Kiɗa Da Waƙoƙin Makaɗa Musa Ɗanƙwairo

0
10

Kiɗa da waƙa ta baka wani fage ne wanda yawancin makaɗa masu tunani da ƙwaƙwalwa da fasahar shirya kalmomi; musamman ta fuskar zaɓensu da baiwa ta hangen nesa da furuci mai cusa tarbiyya ta ruhi da ta gangar jiki suke aiwatarwa ga al’ummominsu.

Wasu ladubban waƙoƙin baka sun haɗa da bayanai na tarbiyyatarwa da faɗakarwa da jan hankali; zuwa ga kyawawan ayyuka da halaye na gari, musamman waɗanda al’umma da addinin al’umma suke aiki da su.

Domin haka, waƙar baka ta ƙunshi wasu matakai da sigogi na aiwatarwa wato shiryawa da ƙullawa; da kuma rerawa tare da sadar da ita ga al’umma. Kuma waɗannan su ne suke ɗaukar hankalin al’umma wajen sauraron waƙoƙin baka da aiki da su.

Makaɗin baka yakan zama tilas ya san waɗannan ladubban waƙar baka; waɗanda Allahu yake yi masa ilhama da su ta hanyoyin koyo da biyayya ko jibilliyya ko bisa wata buƙata ta rayuwa.

Domin karanta cikakken bayani akan Musa Ɗanƙwairo a Koyo da Biyayyar Waƙa danna nan.

Domin karanta cikakken bayani akan Mawaƙan Da Ake Yi Wa Kiɗan Fiyano danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceTarihin Sheikh Malam Muhammad Ɗan Almajiri
Labarin na GabaTatsuniyar Ɗankaɗafi
Prof. Sa’idu Muhammad Gusau
FARFESA SA'IDU MUHAMMAD GUSAU, An haife shi a Gusau jihar Sakkwato, (Maris 24, 1952). Ya yi karatun firamare na Islamiyya daga 1965-1969, ya je kwalejin sarkin Musulmi Abubakar daga Junairu 1970 zuwa Yuni 1973. Ya yi Diploma, Digiri Na farko (B.A), na biyu (M.A) da Digiri na uku (Ph.D) duk a jami'ar Bayero, Kano.