Sakamakon Bincike A Kan Wasan Ƙunshi

0
140

Wannan bincike wanda aka gudanar, an yi amfani da hira da ziyar gani da ido da shiga cikin masu aiwatar da wasan inda ya binciko wasu bayanai masu matuƙar muhimmanci wajen gudumowar da suka bayar game da adana da bunƙasa tarihi da al’adun gargajiya na Hausawa musamman na Arewacin Nijeriya.

Sakamakon binciken takardar ta gano cewa, wasan ƙunshi wasa ne da yake ƙara haɗa kan matasa musamman samari da ‘yan mata na kusa da na nesa, wanda hakan yana samar da soyayya ta ƙullu har a samu zamantakewar aure a tsakani.

Sannan takardar ta gano cewa, wasa ne da ake aiwatarwa sau ɗaya a shekara, wannan ya haifar da son kowa lokacin ya zo domin aiwatar da shi tare da kashe kwarkwatar idanunsa.

Haka kuma, takardar ta gano ce har zuwa wannan lokaci ana aiwatar da shi, duk kasancewar akwai tasirin zamani kamar karatun addini musamman zuwa makaranta allo da islamiya sannan kuma da makarantar boko, wanda waɗannan suna taimaka wajen dusashewar wasan ba kamar yadda ake gudanar da shi a baya ba.

Sannan takardar ta nazarci yadda wasan yake ƙara ƙulla zumunta da son juna Samar da zumunci a tsakanin al’umma da ƙara danƙon zumunta a tsakanin al’umma da ilimantar da jama’a kan zamantakewa da raya al’adun Hausawa na gargajiya da bunƙasa tattalin arziƙin a tsakanin al’umma.

Takarda ta gano masu aiwatar da wasan sukan yaɗa tare da watsa wasan kai tsaye ta amfani da hanyoyi isar da saƙo na zamani ciki da wajen ƙasar nan. Wanda yin hakan ya taimaka gaya wajen sanin wasan da kuma masu bibiyarsa. Haka waɗanda ba su sami damar halarta ba bisa wasu dalilai su ma ba a bar su a baya ba.

Daga ƙarshe binciken ya gano cewa, wasa ne na gargajiya da ake aiwatar da shi tsawon lokaci mai nisan domin babu wanda zai ce ga lokacin da aka fara shi, sai dai a bisa hasashe.

Kammalawa

A cikin wannan takarda da aka aiwatar, an yi taƙaitaccen bayanin game da ma’anar wasa da kuma wasannin gargajiya a ƙasar Gaya, sai kuma aka yi bayani a kan wasan ƙunshi da yadda ake aiwatar da shi da masu gudanar da wasan da rana haɗi da lokacin da ake gudanar da shi a ƙasar Gaya, da ke Jihar Kano.

Har wayau, takardar ta fito wasu hanyoyi da ake bi wajen sanarwa da sadarwa haɗi da shirye-shirye gudanar da tanade-tanade wasan, an kuma yi bayanin masu aiwatar da shi, da kuma bayanin yadda ake gudanar da wasan a jiya. Haka kuma ta fito tare da bayani yadda ake aiwatar da wasan a yau tare da kawo yadda zamani ya yi tasiri a cikinsa. Kazalika takarda ta fito da muhimmmanci wasan yake ɗauke da shi, wasa ne da ya ke bunƙasa zumunci da tattalin arziƙi da kuma adana tarihi.

Manazarta

Alhassan, H. da Wasu, (1982). Zaman Hausawa. Bugu na Biyu. Zaria: Institute of Education, Ahmadu Bello University.

Bunza, A.M. (2006) Gadon Feɗe Al’ada. Lagos: Tiwal Nigeria Limited.

Bunza, D.B. (2016) “Taubashi Bahaushe: Wani Mashigi Na tantance Asalinsa Da Zuriyarsa”. Kaduna: A Cikin The Hausa People, Language And History Past, and Present and Future. Department of Nigerian Languages and Linguistics. Faculty of Arts, Kaduna State University. Garkuwa Publishing Ltd.

Ɗangambo, A. (2008) Rabe-Raben Adabin Hausa. Kano: (Sabon Tsari) Amana Publishers Ltd, No. 1166 Sabon Gari Market.

Ibrahim, M.S. (1982). “Dangantakar Al’ada da Addini: Tasirin Musulunci Kan Rayuwar Hausawa.” Kundin Digiri na Biyu. Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Gaya, M.A. (2018). “Keɓaɓɓun Wasannin Hausawa na Gargajiya a Ƙasar Gaya.” Kundin Digiri na Biyu, Sakkwato: Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo.

Magaji, A. (2002). “Wasu Al’adun Hausawa Yanaye-Yanayensu a Ƙasar Katsina.” Kundin Digiri Na Uku, Kano: Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Sa’id, B. da Wasu (2006). Ƙamusun Hausa. Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Zaria: Ahmadu Bello University Press.

Wanan bayanin an ciro shi ne daga maƙala mai taken Nazarin Wasan Ƙunshi Jiya Da Yau A Ƙasar Gaya wadda Magaji Ahmad Gaya Ph.D Sashen koyar da Hausa Jami’ar Northwest, Kano ya wallafa.

Emai: magaya@nwu.edu.ng

08066009039

Danna nan don karanta Wasan Ƙunshi A Yau

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceSunayen Abinci Ko Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 4
Labarin na GabaYanayin Littattafan Ƙagaggun Labarai Da Suke Koyar Da Tarbiyya
Dr. Magaji Ahmad Gaya
Dr. Magaji Ahmad Gaya shahararren malami ne a fannin harshen Hausa. Ya yi digiri na uku (PhD) a ɓangaren nazarin al’adu a jami’ar Umaru Musa “Yar Adua da ke Katsina. Haka kuma ya yi aikin koyarwa a wasu makarantun firamare da sakandare da kuma Kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kumbotso. A halin yanzu yana koyarwa a Jami’ar Northwest, Kano Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya.