Tag: #nasiha

  • Kira A Kan Haɗin Kai

    Kira A Kan Haɗin Kai

    ‘Yan Najeriya muna cikin wani muhimmi lokaci. Wata mummunar fahimta tana shiga cikin al’ummarmu, tyana canza yadda muke kallon ‘yan-uwanmu da kuma rage darajar kanmu da ƙaunar ‘ƴan’uwanta da ta kasance tana bayyana mu.

    Dole mu dakata mu yi wa kanmu wata muhimmiyar tambaya: a cikin rayuwarmu ta yau da kullum don neman abinci da ci gaba, shin mun taɓa tunanin addinin manomi wanda ya noma shinkafar da muke ci? Shin muna tambayar addinin likitan da ya rubuta maganin da ya ceci rayuwarmu? Idan muka buɗe famfo, shin muna tunanin ko injiniyan da ya tsara tsarin ruwan yana da aƙidarmu?

    Amsar ba ta da shakku, ’A a’. Ba mu yi haka ba. Muna saye, muna ci, kuma muna rayuwa, muna dogaro ga juna a cikin hanyar da ba a iya rabuwa. Rayuwarmu ta yau da kullum shaida ce mai ƙarfi game da haɗin kanmu.

    To, me yasa, a wasu fannonin rayuwa, muka ƙyale a raba mu? Me yasa muke tallata bambance-bambancen addini alhali kuwa tarihinmu na gaba ɗaya ya faɗi wani labari daban?

    Mun yi yaƙi don ‘yancin kanmu tare, a matsayin mutane ɗaya tare da manufa guda. Mun zauna tare a cikin ajujuwa, muna koyo daga malamai ɗaya, muna mafarkin makoma guda ga Najeriya. Muna ciniki tare, muna murna tare, muna makoki tare.

    Wannan rarrabuwa ba hanya ba ce ta Najeriya. Guba ce da ke raunana mu da kuma hana mu ci gaba. Duk gidan da ya rabu da kansa ba zai iya tsayawa ba, balle ya ci nasara a rayuwa.

    Hanyar Ci Gaba: Komawa ga Ƙimar Mu Na Gaba ɗaya

    Don maido da girmanmu, dole ne mu zaɓi haɗin kai da juna. Ga yadda za mu iya farawa:

    1.  Yi Bikin Asalin Mu Guda: Ganin kanmu a matsayin ‘yan Najeriya—’yan’uwa maza da mata na al’umma ɗaya. Imaminmu wani ɓangare ne na asalinmu, ba makami da za a yi amfani da shi a kan maƙwabci ba.

    2.  Ƙarfafa Tattaunawa: Ƙarfafa tattaunawar addini a cikin al’ummominmu. Bari shugabannin mu na addini su yi wa’azin soyayya da haƙuri. Lokacin da muka yi hira, muna rushe ganuwar tsoro da rashin fahimta.

    3.  Mai da hankali kan Manufofi Guda: Talauci, jahilci, da rashin ingantaccen tsaro wannan ba sa bambanta tsakanin Musulmi da Kirista. Waɗannan su ne abokan gabanmu. Kamata ya yi mu karkatar da ƙoƙarinmu don yaƙar waɗannan, maimakon yaƙi da juna. Ci gabanmu gaba ɗaya ya dogara da ƙoƙarinmu gaba ɗaya.

    4.  Maido da Maganar Mu: Dole ne mu ƙi maganganun da ke neman raba mu. A shafukan sada zumunta da kuma a cikin al’ummominmu, mu zama jakadun zaman lafiya, muna raba labarun haɗin kai da abota waɗanda suka fi yawan labarun rikici.

    Najeriya ƙasa ce mai girma, mai albarka da ɗimbin albarkatun ɗan adam da na halitta. Ƙarfinmu yana cikin hadin kai. Kada mu ƙyale rashin fahimta ya canza mana tunani. Muna buƙatar juna don rayuwa da ci gaba.

    Mu zaɓi hanyar ‘yan-uwanta. Mu zaɓi hanyar haɗin kai. Mu zaɓi hanyar Najeriya ɗaya.
    A Haɗe Muke Da Ƙarfi, A Rabe Muke Da Rauni.

    Karanta Yaushe Ne Kwanakin Layya Suke Ƙarewa?

    Edita@rumasau-kallamu

  • Amfanin Haƙuri

    Amfanin Haƙuri

    Haƙuri: Shi ne danne zuciya a kan wani abu mara kyau, wanda ya baƙantawa mutum zuciya.

    Haƙuri yana da matuƙar amfani ga mutane, kamar yadda ya zo a cikin littafin Sheikh Abdulrahim bin Ahmad Alkadhi mai suna “Daƙa’ikul khabar” shafi na 17 babi na goma sha biyu yace, labari ya gangaro cewa wanda aka jarabce shi da wata masifa, sai ya yaga tufafin sa ko ya bugi ƙirjin sa (to hukuncin wanda ya aikata haka) kamar (wanda) ya riƙi makami ne zai yi yaƙi da Allah (Subhanahu wata’ala).

    Sannan kuma an ruwaito daga Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) yace wanda ya ɓalle ƙofa ko ya yaga tufafin sa ya yi da wata masifa ta same shi ko ya bugu wajan zaman sa ko ya sare bishiya ko ya yanke gashin kan sa (saboda tsanani masifar da ta same shi), to za a gina masa gida na wuta a kan kowane gashi (wanda ya cire), sa’annan kuma Allah ba zai karɓi aikin sa na farilla ba ko na nafila matuƙar yana kan wannan hali.

    Har ila yau, Allah zai ƙuntata ƙabarinsa, kuma zai tsananta yi masa hisabi, sannan kuma dukkanin mala’ikun da suke sama da ƙasa za su dunga tsine masa, haka kuma za a rubutawa laifuffuka guda dubu a gare shi, sannan zai tashi a cikin ƙabarin sa tsirara.

    Haka kuma, wanda ya karya gefan jikin sa, saboda wata masifa, to Allah zai karya addinin sa, idan kuma ya bugi ko ya mari kumatun sa ko ya azabtar da fuskar sa, to Allah (Subhanahu wata’ala) ba zai kalle shi ba da rahmar sa ba ranar alƙiyama.

    Bugu da ƙari, kuma ya zo a cikin shafi na 18, babi na goma sha huɗu a cikin wannan littafin yace Sayyadina Aliyu bin Abu-ɗalib (karramallahu wajhahu) yace “haƙuri ana yin sa ne ta hanyoyin guda uku; na farko yin haƙuri a kan yi wa Allah biyayya, na biyu yin haƙuri a kan saɓawa Allah, na uku haƙuri a kan wata masifa wacce ta samu mutum.

    Saboda haka, duk wanda ya yi haƙuri a kan yi wa Allah biyayya, to Allah zai ba shi daraja guda ɗari, sa’annan kuma ko wace daraja yawanta ta kai tsakanin sama da ƙasa.

    Wanda kuma ya yi haƙuri a kan saɓawa Allah, to Allah zai ba shi daraja guda ɗari shida ranar lahira, haka kuma kowace dajara yawan ta ta kai faɗin sama da ƙasa, wanda kuma ya yi haƙuri a kan wata masifa wacce ta same shi, to Allah zai ba shi lada ba tare yi masa hisabi ba (ranar lahira).

    Karanta Tarihin Farfesa Abdallah Uba Adamu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Nasiha A Kan Mata

    Nasiha A Kan Mata

    MATA 10 WAƊANDA  ALLAH YA TSINE MUSU: –

    ﺍﻟﻮﺍﺷﻤﺎﺕ ﻭﺍﻟﻤﺴﺘﻮﺷﻤﺎﺕ
    1. Mata masu tsaga fuskokinsu. –

    ﺍﻟﻨﺎﻣﺼﺎﺕ ﻭﺍﻟﻤﺘﻨﺼﻤﺎﺕ

    2. Mata masu aske gashin gira. –

    ﺍﻟﻤﺘﻔﻠﺠﺎﺕ
    3. Mata masu kankare hakori (wushirya). –

    ﺍﻟﻮﺍﺻﻠﺔ ﻭﺍﻟﻤﺴﺘﻮﺻﻠﺔ
    4. Mai ‘karin gashi da wadda ake ƙara mata gashi. –

    ﺍﻟﺘﻲ ﺳﺨﻂ ﻋﻠﻴﻬﺎ ﺯﻭﺟﻬﺎ
    5.Matar da mijinta ya yi fushi da ita. –

    ﺍﻟﻤﺘﺸﺒﻬﺎﺕ ﺑﺎﻟﺮﺟﺎﻝ
    6. Mata masu shigar maza.

    ﺯﻭﺍﺭﺍﺕ ﺍﻟﻘﺒﻮﺭ
    7. Mata masu yawan ziyartar kabur-bura (maƙabarta).

    – ﺍﻟﻨﺎﺋﺤﺎﺕ
    8. Mata masu kururuwa akan mamaci. –

    ﺍﻟﻤﺤﻠﻞ ﻟﻪ
    9. Mata masu auren kashe wuta. –

    ﻛﺎﺳﻴﺎﺕ ﻋﺎﺭﻳﺎﺕ ﻣﺘﺒﺮﺟﺎﺕ
    10. Mata masu bayyana tsiraicinsu.

    Ka da ku manta TSINUWA ita ce nisanta daga rahamar Allah!
    ﻗﺎﻝ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ : ” ﻳﺎﻣﻌﺸﺮ ﺍﻟﻨﺴﺎﺀ ﺗﺼﺪﻗﻦﻭﺃﻛﺜﺮﻥ ﻣﻦ ﺍﻹﺳﺘﻐﻔﺎﺭﻓﺈﻧﻲﺭﺃﻳﺘﻜﻦ ﺃﻛﺜﺮ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻨﺎﺭ ” ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ
    Manzon Allah (SAW) ya ce: ‘Yaku taron mata! ku yi sadaƙa, kuma ku yawaita neman gafara (Istigifari) Allah ya gafarta Mana.

    Danna nan don karanta Abin Da Ya Kamata Mu Sani

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Nasiha A Kan Rayuwa

    Nasiha A Kan Rayuwa

    Manzon Allah tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi Yana cewa, “Ku yi ƙoƙarin danne abubuwa guda uku a cikin ranku, da rayuwarku.”

    1. Fushi
    2. Sha’awa
    3. Maganganunku.

    Ku himmatu wajen aikata abubuwa biyu:

    1. Ayyukan alhairi.
    2. Abokai na gari.

    Ku ci moriyar abubuwa uku:

    1. Ƙarfi
    2. Lokaci
    3. Lafiya.

    Ku nemi abubuwa uku:

    1. Gafarar Allah
    2. Ilimi
    3. Hikima.

    Allah ya ba mu ikon kiyayewa.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

    Domin karanta Nasiha danna nan

  • Nasiha A Kan Maganganun Mutane

    Nasiha A Kan Maganganun Mutane

    An tambayi Imam Hasanul Basari?
    Me ya sa ba ka damuwa da maganganun mutane? Sai yace,

    “Lokacin da aka haife ni, ni kaɗai aka haifa,
    Kuma lokacin da zan mutu, ni kaɗai zan mutu
    Kuma ni kaɗai zan kwanta a kabarina,
    Kuma ni kaɗai za a tashe ni a yi min hisabi.
    Kuma ni kaɗai za a ba sakamakona,
    Don haka ina ruwana da maganganun mutane?

    Domin in dai maganganun mutane shi ne damuwarka, sai dai idan ba ka shirya zaman duniyar ba.” Allah ya datar da mu.

    Danna nan don karanta Nasiha mai tsoratarwa

    Edita; Rumasa’u M. kallamu

  • Nasiha Mai Tsoratarwa

    BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM.

    Tsira da aminci su tabbata bisa Annabin ƙarshe, da dukkan iyalansa da sahabbai baki ɗaya.

    Yazeedur Raqqashiy ya karɓo Hadisin daga Anas bn Malik (R.A) yana cewa:
    Watarana Mala’ika Jibrilu (A.S) ya zo wajen Manzon Allah (S.A.W) a wani lokacin da bai saba zuwa masa ba. Ya zo, gaba ɗayan launin fuskarsa ya canza. Sai Manzon Allah (S.A.W) yace masa “MAI YASA NA GA LAUNIN FUSKARKA DUK YA CANJA HAKA?”

    Yace “Ya Muhammadu (S.A.W) na zo maka ne a wannan lokacin da Allah ya yi umarni da masu hura wuta su ci gaba da hura ta. Duk wanda ya san cewa Jahannama gaskiya ce, wuta gaskiya ce, azabar kabari gaskiya ce, kuma azabar Allah ita ce mafi girma, to bai kamata ya yi wani farin ciki ba har sai ya tabbatar da cewa ya samu tsira daga wannan”.
    Sai Manzon Allah (S.A.W) yace masa “YA JUBREELU INA SO KA SIFFANTA MUN YADDA
    JAHANNAMA TAKE”.

    Sai yace “Na’am. Haƙiƙa Allah maɗaukakin Sarki yayin da ya halicci Jahannama, ya sa an hura ta tsawon shekaru DUBU. Har sai da ta zama JA -JAWUR. Sannan aka sake hura ta tsawon Shekaru DUBU har sai da ta zama FARI – FAT!! Sannan aka sake hura ta tsawon shekaru DUBU har sai da ta zama BAƘA – ƘIRIN!!! Tana nan har yanzu BAƘA ƘIRIN ce, mai tsananin duhu ce. Harshen balbalinta ba su mutuwa ballantana garwashinta.

    Na rantse da girman Ubangijin da ya aiko ka da gaskiya, da a ce za a buɗe misalin ƙofar allura daga wutar Jahannama, Wallahi sai dukkan ma’abotan doron duniyar nan sun ƙone baki ɗayansu saboda tsananin zafinta.

    Na rantse da girman Ubangijin da ya aiko ka da gaskiya, da a ce za a ratayo tufafi guda ɗaya tufafin ‘Yan wutar Jahannama a maƙalo shi a tsakanin Sararin Samaniya, da sai dukkan ma’abotan doron ƙasa sun mutu baki ɗayansu saboda tsananin warin wannan tufafin. Da kuma zafin da ke tattare da shi. Babu wanda zai yi saura a cikinsu don tsananin abinda za su riska na zafin wannan tufafin.

    Na rantse da girman Ubangijin da ya aiko ka da gaskiya a matsayin Annabi, da a ce za a ɗauko zira’i guda na Sasarin nan na ‘yan wuta (wato sarƙa ɗin da ake ɗaure su da shi sannan a riƙa jan su akan fuskarsu). Wannan wanda Allah ya ambata a cikin Alqur’ani, a ɗora shi bisa wani dutse daga duwatsun duniyar nan, da sai dutsen ya narke ya zagwanye har zuwa ƙasa ta bakwai.

    Na rantse da girman Ubangijin da ya aiko ka da gaskiya a matsayin Annabi, da a ce za a ajiye wani mutum a mafaɗar rana ana yi masa azaba, da sai wanda yake mahudar rana ma ya ƙone ƙurmus saboda bala’in zafinta. Zafinta mai tsanani ne. Zurfinta mai nisa ne.
    Tufafin cikinta na ƙarfe ne. Abin shan cikinta HAMIMU ne (tafasasshen ruwan azaba) da kuma ruwan gyambo.

    Mayafan cikinta kuma an yanko su ne daga Wutar”. Tana da ƙofofi guda bakwai, kowacce ƙofa tana da wani yankin cikinsu da aka tsaga mata (za su shiga ta cikinta) daga mazaje da mataye. Sai Manzon Allah (saww) yace: “SHIN KOFOFIN NAN IRIN NAMU NE?”
    Sai Jibrilu yace: “A a sai dai ita ƙofofin a buɗe suke, wata ƙofar tana ƙasan wata.
    Tsakanin kowacce ƙofa da wata ƙofar, tsawon tafiyar shekara SABA’IN ne.

    Kowacce ƙofa ta ninka wacce take sama da ita a tsananin azaba har ninki SABA’IN.
    Za a riƙa kora maƙiyan Allah cikinta. Kuma duk sanda aka koro wasu (‘Yan wuta) zuwa wata ƙofa, Zabaniyawa ne za su tarbe su da sarƙoƙi da sasarai. Za a zira musu sasari (chains) ta cikin bakinsu sai ya fito ta duburarsu. Sannan za a ɗaure hannunsa na hagu a jikin wuyansa, hannunsa na dama kuma za a fasa ƙirjinsa da shi a turo shi ta cikin zuciyarsa sai ya fito ta bayan kafaɗarsa. Sannan a haɗa a ɗaure da waccan sarƙar.

    Kowanne ɗan Adam za a haɗa shi tare da shaitani guda a cikin sarƙar sasarin, Sannan a riƙa jan sa akan fuskarsa (a cikin garwashin wutar da kuma dagwalonta) mala’iku kuma suna jibgar su da gudumomin baƙin ƙarfe. Duk lokacin da suka nemi fita daga cikinta saboda baƙin ciki da wahala, sai a sake dawowa da su cikinta. Sai Annabi (S.A.W) yace ma Jibreelu (R.A) “SHIN SU WANENE MAZAUNAN CIKIN WAƊANNAN ƘOFOFI?”

    Sai Mala’ika Jibreelu yace: “Ka ga amma ƙofar nan wacce take can ƙarƙashin ƙasa, ita ce mazaunar munafukai da kuma waɗanda suka kafirce daga mutanen Annabi Isa (A.S) (Waɗanda aka ce kar su ɓoye abinci amma suka yi taurin kai suka ɓoye). Da kuma mutanen Fir’auna. Ita wannan wutar sunanta “HAAWIYAH”.

    Sai kuma ƙofar nan ta biyu, waɗanda za su shiga cikinta su ne MUSHRIKAI. Kuma sunanta “AL-JAHEEM”. Ƙofar ta uku kuwa masu bautar taurari ne za su shiga ta cikinta. Su ne mazaunan cikinta. (a wani wajen an ce za su zauna tare da masu wasa da sallah). Kuma sunan wannan wutar “SAƘAR”.

    Ƙofar wuta ta huɗu, ta nan ne IBLIS (L. A.) zai shiga cikinta tare da mabiyansa da kuma
    Majusawa masu bautar Wuta. Kuma sunanta “LAZAA”. Kofa ta biyar kuwa ta cikinta YAHUDAWA za su shiga. Kuma sunanta “ALHUTAMAH”. Kofa ta shida kuwa, NASARA ne za su shiga ta cikinta. kuma sunanta “SA’EER”.

    Daga nan kuma sai Mala’ika Jibrilu ya sunkuyar da kansa ya yi shuru, ya kasa ci gaba da magana saboda jin kunyar Manzon Allah (S.A.W). Sai Manzo (S.A.W) yace masa “SHIN BA ZA KA BA NI LABARIN KO SU WAYE MAZAUNAN CIKIN WANNAN KOFAR TA BAKWAI ƊIN BA?” Sai Jibrilu yace: “Su ne ma’abotan manyan zunubai daga cikin al’ummarka. Idan har suka mutu ba su tuba ba” Nan take Sai Sayyidina Rasulullahi (S.A.W) ya faɗi YA SUMA!!!
    Sai Mala’ika Jibrilu ya ɗauki kansa ya ɗora akan cinyoyinsa har sai da ya farfaɗo sannan
    yace:

    “YA KAI JIBRILU LALLAI MUSIBA-TA TA GIRMA! KUMA BAKIN CIKINA YA TSANANTA!!! YANZU ASHE AKWAI WANDA ZAI SHIGA WUTA DAGA CIKIN AL’UMMATA?” Sai yace “Eh amma ma’abotan manyan zunubai daga cikinsu”. Daga nan Sai Manzon Allah (S.A.W) yasa kuka, Mala’ika Jibrilu ma yana kuka…!!!” Ibnu Katheer ya kawo wannan hadisin da ruwayoyi daban-daban a cikin littafinsa mai suna AN-NIHAYAH FIL FITAN WAL MALAHIM. A cikin babin da ke magana akan wuta da azaba cikinta.

    Allah (S.W.T) Ya yafe mana zunuban mu manya da ƙanana. Amin. Manzon Allah (S.A.W) ya na cewa mutanen da ke kusa da ni a ranar tashin Alƙiyama su ne masu yawan yi min salati! Allahumma salli Ala Muhammad wa sallim!

    Domin karanta Nasiha Tsakanin Musulmi danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Nasiha

    Nasiha

    BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM

    ALKAWARIN ALLAH GASKIYA NE:

    Allah Maɗaukaki Ya ce:

                                                               “أَيْنَمَا تَكُونُوا يُدْرِككُّمُ الْمَوْتُ”
    سورة النساء: 78

    “Duk a in da kuka kasance, mutuwa zã ta riske ku…”

    Ibnu Katheer ya ce:

    Duk in da kuka kasance mutuwa za ta zo ta riske ku, saboda haka ku kasance a kan ɗa’a ma Allah kuma kamar yadda Allah ya umarce ku, domin shi ne alkhairi a gare ku, saboda ita dai mutuwa dole ce kuma babu halin guduwa mata, sa’annan zuwa ga Allah ne makoma take, duk wanda ya kasance mai biyayya ne gare Shi sai Ya saka masa da mafificin sakamako, Ya ba shi mafi cikan lada…

    Allah ya sa mu dace. Allah ya sa mu cika da kyau da imani Bijahi Rasulillahi (S.A.W)

    Danna nan don karanta nauye-nauyen rayuwar aure

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Shirye-Shiryen Gidajen Rediyo A Kano Da Tasirinsu Ga Tarbiya

    Shirye-Shiryen Gidajen Rediyo A Kano Da Tasirinsu Ga Tarbiya

    “Wanda ya mallaki bayanai, ya mallaki duniya”

    -Nathan Rothschild.

    Guglielmo Marconi, Reginal A. Fessenden da sauran waɗanda suka ba da gudumawa wurin samar da rediyo don wasu amfani da a tunaninsu bai taka kara ya karya ba. Amma bayan wasu ƙarnuka masu yawa da wucewar su, an samu ci gaba sosai a rayuwar mutane, wannan yasa an fahimci tasirin rediyo da kuma gidajen rediyo. Musamman idan muka kalli ƙasashen Turai a yaƙin duniya na biyu, sun yi amfani da gidan rediyo don yaɗa  farfaganda. Saboda sanin mahimmanci da tasirin rediyo ya sanya ƙasashe kamar su Birtaniya buɗe sashen Hausa da sauran sassa da ba na Turancin Ingilishi ba, don cimma manufofinsu.

    Gwamnatoci sun fahimci tasirin da rediyo take da shi a rayuwar waɗanda ake mulka, wannan yasa gwamnatoci kakkafa gidajen rediyo don isar da manufofinsu da ƙudurorinsu, wasu lokutan don isar da wata manufa ta ƙashin shugabannin. Haka ma manyan ‘yan kasuwa/attajirai da `yan siyasa sun fahimci wannan tasiri da rediyo take da shi, su ma sai suka fara kakkafa gidajen rediyo don tallata manufarsu na kasuwanci ko siyasarsu.

    Wannan tasiri za mu iya ganin shi a fili, idan muka kalli yadda mutane da yawa suka mai da rediyo makusanciya ta mussaman, wadda ba a iya rabuwa da ita, don harkar saye da sauran mu`amala da ita. Mutane sun mayar da gidajen rediyo wurin samun labaru da sanin abin da yake faruwa na yau da Kullum. Wasu lokuta yadda mutane suka yi amanna da duk abin da aka faɗa a gidajen rediyo, yakan zamo abu mai wahala kafin ka canza su. Ba wani abu ba ne, sai tasirin abin da aka faɗa ta hanyar rediyo da yawan nanata shi.

    A Kano an fara kafa gidan rediyo mai zaman kansa ne a shekarar 2003,  tun daga wannan lokaci ya zuwa yanzu, ana hasashen gidajen radioyo masu zaman kansu sun kai sama da guda ashirin (20+). Mai karatu ya san duk waɗannan ba a banza ake buɗe su ba, amma babban abin lura shi ne an fahimci tasirinsu ne a cikin al`umma da rayuwarsu.

    Duk wanda ya buɗe gidan rediyo yana da dalilinsa da manufar da yake so ya isar ko ya cimma, ba manufar kaɗai ake gabatarwa a waɗannan gidajen radiyo ba, ana gabatar da wasu shirye-shirye na daban waɗanda su ma suke da tasirinsu a cikin  rayuwar mutane. Kamar shirye-shiryen abubuwa da suke faruwa na yau da kullum a cikin al`umma. Duk wanda yake Kano ko yake sauraron shirye-shiryen gidajen rediyoyin Kano, ya san irin waɗannan shirye-shiryen, waɗanda aka samo daga wani shiri daga gidan rediyon Kano mai suna “Taskar Labarai”.

    Waɗannan shirye-shirye suna da matuƙar tasiri a cikin rayuwar mutane fiye da yadda ake tsammani. A mafiya yawan lokuta, a waɗannan shirye-shirye ana yawan kawo labarukan manya-manyan laifuka, kamar fyaɗe ga ƙananan yara. Duk lokacin da aka yi wa masu gabatar da waɗannan shirye-shirye magana kan yadda suke faɗan waɗannan laifuffuka, sai su ce kaso mafi ƙaranci na irin abin da yake faruwa da suka samu haƙiƙanin labarai a kai suke faɗa.

    Tasirin irin waɗannan shirye-shirye ga tarbiyya, abu ne mai girma wanda ba a ganin tasirin abin a lokaci guda. Amma idan an lura sosai suna da tasiri mai yawa ga tarbiyya. Idan muka dubi abin ta ɓangaren tarbiyya, za mu ga irin waɗannan shirye-shirye suna da mummunan tasiri ga tarbiyya ta ɓangarori kamar haka:

    Na farko duk abin da ake faɗa a fili musamman ta hanyar rediyo, bisa dukkan dalilai yakan kai inda ba a zato, to a nan, ana sanar da wanda bai sani ba, sannan ana tunatar da wanda ya manta, ana kuma jaddada wa wanda ya sani wani abu. Shi kuma a shari’ance da tarbiyya, ba a son bayyana ɓarna. A hadisin Abi Hurairah ya ce, na ji  Manzon Allah (SAW) ya ce: “Dukkan al`umata waɗanda ake yi wa rangwamen zunubansu ne (wato ana yafe musu)  sai masu bayyana ɓarna” – ba masu aikin gidan rediyo ake nufi a nan ba, ana nufin waɗanda idan suka aikata ɓarna a ɓoye sai su fito fili suna faɗa. Waɗannan su ake nufi. Amma mene ne dalilin da ya sa aka ce ba a yi wa masu bayyana ɓarna rangwame? Saboda koya wa wasu suke yi, kuma nuna wa wanɗanda da ba su sani ba suke yi da kuma tunatar da waɗanda sun gafala daga aikata ɓarna suke yi. Wannan shi ne abin da suke yi kenan. Wanda bai san fyaɗe ba, an faɗa masa kenan sai ya fara tunanin aikatawa da hanyar da zai kauce, kada a kama shi kamar yadda aka kama na baya.

    Na biyu yawan fadin waɗannan laifuffuka, yakan dasa waɗannan laifuffuka a zuciyar mutane, musamman matasa. Shi yasa za a ga matasa sun fi kowa yawan faɗawa cikin ɓarna da laiffufuka musamman waɗanda ake yawan tallata su”

    Na uku yawan fadin laiffufuka yana ƙara yawaitar su, da ƙaruwarsu. Misali a yanzu zai yi matuƙar wahala a yini ba a ji labarin garkuwa da mutane ba, tun ana jin labarin a Kudancin ƙasar nan, yanzu ga shi har gida kuma ƙaruwa yake yi a kullum. Duk da akwai dalilai daban-daban na ƙaruwarsa, wanda rashin ɗaukar ƙwaƙƙwaran hukunci a kan masu aikitawa yake ƙara yaɗuwarsa da sauransu.

    Misali na biyu na irin shirye-shiryen da gidajen rediyoyi suke gabatarwa mai tasiri sosai a cikin al`umma su ne shirye-shiryen siyasa. Ta yadda ake bai wa mutane dama su faɗi albarkacin bakinsu. Mutane da yawa ba sa lura da mummunan tasirin abin ga tarbiyya. Idan muka duba sosai kafin yaɗuwar gidajen rediyo da waɗannan shirye-shiryen a Kano, malamai da  sarakuna da kuma manyan mutane suna da matuƙar ƙima da daraja a idon mutanen gari, amma a yanzu saboda waɗannan shirye-shirye ya sa mutane da yawa sun samu dama na cin mutuncin malamai da sarakuna da kuma shugabannin al`umma. A Kano kowa ya san a yanzu waɗannan mutanen da na faɗa a sama duk da ƙimar da suke da ita a baya, kowa yana iya shiga gidan rediyo ya faɗi maganar da yake so a kansu kai tsaye. Wannan tasirin waɗannan shirye-shiryen ne kai tsaye. 

    A bangaren tarbiyya, rashin girmama babba a al`umma alamu ne na rugujewar tarbiyya da taɓarɓarewar al’umma, kuma alama ce ta lalacewar wannan al’umma. Tasirin waɗannan shirye-shirye kenan ga tarbiyya.

    Wannan su ne kaɗan daga cikin tasirin gidajen rediyo a rayuwar al’umma da tarbiyyarsu. Saboda haka, ya kamata mu san irin shirye-shiryen da ya kamata mu dinga saurara. Sannan kuma lallai shugabannin addini su tashi su faɗakar da mutane game da irin waɗannan abubuwa da suke lalata tarbiyyar al’umma. 

  • Nasiha Tsakanin Musulmi

    Nasiha Tsakanin Musulmi

    Yin nasiha ga Musulmi a junansu wani babban tsaro ne ga imanin musulmi, ɓarna ba ta yaɗuwa a inda nasiha take aiki, saboda ana murƙushe ta ne tun tana garwashi kafin ta gagara ta zama gobarar daji.

    Duk inda mutum ya ga ɗan’uwansa yana aika ta, ko furta wani abu marar kyau, wanda ya saɓa wa umarnin Allah (S.W.T) ƙarara, to lallai ne wannan mutum ya yi nasiha ga wannan ɗan’uwa nasa ta hanya mai kyau, har sai ya tsamo shi daga halaka. Haka idan ya ga ɗan’uwansa ya taƙaita ga barin aikata wani aiki ko wani hali na kirki, to aikinsa ya yi masa nasiha har sai ya dawo da shi, don ya aikata abin da Allah yake so, kuma mutum zai iya yi wa sauran al’umma nasiha ta hanyar yi musu adalci tare da kyautata aikinsa, ko sana’arsa don amfanin jama’a ba tare da cutar da su ba.
    Sannan kuma, ya kamata a gane cewa ita nasiha, idan akan yi ta tsakani da Allah, to ba sai lallai wani muhimmin mutum kawai zai yi ta ga sauran jam’a ba, a’a tsakanin Uban da ɗa da wa da ƙani, da mata da miji da shugaba da talaka da ubangida da yaron gida, kowa yana iya yiwa kowa nasiha cikin ladabi da girmamawa, da neman yardar Allah. Da haka ne mutane za su taimaki kansu da kansu, su taya juna biyayya ga Allah.

    • Dokoki:

    Daga cikin abin dake taimaka wa mutum a kan biyayya ga Allah, da kuma saɓawa son zuciya, har da kafa dokoki waɗanda za su toshe ƙofar saɓon Allah da kafa waɗanda za su ɓullo da hanyoyin bin Allah a rahusa (cikin sauƙi).
    Wannan aiki ne na shugabanni tare da sauran jama’ar gari baki ɗaya, wato lallai ne shugabannin su kafa doka, kuma su tsare ta, duk dokar da za su kafa su tabbata wadda ta dace da umarnin Allah ce, kuma duk dokar da ta saɓa umarnin Allah, lallai ne su kawar da ita ko wane ne ya zo da ita, domin idan Allah Ya ba da umarni, wani mutum ya soke umarnin Allah, su ka bi na wannan mutum, to babu shakka sun fifita shi a kan Allah, kuma duk ranar da Allah Ya kama su, shi ba zai iya ƙwatarsu ba Allah Ya gafarta mana. ameen.
    Kuma aikin mutanen gari ne da su nemi shugabannin su, a kan su aiwatar musu da dokokin Allah (S.W.T.) kuma su kawar da duk wata doka da ta saɓawa umarnin Allah, sannan su taya shugabannin nasu a kan haka ta kowace hanya shari’antacciya.
    Daga cikin dokokin da ya kamata a kafa su ne: Haramtawa Musulmi shan giya, sayar da ita da ɗaukan dakon ta, da bayar da hayar gidanta, ko tallata ta da haramta karuwanci da duk abin da zai taimaka a yi shi, kamar bayyana tsiraici da cuɗanyar maza da mata a wuraren taro da makarantu, da abubuwan hawa, da kaɗaitar namiji da mace marar dalili da tsananta harkar aure da sauransu.
    A taƙaice a dai dokokin da za su hana dukkan miyagun ayyuka, irin su cin riba da caca da sauransu.
    Sannan su yi umarni da dukkan kyawawann ayyuka, kamar ba da zakka da ayyukan ibada baki ɗaya.
    Na san wannan aiki ne jajawur, amma mene aikin mutum a duniya idan ba jan aiki ba? Don haka lallai ne, mu zage dantse mu tunkari kowane aiki mai kyau mu kuma tuna da cewa Allah zai taimake mu a kan kowane aikin alheri. Allah Ya sa mu dace ameen.
    Don samu sauƙin aiwatar da waɗannan dokokin. Sai an tanadidi ‘yan sanda ɗa’a, waɗanda za a ba su cikakken horo  na yadda za su yi horo da kyakkyawan aiki da hani ga mummunnan aiki, waɗanda za su bazama cikin gari a ko’ina, idan sun ga ana saɓawa dokar Allah sai su kare ta, ta hanyar ilmantarwa, ko tsawatarwa ko kamawa tare da gurfanarwa a gaban shari’a.
    Abu na gaba mafi mahimmanci, kuma wanda zai sauƙaƙe aiwatar da dokokin Allah shi ne, tanadar manhajar ilmi ingantanciya wadda za ta fitar da muminin bawa, salihi, managarci , mai tsoron Allah, sai a tanadi wannan manhaja don aiwatar da ita, a dukkan makarantu na boko da na allo, da na islamiyya.
    Tsarin ilmantarwa da tabiyyantarwa ba zai tsaya kan yara ko ɗalibai kawai ba, a’a, har da dukkan jama’ar gari , kowanne a tanadi hanyar da za ta dace da matsayin hankalikansa da kuma ilminsa don ɗora mutane a kan ayyukan imani da tsarkake zuciya, da neman ilmi don samun yardar Allah.
    Sai da haka ne, sannan doka za ta yi tasiri, amma don an kafa doka kawai, kuma, an yi shelar ta, wannan ba zai yi tasiri ba a al’ummar da ta daɗe tana cin karenta babu babbaka, ƙarƙashin tsarin da yake ta halatta shan giya da zina da caca da kowace irin kaba’ira.
    Daga nan idan muka yi nazari mutum wanda aka haifa daga iyaye masu addini, sannan ya sami tarbiyya mai kyau ta addini, kuma ya rayu tsakanin mutane masu yiwa juna nasiha, kuma a cikin al’umma wadda take da dokoki masu tsare martabar addini, babu shakka za mu ga an sami mutum nagari wanda ya yi sa’ar samun kansa cikin mutane, waɗanda za su taimake shi, su taya shi yin aikin da Allah Ya halicce shi domin sa, ba mutanen da za su yi koyo da shi, ko kuma waɗanda za su taya shaiɗan aikin ɓatar da shi da ƙarfi da yaji ba.

    Wannan bayani An ciro shi ne daga littafin Ɗan Adam Kamar Yadda Allah Yake Son sa. wanda M. Aminu Isma’il Sagagi ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • ƘARSHEN ALEWA

    ƘARSHEN ALEWA

    Halin da muke ciki a yanzun ya kai matakin innalillahI wainna ilairaji”un! Idan ka cire maganar addini gaba dayan ta ka dawo da lamuran rayuwar nan a kan mizanin hankali, sai ka ga babu wani sauran nishaɗi ko kuma jin daɗi da ya rage maka, indai a wannan duniyar da muke ciki kake.
    Duk kuwa da irin damammakin da muka samu na ci gaban da ya zo mana, wadda yake sauƙaƙa mana rayuwa, ba kamar zamanin iyayenmu da kakanninmu da suka gabata ba, duba da cewa, a wannan zamanin inda ka ɗauke amana, tausayi da jinƙan juna babu, abun da suke da shi na more rayuwa, ba su da lantarki, ba su da ruwan famfo, kai hatta gine-ginen gidajensu ma indai ba na mai sarauta ko mai hannu da shuni ba ne, ba wani ƙawata shi ake ba, amma haka bai hana musu rayuwa cikin aminci da yalwatacciyar lafiyar jiki da ta ruhi ba, lafiya mai ɗorewa.
     ‘Yan uwana, akwai wani daga cikinmu da ya taɓa tunanin abin da ya sa iyayenmu suka fi mu ƙarko? Dalilan suna da yawa, amma kaɗan daga cikinsu, mutumin shekara sittin zuwa saba”in baya, ko da shi kafiri ne, za ka same shi da ingantacciyar zuciya, kamala, da wadatar zuci, ba za ka taɓa samun sa da ƙarya ba, ba za ka taɓa samun sa da cin amana ba, sannan jikin matayensu kullum lulluɓe yake kirif! Balle kuma musulmi idan ka lura cutuka da daman gaske shekarun baya babu su, yanzun me ya kawo su? Yawa-yawan alfasha, mutum bai jin tsoro ko kunyar wadda ya halicce shi ba ma, balle kuma abokin halittarsa.
    Idan ka juya wani janibin kuma, mazaje sun kasa sauke nauyi da Allah ya ɗora musu, ba domin ba su dashi ba, a’a, sai domin tunanin a hakan dukiyar za ta taru. Kai subhanallhi, wa”iyazubillahi Allah ta”alah da kanshi ya ce, “Ya zare hannayensa ga duk magidanci da bai sauke nauyin dake kansa ba”.
    Ɗan uwa wane ne ya ba ka ne? Allah ne fa Koh? To ya bar ka da wayonka, ta ya kake ganin samun dacewa? Wani matakin lalacewa da matasa muke a kai yanzu, wai neman auren ma za ai, Amma sai an sanya haramci cikinsa, ba zai taɓa yiwuwa a yi shi cikin tsafta ba.

    Da yawan matsaloli da yara suke ba wa iyayensu, ya samo asali ne daga tushen yadda suka mallaki yaran.

    A wata fuskar kuma, yaran nasu ne, amma ba halalinsu ba, kun san dalilina? Tun kafin a auri uwar, aka samu cikin yaron, kuma a kan cikin aka ɗaura auren bayan an haife cikin Kuma, ba a daddara ba, aka ci gaba da zaman zinar da ake, ɗan uwa ka saɓa wa Allah da ya halicce ka, ta ya kake tunanin ‘ya’yan da ka haife su ba ta hanyar halali ba za su yi maka biyayya? A irin haka ne za ka ji yaro ya kashe ubansa, a’a wani ya yi zina da uwarsa, da dai sauran bala’o’i iri- iri da muke fuskanta a wannan ƙarnin.
    Wannan dalili da wasu daga cikin mazaje suka ginu a kai, ya jawo babbar musibar da take addabar al’ummarmu a yau.
    Mai gida cikin kashi ɗari na nauyin da Allah ya ɗora maka, ba ka sauke kashi saba’in ba, Kuma kana da tabbacin babu wani wadda zai yi maka dole, sai kai ɗin ba ka tunanin halin da uwa za ta shiga? A ƙoƙarinta na neman mafita, har ta faɗa halaka, kuma kai kaine sanadin faruwar komai, Eh, to hallaka mana a cikin nauyin da Allah ya ɗora muku, babu wadda idan babu shi za ai haƙuri, ba zai taɓa yiwuwa a rayu babu abinci ba, ko babu sutura, ko wajen kwanciya, ko kuwa magani, a ciki duk babu wadda za ai haƙuri da shi, dukkaninsu lamura ne na dole.
    Kana tunanin idan ta samu mai ba ta abinci ba za ta karɓa ba ne? Yau da gobe yana ba ta sau ɗaya, idan ya bijiro da buƙatarsa ko da wace iri ce, za ta amsa hannu bibiyu ko don gudun rashin wadda zai ba ta. Wane ne silar hakan?
    Idan kai matashi ne a wannan ƙasar, ban san abin da ya yi maka daɗin da za ka ɓata lahirarka ba, bayan kuma ba ka mori duniyar ba. Eh mana. Kaso saba”in na matasanmu ba su da aikin yi, ba su da wani mafarki a kan gobensu, kuma ba mu da wata madogara da muka jingina rayuwarmu a jiki. Matasa kunnenku nawa? Wallahi wankin hula yana gab da kai mu dare idan har mu ba mu gyara ba, a haka yaranmu za su tashi, su ma haka nasu yaran abu ya zo ya zame mana al’ada.
    Eh al’ada mana, ina jin dai ita ce ake yin ta yau da gobe? Kuma babban abin takaicin a ce wai mun sunnata wa ‘ya’yayenmu abin da ba zai kai su tudun mun tsira ba.

    Eh kwarai da gaske da ni da ku, ai mun san abin da muke aikatawa ba tone-tone. ɗan uwa ko iyaye mahaifanmu kawai suka yi ba su da ikon tsara mana yadda gobenmu za ta kasance.

    Mu ne muke da damar zama abin da muke so, kodai mu zama lalatattu ko kuma nagartattu. Ba mu da lokaci isasshen da za mu ɓata shi wajen saɓon Allah ta”ala, saboda komai ya zo ƙarshe mu muka zo, eh mana, alamomin tashin duniya babu wadda bai bayyana ba ɓaro-ɓaro.
    Mu yi amfani da lafiyarmu, da lokacinmu da ilminmu da dukkanin damar da muka samu domin samar da tsabtatacciyar al’umma, ta haka ne duniya ba za ta manta da sunayenmu ba, ko ƙasa ta yi mana hijabi da ita.
    Ɗan uwa ba ka da lokacin ɓatawa, kay i gaggawar miqa lamuranka ga Mahaliccinka, yi kokari ku rabu lafiya da iyayenka, hanzarta ka sauke nauyin iyalanka, duk azabar da za ka ci wajen yin hakan, domin ta haka ne kaɗai za mu sadu da mahaliccinmu cikin salama!
    Don Allah muso juna, mu yi wa juna uzuri, kuma mu yafi juna, mu gina ingantacciyar rayuwa ko ba don komai ba ma, domin amfanin kawukanmu.

    Fatana Allah ta”ala ya jiɓanci dukkanin lamuranmu..

    Buɗaɗɗiyar wasiƙa zuwa ga iyaye mata domin karanta wannan wasika danna kuren rubutun nan