Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

0
109

Kamar yanda Khadeeja ta faɗa ba ta sake kula hidimar yaran a ranar da ba ita ce da kwana ba, sai dai ranar kwanata tana fitowa ta sallami kowa sanna ta cigaba da harkarta. Idan kuma dare ya yi ta shiga ɗakinta ta yi kwanciyarta don ta tabbatarwa Mustapha cewa ta ba shi kwanan.

Ranar Asabar ce don haka yara babu makaranta duk suna gida, kamar yanda suka saba tunda Khadeeja ta ƙi hidimar yaran to duk ranar girkin Naja Anti Wiyya ce take abinci har yaran. Ita kuma Najan ita ce za ta tsaya a kansu su yi wanka su shirya, sai dai ranar da ba ta tashi ba dole haka Mustaphan yake tashi ya yi ta faman yi musu faɗa har ya samu su gama shiryawa a hankali.

Afaf ce ita kaɗai a parlor ɗin Naja tana kallo saboda TV ɗin parlor ɗinsu Startimes ce ita kuma ta fi son DSTV wadda take parlor ɗin Naja; yayin da Anti Wiyya take ta kai wa da kawowa tana ƙoƙarin dora a bincin rana. Ta wuce Afaf a parlor ta shige ɗakin Naja inda ta same ta a kwance a gefen gado; bayan ta amsa sallamarta ta ƙarasa ta zauna a gefen kafarta kamar a fusace.

Tace ‘Sannu Anti, kina ta hidima. Lallaɓa ta nake yi idan ta ƙoshi goya ta zan yi na fito na taya ki. Salaman ma ina jin yau ba za ta zo ba; ko wa take so ya yi mana wanke-wanke da sharar oho ga girki. Ta yi tsaki ta kawar da kai tace ‘Kin ganni a cike nake da haushinta, ga shi kamar ta shirya wulaƙanci tunda yau wanke-wanken ya fi na kullum yawa sannan ta ƙi zuwa.’

‘Hmm! Ai sai haƙuri masu aikin zuwa da dawowa ba su da kirki, ni ma da na gama jegon nan me kwanan zan ɗauka. Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan Anti Wiyya tace ‘Ita kuma wannan ‘yar taki wallahi ita ma ba ta da mutunci; yaushe za a ce budurwa kamarta ba za ta yi aiki ba komai ƙanƙantarsa?

Sai dai ta dinga bin mutane da kallo suna mata aiki sai kace ubanta sayenmu ya yi. Gaskiya ku sake zama a gidan nan, haba! Idan banda ma rashin mutunci ya za a ce mace tana jego kuma a barta da kula da gida da yara bayan tana da kishiya? Ai kamata ya yi ta karɓar miki aikin. Ko da yake wannan ‘yar mulkin kishiyar taki na kula daga ke har maigidan tsoronta kuke yi.’

Ta tashi zaune ta kwantar da Rukayya wadda ta riga ta yi bacci, ta kama haɓa ta dubi Antin tata tace ‘A a shi dai yake tsoron matarsa, duk abinda ta ga dama tace ba za ta yi ba haka zai yi ta kame-kame saboda ita ba a iya yi mata dole. Ta kalle ta sheƙeƙe tana cewa ‘Kece karkatacciyar kukarsa mai daɗin hawa ko? Shi yasa kina jego amma aka lafta miki aiki?

Ita ko kunya ba ta ji? Sai ta sauko ta ishi mutane da gaishe-gaishe kamar wata musulmar ƙwarai. Cikin damuwa tace ‘Haka take fa, da an haɗu ta yi ta haba-haba da mutum amma mugun halinta yana nan fal cikinta sai mu da muke zaune da ita muka san halinta. Anti Wiyya ta ɗan yi ƙasa da muryarta tace ‘To gaskiya dai dole a yi aiki a kan wannan matar, yanda ta kama maigidan nan tana juya shi ai ba fin mu iyawa ta yi ba.

Kema idan kika zo yawon arba’in da kaina zan kai ki inda za a taimaka miki a ƙwato miki daraja. Wannan kwarjinin da take da shi take yi wa kowa har maigidan ke ma a samo miki shi. Taimako ne da ayar Allah ina da malamina a hannu kuɗi kawai za ki bayar. Har yaran ma don ubansu ko su bi ki su zauna lafiya ko kuma su koma ‘yan kallo.’

Tana ta jijjiga kai saboda gamsuwa tana cewa ‘Babu komai Anti, in sha Allahu za mu je. Don ni ma wallahi zaman haka ya ishe ni. Kuma dama Yaya ma tace za mu je ban san me ya ɗauki hankalinta ba. Nan suka zauna suka gama ƙulla yanda za a yi sannan suka fito suka kama hidimar gidan.

Haka suka cigaba da yi har Naja ta yi arba’in; duk wata kalma da Mustapha zai yi amfani da ita ya sa Khadeeja ta karɓi hidimar nan ba ta yi amfani ba har ya gaji ya sakawa sarautar Allah ido. Sai da Naja ta yi arba’in sanna suka cigaba da rabon kwana. Idan Khadeeja ce da kwana sai Mustaphan ya je ɗakinta yayin da ita kuma Naja take zuwa ɗkinsa.

Kwanci tashi har ya zama ta mayar da saman nasa kamar nata, ya zama kullum tana ciki ko parlor ɗinsa ko ɗakinsa. Ba ta daɗe da yin arba’in ɗin ba kuma Khadeeja ta gama bautar ƙasa; sai dai duk yanda ita da Baffanta suke ƙoƙarin samar mata aiki bai samu ba. Inda ta yi bautar ƙasar ma ta so su riƙe ta amma suka nuna mata ba sa buƙatar ma’aikata.

Ba ta son zaman gidanta, domin ta san in dai ya zama Naja za ta tafi aiki ta barta a gidan da yara to dole Mustapha zai yi duk yanda zai yi ya tursasa ta ta dinga kula da yara. Ya zama shi da matarsa suna yawon neman kuɗi ita tana musu hidimar gida da ta yara. Don haka ta sanar da manager za ta dinga zuwa Litinin zuwa Juma’a tana yi musu aiki kyauta.

Da ya ji haka sai ya sa aka ɗora ta a kan tsarin internship da suke da shi; inda duk wata za a dinga ba ta naira dubu goma sha biyar har zuwa lokacin da za a sami wani gurbi a gidan rediyon kawai sai a ɗauke ta. Sosai hakan ya yi mata daɗi, kuma ba tare da wata fargaba ba ta sanarwa Mustapha sun riƙe ta aiki, ta cigaba da zuwa.

Kusan wata takwas kenan da haihuwar da Naja ta yi; kuma kamar yanda suka tsara an kai ta wajen malami. Bayan malamin ya ji bayaninsu ya ba ta wani abu mai kama da gishiri yace ta yi sati tana zuba musu a abnci duk gidan kowa ya ci har Khadeeja. Haka ta dage ta yi amfani da abun nan sai dai ba ta da tabbcin Khadeeja ta ci abun marmarin da take girkawa tana aika mata, shi ma Habib ba ta da tabbacin cinsa domin ya fi cin abinci a wajen Khadeeja.

A hankali ta fara ganin sauyi, kamar dai duk yaran da Mustaphan suna saurararta; tunda wasu lokutan idan ta sa Afaf aiki haka za ta tashi ta yi ko ba ta so kuma Mustaphan ya daina hanata.

Sun gama magana da ita a kan zai siya mata mota, amma ga shi lokaci yana ta ƙurewa yanzu ya ma ce mata shi ba alkawari ya yi mata ba; shi kawai ce mata ya yi zai yi tunani. Cikin damuwa suke waya ta sanar da Anti Wiyya halin da ake ciki; tace ‘Wallahi Anti nema yake ya canza maganar.

Kuma dama na gaya miki aikin malamin nan ba kullum yake ci ba, tunda ko Mustaphan ya fara saurarar maganata da an kwana biyu sai ya sake komawa kamar da. Gani ma nake kamar duk lokacin da matarsa ta karɓi kwana sai ta warware min aiki, shi yasa nake ta fama da shi. Daga ɗaya ɓangaren Anti Wiyya tace ‘Au haka ne? To bar ni da su, ai ba mu za a yi wa bariki ba.

Akwai wani malamin aikinsa yana da zafi sosai, in kin sami lokaci kiyi min waya sai mu je wajensa. Ke kanki sai kin yi mamakin aikinsa. Suka ƙarasa hirarrakinsu suka yi sallama. Ta jefa wayarta a kan gadonta cike da ƙwarin gwiwa; ta san Mustapha yana ƙoƙari wajen kyautata mata amma ita gani take kamar tsoron khadeeja yake yi. Kuma ma ita so take ya zama gaba ɗaya gidan sai abinda ta faɗa za a yi.

Tana ganin yanda maza suke yi wa matansu kyauta ta burgewa, ita ma haka take so ya dinga yi mata, duk abinda ta nema ya ba ta kawai tunda ta san yana da kuɗin. Idan ma ta sami yanda take so to ko ganin Mustapha yaran ba su isa su yi ba sai da izininta, domin ta kula da yanda yake saurararsu yana bin ra’ayinsu kamar su suka haife shi.

Sai an yi magana yace su marayu ne. Tabbas dole gidan nan gaba ɗaya ya dawo tafin ƙafarta don ta gaji da wannan mulkin da ake mata ana kasa mata hankalin miji tsakanin uwargidansa da yaransa.

Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceSamuwar Rubutun Ajami
Labarin na GabaMenene Wasan Ƙunshi?
Sakina Muhammad Yazid
Ni ma'abociyar son rubuce-rubuce ce, malama kuma mai gudanar da sana'o'i. Ina ƙarfafawa matasa gwuiwa ta hanyar jagorantarsu da koyar da su. Ina rubuta labarai masu jan hankali kuma masu ƙunshe da tsari da al'adun Bahaushe.