Tarihin Garin Kudan

0
7

BABI NA ƊAYA
Allah mai yin yadda Ya so. Garin Kudan, tsohon gari ne da ya ginu bisa mutunci, tsoron Allah da kuma kishin al’umma. Tsuntsaye sukan tashi da sassafe suna rera waƙar alfijir, iska tana taɗa ganyayyaki kamar mai kiran mutane zuwa sabuwar rana. Ko da yake gari ne na tarihi, amma yana da zuciya mai sabuntawa kamar ruwan rafi da ba ya gushewa.

A tsakiyar wannan gari ne ake samun jarumin da tarihinsa ya cika duniyar maƙwabta,wato mai girma Hakimin Kudan (Alhaji Ishaƙ Ashir), mutum mai tarbiyya, mai hangen nesa da kuma don ginshiƙin zaman lafiya. Hakimi mutum ne da ake cewa:

“In ka ji ana yabon gida, to ka san akwai wanda ya kafa.”
A zamaninsa, Kudan ya ɗauki salo na ci gaba, wanda ba kowa ba ne zai iya jagoranta ba. Mutanensa suna kiransa “Uban Kowa,” domin ko gida na makoki ne ko na suna, ko ɗaurin aure, ko taron al’umma, sai ka gan shi cikin mutane, ba tare da girman kai ko zunzurutun mulki ba.

Allah ya yi masa tarin tulin baiwa ta samun ‘ƴa’ƴaye mata da maza kamar: Halima, Mariya, Hindatu, Usman (Ɗanladi), Nafi’u, Balarabe, Isma’il, Mas’ud, Gaddafi, Nasiru, Imrana, Abdulshahid, Umar, Abubakar, Yunusa, Muzammil, Sha’awanatu, Furaira (Hajiyayye), Karimatu, Aisha, Shamsiyya, Raliya… jerin sunaye da ke kamar gini-gini masu ɗora gari kan tushe.

Hakimi kalmarsa ɗaya: “Gari ba ya ci gaba sai al’umma sun zama tamkar juna.”

Ranar damuwa

Ranar Lahadi, 3 ga Yuni 2024, wannan gari mai farin ciki ya shiga duhu. Rana ta fito, amma kamar ba ta da ƙarfi. Tsuntsaye ma sun yi shiru, tamkar suna jin wani abu mai nauyi na shirin faruwa. Sai labari ya bazu cikin ‘yan mintoci:
“Hakimi ya rasu…!”

Kalmar ta yanke zukata tamkar takobi. Mata suka zube suna hawaye, maza suka tsaya cak tamkar dutse. Kudan ta yi shiru, irin shiru mai ciwo. Wani dattijo ya ce:
“Mutum mai kyau idan ya tafi, gari yakan yi kamar ya faɗi.”

Mutanen garin sun yi zaman makoki, sun yi kuka, amma kuma suka yi nazari, domin Hakimi ya riga ya bar saƙon da ba ya mutuwa: al’umma su zama ɗaya.
Bayan jana’iza, gari ya cika. Mutane sun tashi da kalmar:
“Idan ka ga alheri ya dusashe, to ka san akwai wanda bai tsaya a kansa ba.”
A wannan rana aka fara sabuwar tafiya.

BABI NA BIYU

Ranar da aka binne Hakimi, dare ya sauka da wata irin nutsuwa da ba a saba gani ba. Kafin wannan lokaci, Kudan gari ne da yake da annuri da hayaniya, amma wannan dare ya yi kamar an ɗaure shi da sarƙar jimami. Ko iska tana motsawa cikin ladabi saboda mutumin kirki ya yi hijirar da ba a dawo wa.

Amma cikin wannan nutsuwa akwai wani haske da ba kowa ke gani ba, wato hasken da ke fitowa daga zukatan waɗanda Hakimi ya taɓa rayuwarsu da kyawawan ayyuka. Kamar wutsiyar wuta a duhun daji, hasken na neman ya tayar da mutanen gari daga dogon tunani.

Farfesa Mu’azu (Makiyayi mai raya zukatan mutane da ilimi)

Bayan sallar Isha’i, Farfesa Mu’azu ya zauna a gindin bishiyar ɗorawa a cikin gidansa, yana kallon taurari tamkar yana karanta tarihin mutane cikin sararin samaniya. Shi mutum ne mai nutsuwa, mai hikimar magana irin ta magabata. Ana cewa:

“Idan ka ga dattijo yana shiru, ka sani yana magana da zuciyarsa.”
Ya shaida rayuwar Hakimi, ya san jajircinsa, kuma ya yi imani cewa “labarin gari” ba zai kammala ba sai an rubuta tarihin waɗanda suka wakilci zuciyar jama’a. Saboda haka, ya zaro littafi ya fara rubutu cikin dare, yana cewa:

“Ba don jarumtakarsa kaɗai ba, amma don darasin da ya bar mana.”
Farfesa Mu’azu mutum ne da ke haɗa mutane, mai sauƙin kai, mai taimakon marayu, mai ɗaukar nauyin ɗalibai. Hakan ya sa mutane suke kallonsa tamkar hasken fitila a duhun daji. Mutane suna cewa:

“Mai ilimi kamar ruwan sama ne; ko ka ƙi, ko ka so,idan ya sauka, ya yi maka alheri. Shi ne ya fara kiran al’umma zuwa taro a fadar masarauta, bayan kwana uku da rasuwar Hakimi.

Malam Aliyu Labaran (Damo sarkin haƙuri)

A cikin jama’ar Kudan, akwai gwarzon da ba shi da aiki sai ibada da ilimi, wato Malam Aliyu. Mahaddacin Alƙur’ani ne mai ladabi, mai haƙuri da juriya. Idan ya yi magana, harshensa ya yi taushi kamar ruwan zuma.

A taron farko bayan rasuwar Hakimi, shi ya tsaya ya ce: “Gari kamar jiki ne, idan ɗaya ya ji zafi, dukkan su sun ji. Don haka mu yi aiki tare, don cike giɓi. ”Kalmar ta shiga zukata tamkar wuta a cikin busasshiyar ciyawa.

Malam Surajo Yunusa (bango majingina)

Kodayake Malam Surajo ya rasu tun 06/04/2017, amma mutanen gari suna yawan tuna wa da shi. Mutum ne da ya rayu wajen koyar da mutane Alƙur’ani, yana zuwa gidaje ɗaya bayan ɗaya yana cewa: “Ilimi shi ne garkuwar mai rai.”

Rayuwarsa ta zama misali ga matasa. A wannan lokacin da ake neman sabuwar hanya, mutane da yawa suka fara tunanin yadda Malam Surajo zai yi da ya kasance a raye. Wannan tunanin ne ya fara tayar da sha`awar komawa makarantu da karatu.

Idan ka yi tafiya cikin dare a Kudan, za ka ji matasa suna karanta Alƙur’ani a ƙananan makarantun allo da ya bari. Wani kamar ya ce: “Mutum ya mutu, amma alherensa suna raye.”

BABI NA UKU

A gefe guda kuma, Salmanu Faris wanda ya kasance matashi, marubuci, manomi, ɗan jarida kuma almajiri. Bayan bayan taron sai ya ɗora alƙalamin rubutu. Idanunsa sun yi ja, saboda rashin bacci, amma zuciyarsa cike take da wuta irin wutar da ta ratsa zuciyar mai son ci gaban gari. Shi ne ke cewa:

“Idan ka ga gari ya tashi, to matasa sun ce ba za su yi shiru ba.”

Faris ya ga mutanen gari sun shiga tunani, kuma ya yanke shawarar cewa wannan shi ne lokacin da zai tashi tsaye ya rubuta labarin mutanen gari, ya faɗaɗa tunani, ya tunzura matasa, ya yaɗa kiran ci gaba a kafafen sada zumunta da jaridun yankin.

Shigowar Mawaƙa (Murya Mai Ƙarfafa Zuciya)

Labaran, Ashiru, Salahu, Ali (Na Annabi) da Rabilu, su ne mawaƙa, sha’irai, kuma manoma. Sun saba da rubutu da waƙoƙi, amma wannan lokaci suka fito da wani sabon salo. Suna cewa:

“Waƙa ba ta zama waƙa ba sai ta gina zuciya.”

Suka shirya waƙar “Rayuwar Hakimi” wadda ta zama kamar taken sabon tafiya. Yara da matasa suka rera kanta a tituna, manya suka saurare ta cikin kukan sha’awa. Ta zama kamar ƙaho na farfaɗo da al’umma.

Kungiyar Malamai (Garkuwar Zuciya da Ilimi)

Auwal, Salim, Abdulrazaƙ, Abdulhafiz, Sani, Salisu, Abba, Yahaya, Abubakar, Muhammad (Prof), Yasir, su ne suke riƙe da guraben ilimi. Wanda suka kasance malamai na boko da na addini, duk masu haƙuri, nutsuwa da hangen nesa.

Suka yi taro suka yanke shawarar:

1. A buɗe darussa na koyar da rubutu da karatu.

2. A ƙarfafa zaman lafiya.

3. A koyar da matasa sana’o’in dogaro da kai.

4. A fahimtar da al’umma mahimmancin zaman lafiya.

Malam Auwal ya ce:

“Idan ka ilimantar da ɗa, ka ilimantar da al’umma baki ɗaya.”

Abubakar Suleiman (mutum na mutane)

Abubakar, matashi mai arziki, kuma ɗan kasuwa. Ya yi na’am da wannan sabuwar tafiya. Mutum ne da ke da juriya da zuciya mai tausayin talakawa. Ya ce:

“Ku kafa tsari, ni kuma zan tallafa.”

Nan take ya ɗauki matasa 25 aiki, ya ba da kayan aiki, ya ba da tallafi ga makarantu da masu koyarwa. Mutane suka fara ce wa juna:

“Gari zai tashi. Gaskiya gari zai canza.”

Karanta Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTatsuniyar Ɗankaɗafi