Mai Maɗi Ke Talla (Mai Zuma Gida Ake Tad Da Shi)

0
34

Babahabu49

JAN KUNNE GA MATASA KAN SU KYAUTATA RAYUWARSU A YAU BA SAI GOBE BA

DAGA
DR. MU’AZU SA’ADU MUHAMMAD
SASHIN HARSUNAN NAJERIYA
JAMI’AR SULE LAMIƊO
KAFIN HAUSA
JIHAR JIGAWA
07030803404
Email:muazusaadukudan299@gmail.com

TAKARDAR AKA GABATAR A TARON FAƊAKAR DA MATASA WANDA ƘUNGIYAR ƊALIBAN GARIN KAFIN HAUSA SUKA SHIRYA A MAKARANTAR FIRAMARE TA SPECIAL A GARIN KAFIN HAUSA RANAR LAHADI GA ARI 2023, 19 GA SHAWWAL 1444 DA ƘARFE 10:00 NA HANTSI DAIDAI BAN RUWAN DAWAKI.

1.GABATARWA

Da sunan Allah Mai rahama, Mai jinƙai, Mai kowa, Mai komai. Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugaban Ma’aika, Annabi Muhammadu (S.A.W). Wannan muƙala, na da ƙudurin jan kunne ga matasa a kan su san mahimmancin Matasa a rayuwar al’umma. Akwai fagagen da ake buƙatar matasa su wakilci al’ummarsu, matasa kan yi tasiri a tsakanin al’umma ta fuskoki da dama.

Wannan kuwa a bayyane yake a inda sukan yi sanadin hulɗa ta kyautatu da kuma sauran al’amura gaba ɗaya. Akan samu matasan da kan taka rawa a fagage kamar haka: Ilmi, da Siyasa, da Tattalin Arziki, da Kiwon Lafiya, da Harkar Tsaro, da Sauran al’amuran zamantakewarsu, da sauransu. Haƙiƙa wannan ba zai samu ba sai ana da matasa masu nagarta waɗanda suka san ciwon kansu da kishin zuci.

Matasan da ba su da kwaɗayi, babu lalaci, da munafunci, da jahilci, tabbas wannan shi ne zai fitar da wannan yanki namu daga halin da muke ciki a yanzu. Haka kuma tare da fito da fa’idojin samu matasa na gari nagartattu masu tarbiyya, da kuma illolin gurɓatattun matasa marasa tarbiyya.

Bayan wannan kuma an ɗan tsakuro wasu daga cikin haƙƙoƙin yin tarbiyya tare da nuna irin nauyin da rataya a wuyan mahaifa, da Hukuma,da al’umma. Bisa wannan dalili ne yasa na yi wa wannan maƙalar take da “Mai Maɗi Ke Talla (Mai Zuma Gida Ake Tad Da Shi)”. Na kawo taken a matsayin matashiya ne, don ya ba mu damar lalubo mafita.

Manufata ita ce, Matashi mai halin kirki jama’a ke nemansa, shi kuwa lalatacce shi ne ke neman jama’a, amma kuma ana gudunsa. Tare da fatan mai karatu ko saurare zai gano saƙon da ake son isarwa a ƙarshen maƙalar, don samun mafita ko a fid da jaki a duma.

2. FASHIN BAƘI

Ma’anar Maɗi
Ma’anar Talla
Ma’anar Zuma

JAN KUNNE: shi kunne kashi uku ne, akwai fatar kunne shi ne mai faɗi, sannan akwai lilin kunne shi ne wanda mata ke hudawa su sanya ɗan kunne, sai gintsi wani sashi mai tudu mai ƙarfi wanda ya kare ramin kunne.

1.3.0 SAMARTAKA (Saurayi)

Samartaka ita ce rayuwar da yaro namiji ko saurayi kan yi tsakanin shekara 15-27 ko kuma zuwa lokacin da ya yi aure, kodayake wasu sukan wuce wannan matsayi ko shekarun amma ba su yi auren ba.

Duk inda ka ji an cewa mutum saurayi, to lallai ne yana tsakanin waɗannan shekarun, to da zarar yaro ya ga ya kai matsayin saurayi, dukkan ɗabi’un sa sai su canza kamar canzawar murya, fitar gashi a gemun sa (haɓa) ko a hammatar sa, kuma saurayi tun daga nan tunanin sa zai kama, sannan kuma natsuwa ta zo masa amma fa idan akwai tarbiyya daga yarinta, amma wasu za ka gansu akasin abin da aka lissafa a baya, to a na babu tarbiyya ke nan, yarinta ba ta samu kyakkyawar tushe ba ke nan ba.

1.4.0 BUDURCI(Budurwa)

Budurci ita ce rayuwar da yarinya take yi tsakanin shekara 13/14 -20, ita budurwa ƙarƙari shekara ashirin (20), a nan idan yarinya ta wuce haka, to abu dai ba haka aka so shi ba, don rayuwar Bahaushe ta haƙiƙa, budurwar Bahaushe ba ta wuce 18-20 in ta yi tsauri, watau ta ƙi yin girma da wuri, ƙarshen budurci shi ne yin aure.

Duk inda ka samu budurwa, to lallai ne ta kasance mai hankali, tunani, natsuwa da kunya in har akwai tarbiya daga iyaye, abin da yasa ka ji na ambaci kunya a wajen bayanin budurwa shi ne duk inda za ka samu budurwa bata rasa jin nauyin wani ko wasu in da ba an ɓata ta ba, babu wata jayayya a kan haka.

Babban al’amarin da yake nuna cewar yarinya ta zama budurwa shi ne nono ko kuma buɗewar ƙugu ko kuma fara (haila) ɓatan wata kenan, amma ba dukkan budurwa kan fara haila a gidan iyaye ba.

2.0.0 SU WANENE MATASA?

Matasa na nufin kalmar jam’i ce ta kalmar matashi, Matashi shi ne yaro mai shekara 9-13, saurayi kuma daga 14-17.

2.1.0 FAƊAƊA MA’ANAR MATASA

Ko da yake yanzu an faɗaɗa ma’anar Kalmar daga ma’anarta ta asali, an yi masu kuɗin goro samari da ‘yanmata sai a kirasu da matasa. Yanzu haka a wannan zamanin sai ka ji cikakken mutum magidanci ko kuma a kira shi dattijo kusan ɗan shekara 30-45 wai sai a ce masa matashi. Ko da yake ba mamaki ai daman shi mutum yana gudun abubuwa huɗu, kamar haka:1.Laifi, 2. Ƙauyanci, 3.Tsufa, 4.Hauka.

FAGAGEN DA MATASA ZA SU TSAREWA AL’UMMA

Babu shakka, akwai fagagen da ake buƙatar matasa su wakilci al’ummarsu, matasa kan yi tasiri a tsakanin al’umma ta fuskoki da dama. Wannan kuwa a bayyane yake a inda sukan yi sanadin hulɗa ta kyautatu da kuma sauran al’amura gaba ɗaya. Akan samu matasan da kan taka rawa a fagage kamar haka:

  • Ilmi,
  • Siyasa,
  • Tattalin Arziki,
  • Kiwon Lafiya,
  • Harkar Tsaro
  • Da Sauran al’amuran zamantakewarsu.

Haƙiƙa wannan ba zai samu ba sai ana da matasa masu nagarta waɗanda suka san ciwon kansu da kishin zuci. Matasan da ba su da kwaɗayi, babu lalaci, da munafunci, da jahilci,tabbas wannan shi ne zai fitar da wannan yanki namu daga halin da muke ciki a yanzu.
Gaskiya da amana, kamewa da rashin kwaɗayi, sanin ciwon kai daraja Karen farauta
Ma’anar Rago: na nufi mutum, malalaci, mara ƙwazo, ko juriya, shi kuma kishiyar jarumi ne, domin rashin jarumta ke haifar da ragwanci.

4.0 Jarumta A Mahangar Al’ada:

A tunanin wasu masana ana iya cewa jarumta wata ɗabi’a ce muhimmiya. Wannan yasa gaba ɗaya al’adar Bahaushe take ƙaunarta da kuma mai ita. Tabbas mutum mai kyauta na da farin jini da kwarjini da mutunci a cikin al’ummar Hausawa. Matuƙar aka san mutum jarumi ne, a wani lokaci har ƙoƙarin auren ‘ya’yansa ake yi, ko kuma idan shi ya nema a ba shi.

A mafi yawan lokutta, kowa kan so yin ma’ammala da shi. Al’adar Bahaushe ta camfa auren jarumi, shi yasa ake kwaɗayin aurensa ko kuma a auri ‘yarsa, don fatan a haifi ɗa ya gado shi wajen jarumta. Bisa dalilin cewa jarumta na cikin ɗabi’u da akan gada daga uwa.

Haka nan kuma akan iya koyon ɗabi’ar jarumta daga abokin zama ko maƙwabci. Bahaushe ya ce: “zama da maɗaukin kanwa shi ke kawo farin kai”. Bisa wannan dalilai ne yasa Bahaushe ya ɗauki jarumta a matsayin ɗabi’a.

4.1 Jarumta A Matsayin Ɗabi’a

Akwai mutanen da suke kallon jarumta a matsayin ɗabi’a ce wadda akan haifi mutum da ita, kamar ta gado, da kuma ta baiwa daga Allah. Haka kuma akwai masu ganin cewa koyonta ake yi, ko nemanta da ƙarfi ko da magani.

4.4 Rashin Tsoro:Tsoro na nufin firgita, watau dukkan wani abin da ya ɗaga hankalin mutum, wannan abu na iya kasancewa ko dai mutum, ko dabba, kai ko ma mene ne. Sannan wannan na faruwa ne a dalilin baƙunta, watau kamar rashin sabo, ko rashin amincewa, ko yarda. Alhaji Mamman Shata Katsina a waƙar Bakandamiya yake cewa:

Mai tsoro ba shi gwaninta
Mai tsoro ba shi zama gwani
ko wane ne kuma ko ɗan wa
Ka zama kamar ni fili waƙa,
Sararin waƙa bai san tsoro ba,
In na fito Shata ne.

6.0 Mai Sana’a Ya Wuce Tagumi” ma’ana duk wanda yake da sana’a komai ƙanƙantarta ya fi ƙarfin ya yi tagumi wato ya shiga halin ƙaƙa-ni-ka-yi (damuwa). Bahaushe na cewa; ba a dariyar mai noma ko bai sayar ba ya ci abinshi, Allah fid da A’i ga rogo ko ba ta sayar ba ta ci abinta, sana’a goma maganin magasa.

10.1 MATSALOLIN ZAMANTAKEWA A YAU

Al’amarin zamantakewa na fuskantar matsaloli da dama, a sakamakon sauye-sauyen da zamani ya kawo, a rayuwar Bahaushe ta yau da kullum. Misali, kamar cuɗanya da wasu ƙabilu a inda aka samu shigowar baƙin al’adu, sannan kuma suka yi tasiri. Haka kuma zuwan ilmin boko shi ma ya yi tasiri ƙwarai a kan rayuwar Bahaushe.

Don kuwa ya zo da wasu ɗabi’u, sannan ya kuma kawar da wasu ɗabi’u da a ka gada kaka da kakanni. Misali zaman gidan haya da wasu ƙabilu, sannan kuma ɗaki ɗaya ko ciki da falo. Kamar rowar zamani, da ƙyamar haihuwa, da gudun dangi, da son abin duniya, da rashin wadatar zuci. Haka kuma ana iya cewa ya kori wasu abubuwa waɗanda da yake an san Bahaushe da su.

Taimakon mabuƙata, da suka haɗa da ‘yan ‘uwa ne, ko bare, da aka san Bahaushe da shi. Domin haka sai aka samu giɓi a tsakanin ‘yan uwa, ko maƙwabta. Musamman masu hannu da shuni, wannan kuwa ya ƙara nesanta jama’a da dama da sauran ‘yan uwa da abokan arziki. Wanda babu shakka ya kawo lalacewar zumuncin mu’amalla a wurare da yawa. Domin sau da yawa kyauta na ƙara qulla zumunci, rowa kuma na tsinka shi.

Son ‘ya’ya: A halin da ake ciki a wannan zamani ba maƙwabci ba, kai ko da ɗan uwa ne, ko kuma malami ne yanzu in ya hori yaro, sai ka ga an nuna ɓacin rai. Wai cewar ya tsargi yaron ko ya sa masa ido ne , ba domin gyara halin yaron ne ya hore shi ba.

Rashin Girmama Na Gaba: Wanda shi ma ya ƙara durƙusar da zamantakewa ƙwarai da gaske. Domin idan aka dubi baya a zamanin da, zamu ga cewar an san Bahaushe da girmama na gaba da shi. Don ba a gida ɗaya ba, ko a unguwa ɗaya ake, da zarar a ka ce ga wani babban wanda ake girmama shi. Haka kuma da zarar babba ya yi magana a kan wani abu zai yi a saɓa. Duk kuma abin da ya hukunta, ko mene ne ya zauna, babu mai tayarwa, saboda irin matsayinsa.

Bayan haka kuma, a da akan samu biyayya a tsakanin ‘yan uwa kamar wa (yaya) yana da iko a kan ƙaninsa. Ma’ana in ya yi hukunci ta zauna. Haka shi kuma ƙanin ba shi da ikon ya yi jayayya, don biyayya tare da girmamawa. Haka kuma yake har a kan ‘ya’yansu. Shi kuma wannan na da ikon yin hukunci da na ‘yan uwa, babu wata fargaba, don ya san ya fi ƙarfin abin.

Kai ko babu jinin dangantaka a tsakani, ko ta abota ta haɗa mutum da iyaye wani. To sai ka samu ana girmama wannan mutum a matsayin uba. A wannan zamani abin ya zamanton saɓanin haka. Gurɓacewar halayen mutane, wanda ya sa suka yi watsi da waɗannan lamuran yasa zumunci da aka sani a tsakanin Hausawa ya yi rauni. Kowa kansa ya sani, to amma sai wasu na ganin cewa ci gaba ne.

12.0 TO JAMA’A INA MAFITA?

Dole ne mu gyara yanayin mu’amalla a tsakaninmu, saboda shi zai kyautata zamantakewarmu ta hanyar mu faɗawa juna gaskiya. Mu kiyayi duk wani aiki ko wani abu wanda zai kawo saɓani a tsakaninmu. Mu tsaya mu natsu mu san kan mu da darajar da Allah ya ba mu.

Zuciya: In gyara zuciyata, kai ma ka gyara zuciyarka, ke ma ki gyara zuciyarki.
Harshe: In riƙe harshena, kai ma ka riƙe harshenka, ke ma ki riƙe harshenki.
Hannu: In riƙe hannuna, kai ma ka riƙe hannunka, ke ma ki riƙe hannunki.
Ido: In kiyaye idona, kai ma kiyaye idonka, ke ma ki kiyaye idonki.
Amana: Tsare amana ta kaya, ko dukiya, ko ta Magana.

Gaskiya: Mu rungumi gaskiya, mu faɗi gaskiya, mu yi aiki da gaskiya.
Tausayi: Mu tausayawa junanmu a ma’amalla ta kowace fuska.
Biyayya: Mu girmama na gaba da mu a mu’amallarmu.
Kunya: Mu yi amfani kunya a rayuwarmu domin reshe ne na imani.
Ƙarya: Mu kiyayi ƙarya a maganganunmu da ayyukanmu.

Kwaɗayi: Mu kaucewa kwaɗayi ta kowace fuska.
Son abin Duniya: Mu rage dogon buri.
Girmama kuɗi: Mu rage bai wa kuɗi muhimmanci fiye da mutunci.
Tsageranci:Mu guje shi domin shi ne, tushen fitna.
Ha’inci: Mu guji yinsa, domin yana ɓata dangantaka.
Wayar hannu: Mu yi hattara da wayar hannu, tsegumi da gutsuri-tsoma.

KAMMALAWA;

A ƙarshe wannan takarda, ta tsakuro wasu abubuwa a kan rayuwar matasa da matsayinta a wannan zamani tare da tsokaci a kan mahimmancin Matasa a rayuwar al’umma. Haka kuma tare da fito da ma’anar matasa da alaƙarsu da tasirinsu ga rayuwar Bahaushe jiya da yau, sauye-sauye da rayuwar Bahaushe ta gamu da su, tare da gano hanyoyi, ko dalilan da suka jawo waɗannan sauye-sauye.

Ban da wannan kuma, za a dubi irin yadda hakan ya shafi al’adu, da ɗabi’un Bahaushe, har da rayuwarsa gaba ɗaya. Daga nan sai a hararo fa’idojin samu matasa na gari masu tarbiyya, da kuma illolin gurɓatattun matasa marasa tarbiyya. Bayan wannan kuma an ɗan tsakuro wasu daga cikin haƙkoƙin yin tarbiyya tare da nuna irin nauyin da rataya a wuyan mahaifa, da Hukuma,da al’umma. Allah Ya tsare mu Ya bamu ikon gyarawa amin. Assalamu alaikum

MANAZARTA.

Alhassan H. D (1982) Zaman Hausawa. Islamic Publication Bureau,
Lagos.
Bunza A.M.(2006) Gadon feɗe al’ada. Tiwel Nigeria Limited Surulere,
Lagos.
Banbale M.B.(1994) Kukan Kurciya. Ibramud Nigeria Limited, Zaria.
Ɗangambo A. (1984) Rabe-Raben adabin Hausa da Muhimmancinsa ga rayuwar Hausawa.Triunph Publication Kano.
Ɗangambo A.(1983) Kitsen Rogo. Triunph Publication Kano..
Ɗahiru B (2007) Tafsirin Watan Ramadan. Rediyo Najeriya Kaduna.
Imam A.(1937) Magana Jar ice na 1, da 2, da 3.Northern Nigerian Publication Company, Zaria.
Madauci I.(1963)Al’adun Hausawa. Northern Nigerian Publication Company,
Zaria.
Sadiya G.Y. (2005) Talauci Hauka ne? Super Prints Press, Kano.
Williams B.(1979) Human Design.Harvard University Printed USA.
Yaro Y.I. (1971)Tatsunniyoyi da Wasanni. Oxford University Press,
Ibadan.
Zindani A.A.(2000) Human Development. Muslim World League Printing Press.
Saudi Arabia.
Sarki H.A (2000) Zuwan Musulunci a Afirka da shigowarsu Ƙasar Hausa.
G.A. Computer Centre. Ikere – Ekiti, Ekiti State.
Ɗanfodiyo S.U. (2002)Faɗakar da ‘Yan’uwa a kan halayyar Ƙasar Sudan.
(Fassara) Muhammad Mode Shuni. C.I.S Usman Ɗanfodiyo University,
Sokoto.

Don karanta Buki A Bahaushen Tunani

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceFasalin Ƙagaggun Labaran Hausa A Zamanin Zuwan Turawa
Labarin na GabaFasalce-Fasalcen Adabin Kasuwa