MOHAMMED BALA GARBA
Rabbana tuba nake yi,
Nayi saɓo ba kaɗan ba.
Na yi alƙawari gare ka,
Zan yi bauta ba da ɗar ba.
Dana zo shaiɗan ya ja ni,
Ban yi bautar ko kaɗan ba.
Ya raba ni da kai masoyi,
Bai bari na zaunu lau ba.
Ya hana ni saninka Allah,
Bai bari nai ilimi ba.
Shi yake ta zuga gare ni,
Ko zumunta ban idar ba.
Ka hana ya sa ni nayi,
Ban tunanin zunubai ba.
Ka umarta ya hana ni,
Bai bari na aikata ba.
Ya haɗa ni Walidaina,
Ba su yo fahari da ni ba.
Nai wulakanci ga bayi,
Ban ragwantawa na jini ba.
Kuma na yayyaɗa karya,
Ban ko binciki gaskiya ba.
Na yi sata na yi karce,
Ban ji tausan ‘yan uwa ba.
Na yi zunɗe na yi gulma,
Nai harara ba kaɗan ba.
Na yi zamba cikin amince,
Duk da dai ba ka fallasa ba.
Na yi shaidar zur a fili,
Ban tunanin mutuwa ba.
Kana na ha’inci bayi,
Har maƙwabta ban bari ba.
Rabbi nai wasa Sallah,
Ban yi san da kace a yo ba.
Ka haramta na halarta,
Ban zaton haɗuwa da kai ba.
Babu mai ikon hana ni,
Ko ya ce nayi ba da ni ba.
Duka na’u’o’in kaba’ir,
Ɗanbala bai bar guda ba.
Duniya ita ce ƙawata,
Ko da ɗai ba ta kunyatan ba.
Ban tunanin za na ƙaura,
Gunka wai domin na tuba.
Ba shiri mutuwa ta zo min,
Ba ta yo sallama da ni ba.
‘Yan uwana nata kuka,
Ba su so mutuwa a nan ba.
Suka min suturar Musulmi,
Ba su ce Allah tir da ni ba.
Har waɗanda na yi wa cuta,
Suka zo mini ba kaɗan ba.
Suka min sallah da roƙon,
Gafara ba su gajiya ba.
Suka kai ni cikin kushewa,
Addu’a ba su daina yi ba.
Suka juya za su koma,
Nai kiran ba su waiwayo ba.
Daga nan na gano bala’i,
Ban zaton haka a ciki ba.
Ga duhu zafi macizai,
Ko kaɗan ba su tausayan ba.
Sai Mala’iku sukka zo,
Ba su yo sallama da ni ba.
Suka min wasu tambayoyi,
Ban ko amsa guda ciki ba.
Daga nan na shige masifa,
Wanda ban yi zaton gani ba.
‘Yan uwana sai mu farga,
Duniya ba gun zama ba.
Za mu girbi abin da mukkai,
Walla ba maganar wasa ba.
Rabbana shirye mu Allah,
Rabbi ba don nai batu ba.
Har iyayye da ‘yan uwana,
Da Musulmai ban baro ba.
Rabbana ninko salati,
Ga Rasulu ba ka ƙi ya ba.
Ɗanbala daga Borno yai ta,
Ɗan Bahaushe ba Ibo ba.
©
Mohammed Bala Garba
8:27pm
13 August, 2024
Karanta Duka A Murɗe
Edita@rumasau-kallamu