EPILOGUE
Bayan shekaru 3. An yi auren Afaf an kai ta gidanta, yaron da ta aura ƙanin abokin Abbanta ne, da kanta ta je ta kai wa Khadeeja katin bikin nata wanda ta karɓa cike da girmamawa. Ta yi mata magiya a kan ta je amma duk da haka ba ta je ba, domin ba ta son abinda zai haɗa ta da Naja da dangin Mustapha a cikin taro.
Kuma duk yanda Mustapha ya so ya saka ta a cikin shawarar bikin Afaf ɗin da inda zai sayi furniture haka ta zame da wayo da dabara har ya gaji ya rabu da ita. Yana nan dai yana bibiya da kuma addu’ar ta yarda su mayar da aurensu. Yana zaune a ɗakinsa a kan dadduma yana hutawa bayan sallar la’asar kwana biyu bayan auren Afaf haka kawai ya ɗauki waya ya kirawo Khadeeja.
Ya gyara zama ya jingina da bangon da ƙofar ɗakin take jiki ta yanda idan aka buɗo kofar aka shigo zai zama yana bayan ƙofar kenan. Bayan ta amsa suka gaisa suka shiga hirarrakinsu, tana tambayarsa labarin biki. A haka har yace ‘Kin ga da kin yarda ai da tare da namu za a ɗaura.’
Ta yi dariya tace ‘Kai kuwa ka ƙi ka bar maganar nan. ‘Ba zan bari ba Khadija, har sai kin amince. Ko na tsufa ma sai na dawo da ke ko da takaba ne kya yi min sai mu haɗu a aljannah. Dariya kawai ta yi don ba ta da amsar da za ta ba shi. Suka yi shiru na ɗan lokaci sannan yace ‘Duk wani condition da kike so Khadeeja ki saka na yi miki alƙawarin zan cika in dai za ki zama mata ta.
Just one more chance Khadeeja, ki daina wahalar da zuciyata haka. Ta yi murmushi mai sauti ba tare da ta ce masa komai ba; tabbas yana nema ya gamsar da ita ta sake amincewa da aurensa, amma a halin yanzu ba ta san amsar da za ta ba shi ba. Ya gaji da shirun kuma yana ji a jikinsa cewa kalamansa sun fara yi mata tasiri.
Ya katse shirun yace ‘Gobe da safe zan shigo, ok? ‘Ok, Allah ya kai mu. Amma ina da programme da safe so ka bari sai bayan azahar. ‘Ok, I will take you out to lunch then. No execuses. Ta yi dariya ‘Ka dai san ba zan je ba ko? Kada ma ka fara wata rigimar daban.’ ‘In dai rigima ce ai a wajenki na koya. I will see you tomorrow at lunch.’ Ya ajiye wayar ba tare da ya bari tace wani abu ba.
Ko da ba za ta yarda ya fita da ita lunch ɗin ba ya fi so ta bar shi ya kwana da murnan zai fita da Khadeeja gobe, in ya so idan ya je office ɗin su yi faɗan da suka saba. Tana tsaye a jikin ƙofar ɗakin tana jinsa, duk abinda ya faɗa tana ji. Sai da ya ajiye wayar sannan ta banka ɗakin ta shiga a fusace.
Firgigit ya juyo ya kalli ƙofar da aka mako, yace ‘Ya haka kamar za ki fizge ƙofar? Me ya faru ne? Ko wani abun ya biyo ki? Ta tsaya tana masa kallon raini tana jijjiga, sai da gaji da kallon nasa sannan a fusace tace ‘Mustapha na gaji da wulaƙancin da kake mina a kan matar nan, shekara huɗu ana abu ɗaya saboda tsohon naci. Wallahi babu ruwan Allah da kun taɓa aure alaƙarku haramtacciya ce.
Kuma idan ma zina kuke Allah zai kama ku. Faɗan nata bai harzuƙa shi don ya saba ji, idan ma ba ta ji yana waya da Khadeejan ba kullum cikin duba masa waya take. Ba sa magana ta whatsapp don haka kullum cikin duba calls take, da zarar ta ga call ɗin Khadeeja to sai ta yi wannan masifar. Ya miƙee ya naɗe daddumar yana cewa ‘Kada ki kuskura ki jefi khadeeja da wannan kalmar yanzu ranki zai ɓaci, kuma kin sani.’
Ta riƙe ƙugu tana dan zare ido tana cewa ‘Ohh! Yanzu kai ka fi son Khadeeja kenan dan kanka, kai na jefe ka da koma menene amm kada na jefi Khadeeja ko? To wallahi da kai da ita baku isa ba…. ‘Ke kika sani.’ Ya faɗa tun kafin ta ƙarasa faɗin abinda take faɗa, ya ajiye daddumar ya kewayeta ya fice daga ɗakin.
Ta juyo ta bi bayansa da kallo cike da takaici sannan ta wuce ta zauna a gefen gado ta zuba fuskarta a tafukan hannunta ta fashe da kuka. Wannan wane irin wulaƙanci ne, tana murna ya saki kishiyarta amma kullum suna tare, ita kuma tana nan ya kulle ta a gida. Wannan wace irin musiba ce? So take ta ware rana ta je ta sami Khadeejan a office ɗin nata ta tara mata mutane amma dai tana tsoron kada Mustapha ya sake ta a kan hakan; don yanzu ta ga kamar ma ba a haiyacinsa yake ba.
To yanzu babu aure a tsakaninsu yana mata wannan tsohon nacin idan kuma ta dawo ya za a yi? Ita menene makomarta ya dawo da rabin ransa me ƙaunar ‘yayansa. Ta ɗora hannu a ka ta sake rushewa da kuka.
END
Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu
Edita@rumasau-kallamu









