Tag: Zaman lafiya

  • Dabarun Zaman Lafiya Da Mutane

    Dabarun Zaman Lafiya Da Mutane

    A tasa gudunmawar a wannan fanni, shaihun malamı Abdullahi ibn Fodiyo (R.A) ya bayyana muhimman ƙa’i’doji waɗanda in mutum ya bi su, zai iya samun zaman lafiya da kwanciyar hankali da kowane irin jinsi na mutane.

    Malamin ya yi wannan bayani ne a cikin littafinsa mai suna:

    “Aadaabu Mu’aasharat, Litaalibinnajaatı Fiddunya Wal Aakhirat”.

    Ga abin da malamin yake cewa:

    1. Ya ɗan uwa kada ka wulaƙanta kowa, domin kai ba ka san matsayin mutum ba a wurin Allah, wataƙila ya fi ka daraja

    2. Kada gafalallu ‘yan duniya masu sharholiya su ɗaɗa ka da ƙasa, har ka girmama su, saboda duniya ba a bakin komai take a ba wurin Allah.

    3. Ka kare mutuncinka, kada ka roƙi kowa sai Allah, sai dai bisa halin lalura. Kuma kada ka damu, ko ka zargi kowa in ka roƙa aka hana ka.

    4. Kada ka wahalar da kanka wajen yin wa’azi ga wanda ba ka ga wata alamar karɓar wa’azi daga gare shi ba. Kuma ka guji ambaton sunayen mutane (ko ƙungiyoyi) cikin wa’azinka.

    5. Idan ka ga mutane suna girmama ka, to ka gode wa Allah, ka roƙe shi ya tsare ka daga dogara ga mutane.

    6. Idan kuwa suka cutar da kai, to ka haɗa su da Allah, ka nemi kariyarsa daga sharrinsa, kada ka damu da ɗaukar fansa, har sai abin ya yı maka yawa, ka rasa da wanda za ka ji, ka ɓata goma ɗaya ba ta gyaru ba. Allah dai shi ne yake sanya a so mutum ko a ƙishi.

    7. Lokacin da kake cikin mutane, ka saurari maganganu na gaskiya, ka toshe kunnuwanka daga ƙaryace-ƙaryacensu. In za ka faɗi, faɗi gaskiya, ka zama bebe wajen faɗin zancen banza.

    8. Ka karanta abota da mutane, saboda yawancin mutane ba sa yin afuwa. ba sa rufa asiri, suna neman haƙƙinsu, amma su ba sa so su bawa mutane haƙƙinsu, sun fi yarda da ƙarya da kuma gulmace-gulmace. Kai zama da waɗansu mutanen ma dai ba shi da wata riba, farat-farat a fuska, amma a zuci ba sa sonka, kuraye ne su da fatun awaki, a kan zato suke yanke hukunci, ga su da yi da mutane, kuma ba sa da wani buri sai su ga bala’i ya same ka.

    9. Kada ka saki jiki da mutumin da ba ka san halinsa ba ta hanyar zama da shi a gida ɗaya, ko a kasuwa ko halin tafiya. Da kuma halayyarsa lokacin da yake cikin wadata da talauci, da murna da fushi. Sannan ka gwada mu’amala da shi ta kuɗi, ko ka bari sai lokacin da ka shiga cikin wani matsi, ka buƙaci taimakonsa ka gani zai taimake ka ko kuwa.

    Duk mutumin da ka gwada shi cikin waɗannan halaye ka ga ya haye to wannan shi ne mutum, in ya girme ka, ka ɗauke shi a matsayin uba, in ka girme shi ka mayar da shi ɗa, in kuma sa’anka ne, ka ɗauke shi a matsayin ɗan uwa.

    10. Ka karɓi aboki da maƙiyi cikin haba-haba amma ban da wulaƙantar da kai.

    11. Ka ja girman ka, amma ka guji girman kai.

    12. Ka ƙasƙantar da kanka, amma ka da ka wulaƙantar da kanka.

    13. Komai za ka yi, ka ɗauke shı (tsaka-tsaki).

    14. Ka guji yawan waiwaye lokacin da kake cikin jama’a.

    15. Kada ka rinƙa wasanni da sauran abubuwan ƙasƙanci a cikin mutane, kamar wasa da gemu, kwararrasa yatsu, sakace, gyaran hanci, yawan tofe-tofe da kaki, karairaya jiki, yin hamma ko atishawa a fuskar mutane.

    16. Ka zauna cikin nutsuwa, a yi magana cikiņ tsari.

    17. Ka saurari abokin hirarka lokacin da yake magana mai ma’ana. Kada ka zaƙe wajen nuna masa ya burge ka, kada ka nemi ya maimaita maganar.

    18. Ka daina yawan faɗar labaran ban dariya.

    19. Ka daina yawan faɗar nasarorinka da na iyalinka ko wakarka da sauransu.

    20. Ka guji ƙyale-ƙyale da caɓa ado kamar mace, amma kada ka zauna busu-busu kamar baiwa.

    21. Ka guji yawan sa kwalli.

    22. Ka guji naci.

    23. Kada ka goyi bayan kowa a kan zalunci.

    24. Kada ka bari ‘ya’yanka da iyalinka su san yawan kuɗinka, saboda in sun ga ba su da yawa, sai su raina ka, idan kuwa suna da yawa, sai su ci burin da ba za ka iya gamsar da su ba.

    25. Ka rinƙa yin barazana ga iyalinka lokaci-lokaci.

    26. Ka sassauta musu amma kar ya kai yadda za su raina ka.

    27. Kada ka rinƙa yawaita wasa da barorinka, sai su raina ka.

    28. Yayin da husuma ta haɗa ka da wani ka nutsu, ka guji wauta da gaggawa. Ka yi nazari sosai kan hujjojinka, kada ka yawaita waiwaye-waiwaye.

    29. Idan wani mai mulki ya ja ka a jiki, to ka yi taka tsantsan, kada ka saki jiki da shi, ka tausasa masa irin tausayin ka ga ƙaramin yaro, ka faɗi abin da zai faranta masa rai, in dai bai saɓawa shari’a ba. Kada ka yi karambanin shiga cikin harkokınsa da iyalinsa ko ‘ya’yansa ko mataimakansa.

    30. Ka guji abokin ta-faɗi-gasassa, wannan shi ne cikakken maƙiyi lokacin da duniya ta juya maka baya.

    31. Kada ka fifita kuɗi a kan mutunci.

    32. Idan ka shiga cikin mutane ka yi sallama, kada ka ƙetare mutane. ka zauna duk inda ya samu ya samu, ka yi wa na ƙasa da kai sallama.

    33. Ka guji zaman hira a gefen hanya; sai fa in za ka baiwa hanya haƙƙinta, shi ne kau da kai daga kallon haramun, taimakon wanda aka zalunta, agaza wa mabuƙaci, kwatance ga ɓatacce, amsa sallama, taimakon mabaraci, umarni da kyakkyawan aiki da hani ga mummunan aiki da kuma tanadin wuri na musamman domin yin kaki, ban da tofarwa a alƙibla, ko barin dama ko hagu sai dai a ƙarƙashin ƙafarka ta hagu.

    34. Kada ka zauna da masu mulki, in kuwa aka jarrabe ka da zama da su, to ka guji yi da mutane da ƙarya. Ka riƙe sirri, ka karanta buƙatu da kakaci, kai dai ka yi kaffa-kaffa da su. Ban da bankaɗa a irin su ko sukar mulkin su, ko ci musu mutunci, domin masu mulki ba sa yafe waɗannan laifuka.

    35. Kada ka yawaita zama da gama-garin mutane, in zama ya haɗa ka da su, kada ka sa baki a cikin hirarsu, ka kau kai daga munanan lafazuzzukansu, ka ƙaranta haɗuwa da su da yawan kakaci. Saboda yawan kakaci yana zubar da mutunci, da haifar da gaba, da mutuwar zuciya yana sanya rafkana yana janyo ƙasƙanci,, da kashe zuciya. ldan ka zauna a wuri aka yi kakaci yana da kyau kafin a tashi a karanta wannan addu’a:

    “Subhana kallaa humma wa bi hamdika ash hadu an laa ilaaha illaa anta astagfiruka wa a tuubu ilaika”.

    Domin karanta cikakken bayani akan Zaman Lafiya Da Iyali danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Ziyarar Mara Lafiya danna nan.

    Wannan bayanin anciro shi ne daga Littafin Hanyoyin Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali; wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

     

  • Zaman Lafiya Da Iyali

    Zaman Lafiya Da Iyali

    Allah Ta’ala ya ƙaddara rayuwar mace da namiji a tare cikin tsananin buƙatar juna; babu wanda zai iya rayuwa shi kaɗai a cikin su. Saboda haka ya zama wajibi mutum ya nemi hanyoyin zaman lafiya da abokin zamansa.

    A ɓangaren maza, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya yi umarni da juriya da haƙuri da kau da kai, da auna kirkin mace da rashin kirkinta, sai a dubi ɓangaren kirkin a kau da kai daga ɗaya ɓangaren. Kuma a aikace rayuwarsa (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) cike take da misalai kan haƙuri.

    Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam)ya ce; “Ku kyautata wa mata, saboda su an halicce su daga karkataccen ƙashin haƙarƙari, in ka ce za ka miƙar da shi, sai ya karye, karyewar sa shi ne saki”. (Bukhari da Muslim).

    Kuma (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya ce; “Kada mumini ya ƙi (matarsa) mumina, in tana ɓata masa da wasu halayen, ai tana faranta masa da waɗansu”. (Muslim).

    Wannan Hadısi ya nuna wa ma’aurata da su zama masu godiya da afuwa ga juna; kada a rinƙa kallon juna da ido ɗaya, ai idan rai ya ɓaci, to a yi amfani da hankali a duba amfanin juna ga juna, wannan sai ya shafe kowane irin laifi.

    Sannan kai miji duk abin da za ka yi wa matarka, ka yi mata shi saboda Allah kawai! kada ka ɗau don ba ta gode ba, ko ba ta yaba maka ba, mafi yawancin mata ba su san su yi godiya ga alherin mazajensu ba. In ka fahimci haka, sai ka zauna lafiya.
    lta kuma mace, babban abin da yake kanta shi ne, cikakkiyar biyayya da nuna ƙauna ta gaskiya ga mijinta. Tsaftar jiki da tufafi da mahalli da tattali da iya girki da sakin fuska da kuma magana mai daɗi; Sinadarai ne na zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin miji da mata.

    Wani masanin halin ɗan Adam a littafinsa mai suna: “Maganin Farir Jini Da Mallaka” wanda aka fassara shi da Larabci ya lissafa ƙa’i’dojin zaman Lafiya tsakanin miji da mata, ga su a dunƙule kamar haka:

    1. Ki guji saurin fushi da muskilanci da kuma nunƙufurci. Yawancin mata da zarar miji ya dawo sai su haɗe fuska, babu sauran walwala, sai kaushin magana da galatsi. Waɗansu mazan ma haka suke in sun shiga gida, sai fushi da ɓacin rai, kamar ‘yan wuta, amma da sun fita waje sai ka ga murna kamar suna aljanna. Domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a rayuwar aure, ya kamata kowa ya ajiye makamin a sakarwa juna fuska.

    2. Ku yi ƙoƙarin fahimtar halayen juna. In ka san halın mutum, shi ke nan ka ci maganin zama da shi, Ka da ka ce a dare ɗaya za ka canja halayen matarka, waɗanda ba ka so, ke ma ki ƙyale shi ya rayu yadda yake. Canjin hali sai a hankali. Kai a gaskiya mai wani halin zanen dutse ne, babu abin da zai iya kankare shi, to kuwa tun da haka ne, ai kowa sai dai a zauna da shi da halinsa.

    3. idan wani sabani ya faru tsakanin miji da mata, bai kamata a zargi juna ko faɗa ba a gaban yara, ko waɗansu baƙi. Wato bai kamata ka balbale matarka ko ki fada wa mijinki da mita ba, a gaban ‘ya’yanku ko waɗansu baki, ko da kuwa iyaye ne ko ‘yan uwa. A maimako haka, sai ku zauna bayan kowa ya huce ku sasanta da junanku.

    Wannan shi ma tushe ne babba na zaman lafiya.

    4. Duk mutum yana son in ya yi abin kirki a nuna ya yi, kuma a yaba masa, wannan sai ya ƙara masa ƙarfin gwuiwa, ya ninka abin da ya yi, ballantana mace, wacce take da ɗabi’ar son yabo da koɗa kai, koda kuwa kan ƙarya ne. saboda haka yayin da ka ga ta caɓa ado ko ta tsantsara girki to ya kamata ko yaya ka furta kalmomin yabo. Haka ke ma uwargida bai kamata ki mayar da mijinki kamar bawa ba, ko wanda kika baiwa ajiya, ko mai ya kawo ki karɓe ki yi shiru ba na gode, sai kuma in ba a yi ba ki ɗau fushi, yin haka ƙidahumanci ne da toshewar basira.

    5. Wani muhimmin abu mai tabbatar da zaman lafiya tsakanin ma’aurata shi ne, nuna farin ciki lokacin farin cikin abokin zama, kamar bikin ‘yar uwarta ko ƙawarta ko kuma na ‘yan uwan miji, kai ko bikinsa na ƙarin aure. Saboda idan ɗaya ya yi fushi yayin ɗayan yake farin ciki, lallai kam ba zaman lafiya. Saboda haka yana da kyau miji da mata su taya junansu murnar ko baƙin cikin abin da ya samu ɗayansu.

    6. Ya kai mai gida kasance mai hikima wajen nuna wa matarka kuskuranta. Misali idan ka ce ta kawo maka ruwa, sai ta tsaya wani wuni-wuni kuma ba wani aiki ne ya ɗauke ma ta hankali ba; to kawai ta gan ka a bakin rijiya ko famfo ka ɗebo ruwanka.

    Ko kuma ba ta shara da wuri, kai kuma ba ka son ganin wurin kaca-kaca, to tunda sanyin safiya ka ɗau tsintsiya ka kama shara, shi kenan, ka huta da ɓacin rai, ita kuma in dai mai hankali ce, sai ka ga ta gyara halinta. Ka daure ka gwada wannan maganin akwai huce haushi sosai a cikin sa.

    7. Akwai littattafai da dama da aka rubutu waɗanda suke bayanin rayuwar aure musamman ga waɗanda ba su taɓa yi ba. To me zai hana ka karanta ɗaya daga cikin waɗannan littattafan da kai da matarka domin kanku ya waye, ku fita daga duhun jahilci da ƙidahumanci. Saboda bincike ya nuna yawancin rigıngimu tsakanin ango da amarya jahilci ne yake haifar da su.

    Waɗannan ƙa’i’doji guda bakwai, suna da matuƙar amfani ga wanda ya yi aiki da su; wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin ma’aurata.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Mene Ne Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Cin Mutuncin Mutane Da Sunan Hamayyar Siyasa. danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Hanyoyin Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali; wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.