Ke ta’azziya ta Hauwa.
©
Mohammed Bala Garba
12:03pm
2 October, 2025.
Karanta Gyara Kayanka
Edita@rumasau-kallamu