Matsayar Ɗanbala

0
56

Lokacin da muke da manya,
Lau muke ba a kashe wa.

Zamanin da muke da manya,
Babu bandits kaf Arewa.

Sa’ilin da muke da manya,
Babu kinafas Arewa.

Lokacin da akwai su Baba,
Duk da tarbiyya Arewa.

Zamanin Ulama’u na nan,
Babu mai kafurta babba.

Lokacin da muke da manya,
Ba mu yin rigima Arewa.

Lokacin da su Inna na nan,
Kanmu ɗai yake ba rabe wa.

Lokacin Malamai su na nan,
Ƙanƙana na bin na gabba.

Lokacin su Waziri na nan,
Malamai ba su fanɗare ba.

Lokacin da muke da manya,
Ba mu san Boko Haram ba.

Zamanin da akwai mazaje,
Ilimi namu bai zube ba.

Lokacin da su Kawu na nan,
Tsintsiya muke ba kawai ba.

Yanzu da yake babu manya,
Ba mu san asalin gabas ba.

Yanzu da yake mun rasa su,
Sai kashe mu ake Arewa.

Yanzu da yake babu babba,
Ƙanƙana ke zage babba.

Tun da mun yi rashin su Inna,
Dole mui ta ganin mu baibai.

Kuma da yake ba magaji,
Shi ya sa mu muke ta ɓarba.

Babu babba a yau Arewa,
In akwai sunansa kama.

Na faɗa maka babu babba,
In akwai ka kira shi yanzu.

Da a ce ko muna da manya,
Da ba mui ta ganin hakan ba.

Da a ce da akwai su Baba,
Ƙanƙana ba su zagi babba.

Da da wanda muke jin tsoro,
Da ba mu raba al’umma ba.

Shehu Khalidu babu babba,
Yanzu kaf a cikin Arewa.

Wanga ita ce fahimta ta,
Ko a gobe ina faɗa ma.

Da da babba a yau Arewa,
Da ba zan yi musun hakan ba.

Ɗanbala daga Borno ne ni,
Mai yabon a wurin Masoyi.

Ɗan Amina abin nufina,
Na riƙe shi ba zan shika ba.

Ahlihi nasa na riƙe su,
Ba riƙon igiya na yo ba.

Da Sahabu ina biyan su,
Ban da masu kiran gumaka.

©
Mohammed Bala Garba
6:39pm
30 November, 2025.

Karanta Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceMijin Marigayiya Babi Na Ashirin
Labarin na GabaWasu Kayan Aikin Sassaƙa