Tag: Hani

  • Hani A Kan Yin Gaba

    Hani A Kan Yin Gaba

    Gaba: Rashin magana da juna bisa ga wani dalili wanda ya haɗa wasu mutane faɗa ko husuma ko jayayya da dai sauran su.

    Saboda haka, gaba ba ta da wani amfani ga musulmi ko addinin musulunci, saboda addinin musulunci, addini ne wanda yake buƙatar mutanensa su dinga magana da juna, wasa da dariya haɗi da nishaɗantar da juna tare da kyautatawa juna, amma kuma ita gaba duk ta hana aikata haka.

    Haka kuma Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) ya nuna mana irin sharrin da gaba take iya haifarwa ga al’umma, misali tana iya rushe zaman lafiya ga mutane, rashin samun gafarar Allah, rashin samun yarda ko amincewar Allah, rashin samun taimakon Allah da dai sauransu.

    Sannan kuma ita gaba babu wani abu wanda take iya haifarwa , illar rashin jituwa atsakanin musulmi haɗi da daina ko rashin tatttaunawa da junansu, wanda shi kuma addinin musulunci baya buƙatar aikata haka, saboda shi musulunci addini ne na zaman lafiya

    Bugu da ƙari kuma, gaba tana haifar da faɗa, rikici ko rigima atsakanin mutane haɗi da faɗin magan-ganu mara sa daɗi ko amfani ga addinin musulunci

    Misali, idan wani mutumin wani gari yana gaba da wani mutumin wani garin, to wasu matsaloli za su iya faruwa atsakanin su, saboda shaiɗan yana murna da farin ciki, idan an samu wasu mutane suna gaba da juna.

    Sannan kuma Allah (Subhanahu wata’ala) ba ya karɓan addu’ar mutanan da suke gaba da juna, ma’ana idan sun ɗaga hannunsu sun roƙi Allah (Subhanahu wata’ala), to Allah ba zai karɓi addur’ar su ba.

    Haka kuma idan salihan bayin Allah sun yi addu’a ga mutane waɗanda suke da wata buƙata a wajen Allah, to ba za a sanya su a cikin addu’ar ba, har sai sun sasanta junan su haɗi da yafewa akan abin da ya wuce .

    Misali mutum ɗan kasuwa ne ko wanda yake buƙatar Allah (Subhanahu wata’ala) ya kawo masa canji a cikin rayuwar sa, amma kuma yana gaba da wani mutum akan wani dalili, wanda ya haɗa su, to Allah ba zai karɓi addu’arsu ba, har sai ya daina yin gaba da wancan mutumin, saboda ita gaba tana hana addu’ar wucewa lafiya sumul ƙalau.

    Musulmi ɗan uwan musulmi ne a duk inda yake a cikin faɗin duniyar nan, tatttaunawa, tausayawa, taimakawa, shawartawa da juna da dai sauransu, waɗannan su ne ake buƙata a tsakanin musulmai.

    Saboda haka, ya kamata ‘yan uwana musulmai mu fahimci haɗarin da gaba take iya haifarwa haɗi da sharrin da ke cikinta. Sannan kuma gaba tana iya kawo rabuwar kai a tsakanin musulmai, saboda haka idan haka ya kasance a junansu, to maƙiya za su iya samun damar shiga tsakanin su, domin su raba kawunan su.

    Misali kamar rukunin ko garken dabbobi ne, waɗanda suke fita kiwo tare da juna kullum, sai wata rana, wata dabbar daga cikin su, sai ta juyawa sauran baya, ta fita kiwo ita kaɗai, can sai ga zaki da kura nan sun tunkaro ta, sannan kuma ita kaɗai ce a cikin daji, shin akwai wata ƙofar gudu a gare ta?

    Saboda haka, gaba kamar gini ne wanda ya rushe ko kuma jirgi ne wanda ya tashi sararin samaniya, sai kuma mai ya ƙare masa a sama, idan ya faɗo ƙasa, kun san abin da zai iya faruwa da jirgin.

    Har ila yau, gaba tana iya haɗa ƙiyayya mai ɗorewa haɗi da wasiya akan aikata abu mara kyau da dai sauran su. Misali idan wani mutum yana gaba da wani mutum ko kuma akwai gaba a tsakanin su, to yakan iya sanarwa da ‘ya’yan sa waccan gaba take tsakanin su da wannan mutumin haɗi da jaddada musu matsayin sa akan wannan gaba.

    Sannan kuma gaba takan iya haifar da sare-sare haɗi da kashe-kashe a cikin wasu guraran ko unguwannin da suke gaba da juna. Misali idan wani mutum faɗa ya haɗa su da wani mutum har sai da ya kai da sanadiyar sare-sare ga waɗancan mutanan, haka kuma wanda ya samu raunin mai yawa, to mutanen sa za su iya ɗaukar mataki akan aikata haka (fansa), kamar su rama abin da aka yi wa ɗan uwan su ko hana mutanen wancan layin shiga layin unguwar su.

    Saboda aikata haka yana iya kawo rabuwar zukatan musulmai, rashin kulawa da juna, tausayawa juna haɗi da asarar jinane ko kuma rayuka ga waɗanda ba su ji ba su gani ba.

    Sannan kuma Allah (Subhanahu wata’ala)  yace “ku ji tsoran fitinar da za ta faɗawa mutane baki ɗaya”, ma’ana idan wani ko wasu mutane suka janyo rigima a cikin wani gari ko jiha ko kuma ƙasa baki ɗaya, to zai iya shafar kowane mutum, haka kuma su waɗancan mutanan da suka haifar da wannan rigimar, to laifin aikata haka yana kan su.

    Misali idan wani mutum ya koyawa wani mutum karatul Alƙur’ani mai girma, sana’a ko kuma dukkanin wani aikin alheri, to Allah (Subhanahu wata’ala) zai ba shi lada mai yawa a duk lokacin da shi wancan mutumin ya aikata haka.

    Kamar mutumin da ya koyawa wani mutumin aikata aikin sharri ne kamar su ƙarya, zina, sata, fushi, gulma da dai sauran su, to a duk lokacin da shi wannan mutumin ya aikata haka, to shi ma za a rubuta masa zunubi mai yawa akan hukuncin koyar da saɓawa Allah (Subhanahu wata’ala) da manzon Sa (Sallallahu alaihi wasallam) .

    Saboda Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) yace “Duk wanda ya shiryar da mutane akan hanyar (aikata) alheri, to shi ma za a rubuta masa ladan kwatan-kwacin wanda ya aikata haka”. Misali idan wani ko kuma wasu mutane (ƙungiya) a cikin unguwa ko a gari suna ganin waɗansu mutane suna aikata abu mara kyau da amfani ga mutanen wannan unguwar ko garin, sai su yi yunƙurin hana su aikata haka, to Allah (Subhanahu wata’ala) zai ba su lada mai yawa saboda ƙoƙarin hana yaɗuwar ɓarna a doran ƙasa.

    Saboda haka waɗanda suke yunkurin haddasa gaba a tsakanin mutane, to su sani fa kamar waɗanda suke umarni ne da aikata ɓarna ko sabon Allah (Subhanahu wata’ala) a doran ƙasa da dai sauransu.

    Sannan kuma dukkanin wanda ya yi umarni da a saɓawa Allah (Subhanahu wata’ala) a doron ƙasa, to ya san hukuncin sa haɗi da makomar sa a ranar lahira, ma’ana gidan wutane gidan sa a ranar lahira, saboda umarnin da ya yi na bijirewa Allah (Subhanahu wata’ala), bayan kuma Allah ne ya halicce su, ya kuma raya su, sannan kuma ya ba su abin da zai yi musu amfani a rayuwar su.

    Saboda haka, ya kamata dukkanin abin da mutum zai aikata ko kuma muke so a ran mu za mu aikata a cikin rayuwar mu ta yau da kullum, to yana da matuƙar kyau mu tsaya mu yi tunanin sosai kafin mu aikata haka, saboda mu samu damar wucewa kan gadar tsira ranar lahira lafiya sumul ƙalau.

    Bugu da ƙari kuma, yana da mahimmanci akan musulmi ya san hukunce-hukuncen irin abubuwan da yake aikatawa a rayuwar sa ko kuma ya dinga tambayar malamai hukuncin aikata kaza da kaza da fatan Allah(Subhanahu wata’ala) zai daidaita zukatan mu, ameen summa ameen.

    Domin karanta Hani Akan Yin Gori danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Hani Akan Cin Amana

    Hani Akan Cin Amana

    Amana: Wani zance ne ko magana ne, kaya ko dukiya wanda wani mutum ya ɗauka ya ba wani mutum ko ya faɗa masa, saboda amincewar da ya yi da shi.

    Cin Amana: Zambo cikin aminci, yaudara ko ha’intar wani mutum akan wani abu wanda wani mutum ya ɗauka ya ba shi ko ya faɗa masa, saboda yarda da ya yi da shi.

    Saboda haka, addinin musulunci ya hana mu cin amanar juna ta kowane irin siga ko hanya, saboda addinin musulunci, addini ne na tausayawa juna, kulawa da juna, kare mutuncin juna haɗi da dukiyar juna da dai sauran su.

    Haka kuma cin mutuncin juna, wulaƙanta juna, cin amanar juna ta kowane gwadabe, to ba halaye ba ne na addinin musulunci, ɗabi’a ce ta mutane marasa tunani da hankali.

    Bugu da ƙari kuma, duk inda mutum musulmi yake, to ya san akwai waɗansu dokoki wanda Allah ya tsara, domin kula da rayuwar sa ta yau da kullum tare da tunani da hankali mai kyau haɗi da amfanin rayuwar sa.

    Saboda haka yana da matuƙar mahimmanci akan kowane musulmi ya yi iya ƙoƙarin sa wajen bin dokokin addinin musulunci haɗi da al’adar sa, matuƙar addinin musulunci bai hana aikata haka ba.

    Sannan kuma cin amana laifi ne mai girma haka kuma yana ɗaya daga cikin manya-manyan laifuffuka, wanda ya kamata musulmi ya yi la’akari da su sosai, saboda sun iya katange mutum daga shiga gidan aljannah .

    Saboda ita amana malamai sun ce za ta zo ta tsaya akan siraɗi ranar lahira duk wanda ya ci amana, to za ta kama shi ta yi ƙasa da shi da dai sauran su .

    Misali, idan wani mutum ya ba ka amanar wani abu, sai kai kuma ka ci amanar wannan abun, to ranar lahira wancan amanar da ya ci za ta zo ta tsaya akan siraɗi, idan ya zo zai wuce, sai ta kama shi ta faɗa da shi cikin wani rami mai zurfi sosai. Sai a ce da shi waccan ita ce amanar da ya ci.

    Saboda haka sai ya bita ya kamo ta, idan kuma ya tafi zai ka mota, sai ya kamota ya kusa fito da ita waje, sai ta ƙwace ta sake komawa cikin rami wanda shi zurfin ramin tafiyar shekara ɗari biyar ne (500), haka kum mutum zai ta yi, ita kuma tana ƙwacewa.

    Saboda haka mutum ya yi tunani sosai akan aikata haka, kada ranar lahira ya taho da aikin lada mai ɗimbin yawa, amma kuma ya ci amanar mutane, ka ga wannan amanar da ya ci, to sai ta hana shi shiga gidan aljanna.

    Bugu da ƙari kuma riƙon amana yana ɗaya daga cikin abin da yake nuna ilimin mutum haɗi da tunanin sa da hankalin sa. Saboda Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) yace “mutane uku munafikai ne ko da ko sun ambata suna yin sallah, aikin hajji da ummara (su ne waɗanda) idan sun yi alƙawari da wani mutum sai sun saɓa, idan kuma mutum ya amince musu sai su yi ha’inci (cin Amana) da dai sauran su.

    Saboda haka a nan ma ka ga cin amana yana kai mutum zuwa munafunci, sannan kuma shi munafiki idan bai tuba ba, ya mutu a wannan hali, to Allah (Subhanahu wata’ala) yace a cikin Alƙur’ani mai girma “su munafikai suna cikin ƙarƙashin wutar jahannama “. Suratul Ma’ida.

    Saboda haka idan mutum yana aikin gina-ginai, sai wani mutum ya kira shi zai yi masa aikin ginin gida, to wajibi ne a kansa, idan an gama gina gidan, kada ya faɗawa ɓarayi ko kuma waɗansu ɓata garin mutane yanayin ginin gidan, saboda su samu damar shiga cikin gidan a cikin sauƙi, domin su samu damar yin sata.

    Sannan kuma idan mutum yana sana’ar kafinta ko rafta ko kuma saitin setilait, to kada ya yi amfani da wata hanya mara kyau wajen rage katako ko kuma fallasawa waɗansu mutane yanayin tsarin gidan, domin samun damar yin aika-aika, to aikata haka, laifi ne mai girma.

    Misali idan mai dukiya ko wani Alhaji ya kira wani mutum ya yi masa aiki a cikin gidan sa, to wajibi ne akan mai aikin ya kiyaye amanar da aka ba shi ma’ana kada ya ɗauko ɓata gari ko ɓarayi, sannan ya fayyace musu sirrin cikin gidan baki ɗaya, to aikata haka laifi ne mai girma, saboda dai-dai yake da wanda ya ci amana.

    Sannan kuma Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) yana cewa “Dukkanin ku (mutane) masu kiwo ne, sannan kuma za a tambaye ku akan irin kiwon da aka ba ku “.

    Saboda haka mutane ya kamata mu fahimci cewa dukkanin abubuwan da muke aikatawa a rayuwar mu, to mu sani fa amana ce a gare mu, saboda za a tambaye mu ranar lahira yadda muka gabatar da rayuwar mu.

    Haka kuma idan wani mutum ya ba wani mutum wani ko ya faɗa masa wata magana bisa ga sharaɗi ba zai faɗawa kowane mutum ba, to idan ya faɗawa wani mutum wancan magana, bisa ga wannan sharaɗi, to shi ma ya ci amana, saboda wanda ya faɗa masa maganar bai aminta wani mutum ya san wancan maganar ba.

    Saboda haka ita riƙon amana tana da mugun sha’ani kuma ga sanya takura a cikin al’amuran rayuwar wanda yake ɗauke da ita. Misali wani mutum ya ba ka ajiyar waɗansu kuɗi da niyyar zai karɓe su zuwa wani lokaci nan gaba, domin biyan waɗansu buƙatun sa, to kuma sai wata matsala ta samu wanda ya ba shi ajiyar kuɗin.

    To idan ya ɗauki kuɗin ya yi amfani da su ba tare izinin wanda ya ba shi ajiyar kuɗin ba, to ya karya ƙa’idar musulunci, sai dai idan lokacin da zai karɓe kuɗin yace da shi, to fa idan wata matsala da same shi zai yi amfani da kuɗin, sannan kuma sai shi wancan mutumin ya amince akan haka, to babu komai a kansa.

    Sannan kuma idan wani mutum ya ba wani mutum ajiyar dukiya ko kuma kadara, sai kuma a samu wata matsala wacce ta hallaka dukiyar ko kadarar ko kuma ya yi amfani da ita, to sai ya yi saurin sanar da wanda ya ba shi dukiyar, ma’ana halin da ake ciki, domin samun mafita akan wannan matsala .

    Saboda haka dukkanin wanda akwai wani abu wanda yake shugabanta kamar su shugabanci, koyarwa ko aikin gwamnati, jinga ko ƙwadago, kafinta, wanki, direba, gyara da dai sauran su, to yana da matuƙar kyau ko amfani a gare su, su kula da su da idon basira sosai, saboda ranar lahira za a tambaye su akan yadda suka gudanar da su a cikin gidan duniya.

    Bugu da ƙari kuma, dukkanin wanda ya ci amana, to amana shi ma za ta ci shi, wanda kuma ya kiyaye amana a nan gidan duniya, to ita ma za ta kare shi daga shiga wuta, muna roƙon Allah(Subhanahu wata’ala) da ya ba mu ikon sauke amanar da ke kan mu.

    Danna nan don karanta Hanyoyin Tabbatar Da Adalci

    Edita; RMK

  • Hani Akan Yin Gulma

    Hani Akan Yin Gulma

    Gulma: Shi ne ɗaukar zancen wani mutum zuwa ga wani mutum ba tare da yardar sa ba, don tayar da husuma (faɗa).

    Saboda haka, addinin musulunci, addini ne na haɗin kai (zukata), addini ne na zaman lafiya da kwanciyar hankali, wanda yake so ya ga ya haɗa zukatan mutanensa baki ɗaya a duk inda suke a cikin duniya.

    Haka kuma Allah (Subhanahu wata’ala) da manzon Sa annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) sun yi mana bayanin sharrin da gulma take iya haifarwa misali kamar su raba kawunan mutane, husuma ko jayayya, munafunci da dai sauran su.

    Saboda haka ne ma Allah (Subhanahu wata’ala) ya ja kunnen mu da aikata haka ta harshen annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) kamar yadda ya faɗa;

    لا يدخل الجنة نمام. Magulmaci (annamimi) ba zai shiga (gidan) Aljanna ba”. 

    Saboda haka, ka ga wannan hadisin ya ƙara nuna mana sharrin da gulma take iya haifarwa, saboda za ta iya hana mutum shiga gidan aljanna matuƙar ya mutu a wannan hali na gulmace-gulmace . Haka kuma gulma ko ƙarya ta wani fannin tana da ɗan amfani kaɗan, amma kuma ga wanda yake son ya ga ya haɗa kawunan wasu mutane waɗanda suke gaba da juna.

    Misali idan akwai wasu mutane da ba sa jituwa da juna, to ya halatta ko kuma babu laifi akan wani mutum sai ya tashi ya samu wani mutum daga cikin su ya gaya masa magana mai daɗi haɗi da wata kyauta idan yana da hali, sai yace da shi “ga shi abin ka wane ne yace na kawo maka, sa’annan kuma yana gaishe da kai, haka kuma sai ya sake samun ɗayan shi ma ya faɗa masa haka.

    Amma kuma a wannan lokacin gulma ta yi ƙaura a tsakanin mata da mata ta koma maza da maza ko maza da mata, wanda a lokutan baya da suka wuce an fi samun mata da gulmace-gulmace irin na su, amma kuma a yanzu haka wai har ma maza su ma suna yin gulmace-gulmace, kai! Hm! Wai faɗuwar girma ne ga raƙumi ya shanye ruwan ɗantsako.

    Bugu da ƙari kuma, duk me yin gulma shi ne wanda ba shi da aikin yi, saboda wanda yake da abin yi a gabansa, ba shi da lokacin yin gulmar wani mutum . Saboda haka, gulma ta wani fannin tana da alaƙa da hassada.

    saboda idan wani mutum suna faɗa da wani mutum ko kuma wani mutum Allah ya ɗaukaka shi, sai ka ga wani mutum yana faɗar wata magana mara kyau a gare shi, haka kuma sai ka ga yana ɗaukar maganar wani mutum yana faɗawa wani mutum, don ya ga ya haɗa su husuma ko kuma rashin jituwa a tsakanin su.

    Haka kum akwai hanyoyin da za a iya magance gulmace-gulmace da dama, misali idan wani mutum ya kawo maka gulman wani mutum, sai ka ƙyale shi har sai ya gama zayyano maka dukkanin zantukan sa, bayan ya gama, sai kawai kace da shi “to ai wannan gulma ce.

    Sa’annan kuma Allah (Subhanahu wata’ala) haɗi da manzon Sa annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) sun hana aikata haka, saboda haka daga yau kada ka sake kawo min irin wannan maganar, sa’annan kuma ka tuba ka daina aikata haka tun kafin ka haɗu da fushin Allah”, da dai sauran su.

    Danna nan don karanta hani akan yin gori

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Hani Akan Yin Gori

    Hani Akan Yin Gori

    Gori: shi ne yin isgili, shaguɓe, habaici akan wani mutum, wanda yake da kashi a gindinsa, ko kuma wanda yake da wata matsala kamar sata ko zina.

    Saboda haka, addinin musulunci ya hana yi wa wani mutum gori akan wani abu, saboda haka ne ma Allah (Subhanahu wata’ala) ya hana yin gori akan wata kyauta da wani mutum ya yi wa wani mutum, idan kuma mutum ya yi wa wani kyauta, sai kuma wata rana kwatsam ya goranta masa, to kyautarsa ta ɓace, ma’ana ba shi da ladan kyautar da ya yi har abada.

    Haka kuma, an hana yin gori ga wani mutum wanda yake aikata wani laifi a baya, ko dai ta hanyar daina  aikata laifin ko kuma ta hanyar tuba, misali idan wani mutum yana yin zina ko sata a baya, sai kuma yanzu ya gane kuskuren aikata haka, sai ya tuba. To addinin musulunci ya hana kowane musulmi ya yi masa gori akan irin abin da yake aikatawa a baya, idan wani abu  ya haɗa su na cacar  baki ko faɗa kamar “him! aikin banza ai daman can shi ɓarawo ne ko mazinaci” da dai sauran su.

    Saboda haka, akwai wata mace kirista ta musulunta, to sai wani abu ya haɗa su da wata mace musulma, to kuma ita wannan ita ce ba ta da gaskiya (musulmar), sai ta kalli wancan macen, sai tace da ita “Um! ki rufewa mutane baki tubabbiya kawai, kin gama iskancinki yanzu kin zo za ki faɗawa mutane maganganun banza”. Sai ita waccan macen ta yi kamar ta fita daga musulunci, saboda irin waɗancan maganganun da ake faɗa mata, amma da yake addinin ya shiga cikin zuciyarta, sai ta kau da kai.

    Har ila yau, idan wani mutum yana aikata saɓon Allah kamar su ƙarya, ha’inci, gori, shirka, algus, bokanci ko dabo, gulma, da dai sauran su, to idan wani mutum ya musulunta akan irin waɗancan abubuwan da yake aikatawa ko ya tuba daga aikata haka, to shari’ar musulunci ta hana kowane mutum ya faɗawa wani mutum baƙaƙen maganganu kamar su cewa ai maƙaryaci ne, mushriki ne, boka ne, magulmaci ne, maha’inci ne, mazinaci ne da dai sauran su.

    Saboda haka, ya kamata  musulmin da yake aikata haka, ya yi gaggawar daina aikatawa, saboda samun damar tserata daga fushin Allah (Subhanahu wata’ala) da manzon Allah (Salldlahu alaihi wasallam).

    Saboda dukkanin wanda yake yi wa wani mutum gori akan wani abu da ya ba shi ko kuma wani abu wanda wani mutum yake aikatawa mara kyau, sai kuma ya tuba ya daina aikatawa, to wanda yake yi musu gori akan haka, to zai iya shiga cikin fushin Allah (Subhanahu wata’ala) matuƙar bai daina aikata haka ba.

    Saboda haka gori ba shi da wani amfani ga musulmi mai hankali da tunani, saboda addinin musulunci ya yi hani akan aikata haka. Sa’annan kuma ko a a hankalce da tunani, to gori ba shi da wani amfani, saboda a wani lokacin gori yana kamanceceniya da tonon silili, wanda shi ma aikata haka ba shi da amfani ga musulmi.

    Haka kuma tonon silili da wasu mutane suke yi wa junan su, wannan kuskure ne, haka kuma ba shi da amfani ga addinin musulunci. Har ila yau, yunƙurin binciken laifin wani mutum wanda yake aikatawa ko kuma wanda ya daina aikatawa, to yin hakan kuskure ne, saboda idan wani mutum ya shagala da binciken laifin wani mutum, sai kuma ya manta da laifin kansa, to zai yi mutuwar biyu babu ko kuma kamun gafiyar ɓaidu.

    Saboda haka, yana da matuƙar mahimmanci akan musulmi dukkanin abin da zai aikata, to ya yi ƙoƙarin sanin hukuncin aikata haka da fatan Allah ya sa mu dace, sannan kuma mu nisanci aikata haka, haka kuma yana da matuƙar amfani ga mahukunta su ɗauki wani mataki ko tsari ga masu aikata haka, don samun ci gaban addinin musulunci baki ɗaya.

    Danna nan don karanta sauro halittar Allah mai ban Al’ajabi

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Hani Akan Yin Duba 2

    Hani Akan Yin Duba 2

    Ilimin “Geomancy” shi ake kira da “ramli” ko kuma duba akan yashi (har da biro da takarda duk ana yi). Ilimi ne da ya fita daga rubutaccen ilimin taurari (Astrology), don haka yake da sunaye da kuma salon bincike kusan iri ɗaya da na ilimin taurarin kuma an fi kyautata zaton larabawa su ne suka fara yin sa har ya watsu zuwa ƙasashen Africa da Europe.

    Shi ilimin ramli ɗigo-ɗigo a ke yi kusan kala 14 don a fitar da waɗansu abubuwa daga jikin ɗigon. Wanda na koya ina shekara 13 yana aiki ne da zanen da ya fito bayan ka gama zanen da ba ka ƙirga ba kuma ka soke biyu-biyu daga cikinsa. Idan 1 ta fito to za a auna ta da dai-dai buƙatarka, haka ma idan biyu ta fito. Akwai ababan mamaki a cikin ilimin da suke faruwa amma dai shi ma ana ɗora su ne kamar yadda ake ɗora sauran iliman Astrology.

    Akwai ababan mamaki da suke faruwa a cikin irin waɗannan iliman waɗanda har yanzu kimiyya ta kasa gano ya haƙiƙarsa take. Waɗansu abubuwan kamar “Telepathy”, “Entanglement”, “PSI” da sauransu har yanzu suna ba wa masu kimiyya mamaki duk da suna ɗora su a babin “Pseudosciences”.

    Yadda aka iya gano “Kuantum entanglement” to ana zaton za a iya fahimtar waɗansu abubuwan irin waɗannan da tafiyar lokaci. Zamanin amfani da “Classical Physics” na Newton da ya ɗoru akan lissafin Euclid ya wuce. Yanzu muna kan “Kuantum Mechanics” wanda ƙaryata abu ta farar ɗaya, don dogaro da kimiyya (classical physics) na nuna raunin mutum a sanin kimiyyar.

    Ana buƙatar bincike na sosai akan abu kafin a ƙaryata shi. Yanzu muna kan “super string theory” wanda ya ce duniya tana da “10-dimensions” maimakon 3-dimensions ko 4-dimensions da Einstein ya kawo! Hankali zai ruɗe bai gano haƙiƙar abubuwa masu “10-dimensions” ba amma hakan baya nufin cewa “super string” ƙarya ne don kawai ba ka fahimci yadda yake ba.

    Abu Hamidil Gazhali, a cikin “Almunkidh” yana magana akan “secrets of numbers”, yana faɗin cewa akwai abubuwan mamaki a cikin waɗansu lambobin. Ya ba da hoton waɗansu lambobi da ya ce an kasa gane sirrinsu. Lambobi ne kawai a jere amma idan aka haskawa mai ciki a lokacin da take naƙuda sai a ga ba ta shan wahala sosai!

    Ibn Khaldun ya faɗi waɗansu lafuza da yaren “Armenians” inda ya ce in dai ya karanta su to sai ya yi mafarkin abin da yake so! Abubuwan da ban mamaki ta yadda ake buƙatar a yi zurfaffen bincike a kai. Irin wannan to da su aka ɗora iliman “Numerology” da karanta zanen hannun mutum ko ƙirgen da a ke yi da carbi.

    Danna nan don karanta Hani Akan Yin Duba 1

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Hani A Kan Yin Duba 1

    Hani A Kan Yin Duba 1

    Duba: Shi ne bincikar abin da zai iya faruwa da wani abu nan gaba. Duba ta hanyar taurari shi ake kira da “Astrology” (yana da bambanci da “Astronomy” da take nufin kimiyyar taurari), shi kuma duba ta hanyar zanen ƙasa (ramli) shi ake kira da “Geomancy”.

    Waɗannan ilimai, kamar na bayansu, su ma suna da asali daga mutanen Hindu. Saboda asalin ilimin za a same shi a cikin manyan litittafinsu kamar Beda, inda aka samo “Bedic astrology”, da kuma abubuwan da aka ruwaito a litittafansu a yaren Sanskirt. Tun a zamanin Greek ana haɗe ilimin “Astronomy” da “Astrology” guri guda.

    Ptolemy a cikin littafinsa da ya yi bayani akan  ilimin falaki (Astronomy), a inda ya haɗa da bayanin “Astrology” da kuma yadda yake tafiya a fahimtarsa. Yana faɗar cewa, waɗansu abubuwan suna faruwa ne dai-dai da yanayin tafiyar taurari da kuma tafiyar rana da watanni. Don haka idan aka san yadda taurari suke, to za a iya gano yadda gaba za ta kasance. Ta haka zamu gane cewa ilimin taurari ya gangaro musulunci daga iliman Greeks ne.

    Ibn Khaldun a cikin Muƙaddima, yana cewa akwai buƙatar a san cewa babu wani bincike na haƙiƙa da yake tabbatar da tafiyar taurari da kuma faruwar waɗansu lamura.Wato dai tafiyar falaki ba ta nuna wani abu “supernatural” kamar na tsafi ko bokanci ko kuma faruwar wani abu a nan gaba.

    Sir Isaac Newton, kamar yadda aka ruwaito a cikin littafin “Cambridge Companion to Newton”, ya ba da labarin cewa ya tattauna da wani masanin ilimin taurari (Astrology) sai yake gaya masa haƙiƙar ilimin ba gaskiya ba ne amma hanyar cin abincinsu ce!

    Masana halayyar ɗan Adam (psychologists) sun tabbatar da cewa abin da yasa mutane suke aminta da gaskiyar ilimin taurari shi ne yadda suke ganin abu yana faruwa, bayan an faɗa musu zai faru. A haƙiƙar lamari ba faruwa yake dai-dai da yadda aka gaya musu ba.

    Ɗan Adam yana da saurin manta abubuwa ne, don haka idan mai ilimin taurari ya ce abu zai faru to mutum mantawa yake har sai wani lokaci can idan abu makamancin hakan ya faru, to sai ya yi zaton wanda aka taɓa gaya masa zai faru, shi ne ya faru ɗin.

    Misali, idan nace mahaifinka zai mutu bayan na yi duba, to mantawa za kai da na taɓa gaya maka har sai bayan ya mutu ɗin, wataƙila da ƙarin shekaru masu yawa, kawai sai ka tuna maganar sai ka ce ai dama na taɓa duba maka hakan zai faru! Wannan shi ne abin da suka ce game da yadda abubuwa suke faruwa a ilimin “Astrology”.

    Don Karanta Physiology da Hausa danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu