Author: Mubarak Abubakar

  • Nasiha A Kan Mata

    Nasiha A Kan Mata

    MATA 10 WAƊANDA  ALLAH YA TSINE MUSU: –

    ﺍﻟﻮﺍﺷﻤﺎﺕ ﻭﺍﻟﻤﺴﺘﻮﺷﻤﺎﺕ
    1. Mata masu tsaga fuskokinsu. –

    ﺍﻟﻨﺎﻣﺼﺎﺕ ﻭﺍﻟﻤﺘﻨﺼﻤﺎﺕ

    2. Mata masu aske gashin gira. –

    ﺍﻟﻤﺘﻔﻠﺠﺎﺕ
    3. Mata masu kankare hakori (wushirya). –

    ﺍﻟﻮﺍﺻﻠﺔ ﻭﺍﻟﻤﺴﺘﻮﺻﻠﺔ
    4. Mai ‘karin gashi da wadda ake ƙara mata gashi. –

    ﺍﻟﺘﻲ ﺳﺨﻂ ﻋﻠﻴﻬﺎ ﺯﻭﺟﻬﺎ
    5.Matar da mijinta ya yi fushi da ita. –

    ﺍﻟﻤﺘﺸﺒﻬﺎﺕ ﺑﺎﻟﺮﺟﺎﻝ
    6. Mata masu shigar maza.

    ﺯﻭﺍﺭﺍﺕ ﺍﻟﻘﺒﻮﺭ
    7. Mata masu yawan ziyartar kabur-bura (maƙabarta).

    – ﺍﻟﻨﺎﺋﺤﺎﺕ
    8. Mata masu kururuwa akan mamaci. –

    ﺍﻟﻤﺤﻠﻞ ﻟﻪ
    9. Mata masu auren kashe wuta. –

    ﻛﺎﺳﻴﺎﺕ ﻋﺎﺭﻳﺎﺕ ﻣﺘﺒﺮﺟﺎﺕ
    10. Mata masu bayyana tsiraicinsu.

    Ka da ku manta TSINUWA ita ce nisanta daga rahamar Allah!
    ﻗﺎﻝ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ : ” ﻳﺎﻣﻌﺸﺮ ﺍﻟﻨﺴﺎﺀ ﺗﺼﺪﻗﻦﻭﺃﻛﺜﺮﻥ ﻣﻦ ﺍﻹﺳﺘﻐﻔﺎﺭﻓﺈﻧﻲﺭﺃﻳﺘﻜﻦ ﺃﻛﺜﺮ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻨﺎﺭ ” ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ
    Manzon Allah (SAW) ya ce: ‘Yaku taron mata! ku yi sadaƙa, kuma ku yawaita neman gafara (Istigifari) Allah ya gafarta Mana.

    Danna nan don karanta Abin Da Ya Kamata Mu Sani

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Nasiha A Kan Rayuwa

    Nasiha A Kan Rayuwa

    Manzon Allah tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi Yana cewa, “Ku yi ƙoƙarin danne abubuwa guda uku a cikin ranku, da rayuwarku.”

    1. Fushi
    2. Sha’awa
    3. Maganganunku.

    Ku himmatu wajen aikata abubuwa biyu:

    1. Ayyukan alhairi.
    2. Abokai na gari.

    Ku ci moriyar abubuwa uku:

    1. Ƙarfi
    2. Lokaci
    3. Lafiya.

    Ku nemi abubuwa uku:

    1. Gafarar Allah
    2. Ilimi
    3. Hikima.

    Allah ya ba mu ikon kiyayewa.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

    Domin karanta Nasiha danna nan

  • Sunnonin Ranar Juma’a

    Sunnonin Ranar Juma’a

    Ranar Juma’a, rana ce ta musamman a wurin Musulmai, rana ce babba, mafi daraja daga sauran ranakun mako. Rana ce da Allah ya zaɓa, kuma aka farlanta ibada ta sallah mai daraja a cikin ta. Rana ce da Allah SWT ya saukar da surah guda da sunanta.

    Saboda muhimmancin ranar, akwai wasu ɗabi’u da halaye da ladubba da ake so musulmai su riƙa aikatawa a kowacce ranar Juma’a.

    1. Yin wanka
    2. Sanya Turare
    3. Sanya tufafi masu kyau
    4. Yin asuwaki
    5. Neman dacewa da lokacin amsar addu’a
    6. Karanta Suratul Kahf
    7. Tafiya masallaci da wuri.
    8. Yawaita salati ga Annabi S.A.W.

    Allah ya ba mu albarkar ranar Juma’a.

    Danna nan don karanta Shakku a Cikin Sallah

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

     

  • Sakamakon Alheri, Alheri Ne

    Sakamakon Alheri, Alheri Ne

    1. Ka ciyar Allah Ya ciyar da kai.
    2. Ka tufatar Allah Ya tufatar da kai.

    3. Ka taimaka Allah Ya taimaka maka.
    4. Ka rufa asirin wani Allah Ya rufa naka.
    5. Ka yaye wa wani damuwa Allah Ya yaye maka damuwar ka.
    6. Ka tausaya Allah Ya tausaya maka.
    7. Ka sauƙaƙa Allah Ya sauƙaƙa maka.
    8. Ka agaza Allah Ya agaza maka.
    9. Ka bayar Allah Ya ba ka.
    10. Ka tallafa Allah Ya tallafa maka.
    11. Ka miƙa Allah Ya miƙo maka.
    ‘Yan uwa mu yawaita alheri, domin alheri danƙo ne, ba ya faɗuwa ƙasa banza. Allah ya sa mu dace alfarmar Rasulullahi da Alƙur’ani.

    Domin karanta Nasiha Mai Tsoratarwa danna nan

    Edita; Rumasa’u m. kallamu

     

  • Mu Koyi Addini Kashi Na Biyu

    Mu Koyi Addini Kashi Na Biyu

    KAN FASALIN ALWALA

    • Wanda ya manta da wata farilla daga gaɓoɓinsa, idan ya tuno sai ya aikata ta da abinda ke bayanta, idan kuma ya yi nisa sai ya aikata ta ita kaɗai, ya kuma sake abinda ya sallata bayan faruwar abin.

    • Idan kuma ya bar sunna, to sai ya aikata ta ita kaɗai ba zai sake sallah ba.

    • Wanda kuma ya mance lam’a sai ya wanke ta ita kaɗai da niyya, in kuma har ya yi sallah bayan faruwar hakan toh sai ya sake ta.

    • Wanda ya tuna da kurkurar baki ko shaƙa ruwa bayan ya riga ya ya fara wanke fuska, to ba zai dawo gare su ba har sai ya gama alwalarsa, sannan sai ya yi su.

    • Tsettsefe ‘yan yatsun hannuwa yana wajaba, an so a tsettsefe ‘yan yatsun ƙafafuwa, tsefe gemu mara duhu yana wajaba a cikin alwala, tsefe gemu yana wajaba a cikin wanka koh da mai duhu ne.

    AKAN FASALIN ALWALA (2)

    • Ba ya halatta ga wanda ba shi da alwala ya yi sallah, koh ɗawafi, ko ya taɓa Alqur’ani ko da a cikin gafakarsa ne, ba da hannunsa ba sai dai idan juzu’i ne ga mai neman ilimi a cikinsa.

    • Yaro a wajen taɓa Alqur’ani kamar babba yake, amma laifin yana wuyan wanda ya ba shi Alqur’anin ya taɓa.

    • Wanda ya yi sallah da gangan ba tare da alwala ba to shi kafiri ne. Allah ya kiyashe mu.

    Danna nan don karanta Mu Koyi Addini Kashi Na Farko

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Mu Koyi Addini Kashi Na Farko

    Mu Koyi Addini Kashi Na Farko

    Farillan alwala guda 7 ne:
    • Niyya
    • Wanke Fuska
    • Wanke hannaye zuwa gwuiwar hannu
    • Shafar kai
    • Wanke ƙafafuwa
    • Cuccuɗawa
    • Gaggautawa

    SUNNONIN ALWALA

    • Wanke hannaye zuwa wuyan hannu
    • Kurkure baki
    • Shaƙa ruwa
    • Fyacewa
    • Juyo da shafar kai
    • Shafar kunnuwa
    • Sabunta ruwa a garesu
    • Jeranta tsakanin farilla

    MUSTAHABBAN ALWALA

    • Yin bismilla
    • Goga asuwaki
    • Ƙari akan wankewa ta farko a fuska da hannaye
    • Farawa daga goshi
    • Jeranta sunnoni
    • Ƙaranta ruwa a bisa gaɓoɓi
    • Gabatar da dama kafin hagu.

    Danna nan don karanta Nasiha

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Tarbiyyar Yara

    Tarbiyyar Yara

    KU KOYAWA YARANKU HALAYE UKU:

    1. Yawan gaishe da na gaba da su.
    2. Nutsuwa da barin wasa a hanya.
    3. Fita cikin kyakkyawar shiga.

    KU HANA YARANKU HALAYEN NAN:

    1. Yawan yawace-yawace.
    2. Yawan Abokai/ƙawaye barkatai.
    3. Rashin kunya da faɗace-faɗace.

    KU RIƘA GWAƁE BAKIN YARANKU:

    1. Idan suna sa baki a maganar manya.
    2. Idan suna kawo tsegumi da gulma.
    3. Idan suna zagi ko ƙaryata manya.

    KU YI MUSU HORO MAI TSANANI:

    1. Idan suna wasa da Sallah.
    2. Idan suka fara kwaɗayi da roƙo
    3. Idan suka fara ƙarya da lalaci.

    KU ƘARA JAWO YARANKU JIKI:

    1. Idan suka balaga.
    2. Idan ba su da lafiya.
    3. Idan kuna gida a zaune.

    KU KWAƊAITAR DA YARANKU:

    1. Nacin karatu da rubutu.
    2. Dagewa wajen cimma buri.
    3. Lada da nasara in an bi hanyar Allah.

    KU NUNAWA YARA MUHIMMANCIN:

    1. Riƙo da addinin musulunci.
    2. Zumunci da ziyarar dangi.
    3. Lafiya, lokaci da chance/ƙuruciya.

    KU DAINA WAƊANNAN A GABANSU:

    1. Bayyana tsiraici/mu’amalar aure.
    2. Wasan banza na ƙuruciya, kallo.
    3. Bayyana rashin jituwa a tsakaninku.

    KU YAWAITA A GABAN YARANKU:

    1. Karatun Alƙur’ani da salloli.
    2. Aikata gaskiya da riƙon amana.
    3. Wadatar zuci da godiyar Allah.

    SUKE JIN TSORON KU TA HANYAR:

    1. Tsawatar musu in sun zo da wargi.
    2. Rashin barinsu babu abin yi.
    3. Taƙaita nuna musu so ƙuru-ƙuru.

    KU DAGE KU CIREWA YARANKU:

    1. Tsoron mutuwa.
    2. Tsoron talauci.
    3. Tsoron wanda ba ya tsoron Allah.

    KU GOYI BAYAN YARANKU IN HAR:

    1. Su ne ke da gaskiya.
    2. Ba saɓo suka aikata ba.
    3. Sun yi abu domin kare mutuncinku.

    KUKE TSORATAR DA YARANKU:

    1. Illar haɗama.
    2. Fitinar rigima.
    3. Haɗarin taƙama da girman kai.

    KU RIƘA SANAR DA YARANKU:

    1. Asali da tarihi.
    2. Mutuwa da kabari.
    3. Daɗi da rashin sa.

    KU BA WA YARANKU HORO NA:

    1. Taƙaita cin abinci.
    2. Ƙarancin bacci da zaman hira.
    3. Watsar da dogon buri da sharholiya.
    Allah ya ba mu ikon tarbiyyar yaranmu.

    Don karanta Ra’ayin Wani Masani Game Da Tasirin Bincike A Rubutu danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Rijistar CAC Da Muhimmancinta

    Rijistar CAC Da Muhimmancinta

    Menene CAC Certificate?

    CAC (Corporate Affairs Commission) shi ne certificate ko kuma shaida ce da ake yi wa sana’a babba ko kuma ƙarama. Wannan shaida ta CAC ita ke ba da dama mai yawa a gwamnatance ko daga ɓangaren ƙungiyoyi masu zaman kansu.

    Kowanne kasuwanci yana ƙara inganta ne idan ya kasance ya mallaki wannan shaidar ta CAC, kuma kowa kan yi ƙoƙarin hulɗa da kai ba tare da kokwanto, ko kuma tunanin cutarwa ba.

    A lokuta da yawa da suka wuce gwanatin tarayya da ta jiha sukan ƙirƙiro wani tsare-tsare da za a tallafawa ‘yan kasuwa amma saboda rashin wannan shaida ta CAC kaɗan ne daga cikin al’umma suke amfana, a bayannan gwamnatin tarayya ta fitar da tsarin Survival Fund amma waɗanda suka mori tsarin cikin kwanciyar hankali su ne waɗanda suke da CAC Certificate.

    A wannan gaɓa nake shawartar ‘yan kasuwa manya da ƙanana da su je su yi wannan Certificate na CAC domin yana da matuƙar mahimmanci ga kasuwancin gida da waje.

    Danna nan don karanta yadda ake addu’ar shiga kasuwa

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Menene Writer’s Block?

    Menene Writer’s Block?

    Writer’s block, yanayi ne da marubuci ko marubuciya ke jin kasalar kasa rubutu kwata-kwata, ko kuma an fara rubutun a ji an gaji ba a so a ci gaba. Haka nan writer’s block, na iya zama kufcewar basira yayin rubutu, wato a nemi basira sama ko ƙasa a rasa.

    Shin kun taɓa fuskantar irin wannan yanayin? Idan irin Haka ta faru me ya kamata marubuci ko marubuciya su yi?

    1. Barin rubutu na ɗan wani lokaci, ƙwaƙwalwa ta huta, wato a samu hutu. Yin hakan zai taimaka tunanin mutum na abin da ya kamata ya rubuta ya dawo.

    2. Sauya muhallin zama: wato mutum ya bar wurin da yake zaune zuwa wani sabon wuri daban, hakan zai taimaka masa sosai.

    3. Yin abubuwa da suka shafi nishaɗi, lamar wasannin mosta jiki, kallon fim, ko sauraron kaɗe-kaɗe.

    4. Tafiya, wato mutum ya bar wurin ya yake ya yi tafiya, da yake an ce tafiya mubuɗin ilimi.

    Danna nan don karanta Amfanin Yin Bincike A Rubutu

    Edita; RMK

  • Nasiha A Kan Maganganun Mutane

    Nasiha A Kan Maganganun Mutane

    An tambayi Imam Hasanul Basari?
    Me ya sa ba ka damuwa da maganganun mutane? Sai yace,

    “Lokacin da aka haife ni, ni kaɗai aka haifa,
    Kuma lokacin da zan mutu, ni kaɗai zan mutu
    Kuma ni kaɗai zan kwanta a kabarina,
    Kuma ni kaɗai za a tashe ni a yi min hisabi.
    Kuma ni kaɗai za a ba sakamakona,
    Don haka ina ruwana da maganganun mutane?

    Domin in dai maganganun mutane shi ne damuwarka, sai dai idan ba ka shirya zaman duniyar ba.” Allah ya datar da mu.

    Danna nan don karanta Nasiha mai tsoratarwa

    Edita; Rumasa’u M. kallamu