Tag: ilimin addani

  • Falalar Salati Ga Manzon Allah (S.A.W)

    Falalar Salati Ga Manzon Allah (S.A.W)

    An karɓo daga Abdullahi Ibn Mas’ud (RA) haƙiƙa Manzon Allah (S.A.W.) ya ce: “Haƙiƙa mutane da za su fi kusanci da ni rana alƙiyama su ne, waɗanda suka fi yawaita salati a gare ni” (Tirmizi 446).

    An karɓo daga Abdullahi Ibn Malik (RA) ya ce: Manzon Allah (S. A. W.) ya ce: “Wanda ya yi min salati guda ɗaya, Allah zai yi masa salati goma, kuma za a kankare masa zunubi goma, kuma za a ɗaga darajojinsa” (Nisa’I 1280).

    An karɓo daga Abdullahi Ibn Amr Ibnul As (RA) haƙiƙa ya ji Manzon Allah (S.A.W.) yana cewa: “Idan kuka ji mai kiran salla, ku faɗi irin abin da yake faɗa, sannan ku yi min salati, sabo da duk wanda ya yi min salati ɗaya, Allah zai yi masa goma, sannan ku roƙa min Allah ya ba ni matsayin wasila, saboda wasila wani matsayin ne da mutum ɗaya ne kaɗai a cikin bayin Allah zai cancance shi, ina fatan na kasance ni ne wannan bawan, Kuma duk wanda ya roƙa min wasila, cetona ya tabbata a gare shi” (Muslim 577).

    Falala da fa’idodin salati ga Annabi (S.A.W.) suna da yawan gaske, yana haskaka zuciya da da kaifafa ƙwaƙwalwa, yana sanya a gafarta zunuban mutum, addu’ar da ake fara da shi karɓaɓɓiya ce, yana yaye baƙin ciki da ɓacin rai da suran fa’idoji masu yawa.
    Haka kuma akwai wurare da ake son a yi wa Annabi (S.A.W.) salati kamar a ƙarshen kiran salla da tahiyar farko da ta biyu, a lokacin addu’a da duk lokacin da aka ambaci sunansa da sauransu.

    Faɗakarwa

    Ya kamata ‘yan uwa mu sai cewa babu wani salati mai falala da daraja in ba salatin da ya fito daga bakin fiyayyen haitta ba (S. A. W.) a ingantattun hadisansa. Saboda haka, mu riƙi irin waɗanna salalatai mu bar kame-kame.

    Sigogin salati da suke da inganci da Manzon Allah (S.A.W.) za su kai goma sha bakwai, sai a tuntuɓi malaman sunna domin ƙarin bayani. Allah ya sa mu dace.

  • Yadda Halittar Lokaci Da ƙarewarsa Yake

    Yadda Halittar Lokaci Da ƙarewarsa Yake

    Ƙudurar Ubangiji  kadai itace wanzanjjiya. Domin kuwa tun farko babu jiya babu yau, ba nan ba can , babu gaba  ba baya.

    Ba a san nisa da kusanci ba, balantana kuma ko banbanci, kamshi ko wari babu su, dare da rana babu zuriyarsu, lissafi da kwatance ba mai tunani su.

    Domin babu sama, ba ƙasa, ba  halitta. Sai ALLAH ya halicci sarari da lokaci sannan ya samar da halittu da rayuwa da mutuwa da ma’auni Ayoyi masu zuwa na ƙarfafa wannan ma’ana:

    Sannan ya daidaita zuwa ga sama alhali kuwa ita (a lokacin) hayaƙi ce,sai ya ce mata, ita da ƙasa ku zo bisa ga yarda ko akan tilas “suka ce muzo, muna Da’a
    Sura fussilat-Aya 11

    Wannan Aya na nuna farko halittar sarari (space) tun a farkon al’amari. Daganan kuma halittu suka bigire da matsuguni. Kamar yadda Ubangiji maɗaukaki  ke faɗa dangane da farkon halittar  Annabi Adamu a lokaci yana cikin aljanna da matarsa Hauwa’u:

    Kuma kuna da matabbaci da ɗan jin daɗi izuwa wani lokaci a bayan ƙasa (doron duniya)’’. Sura Bakara Aya 36

    Rayuwa ɗan-Adam a doron ƙasa ba zata yiwu ba, ba don Ubangiji yahore tagare shi ba. Ubangiji na cewa:

    kuma yahore muku rana da wata dawwamammu da kuma dare kuma ya baku dukkan abinda kuka roƙe shi. Da zaku ƙirga ni’imomin Allah (Maɗaukaki) ba za ku iya ƙididige su ba

    sura-Ibrahim:33-34

    Ubangiji Maɗaukaki na cewa:

    shi ne wanda ya sanya rana mai haske wata kuma mai haskawa. Ya gwargwaje shi a masauki don ku san ƙididdigar shekaru da lissafi. Allah (MAɗaukaki) bai halicci wannan ba  sai don gaskiya yana rarrabe ayoyi ga mutane masu sani.
    “Yunus-Aya 5

    Saboda kimar lokaci kuwa ubangiji maɗaukaki ya yi rantsuwa da shi a wurare da yawa cikin Alqurani:

    • (Ina) rantsuwa da lokaci (zamani)…………………..
    • A wani gurin yace (Ina) rantsuwa da alfijir…………………………….
    • Wata ya yar kuma (Ina) rantsuwa dada lokacin walaha……………….
    • (Ina) rantsuwa dada Dare……………………………

    Malam tafsir na cewa idan Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da wani abu to akwai ishara izuwa ga irin girman wannan al’amari da tasirinsa da amfaninsa. Lokaci na shuɗewa ne ta yadda mutum ba zai  Ankara ba har sai ya zagayo, wata ya wuce shekara ta zo ta tafi.

    Wani mai hikima na cewa.
    • Ɗaya ta wuce biyu ta biyo ta:
    • Uku na nufin cin didigenta
    • Hudu ko kamar na rarako ta:
    • Zancen ya shekara ba wuya
    • Ka san da ranar haihuwarka:
    • Yau ga shi ka zama ɗan gidanka:
    • Domin gudu nata duniya

    Ka lura da kyau daga ƙuruciyarka zuwa yau din nan, zaka ga kamar sati ne ya wuce. Babban misali a nan shine: ɗaukar ciki da haife shi. Yaye  da shayi Gama karatun firamare da sakandare. kammala ilimin jami’a. Ga shi yau har ka yi aure ka zama magidanci. Ashe dai lokaci gudu yake yi amma ba mai gani sai mai idanuwan zuciya da lura.

    LOKACIN RAYUWA KAMAR ZAREN KASET NE

    Lokaci rayuwa ga kowannemu ya danganta da irin yadda Ubangiji Maɗaukaki ya ɗeba masa. Manzon Allah (SAW) na cewa rayuwarmu shekaru sittin ko saba’in kadan ne ke wuce wannan.

    Mu ɗauka wasu za su kai shekaru casa’in wasu ɗari. Wasu kuwa talatin wasu arba’in ko hamsin da sauransu. To ka ga kuwa rayuwarmu tamkar kaset ne mai 60 ko 70 ko 90 ko 100 ko 30 ko 40 ko 50 gwargwadon yawan shekarun da aka qaddara mana ba daɗai ba ragi.

    Da zarar an haifi jariri sai  kaset ɗin rayuwarsa ya fara naɗe bayanan motsinsa da ayyukansa masu kyau da munana. Hatta minshari da kakaki da ihu  da ashariya da ibada, kaset ɗin zai cigaba da juyawa cikin zaren lokaci ba tsayawa. Ruwan mutum ya kama tasbihi ko karatun Alƙur’ani ko barci ko ya shiga kakaci da batsa, kaset ba zai tsaya ba. Kuma ba zai dena naɗa ba har sai ya je ƙarshe.

    Da yaje ƙarshe kuwa mutum zai bar duniya ko da shiri ko ba shiri. Jama’a mu lura a kowanne lokaci zaren rayuwarmu ƙarewa yakeyi kullum cikin daƙiƙa. Mu ribaci lokutanmu don in ya tafi ba zai dawo ba. Ubangiji Maɗaukaki Na cewa:

    Lallai ajalin Ubangiji Maɗaukaki in ya zo ba a jinkirta shi. Da kun sani (hakan)”. Sura munafiƙun-Aya-11

    Game da gaggauta ayyuka na gari kuwa Ubangiji Maɗaukaki na cewa:

    “Ku ciyar daga abinda muka azurta ku tun kafin mutuwa ta zo wa dayanku. Sannan ya ce Ubangijina ina ma ka jinkirta min izuwa ɗan lokaci na zamo cikin nagartattu.”

    Allah (maɗaukaki) baya taɓa jinkirtawa wata rai idan ajalinta ya zo. Kuma Allah (maɗaukaki) Mai bada labari ne game da abinda kuke aikatawa”-Sura Munafiƙun: Aya 10

    KIMAR LOKACI A RAYUWAR ƊAN ADAM

    Manzon Allah (SAW) ya ce: Ka ribaci abubuwa biyar kafin abubuwa biyar (suzo)

    1. Quruciyarka/kafin tsufanka
    2. Lafiyarka kafin rashin lafiyarka
    3. Wadatarka kafin talaucinka
    4. Faragarka kafin shagaltuwarka
    5. Rayuwarka kafin mutuwarka

    Bugu da Ƙari Manzon Allah (SAW) yace:” Ƙafafun Ɗan adam ba za su gushe ba a ranar alƘiyama har sai an tambaye shi game da abubuwa huɗu:

    • Rayuwarsa ta yaya ya ƙarar da ita?
    • Quruciyarsa ta yaya ya ƙarar da ita?
    • Dukiyarsa ta ina ya same ta, kuma ta yaya ya kashe
    • Iliminsa ya yayi da shi?

    Akwai hadisi da Bukhari ya ruwaito Manzon Allah (SAW) ya ce: “Ni’imomi biyu ana yiwa mutane da yawa kumunga a cikinsu”. Ma’ana suna tozarta su cikin abinda ba zai bayar da amfani ba. Lafiya da samun dama”.

    domin samun cikkekken littafin danna koren rubutu

  • Yadda Ɗabi’un Annabi (S.A.W) Suke

    Yadda Ɗabi’un Annabi (S.A.W) Suke

     Manzon Allah (S.A.W) ya kasance mai yawan murmushi da sakin fuska. Wani lokaci yakan yi dariya, har haqoransa na gaba ko wushiryasa ta bayyana.

    Idan ya yi fushi jijiyar fuskarsa takan kumbura da jini. Amma fa baya yin fushi domin an cuce shi, sai domin an saɓa wa Allah. Ya kasance mai nutsuwa da yawan zurfafa tunani. Ba shi da yawan wasa da kakaci koda dai yakan yi barkwanci (ko abin da ake kira zolaya), a wasu lokutan. Idan zai yi Magana yakan yi ta filla-filla, yadda kowa zai gane abin da yake nufi. Kalmominsa ‘yan kaɗan sukan ƙunshi bayani masu yawa. Wannan shi ake kira (kalmomi ‘yan kaɗan, waɗanda suka ƙunshi abubuwa masu yawa).

    Ya kasance yana da son ƙamshi, ba ya son wari ko kaɗan. Yana da son yin abubuwa da dama. Kamar taje kai da sanya takallmi da yayin yin wanka da dukkanin al’amuransa5. Yakan yi tafiya da takalmi, wani lokaci ba sai da takalmi ba. Yana yin tafiya cikin sauri, tare da ɗaga kan tudu. Idan zai yi waiwaye yakan juya da jikinnsa gabaɗaya.

    Annabi Muhammad (S.A.W) ya kasance yakan yi zaman haɗe jiki. Watau yakan zauna cinyarsa a haɗe da cikinsa, alhali ya sa hannayensa ya haɗo qafafuwansa. A wasu lokutan akan ga ya yi rigingine, ya ɗora ƙafarsa ɗaya a kan ɗaya. Ya kasance idan zai ci abinci yakan ci a durqushe. Yana ci da ‘yan yatsu uku. Musamman abincin da zai ciwu a haka. Kamar dabino da gurasa da sauransu.

    Idan zai sha ruwa ba ya yin numfashi a cikin mazubin, kuma yana sha a zaune. Kodayake a wasu lokuta a kan ga sha ruwa a tsaye. Ya zo a cikin As Shama’lun Nabawiyya cewa, Annabi Muhammad (S.A.W) yana da son koren abu. Kuma ya fi son na ƙafafuwan ƙaramar dabba.

    Bai taɓa yin kwana uku yana ƙoshi da gurasar alkama ba. Ya fi cin gurasar sha’ir. Mu sani cewa shi sha’ir kamar alkama ya ke. Bai taɓa cin gurasar da romo ba har ya bar duniya. Watau sai dai da mai. Idan ya isa gidan mutane yakan tsaya a gefen dama na ƙorar gidan, ya yi sallama. Ya kasance idan zai kwanta yakan ɗora kansa a kan hannunnsa na dama, ya ambaci Allah, sannan ya yi bacci.

    Daga ka’abun bin Malik (RA) ya ce: “Manzon Allah (S.A.W) ya kasance fuskarsa takan zama kamar wani yanki ne na farin wata, idan yana farin ciki” (Bukhari ne ya ruwaito).

    “Daga Aliyyu (RA) ya ce: “Manzon Allah (S.A.W) ya kasance idan yana tafiya, yakan yi ta cikin sauri da ɗaga ƙafa, kamar yana gangarowa daga tudu”, (Tirmizi ne ya ruwaito).

    Amma idan yana yin tafiya tare da sahabbansa yakan sa su a gaba. Yakan ce: “Ku bar bayana domin mala’iku”.

    Idan Annabi Muhammad (S.A.W) ya isa wurin taron jama’a, yakan zauna a ƙarshen duk inda ya iske da wuri. Ba ya tashin wani ya zauna a wurinsa. Idan mutum yana Magana da shi yakan saurare shi, ya bashi hankalinsa, sai ya gama. Ba ya yin mugun baki (watau Magana marar kyau). Ba ya la’ana. Ba ya ɗaga murya a kasuwa (S.A.W).

    Ya kasance yana da kau da kai. Ba ya saka mummuna da mummuna. Kamar yadda muka faɗa a baya, ba ya yarda mutane su rufe masa baya idan yana tafiya. Ba ya nuna fifiko a kan bayinsa da masu yi masa hidima. Bai taɓa zargin wanda yake yi masa hidima ba.

    Yana rama hidima ga wanda ya yi masa. Wata rana yana halin tafiya tare da mutane, sai aka buƙaci  yanka akuya da gyara ta.. Sai wani daga cikinsu y ace: “Ni zan yanka”, wani ya ce,Nizan feɗe, wani ya ce: “Ni zan dafa” “Sai shi kuma ya ce:”Ni zan debo ƙirare” “Sai suka ce: “Ka bari mu za muyi”. Sai ya ce: “Ba na son na fifita a tsakaninku. Allah yana ƙin bawansa idan ya ga yana fifituwa a tsakanin mutanensa”. Sai ya je ya yiwo ƙiraren.

    Majalisin Annabi Muhammad (S.A.W), majalisi ne na nutsuwa da ladabi da aminci da girmama juna. Annabi Muhammad (S.A.W) yana da mutuƙar nutsuwa da kwarjini a majalisin sa. Bay a yin Magana saida buƙata.. Idan yana yin Magana duk sahabbansa sukan yi tsit, su sunkuyar da kawunansu, kai ka ce tsuntsaye  ne a kawunan nasu. Ba sa yin  musu ko jayayya a tsakaninsu. Duk wanda ya zo ya tambaye shi wata buƙata ba ya barinsa ya tafi sai ya biya masa ita, ko ya yi masa Magana mai daɗi, ta haƙurƙurtarwa.

    Ya kasance ya na haɗa kan sahabbansa. Ba ya barin duk abinda zai raba tsakaninsu. Yana tambayar lafiyar duk wanda bai gani ba daga cikinsu. Idan wani ya yi abu mai kyau yana yaba masa, kamar yaddaa idan wani ya yi abu marar kyau yakan kwaɓe shi. Wani lokaci kuma yakan kawar da kansa idan ya ji wata Magana marar kyau ko wani abu marar kyau, domin su gane sun yi ba daidai ba.

    Yana tambayar sahabbansa halin da jama’ar gari suke ciki. Yana girmama shugaban kowace ƙabila ko dangi. Idan ya fara Magana daga ciki sahabbansa sukan dakata, sai ya gama, sannan wani ya fara tasa6.

    Annabi Muhammad (S.A.W) yana zuwa duba marar lafiya,, ba tare da duban matsayinsa ba. Shi yake sallatar jana’iza ya bi ta har ƙabarinta. Ba ya raina gayyata ga duk wanda ya gayyace shi gidansa, ko da kuwa mace ce ko yaro.

    Domin samun cikkakken bayani akan Yadda Siffar Jikin Annabi (S.A.W) Take: danna koren rubutu

  • Yadda Siffar Jikin Annabi (S.A.W) Take:

    Yadda Siffar Jikin Annabi (S.A.W) Take:

    Allah (SWT) ya fifita Manzonsa da kyan halitta, fiye da sauran bayinsa. Annabi Muhammad (S.AW) mutum ne madaidaicin halitta. Ba dogo ba, ba kuma gajere ba. Watau shi matsakaici ne.

    Annabi Muhammad (S.A.W) fari ne mai surkawa da jaja-jaja. Watau ba fari gau ba. Allah ya halicce shi da fuska mai haske. Yadda fuskarsa take a tsakanin mutane, kai ka ce farin wata ne, irin yadda yake haskaka sauran halittu  na duniya. Yana da yalwar goshi da karan hanci. Yana da gashin ido da na gira, masu duhu. Yana da tsagar baki mai ɗan tsayi, ba tsukakkiya ba. Haka nan yankan tsagar idanunsa su ma suna da ɗan tsayi.

    Ƙwayar idanunsa fara ce tas, baƙin kuma baƙi suɗuk. Wuyansa yana da ɗan tsayi. Yana da wushirya a tsakanin haƙoransa na gaba. Gashin kan Annabi Muhammad (S.AW) baƙi ne wuluk, kuma mai tsayi. Wani lokacin, Idan ya bar shi, yakan kai iya kunnuwansa, daga bayansa.

    Kuma yakan zuba a kan kafaɗunsa. Yana da gemanya mai duhu. Kuma yana barinta ta yi tsayi. A ƙarshen rayuwarsa ya yi furfura a kansa da gemanyarsa, wadda bata fi ƙidaya ba.

    Annabi Muhammad (S.A.W) yana da faɗin ƙirji. Watau akwai faɗi a tsakanin kafaɗunsa. Cikinsa ba shi da tudu. Yana da gaɓoɓi watau ƙasusuwansa suna da girma. Akwai gashi daga tsakiyar ƙirjinsa zuwa cibiyarsa.

    Akwai hatimin annabta a gefan kafaɗarsa ta hagu, daga baya. Yana da tsayin hannaye madaidaita. Tafukan hannayensa suna da ɗan tudu da taushi. Ba a ƙarmashe suke ba. Haka nan kasangalalinsa da tafukan ƙafafuwansa. Amma ba shi da nama a agararsa. Watau agararsa a motse take. Tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi.

    Daga Is’haƙa ya ce:, na ji Barra’u yana cewa: “Manzon Allah (S.A.W) ya kasance ya fi kowa kyan halitta. Ba kuma gajere ba”. (muslim ne ya rawaito)

    Daga Aliyu bin Abi Ɗalibin (RA), ya ce: “Annabi Muhammad (S.A.W) fari ne, mai cizawa da jaja-jaja” (Albani ne ya ruwaito a cikin Aljami’us Sahihu).

    Daga Abdur Rahman ɗan Abdullahi ɗan Ka’bu (ya ce. “Abdullahi ɗan Ka’bu ya ce: “Na ji Ka’bu ɗan Maliku yana bayani game da (abin da ya faru sanda Allah ya karɓi tubansu na rashin zuwa masallaci), ya ce: Na yi sallama ga manzon Allah (S.A.W) alhali fuskarsa tana ƙyalƙyali saboda farin ciki ya kasance idan ya yi farin ciki sai fuskarsa ta yi haske, kai ka ce wani yanki ne na farin wata. Mun kasance muna gane haka game da shi “(Bukhari ne ya ruwaito).

    Galibi ana sIffata fuskar Annabi Muhammad (S.A.W) da farin wata, saboda haske da walwala da fuskarsa takan yi (musamman) a yayin da yake cikin farin ciki. Wannan yana nufin cewa, kamar yadda farin wata yake a duniya, to haka Annabi yake a cikin mutane.

    Amma a wannan Hadisin na Ka’abu bin Malik ya ware wani kashi ne na wata, domin yin ishara da  goshin Annabi Muhammad (S.A.W), inda hasken ya fi bayyana, a sanda yake cikin farin ciki. Shi yasa ya keɓance shi da wani yanki na wata.

    Daga Abu Is’hak ya ce: An tambayi Barra’u (RA), shin fuskar Annabi Muhammad (S.A.W) kamar (hasken) takobi take? Sai ya ce: “A’a”, kamar (hasken) wata take” (Bukhari ne ya ruwaito)

    Daga Jabir ɗan Samuratu, ya ce: “Manzon Allah (S.A.W) ya kasance mai faɗin baki, mai tsayin yankan idanu, Mai siraren maƙyangyama…” (Muslim ne ya ruwaito).

    domin samun cikkakken bayani akan littafin danna koren rubutun nan.
  • Yadda Sahabbai Suka Yi Koyi Da Annabi Muhammad (S.A.W)

    Yadda Sahabbai Suka Yi Koyi Da Annabi Muhammad (S.A.W)

    Sahabban Annabi Muhammad (S.A.W) sun yi koyi da shi a cikin dukkanin harkokin rayuwarsu. Ba kawai sai a salla, zakka, Azumi da Hajji kaɗai ba. Ga wasu misalai ‘yan kaɗan da za su nuna mana haka.

    Dab da Annabi Muhammad (S.A.W) zai yi wafati ya zartar da wata rundina ta yaƙi, ƙarƙashin shugabancin Usamatu bin Zaid. Bayan wafatin annabi Muhammad (S.A.W) sai wasu suke ganin ya kamata a dakatar da wannan runduna tukuna, kasancewar an sami wasu suna ƙin bayar da zakka. Har ma aka zama cikin tsoron kawo hari cikin Madina. Me Abubakar yayi a matsayinsa na shugaba? Abubakar bai yarda a dakatar da wannan runduna ba. Cewa ya yi:

    “Ba za ta yiwu ba a gare ni, na kwance tutar da Manzon Allah (S.A.W) ya ƙulla”.

    Haka nan sauran sahabbai suka goyi bayan Abubakar, Usamatu ya shugabanci wannan yaƙi kuma aka yi gagarumar nasara. Game da Madina kuwa, abin da Abubakar ya yi shi ne, sai ya sanya wasu daga cikin manyan sahabbai suka shugabanci wata runduna domin ba ta kariya, kamar su: Aliyyu bin Abi Ɗalib,
    Zubairu binil Auwam, Sa’adu bin Abi Waƙƙas, Abdullahi bin Mas’ud da abdur Rahman bin Aufin.

    Wani abin da Sayyidina Abubakar ya yi (na ruqo da tsarin Annabi) bayan wafatinsa (S.A.W), wanda yake nuna dagewarsa, shi da sauran sahabbai, a kan Sunnar Annabi Muhammad (S.A.W) (watau tsarinsa na rayuwa) shi ne, wasu Larabawan ƙauye sun ƙi bayar da zakka bayan wafatin Annabi Muhammad (S.A.W). A wannan lokacin cewa ya yi:

    “Wallahi! Idan da za su hana ni dabaibayi, wanda suka kawo wa Manzon Allah (S.A.W), da sai na yaƙe su”.

    Wani abin da za mu sake lura da shi shi ne, yanayin da Nana faɗinmah ‘yar Manzon Allah (S.A.W) ta nemi gadon Annabi Muhammad (S.A.W), a nan ma sai y ace mata ya ji Manzon Allah ya ce:
    “Mu jama’ar Annabawa ba a gadon mu. Abin da muka bari, sadaka ne”

    (Bukhari da muslim ne suka ruwaito).

    Wani misalin shi ne, wata rana Sayyidina Umar ya zo zai sumbaci  Hajarul Aswadi sai ya tsaya ya ce:

    Ni na san kai dutse ne. Ba ka cutarwa, ba ka amfanarwa. In ba domin na ga  annabi  (S.A.W) yana sumbatar ka, da ba zan sumbace ka ba”.

    (Bukhari ne ya ruwaito).

    Wata rana Abdullahi bin mas’ud ya zo zai shiga masallaci sai ya ji Annabi Muhammad (S.A.W) yana
    cewa:

    “A zauna”. Sai ya zauna a kan dokin ƙofar masallaci. Bai ƙara yin gaba ba ko kaɗan, sabo da cika umarni.

    Haka nan sahabbai suka yi ta koyi da Annabi Muhammad (S.A.W), a dukkanin tsare-tsaren rayuwa. Wata rana Abdullahi bin Mugaffal ya ga wani mutum (ko wani ɗan ɗan’uwansa), yana yin jifan da ake kira ‘Hazfu (wadda akan sa tsakuwa a tsakanin babban ɗan yatsa da ɗan ali, a wulla ta). Sai ya ce da shi:

    “Manzon Allah (S.A.W) ya hana yin hazfu. Da ya sake ganinsa yana yi sai ya ce:

    “Ina gaya maka Manzon Allah (S.A.W) ya hana yin hazfu kana sake yi? Ba zan sake yin magana da kai ba, har abada

    (Bukhari da Muslim ne suka ruwaito).

    Har ma ta kai cewa wasu daga cikin sahabbai suna koyi da Annabi, hatta a abubuwan da Annabi yakan y,i ba da nufin lallai sai an yi koyi da shi ba.

    Abdullahi bin Umar ya shahara game da haka.

    Abdullahi bin Umar ya kasance yana zuwa ƙarƙashin wata bishiya a Madina, ya yi baccin rana. Da aka tambaye shi game da haka, sai ya ce shi kawai ya ga Annabi yana yin baccin rana a ƙarƙashinta.

    Wata rana Abdullahi bin Umar yana cikin tafiya tare da mutane, sai aka ga ya kewaye wani wuri, bai bi ta wurin ba, (Alhali babu komai a wurin), da aka tambaye, shi sai ya ce, ya ga Annabi wata rana suna tafiya ya kewaye wurin.

    Haka nan wata rana an ga ya sauka a wani wuri tsakanin Makka da Madina, ya yi salla, dalilin sa shi ne, ya ga Annabi ya yi sallah a daidai wannan wurin suna halin tafiya. Duk da kasancewar a lokacin mutane sun yi masallaci a kusa da wurin, shi sai ya ƙi yin salla a masallacin, ya je ya yi a daidai inda Annabi ya yi (S.A.W)

    Domin karanta cikekken littafin danna wannan koren rubutu

  • Mece Ce Sana’ar Mahaifin Manzonmu?

    Mece Ce Sana’ar Mahaifin Manzonmu?

    Mece ce sana’ar Mahaifin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wassalama

    1.Kasuwanci

    Domin sannin wace ce mahaifiyar manzon Allah danna koren rubutun nan