Tag: hausa novels

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ƙarshe

    Mijin Marigayiya Babi Na Ƙarshe

    EPILOGUE

    Bayan shekaru 3. An yi auren Afaf an kai ta gidanta, yaron da ta aura ƙanin abokin Abbanta ne, da kanta ta je ta kai wa Khadeeja katin bikin nata wanda ta karɓa cike da girmamawa. Ta yi mata magiya a kan ta je amma duk da haka ba ta je ba, domin ba ta son abinda zai haɗa ta da Naja da dangin Mustapha a cikin taro.

    Kuma duk yanda Mustapha ya so ya saka ta a cikin shawarar bikin Afaf ɗin da inda zai sayi furniture haka ta zame da wayo da dabara har ya gaji ya rabu da ita. Yana nan dai yana bibiya da kuma addu’ar ta yarda su mayar da aurensu. Yana zaune a ɗakinsa a kan dadduma yana hutawa bayan sallar la’asar kwana biyu bayan auren Afaf haka kawai ya ɗauki waya ya kirawo Khadeeja.

    Ya gyara zama ya jingina da bangon da ƙofar ɗakin take jiki ta yanda idan aka buɗo kofar aka shigo zai zama yana bayan ƙofar kenan. Bayan ta amsa suka gaisa suka shiga hirarrakinsu, tana tambayarsa labarin biki. A haka har yace ‘Kin ga da kin yarda ai da tare da namu za a ɗaura.’

    Ta yi dariya tace ‘Kai kuwa ka ƙi ka bar maganar nan. ‘Ba zan bari ba Khadija, har sai kin amince. Ko na tsufa ma sai na dawo da ke ko da takaba ne kya yi min sai mu haɗu a aljannah. Dariya kawai ta yi don ba ta da amsar da za ta ba shi. Suka yi shiru na ɗan lokaci sannan yace ‘Duk wani condition da kike so Khadeeja ki saka na yi miki alƙawarin zan cika in dai za ki zama mata ta.

    Just one more chance Khadeeja, ki daina wahalar da zuciyata haka. Ta yi murmushi mai sauti ba tare da ta ce masa komai ba; tabbas yana nema ya gamsar da ita ta sake amincewa da aurensa, amma a halin yanzu ba ta san amsar da za ta ba shi ba. Ya gaji da shirun kuma yana ji a jikinsa cewa kalamansa sun fara yi mata tasiri.

    Ya katse shirun yace ‘Gobe da safe zan shigo, ok? ‘Ok, Allah ya kai mu. Amma ina da programme da safe so ka bari sai bayan azahar. ‘Ok, I will take you out to lunch then. No execuses. Ta yi dariya ‘Ka dai san ba zan je ba ko? Kada ma ka fara wata rigimar daban.’ ‘In dai rigima ce ai a wajenki na koya. I will see you tomorrow at lunch.’ Ya ajiye wayar ba tare da ya bari tace wani abu ba.

    Ko da ba za ta yarda ya fita da ita lunch ɗin ba ya fi so ta bar shi ya kwana da murnan zai fita da Khadeeja gobe, in ya so idan ya je office ɗin su yi faɗan da suka saba. Tana tsaye a jikin ƙofar ɗakin tana jinsa, duk abinda ya faɗa tana ji. Sai da ya ajiye wayar sannan ta banka ɗakin ta shiga a fusace.

    Firgigit ya juyo ya kalli ƙofar da aka mako, yace ‘Ya haka kamar za ki fizge ƙofar? Me ya faru ne? Ko wani abun ya biyo ki? Ta tsaya tana masa kallon raini tana jijjiga, sai da gaji da kallon nasa sannan a fusace tace ‘Mustapha na gaji da wulaƙancin da kake mina a kan matar nan, shekara huɗu ana abu ɗaya saboda tsohon naci. Wallahi babu ruwan Allah da kun taɓa aure alaƙarku haramtacciya ce.

    Kuma idan ma zina kuke Allah zai kama ku. Faɗan nata bai harzuƙa shi don ya saba ji, idan ma ba ta ji yana waya da Khadeejan ba kullum cikin duba masa waya take. Ba sa magana ta whatsapp don haka kullum cikin duba calls take, da zarar ta ga call ɗin Khadeeja to sai ta yi wannan masifar. Ya miƙee ya naɗe daddumar yana cewa ‘Kada ki kuskura ki jefi khadeeja da wannan kalmar yanzu ranki zai ɓaci, kuma kin sani.’

    Ta riƙe ƙugu tana dan zare ido tana cewa ‘Ohh! Yanzu kai ka fi son Khadeeja kenan dan kanka, kai na jefe ka da koma menene amm kada na jefi Khadeeja ko? To wallahi da kai da ita baku isa ba…. ‘Ke kika sani.’ Ya faɗa tun kafin ta ƙarasa faɗin abinda take faɗa, ya ajiye daddumar ya kewayeta ya fice daga ɗakin.

    Ta juyo ta bi bayansa da kallo cike da takaici sannan ta wuce ta zauna a gefen gado ta zuba fuskarta a tafukan hannunta ta fashe da kuka. Wannan wane irin wulaƙanci ne, tana murna ya saki kishiyarta amma kullum suna tare, ita kuma tana nan ya kulle ta a gida. Wannan wace irin musiba ce? So take ta ware rana ta je ta sami Khadeejan a office ɗin nata ta tara mata mutane amma dai tana tsoron kada Mustapha ya sake ta a kan hakan; don yanzu ta ga kamar ma ba a haiyacinsa yake ba.

    To yanzu babu aure a tsakaninsu yana mata wannan tsohon nacin idan kuma ta dawo ya za a yi? Ita menene makomarta ya dawo da rabin ransa me ƙaunar ‘yayansa. Ta ɗora hannu a ka ta sake rushewa da kuka.

    END

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Dole tana ji tana gani ya kafa mata doka idan dai har zai ci abinci to parlor ɗin kasa zai ci. Babu yanda ba ta yi da shi ba yaran su dinga hawowa sama amma yace ba za su hau ba tunda ita saman take so a bar mata, haka ta haƙura ta saka masa ido saboda abun yana nema ya zama matsala a tsakaninsu.

    Duk wani taimako da aiki da malamai za su yi mata tana kan yi sai dai abun ya ƙi yi, idan ya yi kamar zai kama sai kuma ya sake botsare mata. Idan dai tana son ganin walwalarsa to ta yi wa yaran nan yanda suke so kuma ba tare da ta yi masa wani ƙorafi ba. Burinta ɗaya yanzu a aurar da Afaf domin haka ne kawai take ganin za ta sami natsuwa a gidan nan.

    Don a halin da ake ciki komai zai yi da Afaf yake shawara, wasu lokutan ko ta ba shi list ɗin cefanen gidan sai ya tambayi Afaf abinda take buƙata ita da kannenta ya siyo musu. Idan kuma ya kawo kayan sai ya tsaya a ƙasa Afaf ɗin ta ware nasu kayan sannan ya hau mata sama da sauran. Haka dai take haƙuri, musamman da yake ya iya lallaɓa ta ya tsara ta kawai dai ya nuna mata yaran nan nasa ba za su taɓu ba.

    Haka rayuwarsu ta cigaba.

    Duk yanda yake jin zai samu Khadeeja ta saurare shi ya gagara, ga shi kuma sai a yanzu Allah ya jarrabe shi da ƙaunarta. Kusan kullum sai ya yi mata waya, idan ta ga dama ta ɗauka idan kuma ba ta ga dama ba ta ƙi ɗauka. Ya mayarwa kansa duk Juma’a da yamma sai ya je gidan duba Hammad, sai dai hakan bai ba shi damar ganinta ba.

    Domin idan ya je ko da ya yi mata waya haka za ta saka a buɗe masa parlor ɗin baƙi ta turo masa Hammad, har ya gama hirarsa da Hammad ya tafi ba za ta fito ba. Don haka wasu lokutan sai kawai ya rutsa ta a office inda dole ta zauna su gaisa har su ɗan yi hira. Abu ɗaya ne yake hana shi zaƙewa a kan maganarta saboda har yanzu yana jin kunyar Baffanta, bai san da wane bakin zai je yace masa ya sake ba shi auren Khadeeja ba.

    Shi yasa ya dage yake ƙoƙarin ganin ya gamsar da Khadeejan ta je wa Baffan da maganar da kanta. Kwanci tashi har shekara ta zagayo. Tun da ya gama haɗa takardun yake cike da farin ciki, haka ya kwana cike da zaƙuwa sabodan yanda yake son gari ya waye ya je ya sami Khadeeja ya yi mata albishir.

    Yana fita office ɗinta ya fara tsayawa, ya yi sa’a kuwa ta riga ta zo. Kamar yanda ya saba a cikin office ɗin ya same ta tana zaune tana editing script ɗin da za ta yi amfani da shi wajen gabatar da show ɗinta. Yana shiga ya tura ƙofar sannan ya yi wa kansa mazauni a kujerar gabanta cike da walwala. Bayan sun gaisa yace ‘Kina jin daɗinki fa, kin ga yanda kike sheƙi kuwa.

    Ta yi dariya tace ‘Don Allah ka bari, haba. Ko waya ma ba ka yi min ba kace min za ka zo to da ka zo na riga na shiga studio fa? Shi ma dariyar ya yi yace ‘Sai na jira ki mana. Ai idan kina son na daina zuwa wajen nan to ki yarda mu mayar da auren mu mu huta, in ba haka ba dole kullum na zo nan na yi attendance don duk masu shirin yi min shigar sauri su ganni su san ina nan ba fashi.’

    Ta sunkuyar da kai don ba ta san me zata ce masa ba, amma dai yawan zuwan nashi office ɗin ya fara gundurarta. Ba wai don ba ta so a gan shi ba ne kuma ba wai tana jin ya isa ya hana ta kula wanda take son kulawa ba; kawai dai tana so ya ɗan ba ta space tunda ita dai ta gama magana a kan lallai ba za ta koma gidansa ba kuma har yanzu hakane a ranta.

    Muryarsa ce ta katse mata tunanin da ya kirawo sunanta, ta ɗago ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta kawar da kai. Yace ‘Ki sauwaƙe mana wahala ki yarda mu mayar da aurenmu, duk wani abu da ya ɓata miki rai a baya na yi miki alƙawarin ba za ki sake gamuwa da shi ba a zamanmu.’

    Ta jijjiga kai ‘Na fahimce ka Mustapha, amma dai ka yi haƙuri. Ba wai kai ne ba zan aura ba, auren ne gaba ɗaya ba zan yi ba. Don Allah ka daina wannan maganar, ka mayar da hankali wajen kula da iyalinka. Ka ga yanzu ni babu aurenka a kaina, idan ta ji kana zuwa wajena zaku iya samun matsala. Ka zo kai ba ka sami natsuwa da ta gidan ba kuma ni ba aurenka zan sake yi ba.’

    Ya jijjiga kai don ba ya son wannan maganar, shi yana ji a jikinsa Khadeeja matarsa ce shi kaɗai don haka duk tsawon lokacin da za ta ɗauka tana yi masa yanda zai jure. Ya zaro envelope daga aljihunsa ya ɗora a kan tebur ɗin ya tura mata gabanta yana murmushi yana cewa ‘Wannan na zo kawo miki daman. Ta ɗauko tana dubawa tana cewa ‘Me na samu?’

    Ta zaro takardun daga envelop ta fara dubawa; kujerar Hajji Mustapha ya ba ta. Tana dubawa tana murmushi saboda yanda tunanin za ta je Hajji ya faranta mata zuciya. Ta ninke takardu ta fara mayarwa cikin envelop ɗin a daidai lokacin da murmushinta ya ragu. Ta tura masa gabansa tace ‘Na ji daɗi Abban Hammad, na gode Allah ya ƙara arziki da rufin asiri.

    Amma ka yi haƙuri ba zan iya karɓa ba, ba wai don na raina ba ko wani abu. Na gaya maka ba zan sake aurenka ba so ka ga babu wani dalili da zai sa na karɓar maka kujerar Hajji. Kuma ko na karɓa ma Baffa ba zai taɓa barina na je ba sai dai a ɗaura mana aure kafin na tafi; kuma wannan ba zai yiwu ba. Please ka yi haƙuri! Amma na gode sosai.’

    Kafin ta gama bayanin fuskarsa ta canza gaba ɗaya, ba tare da ya ɗauki takardun ba yace ‘To ki karɓa mana Khadeeja ki bari a ɗaura mana auren, please ki daina guduna haka. Ta sunkuyar da kanta cikin damuwa tace ‘Ba gudunka nake ba, amma dai ba zan iya ƙara aure ba.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci. Jimawa kaɗan yace ‘To yanzu ya kike so a yi? Ni da sunanki na biya wannan kujera. Ka yi hakuri ba zan iya karɓa ba. Suka sake yin shiru na ɗan lokaci. Kafin su yi magana aka ƙwanƙwasa ƙofar, ta amsa ta ba da izini aka shiga. Wata mace ce abokiyar aikinta ta ɗan leƙo tace ‘Anti Khadeeja yallaɓai yace ke ake jira a studio za a fara.’

    ‘Yanzu zan shigo.’ Ta faɗa tana shirin miƙewa. Ta dubu Mustapha tace ‘Bari na je kada ka sa a kore ni aiki. Ya yi dariya shi ma ya miƙe, sai dai tana kula da shi bai ɗauki takardun ba. Ta miƙa hannu ta ɗauka sannan ta zagayo ta tsaya a gabanshi, ta miƙa masa takardun tana murmushi tana cewa ‘Ka yi haƙuri ka tafi da wannan, wallahi ba zan iya karɓa ba.

    Idan na karɓa ba zan iya da rigimar Baffa ba tunda na san ba zan aure ka ba. Ka yi haƙuri please. Ya miƙa hannu ya karɓi takardun yana tsare ta da ido kamar mai binciken wani abun a idonta, har sai da ta kawar da nata idon. Ta wuce ya biyo ta a baya suka fito daga office ɗin, suka jero har zuwa reception sannan ta yi masa sallama ya fice ita kuma ta miƙe ta nufi studio ɗin.

    Tana fatan Allah ya sa dai kada ta kwafsa saboda yanda Mustapha ya jagula mata lissafi; me za ta yi da kujerar makansa? Wato ma shi har yanzu tunani yake saboda kujerar Makka yasa ta ƙi komawa gidansa? Bai ma san wacece ita ba kenan, zaman da suka yi tare bai sa ya fahimce ta ba.

    Ba ta buƙatar kujerarsa kuma ta san tabbas idan ba aurensa ta kuma yi ba ko kashi ta kai gida tace shi ya ba ta sai sun yi rigima da Baffa, kuma ba ta shirya ƙarya ba saboda Mustapha wanda take so ya rabu da ita ya daina damun rayuwarta.

    Tana tashi daga waje aiki ta wuce gidan Yaya Mama, ta yi sa’a yaran duk sun tafi islamiyya don haka ta sami Yaya Mama ita kaɗai. Bayan sun gaisa Yaya Mama tace ‘Bari na samo miki ruwa ko lemo. Ta dafe cinyarta tace ‘Bar shi kawai sai da na tsaya na ci abinci sannan na ƙaraso.’

    Ba tare da ɓata lokaci ba ta fara ba ta labarin kujerar Makkan da Mustapha ya kawo mata ɗazu. Sai da ta gama ba ta labarin suka sheƙe da dariya a lokaci guda sannan tace ‘Wai ni zai saya da kujerar Makka ɗan rainin hankali. Yaya Mama tace ‘Ai kuwa ɗan rainin hankali lamba ɗaya, wato tunda kin ce ya sake ki saboda kujerar Makka bari ya biya ki sai ki yarda ya mayar da aurenku.’

    ‘Ashe kin gane. Suka cigaba da hira suna tuna abubuwan da Mustaphan ya yi a baya. Sai da Magriba ta fara kawo jiki sannan Khadeeja ta fara shirin tafiya. Bari na wuce kada magriba ta yi min a nan. ’Yaya Mama ta dafa hannunta tace ‘Khadeeja, idan fa za ki koma gidan Mustapha kin san babu wanda zai hana ki ko? Don ni ina ganin ma gara ki koma can ɗin tunda kin ga ko babu komai ga Hammad.

    Kuma na ga har yanzu ba ki da wani manemin; duk da ma duk wanda za ki aura mijn wata ne don haka kin ga dole ki zauna da kishiya. Ni ina ga gara gidan Mustaphan tunda dai ya yi nadama har yana ƙoƙarin ya faranta miki. Nan take ta ɓata rai, ta zare hannunta ta ɗan matsa daga kusa da ita sannan tace ‘Ba zan taɓa komawa gidan Mustapha ba, aure kuma ba ya gabana balle na fara damuwa da rashin manemi.

    Idan Allah ya saka ina da rabon aure a gaba to duk wanda Allah ya sa shi ne mijina zan aura amma fa in sha Allahu ba zan sake auren Mustapha ba. Mutumin da ya ɗauke ni ne kawai a matsayin solution to his problem. Ko yanzun ma da yake ta ƙoƙarin na koma gani ya yi ƙiriƙiri matar tasa ta kasa kula masa da gidan da yara kamar yanda na yi.

    Shi yasa ya lallaɓo ya mayar da ni cikin wahalar da Allah ya raba ni da ita. Ba zan koma na, can su ƙarata. Ta miƙe ta ɗauki jakarta, don haka ita ma Yaya Maman ta miƙe. Ta san idan ta fiya takurawa da maganar yanzu za su yi faɗa don haka sai ta ƙyale ta suka yi sallama ta kama hanya.

    Wunin ranar gaba ɗaya bai yi masa daɗi ba. Ko da dai bai sa ran Khadeeja za ta karɓi kujerar ba tare da an kai ruwa rana ba amma kuma bai sa ran za ta ƙi karɓa haka gaba ɗaya ba ba tare da wata ƙofa ta sulhu ba. Haka ya wuni a office ɗin babu walwala. Sai da yamma ta yi sannan ya kwashi kayansa ya koma gida.

    Yana shiga ɗakinsa ya ajiye takardun hannunsa a kan mudubi; takardar kujerar da ya ba wa Khadeeja ce a sama tare da wasu takardun na office. Tunda ya je sallar magriba masallaci ya dawo ya yi zamansa a ƙasa shi da yara. Da farko ta ɗan zauna a wajensu ana hira gaba ɗaya, daga baya kuma sai ta tashi ta haye sama ta bar su.

    Ɗakinsa ta shiga don ta samu ta huta domin nan ne kawai idan ta rufo ƙofar Rukayya ba za ta so ta buga ta tashe ta ba. Har ta wuce mudubin sai kuma ta koma da baya, ta sa hannu ta ɗauki envelope ɗin da ta ja hankalinta. A buɗe take don haka sai kawai ta zaro takardun ta fara karantawa.

    Nan da nan kanta ya kulle; tabbas wannan sunan Khadeeja ne. To me hakan yake nufi?Suna tare kenan yanzu ta zama bazawararsa ko me? Tunda idan ba wata alaƙa ce tsakaninsu ba me zai saka har ya biya mata kujerar Makka? Kenan ma ita Mustapha zai rainawa hankali, ya saki matar sannan ya koma yana bin ta? Gaskiya ba za ta yarda ba.

    Ta ɗaga kanta ta hango wayarsa tana chaji a kan bedside durowa; nan da nan ta ajiye takardun ta ƙarasa ta ɗauki wayar. Ta riga ta san PIN ɗin don haka kai tsaye ta buɗe ta fara duba whatsapp; sai dai har ta gama dubawa ba ta ga sunan Khadeeja ba. Tana duba calls ta ga sunan ‘Sweetheart’ shi ne sunan da ya yi saving lambarta tun yana zuwa zance kuma bai taɓa canzawa ba.

    Bayan rabuwarsu Najan ta goge ta saka maman Hammad amma ba ta san yanda aka yi ya mayar ba. Ta mayar da wayar ta ajiye cike da damuwa da takaici. Ta tashi ta dawo ɗaya gefen gadon ta zauna ta zuba tagumi; tabbas za su yi rigima da Mustapha don ba zai yiwu ba ya dinga zagayawa wajen tsohuwar matarsa suna raina mata hankali.

    Sai wajen ƙarfe tara na dare ya hawo saman, lokacin ya je sallar isha’i ya dawo kuma sun gama cin abinci da yara. Zuwa lokacin ita ma ta gama duk abinda take yi ta kwantar da yara tana kwance a kan gadon ɗakinsa sanye da rigar bacci ta miƙe kafa tana kallo a waya ya shiga ɗaki. Bayan ta amsa sallamarsa ta mayar da hankali kan wayar hannunta.

    Kai tsaye ya wuce ciki ya canza kayansa sannan ya zauna a kan carpet ɗin da ke gaban gadon ya miƙe ƙafa ya janyo computer ɗinsa ya kunna ya kama aiki. Yawanci idan dai har yana da aiki to ya kan kai dare sosai a zaune yana aikin, ita kuma ba za ta iya jira ba. Don haka ta miƙe ta zauna ta ajiye wayar da take hannunta ta yi gyaran murya sannan tace ‘Uhm, na ga wata takarda, wai Maman Hammad ka biyawa Makka?’

    Bai yi mamakin jin tambayar daga gareta ba duk da bai sa rai da ita ba, amma dai ya san ya manta ya ajiye takardun a kan mudubinsa. Ba tare da ya bar aikinsa ba yace ‘Eh ita na biyawa, akwai matsala ne. Cike da neman rigima tace ‘To kuma a yanzu meye tsakaninka da ita tunda na ga dai babu aure. Ko kuma kun mayar da auren ne ni ce ban sani ba.’

    Har yanzu hankalinsa yana kan aikin yace ‘Ba mu mayar ba muna dai kan hanya. To shi ne kuma ka biya mata Hajji. Ya ɗago ya dube ta yace ‘Eh, akwai matsala ne? ‘Gani dai na yi bai dace ba tunda babu aure a tsakaninku. ‘Wannan ra’ayinki kenan. Ta kula so yake ya yi mata wulaƙanci don haka ta miƙe ta zauna sosai tace ‘Ina fatan dai ka san yanzu ita ɗin ba muharramarka ba ce.

    Kuma ina fatan ka san ba zai yiwu ina nan gida ina maka biyayya wai ni matar aure ba ka dinga zagayewa wajen tsohuwar matarka wadda ka saka da hannunka, ba zan ɗauka ba gaskiya.’

    Ya ɗago ya kalle ta rai a ɓace yace ‘Sai ki ɗau mataki a kai. Ta kula kamar haushinta yake ji sai dai ba ta san dalili ba, don lafiya ƙalau suka rabu da safe ya ajiye ta a office sannan ya fice; to meye ya harzuƙoshi hakan daga yin magana? Kada fa ka gaya min magana daga tambaya, na dai gaya maka ba zai yiwu ba ina nan ka kulle ni a gidanka a dinga ganinka a gari kana yawo da wata matar banzan.

    Ta faɗa tana miƙewa tsaye. A fusace yace ‘Khadeejan kike cewa matar banza saboda wulaƙanci? Sai dai kafin ya rufe bakinsa ta fice daga ɗakin ta rufe masa ƙofar; wanda wannan ɗabi’arta ce idan dai ya ɓata mata rai sai ta gaya masa magana mai zafi sannan take fita daga inda yake. Ya yi tsaki ya cigaba da aikinsa don so yake ya gama aikin kafin ya kwanta.

    Haka rayuwarsu ta cigaba. Khadeeja ta ƙi yarda a mayar da aurensu sannan shi kuma ya kasa tunkarar Baffanta da maganar don ya san ba za a yi mata auren dole ba. Amma kuma ya ƙi ya daina bibiyarta; har ta kai ba ya iya sati bai neme ta yaganta ba. Idan ya je gidansu wajen Hammad ta ƙi fitowa to tabbas zai same ta a office. Waya kuwa daman ba ta yankewa don idan ma ta ƙi ɗauka haka zai yi ta kiranta har sai ta gaji ta ɗauka.

    Duk wata kalma da zai yi amfani da ita wajen ganar da ita ta yarda su mayar da aurensu ya yi amma ta sanar da shi ba za ta iya komawa ba. Duk lokacin da ta ji kamar za ta haƙura su koma idan ta tuna yanda yake banzatar da ita a gidan kuma ta tuna yanzun ma sai da ya rasa yanda zai yi da gidan sannan ya fara nemanta sai kawai ta ji ta fasa.

    Tana sane da duk wata rigima da ta faru a gidan tunda kusan duk Asabar a wajenta Habib yake wuni, duk abinda ya dame shi sai ya je ya same ta ya gaya mata. Lokaci zuwa lokaci tana samun masu nuna sha’awar aurenta sai dai auren gaba ɗaya ya fice mata daga rai; don haka yawancinsu ba ta ma bari su zo gidansu.

    Kuma duk inda ta je idan dai ba an santa a wajen ba to tana gabatar da kanta ne a matsayin matar aure don ma kada wani ya zo mata da wata magana; don haka mutanen da suka santa sai suka kasu kashi biyu, wasu suna ganin tana da aure wasu kuma suna ganin ba ta da aure. Amma kuma yawancin mutane kasa tambayarta suke yi.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin

    Ba ƙaramin mamaki Hajia da Alhaji suka yi ba da Mustapha ya gaya musu ya saki Khadeeja. Shi kaɗai ya shiga da yaran don ita Naja ma cewa ya yi ta zauna a mota saboda kada taɓbata musu lokaci. Suna shiga yaran suka wuce cikin gida shi da Hajia da Alhaji suka tsaya a parlor yana musu bayanin abinda ya faru.

    Alhaji yace ‘To kai wane irin rashin hankali ne wannan? Ai don mace tace a sake ta ba a sakin nata. Zuciya ce ta kwashe ta kuma sai daga baya za ta zo tana nadama. Da ka sani ka ba rta da aurenta idan ma tafiyar za ta yi ta tafi idan ka dawo ƙalau za ka ga ta dawo.’

    A fusace yace ‘Alhaji yarinyar ce ta ƙure ni, ita kullum sai dai a yi mata yanda take so amma ita ba za ta yi yanda ake so ba? Ta je idan mutuwar aure daɗi ne ai ta samu sai ta ɗana ta fi shiga hankalinta. Hajiya tace ‘Ai shikenan tunda haka ta zaɓa. To yanzu ina Hammad ɗin da Rukayya? Ban gansu tare da ‘yan uwansu ba.’

    ‘Shi Hammad dama yana gidansu, ita kuma Rukayya gidansu ta kai ta. Ai shikenan, Allah ya sauwaƙe. Idan ka dawo a san yanda za a yi domin dai aure bai kamata ya mutu saboda kujerar hajji ba.’ Alhaji ya faɗa cike da nadama. Mustapha ya dubi Hajia yace ‘Mukullin gida yana hannun Habib in an jima Baba Sani abokina zai zo ya kai su shi da Afaf su ɗebo kayansu su rufo gidan.

    Idan sun dawo sai ya ba wa Alhaji mukullin gidan ya ajiye min. Akwai ATM card ɗina hannun Afaf idan ana buƙatar wani abu na kuɗi sai ta je ta ciro ta bayar. Ya yi musu sallama ya fice zuciyarsa cike da damuwa.

    Zuciyarta fayau ta fito daga gidan tana addu’ar Allah ya sa iyakar zamanta kenan da Mustapha tunda ta san saki ɗaya ya yi mata. Suna tsaye a bakin titi ita da Hafsa suna jiran mota ya zo ya wuce su a guje a tashi motar. Ta bi bayan motar da kallo tana murmushi; ta tuna lokutan da yake zuwa ya wuce ta a titi za ta tafi makaranta amma ba zai iya rage mata hanya ba.

    Ta yi murmushi ta kawar da kai. Jimawa kaɗan da wucewarsu ta sami mota, suka hau suka nufi gidan Mommy. Tana tura gate ɗin gidan Baffa ne a tsaye yake rufe motarsa, da alama dawowarsa kenan. Suna haɗa ido da shi hawayen da ta kasa fitarwa ya ƙwace, ta saki akwatin da take ja.

    Ahmad wanda yake tsaye a kusa da shi ya ƙarasa ya riƙe akwatin yayin da ita kuma ta ƙarasa ta faɗa jikin Baffa wanda yake bin ta da kallon mamaki. Ya rungume ta sannan ya dafa kanta wanda ta kwantar a ƙirjinsa yana cewa ‘Subhanallahi! Me ya faru da ku Khadeeja? Ta kasa magana sai kuka kawai take har da shessheƙa.

    Baffa ya fara shafa bayanta yana cewa ‘Ya isa haka, ya isa, ki gaya min me ya faru? ‘Ya sake ni.’ Ta faɗa a cikin shessheƙar kuka kamar mai raɗa. Take fuskar Baffa ta canza, ranshi ya yi matuƙar ɓaci. Yace ‘Mustaphan ya sake ki? Ta ɗaga masa kai. Ya sake shafa kanta cikin yanayi na lallashi yana cewa ‘To shikenan, ya isa haka.’

    Ya ja hannunta suka shige gidan; da yake Mommy tana ɗakinsa kai tsaye can ya wuce da Khadeeja. Mommy tana ƙoƙarin yi masa sannu da zuwa ta kula da Khadeeja, tace ‘A a, Baffa a ina ka samo wannan? Ya zaunar da ita a gefen gadonsa yace ‘Mustapha ya sake ta. ‘Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un! Saki kuma? A yau ɗin? Na ɗauka ce min kika yi yau jirginsu zai tashi?’

    Ta share ragowar hawayenta ta ajiye jakar hannunta sannan tace ‘Eh, kafin su tafi airport ɗin ne ya sake ni saki ɗaya. Lallai Mustapha, to me kika yi masa ya sake ki? Ko kuwa dai tsabar wulaƙanci ne ya ga gara ya sake ki kafin ya wuce ya yi ibada?’ Mommy ta tambaya tana daga tsaye.

    Ba ta yi tunanin wata amsa da za ta bayar idan an yi mata wannan tambayar ba, amma dai tana jin gara ta faɗi gaskiya don ma kada ya zo shi ya ba da amsa da ta bambanta da tata. Ta ɗaga fuskarta suka haɗa ido da Mommy sannan ta sunkuyar da kai. Murya kasa-kasa tace ‘Ni nace ya sake ni.’

    Saura kaɗan wayar da take hannun Mommy ta kufce ta faɗi, ta riƙe wayar sannan tace ‘Kika ce ya sake ki Khadeeja? Saboda rashin hankali ko saboda me? Baffa da yake tsaye a gaban wardrobe ɗinsa yana rataye babbar rigarsa ya zagayo ya zauna a kusa da ita yana kallonta yace ‘Dije me yasa kika ce mijinki ya sake ki?’

    Kafin ta yi magana Mommy tace ‘Saboda wulaƙanci mana, ko kuma saboda yace ba zai je da ita aikin Hajji ba sai ya je da amaryarsa. Kallonta kawai Baffa ya yi ta yi shiru, ta gyara tsayuwarta tana binsu da kallo. Ya dubi Khadeejan ya sake cewa ‘Deeje me yasa kika ce mijinki ya sake ki?’

    Ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta sake sunkuyar da kai tace ‘Baffa na gaji, wallahi Baffa ba ka ga zaman da muke yi a gidan nan ba. Tun kafin ya auri matarsa Baffa dama haƙuri nake, matsayina a gidan da kaɗan ya wuce matsayin ‘yar aiki. Kuma bayan ya auro ta ma ya kara tabbatar min da hakan; duk wani abu na walwala da jin daɗi da ita ake yi amma wallahi idan aiki ne da wahala Baffa ni zai kawowa kuma dole na yi.

    Ita kanta matar tasa haka yake saka ni na yi mata aiki babu sannu bare na gode. Shi yasa kwanaki da nace ba zan yi ba ya zo ya kawo maka ƙarata. Wallahi Baffa a lokacin sai da na yi wata takwas ina mata aikin gida da girki da komai kuma kullum shi a wajenta yake kwana.’Ta sake sunkuyar da kai ‘Na gaji Baffa, ba ya sona, wulaƙancin da yake min suna da yawa, gara na haƙura kawai shi yasa nace ya sake ni.’

    Ya kama hannunta wanda take wasa da shi a kan cinyarta ya kalle ta suka haɗa ido yace ‘To ya isa, kuka ya isa haka. Ki je ki kai kayanki ɗaki ki huta ma yi magana wani lokacin.’ Ta gyaɗa kai ta miƙe ta fice daga ɗakin. A fusace Mommy ta bi bayanta, cikin sauri Baffa yace ‘Zo mana.’

    Ta juyo a daidai lokacin da Khadeejan ta rufe ƙofa, ya nuna mata inda Khadeejan ta tashi ta zauna. Sai da ya ɗauki lokaci yana kallonta sannan yace ‘Ki bi ta a hankali tunda dai kin ji bayaninta. Ni da na ba shi aurenta ai ba ‘yar aiki na ba shi ba ko? In ya dawo ya zo ya yi bayani in ya so sai a san matakin da za a ɗauka.

    Shi a zaman aure ma wani lokacin hutu kawai mutum yake buƙata; kada ki je ki ɗaga mata hankali. Ki barta ta huta ƙarshenta in ya dawo sai dai ki ji da kanta tana gaya miki ya mayar da ita za ta koma. Da-Allah kada ki ɗaga mata hankali tunda dai ita ta kawo mutumin nan tace tana so ai ba laifi ba ne idan ta dawo tace bata son shi.

    Ki ba ta lokaci ta sami nutsuwa tukunna. Ta sauke numfashi sannan tace ‘To. Ta tashi ta fice ta bar shi a ɗakin. A nan gidan Hajia ya ajiye motarsa ya samar musu taxi wadda za ta kai su airport, ya shiga gaban mota ita kuma ta shiga baya. Suna kama hanya ta zaro wayarta ta lalubo lambar Anti Wiyya ta tura mata sako ta wahtsapp tana sanar da ita an saki Khadeeja.

    Bayan sun gama hirarrakinsu na murna da nuna jin daɗi Anti Wiyya ta turo mata saƙo kamar haka “Kije ki yi ta addu’a Allah ya sa kada kuna dawowa ya dawo da ita. Nan ma in sha Allah akwai wani malami da zan kai wa abin sadaka ya yi miki aikin da ba za ta taɓa dawowa gidan ba, kin ga kin ci gida se yanda kika yi.”

    Ta turo mata emoji na dariya ta rufe wayar, ta mayar da hankalinta kan hanya zuciyarta fes cike da fatan Allah ya sa kada ya dawo da Khadeeja tunda ya ce saki ɗaya ne; in ya so sai ta ji da yaran kawai. A hankali Khadeeja ta ba je kayanta a gida; ta sanar da Baffa ko da ya dawo ma ba za ta koma ba domin ko ya mayar da aurenta to kotu za ta kai shi ya sake ta.

    A haka dai aka bar maganar domin shi Baffa gani yake kamar idan aka ba ta lokaci ta huce za su yi wa kansu sulhu ita da shi. Tun Baffa yana sa rai zai ji kira daga wajen iyayen Mustapha sun biyo sawu har ya fitar da rai. Saura kwana biyu babbar sallah suna zaune a parlor shi da Mommy suna hira yace ‘Mutanen nan dai shiru, babu wanda ya biyo sawun Dije.

    Na san dai babu yanda za a yi su ce ba su san ya sake ta ba tunda ai za su ga ba ita ya barwa yaransa ko? ‘Uhm, ni abun har ya ishe ni ma wallahi. To amma ko tuntuɓarsu za ka yi ka ji, tunda ai ba za mu taru mu zama ɗaya ba ko?’ Mommy ta ba shi amsa. Ya yi ‘yar dariya yace ‘Babu wanda zan tuntuɓa tunda ai da zan ba su aurenta ba ni na tuntuɓe su ba su suka zo har gida suka tuntuɓe ni.

    Idan na tuntuɓe su haƙuri zan ba su ko me? Ni aka yi wa wulaƙanci aka saki ‘yata ko ma don wanne dalili ne amma kuma ni ake jira na yi magana? To su cigaba da zamansu kada ma su zo inda nake. A haka suka bar zance domin Mommy ta san in dai Baffa ne yanda ya kafe ba zai yi magana ba to tabbas ba zai yin ba.

    Su ma daga can gidansu Mustapha a tunaninsu Baffan Khadeeja ne ya kamata ya neme su don ya kamata idan ta je gida a bincika a ji, sai dai har aka shiga hidimar bikin sallah babu wanda ya neme su. Sai suka bar maganar kawai suna jiran Mustaphan ya dawo su ji ko shi ya yi magana da iyayen nata.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Tara

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

    Kamar yanda Khadeeja ta faɗa ba ta sake kula hidimar yaran a ranar da ba ita ce da kwana ba, sai dai ranar kwanata tana fitowa ta sallami kowa sanna ta cigaba da harkarta. Idan kuma dare ya yi ta shiga ɗakinta ta yi kwanciyarta don ta tabbatarwa Mustapha cewa ta ba shi kwanan.

    Ranar Asabar ce don haka yara babu makaranta duk suna gida, kamar yanda suka saba tunda Khadeeja ta ƙi hidimar yaran to duk ranar girkin Naja Anti Wiyya ce take abinci har yaran. Ita kuma Najan ita ce za ta tsaya a kansu su yi wanka su shirya, sai dai ranar da ba ta tashi ba dole haka Mustaphan yake tashi ya yi ta faman yi musu faɗa har ya samu su gama shiryawa a hankali.

    Afaf ce ita kaɗai a parlor ɗin Naja tana kallo saboda TV ɗin parlor ɗinsu Startimes ce ita kuma ta fi son DSTV wadda take parlor ɗin Naja; yayin da Anti Wiyya take ta kai wa da kawowa tana ƙoƙarin dora a bincin rana. Ta wuce Afaf a parlor ta shige ɗakin Naja inda ta same ta a kwance a gefen gado; bayan ta amsa sallamarta ta ƙarasa ta zauna a gefen kafarta kamar a fusace.

    Tace ‘Sannu Anti, kina ta hidima. Lallaɓa ta nake yi idan ta ƙoshi goya ta zan yi na fito na taya ki. Salaman ma ina jin yau ba za ta zo ba; ko wa take so ya yi mana wanke-wanke da sharar oho ga girki. Ta yi tsaki ta kawar da kai tace ‘Kin ganni a cike nake da haushinta, ga shi kamar ta shirya wulaƙanci tunda yau wanke-wanken ya fi na kullum yawa sannan ta ƙi zuwa.’

    ‘Hmm! Ai sai haƙuri masu aikin zuwa da dawowa ba su da kirki, ni ma da na gama jegon nan me kwanan zan ɗauka. Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan Anti Wiyya tace ‘Ita kuma wannan ‘yar taki wallahi ita ma ba ta da mutunci; yaushe za a ce budurwa kamarta ba za ta yi aiki ba komai ƙanƙantarsa?

    Sai dai ta dinga bin mutane da kallo suna mata aiki sai kace ubanta sayenmu ya yi. Gaskiya ku sake zama a gidan nan, haba! Idan banda ma rashin mutunci ya za a ce mace tana jego kuma a barta da kula da gida da yara bayan tana da kishiya? Ai kamata ya yi ta karɓar miki aikin. Ko da yake wannan ‘yar mulkin kishiyar taki na kula daga ke har maigidan tsoronta kuke yi.’

    Ta tashi zaune ta kwantar da Rukayya wadda ta riga ta yi bacci, ta kama haɓa ta dubi Antin tata tace ‘A a shi dai yake tsoron matarsa, duk abinda ta ga dama tace ba za ta yi ba haka zai yi ta kame-kame saboda ita ba a iya yi mata dole. Ta kalle ta sheƙeƙe tana cewa ‘Kece karkatacciyar kukarsa mai daɗin hawa ko? Shi yasa kina jego amma aka lafta miki aiki?

    Ita ko kunya ba ta ji? Sai ta sauko ta ishi mutane da gaishe-gaishe kamar wata musulmar ƙwarai. Cikin damuwa tace ‘Haka take fa, da an haɗu ta yi ta haba-haba da mutum amma mugun halinta yana nan fal cikinta sai mu da muke zaune da ita muka san halinta. Anti Wiyya ta ɗan yi ƙasa da muryarta tace ‘To gaskiya dai dole a yi aiki a kan wannan matar, yanda ta kama maigidan nan tana juya shi ai ba fin mu iyawa ta yi ba.

    Kema idan kika zo yawon arba’in da kaina zan kai ki inda za a taimaka miki a ƙwato miki daraja. Wannan kwarjinin da take da shi take yi wa kowa har maigidan ke ma a samo miki shi. Taimako ne da ayar Allah ina da malamina a hannu kuɗi kawai za ki bayar. Har yaran ma don ubansu ko su bi ki su zauna lafiya ko kuma su koma ‘yan kallo.’

    Tana ta jijjiga kai saboda gamsuwa tana cewa ‘Babu komai Anti, in sha Allahu za mu je. Don ni ma wallahi zaman haka ya ishe ni. Kuma dama Yaya ma tace za mu je ban san me ya ɗauki hankalinta ba. Nan suka zauna suka gama ƙulla yanda za a yi sannan suka fito suka kama hidimar gidan.

    Haka suka cigaba da yi har Naja ta yi arba’in; duk wata kalma da Mustapha zai yi amfani da ita ya sa Khadeeja ta karɓi hidimar nan ba ta yi amfani ba har ya gaji ya sakawa sarautar Allah ido. Sai da Naja ta yi arba’in sanna suka cigaba da rabon kwana. Idan Khadeeja ce da kwana sai Mustaphan ya je ɗakinta yayin da ita kuma Naja take zuwa ɗkinsa.

    Kwanci tashi har ya zama ta mayar da saman nasa kamar nata, ya zama kullum tana ciki ko parlor ɗinsa ko ɗakinsa. Ba ta daɗe da yin arba’in ɗin ba kuma Khadeeja ta gama bautar ƙasa; sai dai duk yanda ita da Baffanta suke ƙoƙarin samar mata aiki bai samu ba. Inda ta yi bautar ƙasar ma ta so su riƙe ta amma suka nuna mata ba sa buƙatar ma’aikata.

    Ba ta son zaman gidanta, domin ta san in dai ya zama Naja za ta tafi aiki ta barta a gidan da yara to dole Mustapha zai yi duk yanda zai yi ya tursasa ta ta dinga kula da yara. Ya zama shi da matarsa suna yawon neman kuɗi ita tana musu hidimar gida da ta yara. Don haka ta sanar da manager za ta dinga zuwa Litinin zuwa Juma’a tana yi musu aiki kyauta.

    Da ya ji haka sai ya sa aka ɗora ta a kan tsarin internship da suke da shi; inda duk wata za a dinga ba ta naira dubu goma sha biyar har zuwa lokacin da za a sami wani gurbi a gidan rediyon kawai sai a ɗauke ta. Sosai hakan ya yi mata daɗi, kuma ba tare da wata fargaba ba ta sanarwa Mustapha sun riƙe ta aiki, ta cigaba da zuwa.

    Kusan wata takwas kenan da haihuwar da Naja ta yi; kuma kamar yanda suka tsara an kai ta wajen malami. Bayan malamin ya ji bayaninsu ya ba ta wani abu mai kama da gishiri yace ta yi sati tana zuba musu a abnci duk gidan kowa ya ci har Khadeeja. Haka ta dage ta yi amfani da abun nan sai dai ba ta da tabbcin Khadeeja ta ci abun marmarin da take girkawa tana aika mata, shi ma Habib ba ta da tabbacin cinsa domin ya fi cin abinci a wajen Khadeeja.

    A hankali ta fara ganin sauyi, kamar dai duk yaran da Mustaphan suna saurararta; tunda wasu lokutan idan ta sa Afaf aiki haka za ta tashi ta yi ko ba ta so kuma Mustaphan ya daina hanata.

    Sun gama magana da ita a kan zai siya mata mota, amma ga shi lokaci yana ta ƙurewa yanzu ya ma ce mata shi ba alkawari ya yi mata ba; shi kawai ce mata ya yi zai yi tunani. Cikin damuwa suke waya ta sanar da Anti Wiyya halin da ake ciki; tace ‘Wallahi Anti nema yake ya canza maganar.

    Kuma dama na gaya miki aikin malamin nan ba kullum yake ci ba, tunda ko Mustaphan ya fara saurarar maganata da an kwana biyu sai ya sake komawa kamar da. Gani ma nake kamar duk lokacin da matarsa ta karɓi kwana sai ta warware min aiki, shi yasa nake ta fama da shi. Daga ɗaya ɓangaren Anti Wiyya tace ‘Au haka ne? To bar ni da su, ai ba mu za a yi wa bariki ba.

    Akwai wani malamin aikinsa yana da zafi sosai, in kin sami lokaci kiyi min waya sai mu je wajensa. Ke kanki sai kin yi mamakin aikinsa. Suka ƙarasa hirarrakinsu suka yi sallama. Ta jefa wayarta a kan gadonta cike da ƙwarin gwiwa; ta san Mustapha yana ƙoƙari wajen kyautata mata amma ita gani take kamar tsoron khadeeja yake yi. Kuma ma ita so take ya zama gaba ɗaya gidan sai abinda ta faɗa za a yi.

    Tana ganin yanda maza suke yi wa matansu kyauta ta burgewa, ita ma haka take so ya dinga yi mata, duk abinda ta nema ya ba ta kawai tunda ta san yana da kuɗin. Idan ma ta sami yanda take so to ko ganin Mustapha yaran ba su isa su yi ba sai da izininta, domin ta kula da yanda yake saurararsu yana bin ra’ayinsu kamar su suka haife shi.

    Sai an yi magana yace su marayu ne. Tabbas dole gidan nan gaba ɗaya ya dawo tafin ƙafarta don ta gaji da wannan mulkin da ake mata ana kasa mata hankalin miji tsakanin uwargidansa da yaransa.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Shida

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Shida

    Tana jiyo motsin shigowar Mustapha gidan amma ba ta yi zaton zai tafi da sauri ba, don haka ma ta jira sai da ta gama abinda take yi tunda ta jiyo shi da Baffa a tsakar gida. Sai dai ga mamakinta ko da ta fito Baffa ta tarar shi kaɗai, yana shirin shigewa mota ta yi sauri ta karasa.

    Tace ‘Na ji kamar kai da Mustapha ne, ko har ya tafi ne? Ya tsaya yana riƙe da murfin mota yana cewa ‘Shi ne, matar tasa ce ta fara gwada masa tutsun nata shi ne ya taho kawo ƙara da sassafe. Ikon Allah, Khadija Iya-rigima. Me ta yi kuma?’

    Nan ya ba ta labari kamar yanda Mustapha ya ba shi, ya ƙara da ‘Na ce su zo bayan Magriba don ita ma yanzu zan kirawo ta na sanar da ita kada ta yi taurin kai, kin san hali. Ta yi dariya ‘To Allah ya kai mu, ai an auna arziƙi ma da aka ɗauki lokaci haka ba ta fara rigimar ba. Suka yi dariya ta yi masa a dawo lafiya ya wuce sannan ta koma ciki.

    Sai da yamma ta yi sannan ta kirawo Khadeeja a waya, bayan sun gaisa tace ‘Me ya haɗoki da Mustapha ne ya kawo ƙararki da sassafe ne? Ta yi dariya sannan ta ba ta labari, bayan ta gama ji tace ‘Ikon Allah, to neman mata Mustaphan yake yi kenan ko kuwa dai aure yake nema?’

    ‘Ni ma ban sani ba Mommy, amma dai ko ma menene ai da akwai cin fuska a ce ina yawo a taxi ita kuma tana yawo a motar mijina; at least ya bari ta aure shi sai ya ba ta wannan ikon. Kuma sannan idan ita ce za ta dinga yi masa hidimar yaransa ai sai ta karɓa gaba ɗaya ni kuma na huta gaba ɗaya.’

    Mommy tace ‘Um! Da wannan, amma dai ki bari a bi abun a hankali. Saura kuma idan kun zo ki yi shiru ki ƙi yi wa Baffa bayani ya yanke miki hukunci in ma ya ga dama yace ki ba wa Mustaphan haƙuri. Ta yi ‘yar dariya ‘Ba zan yi shiru ba Mommy. Suka yi sallama suka ajiye wayar.

    Sai dab da magriba ya dawo gidan, ya yi mamaki da ya jiyo Rashida da Afaf a kitchen suna ƙoƙarin dafa abincin dare; a tunaninsa tunda ya san Baffa ya gaya mata yana nemansu ya kamata a ce ta shiga hankalinta. Bayan ya amsa sannu da zuwansu ya wuce ɗakinta; ƙofarta a rufe take, ya saka mukullinsa ya ji har yanzu ba ta cire mukullin ba don haka ya daure ya ƙwanƙwasa.

    Sai da ta gama yauƙinta sannan ta buɗe ta rige hannun kofar ta matsa ya shige. Ya so ya zare mukullin kofar to amma sai ya ga idan ya zare ai duk da haka ba lallai ta dinga fita daga ɗakin ba balle ma ta dinga yin hidimar da ta saba; tunda dai wulaƙanci ne kawai ta shirya za ta yi.Don haka ya bi bayanta suka shige ɗakin, tun kafin ta gama zama a inda ta tashi yace ‘Baffa ya gaya miki mu je yana nemanmu ko?’

    Cikin halin ko in kula tace ‘Ƙarfe nawa za mu je? Ya so a ce ta ba shi dama su yi magana su kashe wannan rigimar in ya so ya kirawo Baffa yace masa sun shirya amma sai dai ga alama ta fi so su je wajen Baffan. Yace ‘Da na dawo daga masallaci sai mu je.’

    Ya juya ya fice daga ɗakin ba tare da ya saurari amsarta ba. Ta bi bayansa da harara tana dariya; wato shi uban ‘yan son kai har yanzu bai ga laifinsa ba don haka ita yake tsammani ta ba shi haƙuri kenan. Tabbas yau sai ta ƙure wannan son zuciyar na Mustapha duk da har yanzu wata zuciyar tana gaya mata kada ta je ta yi wa mijinta tonon asiri a wajen iyayenta.

    Yana dawowa daga masallaci ya same ta a shirye, ko zama bai yi ba suka sallami yara suka fice daga gidan. Suna shiga gidan suka sami Mommy wadda ta ba su umarni su ƙarasa parlor ɗin baƙi domin Baffa yana can yana jiransu. Yana zaune a kan kujera 3-seater don haka Mustapha ya zauna daga gefen damansa jikin 2-seater ita kuma Khadija ta koma ɗaya gefen jikin single seater ta zauna.

    Bayan Baffa ya amsa gaisuwarsu ya dubi Khadeeja yace ‘Dije, me ya haɗa ki da maigidanki ne kika daina kula shi shi da yaransa? Ta sunkuyar da kai cikin sanyin murya tace ‘Baffa ba daina kula su na yi ba. Kafin Baffa yace wani abu Mommy ta shigo da sallama Nabila tana biye da ita ɗauke da tray wanda aka jera ruwa da lemo a kai, don haka Baffa ya tsaya ya amsa sallamarta.

    Ta nunawa Nabila inda za ta ajiye tray ɗin daga kusa da Mustapha, ta ajiye ta gaida Mustaphan sannan ta miƙe ta fice daga parlor ɗin ita kuma Mommy ta kara ta zauna a kan kujerar da Khadija take zaune a ƙasanta. Ya juya ya gaida Mommy, bayan ta amsa Baffa ya sake duban Khadeeja yace ‘Ya aka yi Dije ina saurarenki.’

    Tace ‘Baffa ba daina kula su na yi ba fa. To ai ya ce kusan kwana uku kenan ba kya kula kowa sai dai kawai ki kulle kanki a ɗaki kin bar yara da mai aiki sannan kuma gari yana wayewa sai ki fice ki tafi makaranta. Kawai saboda ya tura sakatariyarsa ta je makarantar yara kun haɗu.’

    Ta faki ido ta share ƙwalla; ya riga ya ba wa Baffa kanun labaran don haka duk yanda take son ta kare mutuncinsa ba zai yiwu ba domin ita ma dole ta kare kanta a wajen mahaifinta. Ta gyara zama tace ‘Wallahi Baffa ina bakin ƙoƙarina wajen kula da gidan da yaran, kuma babu laifi duk mun sami fahimtar juna da yaran gaba ɗaya.

    Duk wata hidimarsu ni nake yi, kuma ni ce nake ɗauko su daga makaranta ranar da ba na nan kuma sai mai-aikina ta ɗauko su. To shi ne ranar Monday suka yi open day a makaranta; ni ce na saba zuwar musu don haka tun weekend suka gaya min, shi kuma na manta ba mu yi maganar ba.

    Don haka gari na wayewa da na shirya zan tafi school sai na tsaya makarantarsu. Shi ne sai na ga har ya tura sakatariyarsa ta je musu. Baffa ya yi dariya yace ‘To ai babu komai Dije, wataƙila don ba ku yi maganar ba ne kuma kin ga ita ɗin ai sakatariyarsa ce zai iya saka ta wannan aikin duk da dai personal ne.’

    ‘Ni Baffa ba zuwanta ne ya ɓata min rai ba…’ nan ta ba shi labarin yanda ta ga sakatariyar a motar Mustapha ɗin da kuma yanda tunda ta aure shi sau ɗaya ya taɓa kai ta makaranta a motarsa da kuma yanda ko ta shirya ba ya yarda ya fita da ita. Da kuma yana wasu lokutan tana tsaye a bakin titi yake dawowa daga kai su; ba ta sani ba ko yana ganinta amma ita dai tana ganinsa.

    Baffa ya kalli Mustaphan ya kalli Mommy sannan ya kalli Mustapha wanda ya yi tsamo-tsamo don bai za ta Khadija za ta kawo wannan maganar ba; shi da ya ga ta daina damuwa ya rage mata hanya ma ya zata ta haƙura gaba ɗaya don haka bai san tana jin haushinsa a kan wannan ba.

    Yace ‘Ikon Allah, yanzu a ce a ki ragewa mutum hanya sai ka ce wani wanda ake jin haushi? Ko dai akwai wata matsalar ne Mustapha?’ Nan da nan ya fara gyara zama kansa a ƙasa cikin rawar murya yace ‘Babu wata matsala, em… dama yawancin lokutan ne ai ba ta shiryawa da wuri su kuma yaran idan 7:30am ta yi rufe musu gate za a yi.

    Umm.. shi yasa dole muke tafiya, kuma wasu lokutan ma idan na kai su gidan nake dawowa sai daga baya nake fita. Tace ‘Baffa ai ko ya dawo zai fita idan nace ya rage min hanya sai ya san abinda zai faɗa wanda zai sa ba zai tafi da ni ba don haka ma tun tuni na daina tambayarsa.’

    Suka ɗan yi shiru na ɗan lokaci Mustapha yana ta ƙoƙarin haɗa ido da ita yayin da ita kuma take ta ƙoƙarin kauce masa don ko gefen da yake ba ta kalla ba. Baffa yace ‘Shikenan abinda ya saka ki fushin ko akwai wani abun?’ Kana jin muryarsa kuma ka kalli fuskarsa za ka san ransa ya sosu matuƙa, domin karsashi da rahar da ya fara wannan tattaunawar da su duka babu.

    Har ta gyaɗa kai Mommy ta zungure ta da kafa, ta dago suka haɗa ido. Ta sunkuyar da kanta tace Baffa ita sakatariyar tasa kuma na tambaye shi menene a tsakaninsu; idan ma aurenta zai yi ai sai ya gaya min ba wai kawai na dinga ganinta a motarsa ba tana yawo a gari ni ina yawo a tasi.

    Saboda ni dai yanda na ga ta nuna alaƙarsu ta fi ƙarfin ta office kawai, don yaran ma duk sun santa ni kaɗai ce a gida na fara ganinta ranar. Baffa ya mayar da idonsa kan Mustapha wanda ya yi sauri ya sunkuyar da kansa ƙasa, ji yake kamar ya zura da gudu don bai taɓa zata Khadeeja za ta kawo waɗannan maganganun a gaban Baffa ba.

    Suka yi shiru na ɗan lokaci kowa yana sauraron abinda Mustaphan zai ce, shi kuma ya sunkuyar da kai ya yi shiru kamar wanda ruwa ya ci. Mommy ce ta gaji da shirun ta yi gyaran murya tace ‘Uhm, ai gara ka gaya mata idan auren sakatariyar za ka yi ka ga tunda dai na san cewa ta san ka kai ka ƙara auren.’

    Ya gyara zama yana shafa ƙeya yace ‘A a ba ma shi ba ne, kawai dai da na aiketan ne to kuma ana ɗan wahalar mota shi ne na ce ta je a motata tunda ta iya tuƙi. ’Jimawa kaɗan Baffa yace ‘Allah ya sauwaƙe. ’Mommy tace ‘Amin dai.

    Suka sake yin shiru na ɗan lokaci, sannan Baffa ya kirawo sunan Khadeeja, ta amsa ta dube shi suka haɗa ido sannan yace ‘Ki yi hakuri Dije, kin ji. Ta gyada kai shi kuma ya ɗan numfasa sannan ya cigaba ‘Ki yi hakuri ki bi mijinki, kin ji bayanin da yayi. Kuma idan ma yace zai auri waccan yarinyar wannan bai kamata ya zama matsala ba tunda dai kin san duka wani namiji mijin mace huɗu ne.

    Ki yi haƙuri ki cigaba da hidimarki kamar yanda kika saba, kin ji. Batun kai wa makaranta kuma kin ga shi ‘yayansa yake zubawa a mota yake kai su a makaranta kuma tabbas haka ya kamata uba nagari ya kasance, don haka idan kika gama shirya masa nashi yaran ke ma ki shirya ki yi min waya sai na zo na kai ki tunda dai ke ma ‘yata ce; kai ki makaranta kuma ba baƙon abu ba ne a wajena.’

    Ya gyara zama ya ɗago kai a razane ‘A a Baffa a yi haƙuri ai ba sai an yi haka ba, in sha Allahu za mu dinga tafiya ma. Dama ai ba ta gaya min ne shiryawa kawai take tace ta tafi. Kada ka damu, zan dinga zuwa ina kai ta wannan aikina ne.’ Baffa ya ba shi amsa rai a ɓace.

    ‘A yi haƙuri Baffa, in sha Allahu ba za sake ba, ni ɗin ma zan dinga kai ta. A yi haƙuri.’ Mommy tace ‘Ke kuma ki yi haƙuri da yaranki tunda su ba su yi miki komai ba, ki kula da su ku zauna lafiya. Shi ma kuma kin ji bayaninsa, ki je ku yi zamanku lafiya kamar yanda kuka saba saboda Allah. Ita rayuwar aure haƙuri ce, ku dinga haƙuri da juna.

    Kuma nan gaba ko wata matsala ta taso muku ku yi ƙoƙari ku kashe ta a tsakaninku. Toh.’ Ta amsa cikin sanyin murya. Jimawa kaɗan suka yi wa Baffa da Mommy sallama suka fice; Khadeeja ta so shiga cikin gidan wajen Nabeela amma Mommy tace kada ta shiga ta bar shi yana jira idan ta shirya ta dawo su yi hirar.

    Tunda suka shiga motar bai ce komai ba sai muzurai kawai yake, don haka ita ma zuciyarta wasai take. Ta ji daɗin yanda Baffa ya nunawa Mustapha cewa ita ma da gatanta; duk da dai har yanzu tana jin cewa ba za ta ɗorawa kanta jiransa ya kai ta makaranta ba balle ta ɗorawa kanta damuwa.

    Suna shiga gidan ta wuce ɗakinta shi ma ya wuce nashi ɗakin. Sai da ta yi sallah sannan ta fito wajen yaran; zuwa lokacin Shukra har ta riga ta yi bacci. Bayan ta tabbatar sun ci abinci ta wuce kitchen, ta kirawo Rashida tana tambayarta me suka dafa da daddare. Ta gaya mata indomie suka dafa saboda haka Afaf tace, ta nuna mata indomie ɗin da ta saka a flask ta ajiyewa Abbansu.

    Ta riga ta san ba ya son indomie, musamman idan ta fara sanyi kuma ita ma yunwa take ji ba ta son cin indomie mai sanyi. Don haka Rashida ta taya ta ta gyara busasshen kifi ta dafa musu jollof sphageti mai rai da lafiya. Nan da nan gidan ya ɗauki ƙamshi; zuwa loakacin yaran duk sun kwanta.

    Ta jera abincin a dining table sannan ta haɗa masa shayi mai kayan ƙamshi irin wanda yake so sanna ta wuce ɗakinsa ta tura ƙofa ta shiga. Saura kaɗan ta yi dariya saboda ganin yanda ɗakin ya yi kaca-kaca; ga ƙura ga kaya da tarkacensa ko ina. A ranta tace mutum sai kace kuturu, ya sa hannu ya gyara makwancinsa kawai ya gagare shi.

    Ta ɗan yi gyaran murya tace ‘Ga abinci can na saka a dining,’ Dama tunanin abincin yake don yunwa yake ji sosai; ya riga ya san indomie suka dafa tunda jiya ma ita suka dafa don haka ya riga ya fara tunanin yanda zai yi sai kuma tace masa ga abinci. Ya dube ta ya ɗan sassauta fuskarsa yace ‘Yanzu zan fito.’

    Ba tare da ta ba shi amsa ba ta juya ta fice, ya bi bayanta da kallo yana murmushin yaƙe. Ya rasa daɗi zai ji ta ba shi abinci wanda hakan yake nuna za ta cigaba da hidimarta; ko kuwa haushinta zai ji saboda yanda ta yaga shi a gaban Baffanta. Haka dai ya taso ya fito, babu kowa a parlor ɗin don haka ya zauna ya ci abincinsa ya ƙoshi; irin ƙoshin da ya kwana biyu bai yi ba.

    Sai da ya gama cin abincinsa ya huta sannan daga baya ya je ya kullo gidan ya shiga ɗakinsa; har ya kwanta kuma ya tashi ya bi bayan Khadeeja. Ya kula idan ya biye mata ba za ta neme shi ba, ko ba komai kuma yana so su yi magana ya ƙara kwantar mata da hankali game da maganar Naja don ba yanzu yake so ta sani ba. Sannan kuma yana so ya nuna mata rashin jin dadinsa game da yanda ta je ta kunyata shi a gaban Baffa.

    Duk yanda yaso ta taso su koma ɗakinsa su kwana kamar yanda ya saba bai samu ba, daga haka ya gane idan ya fiye takura mata zata sake ɗauke musu wuta; don haka sai ya haƙura ya zubar da duk maganganun da ya taho da niyyar gaya mata. Ya haƙura suka kwana a nan ɗakin nata tunda tace ta fara bacci ba ta son canza ɗaki.

    Tun asuba ta tashi kamar yanda ta saba, nan da nan ta shiga hidima da yara da taimakon Rashida. Ba ƙaramin daɗi ya ji ba da ya dawo daga masallaci sallar asuba ya jiyo ta a kitchen, don haka cike da walwala ya wuce ɗaki ya koma bacci kamar yanda ya saba.

    Ƙarfe bakwai na safe yana fitowa kowa ya shirya yayin da Khadeeja take kai wa da kawowa tana jera masa nasa abincin a dininga table. Bayan ya amsa gaisuwar yaran yace ‘To kowa ya ɗauki kayansa mu wuce ko? Nan da nan suka miƙe suka fara ficewa. Ya dubi Khadeeja wadda take fitowa daga kitchen yace ‘Ba ki shirya ba ke, ko sai an jima za ki tafi?’

    Da murmushi tace ‘No, yau ba mu da lecture ba zan je ba. ‘Ok.’ Ta yi musu a dawo lafiya suka wuce. Bayan ya dawo haka ya yi ta tambayarta idan ta san za ta je makaranta ta gaya masa ya jira ta ya tafi da ita ya kai ta; sai da ta tabbatar masa ba za ta fita ba sannan ya fita ya tafi office.

    Washegari ranar Juma’a ce; kamar yanda ya saba yana kwance a ɗaki bayan ya dawo daga masallaci yana rage bacci kafin a gama shirya yara ya kai su makaranta. Wayar Khadeeja ce take ta faman ringing a ɗakin tana katse masa bacci, baya son tashi don haka ya yi tsaki ya gyara kwanciyarsa.

    Sai dai wayar da ta tsinke sai a sake bugowa; to waye ma yake kiranta da wannan safiyar bayan ko wayewa garin bai gama yi ba? Wayar tana fara ringing a karo na uku ya mirgina ya miƙa hannu ya ɗauko wayar daga kan durowar gefen gado. Ya kallin screen ɗin inda sunan wanda yake kiran ya bayyana “Baffa” ya karanta a fili yana wattsakewa.

    To me yasa Baffan Khadeeja yake kiranta yanzu? Allah ya sa dai ba wani abun ne ya faru a gidan nasu ba. Nan da nan ya sauko daga kan gadon ɗauke da wayar ya nufo kitchen inda Khadeejan take faman zubawa yara abinci suna tsaye kowa yana karɓar nasa. Ya miƙa mata wayar wadda take ringing yana cewa ‘Ki amsa Baffa ne yake ta kiranki kin baro wayar a ɗaki.’

    Tana karɓa ta amsa ta kara a kunnenta; yana tsaye yana kallonta yana tsoron kada a ce wani abu ne ya faru a gidan nasu. Bayan sun gama gaisawa da Baffan tace ‘A a Baffa, ina nan ne muna shirin makaranta ni da yara.’

    Daga ɗaya ɓangaren Baffa yace ‘Ƙarfe nawa ne lecture ɗin naki Dije? ’Tace ‘Karfe takwas. Idan nazo 7:30am ai kin gama shiryawa ko? ‘Eh Baffa. ‘To ki shirya idan na ƙaraso zan yi miki waya ki fito na kaiki makarantar sai na wuce office. ’Cike da girmamawa kamar wadda za ta tsuguna a wajen tace ‘To Baffa na gode, Allah ya ƙara lafiya.’

    Ta ajiye wayar bayan ya amsa, kafin ta yi wani abu Mustapha yace ‘Lafiya ƙalau dai naga Baffa yana kiranki da safe. Ta miƙawa Habib shayinsa da ta haɗa masa tana cewa ‘Uhm zai zo ya kai ni school ne shi ne yake tambayata ƙarfe nawa zai zo. Habib ya karɓi shayinsa ya fice yayin da Mustaphan ya matsa kusa da ita cike da kulawa da damuwa yana cewa ‘Makaranta kuma?

    Ba nace zan dinga kai ki ba? Yanzu ke saboda rashin tausayi sai ki taso shi da wannan safiyar kawai don ya kai ki makaranta? Ke abu ba zai wuce a wajenki ba? Ta juya cikin halin ko in kula tana cewa ‘Shi ne ya karɓi timetable ɗina yace zai dinga zuwa yana kai ni ko? Ai a gabanka ya faɗa.’

    ‘Kuma a gabanki na ba shi haƙuri ai; wannan wanne kalar abin kunya ne ina nan kuma ina da abin hawa amma za ki taso Baffa ya zo ya kai ki makarnta don Allah? Dariyace take son ta ƙwace mata saboda yanda duk ya muzanta kamar ma Baffa yana tsaye yana kallonsa. Kafin ta ba shi amsa ya ɗauki wayar tata ya dannawa Baffa kira ya miƙa mata waya yana cewa ‘ki gaya masa zan kai ki ba sai kin yi min wulaƙanci ba.’

    Kafin ta yi magana har Baffan ya ɗauka, don haka ta kara a kunnenta tace ‘Um Baffa ka bari ma Abban Afaf zai kai ni makarantar. ’Yace ‘Ah, kin tabbata dai ko? ‘Eh Baffa, ga su ma tare za mu fita gaba ɗaya shiryawa muke.’

    Ya zare wayar daga hannunta kafin ta sake magana ya kara a kunnensa cike da girmamawa yace ‘Baffa za mu tafi tare in sha Allahu, zan dinga kai ta. A yi haƙuri. Yace ‘To, to babu laifi. Allah ya yi muku albarka. Ya ajiye wayar yana harararta yana cewa ‘Yanzu zan je na shirya, ke ma ki shirya sai mu fita gaba ɗaya ko kuma idan na kai su sai na dawo kafin nan kin ƙarasa sai mu wuce.’

    Tace ‘Um, ka ga babu komai fa, za ku iya tafiya ma sai na wuce kawai ba sai na gayawa Baffan ba.’ Ya kakkafe ta da ido yana harararta har sai da ta sunkuyar da nata idanun, ya juya yana cewa ‘Ki shirya nace. ’Ya fice ya bar ta a nan. Ta yi dariya ta cigaba da aikinta.

    Ba ta da zaɓi haka ta shirya suka fita tare, kuma daga wannan lokacin ya zama ko da wanne lokaci zata makaranta haka yake barin abinda yake yi ya zo ya kai ta. Sai dai idan ta gama abinda take yi kawai sai ta hawo motar haya ta dawo.

    Karanta  Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyar

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Uku

    Ranar Juma’a suna gida da yake yara babu islamiyya; ranar ne kuma suke gyara gashin yaran mai kitso za ta zo. Tun da wuri Afaf ta tsefe nata kan, ita kuma Shukra da yake tun suna makaranta Khadeejan ta tsefe mata babu wanda ya ji kansu. Tun da suka gama cin abincin rana take faman lallaɓa Nasreen ta bari a tsefe mata amma har aka kusa kiran la’asar guda biyu suka tsefe. Bata  son a taɓa gashinta kwata-kwata don haka ta ƙi ma zama a tsefe.

    Khadeeja ta kamo hannunta tace ‘Zo kin ji Nas, kin ga fa Shukra za ta fi ki kwalliya tunda ta tsaya  an gyara mata nata. Ta zauna, har an fara tsifar ta zame kanta ta matsa tana zumɓura baki. Afaf tace ‘Anti wallahi  idan ba ki zare mata ido ba haka za ki yi ta fama da ita, sai a yi sati ana tsefe kanta a gidan Mama.’

    Ta cigaba da lallaɓata amma sam ta ƙi tsayawa; don haka ta kama hannunta ta zaunar da ita  tana cewa ‘Idan kika sake tashi sai na zane ki Nasreen, ko na sa almakashi na aske gashin kan  ya koma kamar na Yaya Habib.’ Ta dubi Afaf tace ‘Yaya Afaf ɗauko min slippers mai zafi idan  ba ta tsaya an tsefe ba zane ta zan yi.’

    Da sauri Afaf ta ɗauki slippers ta zo ta ajiye a gaba Nasreen wadda ta fara shessheƙar kuka tana  fizge-fizge. Khadeeja ta ɗan riƙe gashin tace zan dake ki fa Nasreen, ki rufe min baki bana son  jin kukanki.’

    Nan da nan ta haɗiye kukanta tana shessheka aka cigaba da tsifa Shukra tana mata dariya.

    Daga masallacin Juma’a ya wuce gida don ya gaida Hajia, da ya gaishe ta sai ya wuce gida don  Khadeeja tace idan ya dawo zai kai su saloon ita da yara a wanke musu kai da yamma kuma  akwai mai kitso a maƙota dama ita take musu.

    Yana shiga gidan ya sami Yaya Jidda da yaranta biyu ‘yan mata Naja da Farida, bayan sun gaisa  gaba ɗaya Yaya Jidda ta dube shi tace ‘Gidanka fa za mu tafi yanzu ni da yara, Hajia tace mu je  mu dubo su Afaf.’

    Yace ‘To ai sai ku tsaya mu tafi, don ni ma gaisawa kawai za mu yi na wuce.’  Kafin minti goma sun gama, suka shiga mota ya ja su suka kama hanya, suna tafe suna hira.  ‘To ya yaran? Ana kula da su dai ko?’ Ta tambaye shi.

    ‘Ah Alhamdulillah, gaskiya tana ƙoƙari.’ Ya faɗa cike da fara’a.To ai haka ake so, Allah ya sa ta ɗore.’ Tun a bakin gate ya yi hon, gaba ɗaya yaran suka fito ban da Nasreen. Habib ya taya shi buɗe  gate, bayan ya shigo da motar gaba ɗayansu suka yi masa sannu da zuwa.

    A nan suka fara gaida Yaya Jidda, bayan ta amsa tace ‘Ina Nasreena?’ Afaf tace ‘Tana ciki tsifa Anti Khadeeja take mata.’

    Suka wuce gaba ɗaya suka shiga gidan; kafin Khadeeja ta amsa sallamarsu Nasreen ta fizge  kanta wanda saura ɗaya a gama tsefe shi ta tashi tana share hawaye tace ‘Abbaaa.’ ta faɗa tana  zumɓura baki.

    Da sauri ya rungumeta ‘Ya haka na ganki wujiga-wujiga? Wa ya taɓa ki?’ Shukra ta tintsire ta dariya ta daga slippers ɗin da aka ajiye tace ‘Kukan tsifa take Abba shi ne  Anti za ta zane ta da slippers, ka ga nawa Anti yalash ɗin ko kuka ban yi ba har aka tsefe yanzu za  mu je saloon amma ban da ita. Anti tace tunda ba ta so a taɓa kanta aske shi za ta yi kamar na  Yaya Habib.’ Sannu da zuwa Yaya.’ Khadija ta faɗa tana karkaɗe jikinta. Yauwa.’ ya amsa ba yabo babu fallasa.

    Ta ƙare musu kallo tana ƙoƙarin zama tana cewa ‘To yanzu kuma tsifar ce sai an yi zaniya ni ‘ya  su?’ Kafin Khadeeja tace wani abu Afaf tace ‘Anti wallahi idan aka biye mata sai an yi sati ana wannan  tsifar, kullum haka ake fama da ita.’ Khadeeja tace ‘Ai ba a ma yi zaniyar ba ta bari an tsefe.’ Ta tsuguna ta gaida ita yayin da shi kuma ya ja hannun Nasreen ɗin suka shige ciki.

    Sai da ta kawowa Yaya Jidda ruwa sannan ta bi shi ɗakin. Tana shiga ta same shi a tsaye yana  cire kaya yayin da Nasreen take kwance a kan kujerar ɗakin, kafin tace wani abu yace ‘Wai me  yasa ne sai an yi duka sannan za a yi tsifar? Na ga tun tuni dama ana mata kitson ban taɓa ji an  doke ta ba.’ Tace ‘Yanzun ma ba a doke ta ba, ko Nasreen? Ta dai ƙi tsayawa a tsefe ne na takurata na tsefe  mata, amma ba a yi duka ba.’

    Ya kawar da kai ‘Ni dai bana son dukan yara, don Allah duk abinda yaro ya yi kada a dokar min shi. Uwarsu ma ba ta dukansu, ba na bari gaskiya.’ Ta sunkuyar da kai cikin ƙosawa tace ‘In sha Allah za a kiyaye.’

    Ta ajiye masa ruwan da ta kai masa tana cewa ‘Lunch ɗinka yana nan a table.’ sannan ta fito ta  bar shi a ɗakin.

    Bayan ta dawo parlor ɗin ta tarar Yaya Jidda tana ta yi wa Afaf tambayoyi, ta wuce su ta shige  kitchen. Ta tsaya a tsakiyar kitchen ɗin gaba ɗaya kanta ya kulle; daga shigowarsu suna nema suce ta  doki Nasreen, to yanzu haka suke so a bar Nasreen ɗin ta dinga yawo da kanta? Ga shi Afaf tace makarantarsu ana duba kitso duk ranar Monday. Ta jijjiga kai ta ƙarasa ta ɗauki saucer ta zuba  cake da cin-cin ta ɗebo lemo a fridge ta jera a tray ta kawo wa Yaya Jidda da yaranta, bayan ta  ajiye a gabanta tace ‘Ya wajen su Hajiya?’

    ‘Lafiya ƙalau.’ Ta amsa ba yabo babu fallasa. Suka yi shiru sai surutun Afaf da take ta bawa Naja labari. Shukra ta matso ta kwanta a jikin  Khadeeja tace ‘Anti ni ma lemon.’ Ta shafa kanta ta dubi Afaf tace ‘Yaya ki ɗauko mata lemon wanda babu sanyi.’ Ta miƙe, har ta kama hanyar kitchen ɗin Yaya Jidda tace ‘Ku ba za ku sha lemon ba?’ Afaf tace ‘Ai da shi muka je school.’

    Shukra tace ‘Anti tace idan an kawo wa baƙi abinci mutum ya daina cewa zai ci, ni ma dai kawai  lemon zan sha.’ Khadeeja tace ‘Ki ɗauko muku lemon idan kuna so.’

    Jimawa kaɗan Abbansu ya fito daga ɗakin ya wuce dining ya zauna ya fara cin abinci; yana cikin cin abincin ya juyo yace ‘Kai Habib kun ci abinci ne?’ Yace ‘Tun ɗazu Abba, acici har ta yi round 2.’ Ya faɗa yana zungurar Nasreen.

    Khadeeja ta miƙe ta shige ɗaki, don gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi. Ta kula ƙiri-ƙiri neman laifinta ake yi; kamar ma Yaya Jiddan zuwa ta yi ta bincike ta. Ta ƙarasa ta zauna a kan gadonta ta zuba  tagumi. Bayan ya gama cin abincin ya shiga ɗaki ya fito da mukullin motarsa, ya dubi Khadijan yace ‘Idan  kun shirya muje na kai ku saloon ɗin.’

    Gaba ɗaya suka fice har da su Yaya Jidda, ya ajiye su a hanya sannan ya wuce. Tun daga wannan lokacin kuma sai Yaya Jidda ta mayar da shi ɗabi’a, duk Juma’a sai ta zo gidan.  Haka za ta zauna a parlor ta yi ta ƙare musu kallo tana kula da duk wani motsinsu, ga tambayoyi  waɗanda idan ta gama yi wa yaran za ta bi Khadeeja da neman ƙarin bayani. Sai dai ba ta taɓa  samun wani abu na zargi ba kuma Khadeejan ba ta taɓa ba ta dama ta yi wata fitna ba don duk abinda ta tambaya tana daure zuciyarta ta ba ta amsa gwargwadon iko, kuma cikin girmamawa.

    Ranar Talata ce kuma a ranar Khadeeja take sa ran za ta koma makaranta, tun dare ta sanarwa Mustapha. Ya amsa mata ba tare da wata matsala ba.

    Haka ta tashi tun kafin asuba ta shirya yaran tsaf, suna tafiya makaranta ta yi maza ta yi wanka sannan ta ɗan rage aiki don tana da lecture 9am. Bayan sun gama breakfast ta miƙe daga dining table tana tattara plates ɗin tana cewa ‘Babe bari na saka hijabi na sai ka yi dropping ɗina a school.’

    Yace ‘Ok, but kada ki ɓata lokaci don kada ki makarar da ni.’ Kusan a lokaci guda suka fito daga ɗakin kowa a shirye, sun kawo tsakiyar parlor ta dube shi tace ‘Yau kai za ka ɗauko yara ko? Don ni ina da lectures 9am to 4pm.’

    Ya ɗan ɓata rai cikin nuna damuwa yana cewa ‘I thought za ki dawo ki ɗaukosu, kin san ni sai 5pm nake tashi daga wajen aiki.’ ‘To ai ka ga ni ma sai 4pm zan tashi, kuma I can’t miss these lectures don last week ma ka ga ban je ba. Gara dai ka sami wani ya ɗauko su kawai.’

    Ya buɗe motar ya zauna yayin da ita ma ta zauna a kujerar gaba, yace ‘To ai ko an ɗaukosu ma wajen wa za a kawo su tunda ba kya gidan?’ ‘Haka ne fa, most days ma lectures ɗina har 4pm ne.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci; gaba ɗaya ma shi ya manta tana wata makaranta. Yanzu ya take so ya yi da yaran? Wa zai ɗauko su kuma wa zai zauna da su? Wannan ai shi ne an gudu ba a tsira ba. Muryarta ce ta katse masa tunani tana cewa ‘Babe ka ga da muna da mai aiki sai ta ɗaukosu ta shirya su su tafi islamiyya kafin na dawo; musamman idan Babba ce.’

    Cikin jin daɗi yace ‘Ƙwarai kuwa, zan yi wa Yaya Jidda magana sai a sami mai aikin kafin next week.’ ‘No, ka bari idan na yi wa Mommy magana za ta sa a samo mana a garinsu, mutanen suna da amana sosai ga aiki.’ Ba tare da ya kalle ta ba yace ‘Ki bari tukunna idan aka rasa a wajen Yaya Jidda sai a gayawa Mommy ɗin.’ Ba ta ji daɗin wannan maganar ba kuma ta san da ya kalle ta da zai gane sai dai son zuciyarsa ne a gabansa; don haka sai kawai ta yi shiru. Ba ta son abinda zai haɗa ta da Yaya Jidda don gaba ɗaya matar ta fice daga ranta, ta kula kamar tana neman laifinta ne ido rufe.

    A bakin department ƙawayenta Maryam da Jamila suka tare ta, ana ta ihu ana murna ga amaryar Babe. 9am to 11am suka fito daga lecture, wanda zai yi musu 12pm to 2pm ya aiko aka gaya musu ba zai zo ba. Don haka suka wuce hostel ɗakin su Maryam. Suna shiga Khadeeja ta nemi waje ta kwanta, Jamila ta taɓata tace ‘Ke da za ki bamu labarin amarci kuma sai ki kama wani bacci.’

    Ta bige hannunta tana cewa ‘Bar ni wallahi baccin da yake kaina ya fi na wata guda.’ Maryam ta yi dariya tace ‘Bar ta Jamila, kin san kwanan ibada take yi.’ Haka suka yi ta hirarrakinsu a kanta tana ta faman bacci. Har suka gama hirarrakinsu tana bacci, don haka ba su tashe ta ba suka fice sayen abinci. Basu daɗe da fita ba ta farka, bayan ta wanke fuska ta yi alwala ta yi Sallah. Ta zauna a kan dadduma tana tunani; tun ba a yi nisa ba ta gaji da auren Mustapha. To amma tana son shi, matsalarta kawai yaransa kuma da yanda ba zai bari ta yi musu tarbiyya ba. Kusan tun da ya kawo mata yaransa ba ta huta ba, wannan baccin da ta yi ji ta yi kamar an ɗauke wani dutse da ta daɗe tana dakonsa. Ko ina a jikinta ciwo yake, fatan ta kawai a samo mai aikin nan ko za ta huta. Duk da tana tsoron a kawo mai aiki daga gidan Yaya Jidda; gani take kamar CCTV camera ce kawai za a kawo mata.

    Tana zaune tana wannan lissafin wayar Yaya Mama ta shigo; bayan sun gaisa tace ‘Ya na ji ki haka ne amarya? Ko bacci kike yi ne?’

    ‘Wallahi ina hostel Yaya, kin ganni gyangyaɗi na gama.’ ‘To ya maganar mai aikin, tunda dai gaskiya aikin gidan nan ya fi ƙarfinki ga yara huɗu.’

    ‘Ya ce yayarsa za ta kawo mai aikin.’ ‘To ai shikenan, duk ɗaya ne. Kawai dai idan ta zo sai ki sa ido, kada ki bari ta shisshige miki; ke ko a cikin gidan ki kula kada ki kuskura ki dinga barinta tana shigar miki ɗaki, kitchen da store ma duk ki kula da motsinta. Yaran ma ki dinga kula da alaƙarta da su idan ba haka ba sai ta zame muku fitna.’ Yaya Mama ta faɗa.

    Cikin sanyin murya tace ‘To Yaya.’ Yanda ta ji muryarta bai gamsar da ita ba tace ‘Ko da wata matsala ne?’ No, ba wani problem. Ni ga ni ma a school na dawo sai yamma zan koma gidan.’’Ok, Mommy ma tace min kun je weekend ke da yaran naki.’ ‘Eh.’ Suka dan taɓa hira daga baya suka yi sallama suka ajiye wayar.

    Khadeeja ta bi wayarta da kallo kawai sai ji ta yi tana hawaye; ta yi kewar gida sosai, gaba ɗaya a yanzu ma ba ta san me take so ba, kawai dai ta gaji. Motsin su Maryam ya sa ta share hawayenta ta basar.

    Kwana biyu da yin maganar kuwa sai ga mai aiki; dattijuwa ce Baba Habi. Yaya Jidda da kanta ta kawo ta. Sai da ta tafi sannan Khadeeja ta nuna mata ɗakin yara inda a nan za ta dinga kwana.

    Ta nunnuna mata ayyukan kafin yaran su dawo daga islamiyya. Nan da nan ta fara ba tare da nuna wata kyuya ba, ga shi tana da hanzari wajen yin aikin.

    Yan kwanakin nan gaba ɗaya ba ta jin daɗin jikinta, gaba ɗaya ba ta san me yake damunta ba. Ranar Laraba ce, tana jin Mustapha yana tashinta daga bacci kafin asuba yana cewa ‘Ki tashi yara za su makara fa.’ Ta juyo tana yamutsa fuska tace ‘Babe bana jin daɗi wallahi, daga kwancen nan ma ni jiri nake ji ga headache. Bana jin zan iya tashi yau.’

    Ya miƙa hannu ya taɓa jikinta yana cewa ‘Subhanallah, me yake damunki?’ Ni ma ban sani ba, ta amsa muryarta na rawa. Ya matsa ya leƙa fuskarta, sai kuma ya sauka daga kan gadon yana cewa ‘Bari na gama da yara sai na kai ki asibiti, amma ki daure ki tashi ki shirya.’

    ‘To, ka bari gobe ma je asibitin mana.’ No, yau za mu je kin ga ana maganar za a saka lockdown saboda COVID 19 idan aka rufe ban san lokacin da za a buɗe garin ba. Gara mu je mu gama komai a siyo miki magani yanzu haka malaria ce.’ Ya faɗa sannan ya fice daga dakin.

    Baba Habi ce ta shirya yaran, duka da kasancewar ita ba ta iya girki ba haka suka haƙura Afaf ta nuna mata ta dafa musu indomie. Bayan sun sha shayi da burodi ta zuba musu indomie a lunchbox. Duk yanda ya so ya koma baccin bayan asuba ranar haka ya hakura ya zauna a parlor ɗin yana taya su shiryawa. Bayan ya kai su makaranta ya dawo ya shirya, ya taimakawa Khadeeja ita ma ta shirya suka wuce asibiti suka bar Habi a gidan.

    Suna zuwa likita ya tabbatar musu da cewa ciki ne da ita, aka ba ta magungunan suka taho. Kafin su isa gida sai da ya siyo magungunan, suna dawowa ya miƙawa Baba Habi magungunan ya yi mata bayani. Ya shiga ɗakini inda Khadeeja take kwance ya tsaya a kanta yace ‘Ki daure Habi ta haɗa miki abinci ki ci ki sha magani, shi ne za ki ji daɗin jikinki. Kin ga waɗannan magungunan ita Ma’u idan tana sha ko laulayin kirki ba ta yi, haka take ci gaba da harkokinta har ta haihu.’

    ‘Yanzu zan fito ai.’ Ya yi mata sallama ya tafi office. Indomie ɗin dai Baba Habi ta dafa mata sannan ta shiga ɗakin ta taso ta, ta sha maganin ta ɗan ci abinci sannan ta koma ta sake kwanciya. Kafin Habi ta ɗauko yara daga makaranta ta ɗan ji ƙwari, zuwa dare rashin ƙwarin jikin ya ragu don da kanta ta lallaɓa ta yi musu tuwo miyar kuka. Kwana biyu laulayin ya yi wa Khadeeja sauƙi don tana dagewa tana shirya yara makaranta kuma tana shiga kitchen ta yi abinci da taimakon Baba Habi.

    Ranar laraba suna zaune a parlor da magriba ita da yara da Abbansu; tana zaune a tsakiyarsu tana yi musu homework yayin da shi kuma Abbansu yake zaune a kan kujera yana ta faman danna waya yana kuma kallon labarai a BBC. Baba Habi ta fito daga dakin yara da sallama, bayan Khadeeja ta amsa sallamarta ta tsuguna daga gefe ta dubi Khadeeja tace ‘Uwar dakina ina so zuwa gida gobe, na ji an ce za a kulle garin. Zan je na dubo yarana idan na kwana ɗaya sai na dawo kafin a rufe garin.’

    Abbansu ya ɗago kansa daga kallon wayar yace ‘Baba ai da kin bari mu ga abinda hali zai yi tunda kin ga ita ma Khadeejan ba ta da lafiya.’ Ta juya Kai ‘To ai Yallaɓai kafin a kulle garin, na baro yara gara na je na dubo tunda ana maganar idan an rufe garin za a yi watanni kafin a buɗe.’

    Kafin ya yi magana Khadeeja ta dube shi tace ‘Ka bari ta je ai na ɗan ji sauƙi, gara ta je ta dawo kafin a rufe garin ga azumi ma yana tahowa.’ ‘Haka ne.’ Ya amsa ya cigaba da abinda yake yi.

    Gari yana wayewa bayan ya dawo daga kai yara makaranta ya ba wa Baba Habi kuɗin mota Khadeeja kuma ta haɗa mata abin da za ta ba ta ta kama hanya a kan jibi za ta dawo.A ranar da daddare aka sanar da total lockdown a Nigeria, an hana duk wata zirga zirga sai dai kowa ya zauna a gida a ga abinda hali zai yi.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Gizo Da Namun Daji

    Tatsuniyar Gizo Da Namun Daji

    Ga ta nan ga ta nan ku

    Gizo ne dai yana son ya ci nama, amma ba shi da shi. Ya rasa yadda zai yi. Sannan ya ce a ransa, “Bari dai in yi wata dabara”. Sai ya sayo goro ya rarraba wa namun daji da tsuntsayen gida. Sai ya fara kai wa kaza, ya ce, “Ga shi, goron wasa ne wanda za a yi a cikin daji, naki ne wannan” .

    Sai kaza ta ce, “To. Amma fa kada ka kai wa muzuru”. Sai ya ce, “Haba, me zai sa in kai masa?” Da gizo ya fita, sai ya shiga gidan muzuru, ya kai masa goro. Sai shi ma muzurun ya ce, “To, amma kada ka kai wa kare”. Sai gizo ya ce, “Haba me zai sa in kai masa?”

    Da dai gizo ya fita, sai ya shiga gidan kare ya ba shi nasa goron. Kare ya ce, “To, amma fa kada ka kai wa kura”. ‘Gizo ya ce, “Haba me zai sa in kai mata?” Da ya fita, sai ya kai wa kura nata goron. Kura ta ce, “To, amma fa kada ka kai wa Zaki”.

    Ya ce, ‘Haba kura, me zai sa in kai wa Zaki?’

    Shi ke nan, sai ya kai wa Zaki nasa goron, ya ce, “Ranka ya daɗe. Wani ɗan wasa za a yi na kawo maka goro”. Da Zaki ya karɓa, sai ya ce, “To, Allah ya kai mu”. Shi ke nan. Da ya fita, sai ya shiga ya kai wa damisa. Damisa ta ce, “In ce ko dai ba ka kai wa Sarki Zaki ba?”
    Sai Gizo ya ce, ‘Haba, haba. Wane ni da gayyatar Sarki?’ Sai damisa ta ce, ‘To, Allah ya kai mu”.

    Da ya fito sai kuma ya shiga gidan giwa ya kai mata nata goron. Sai giwa ta ce, “To, in ce ko baka kai wa manyan dawa ba?’ Ya ce, “Mhm! Yaya zan kai?” Ko kai masa ne ma ai ke zan bai wa ki kai masa “. Shi ke nan. Ana nan ana nan, sai ranar wasa ta zo. Gizo ya bayyana musu wurin da za su haɗu a yi wasan. Ya ce musu, “To, ku tafi zan same ku. Ni daga baya zan taho tare da makaɗa’. Shi ke nan. Sai kaza ta fara tafiya. Ashe ba su sani ba, gizo ya riga su isa can. Sai kaza ta isa can. Gizo ya yi mata maraba. Ya ce,

    “Shiga wannan bukkar kafin su zo”.

    Shi ke nan. Kaza ta shiga, ta zauna. Daga can sai ga muzuru ya taho. Sai Gizo ya gaya wa muzuru cikin raɗa, ‘Maraba’. Shiga tana nan a ciki’. Shi ke nan sai muzuru ya shiga ya tasar wa kaza zai cinye ta. Ya cinye ta. Can kuma sai ga kare ya taho. Shi ma dai Gizo ya gaya masa kamar yadda ya gaya wa muzuru. Sai shi ma karen ya cinye muzuru.

    Daga nan kuma sai ga kura. Ita ma ya gaya mata kamar yadda ya gaya wa kare da muzuru. Sai kura ta shiga ta cinye kare. Kura kuma tana zaune a cikin rumfa. Sai ga Zaki ya taho. shi ma Gizo ya gaya masa haka. Ya shiga ya cinye kura. Daga nan sai ga giwa da damisa sun jero sun taho. Sai Gizo ya ce, “To, ku shiga nan bukkar mana”. Daga shigar su, sai suka kaure da faɗa tun daga cikin rumfar har suka yiwo waje. Idonsu duk ya rufe, suna ta faɗa. Sai Gizo ya samo ganga, ya soma kiɗa yana waƙa:
    Zaki bari, damisa bari.
    Giwa bari.

    Faɗanku na manya,

    Wa yake shiga?
    Sai wawa, sai mahaukaci.
    Sai ko ni da ba ni da hankali.

    Suna ta faɗa, can da giwa ta ga abin ba dama, sai ta fito ta yi tafiyarta gida, ta bar zaki da damisa suna karawa. Sai Gizo ya ci gaba da yi musu waƙa. Ya yi ta yi, su kuma suna ta faɗa. Ashe Gizo da ma ya zo da yaji a ƙunshe. Sai ya ɗauko yajin nan ya barbaɗa musu a idanunsu. Sai fa faɗa ya rincaɓe, idanunsu suka rufe ruf. Daga can sai Gizo ya ɗauko wuƙa ya ce, “Yan banza. Ana so a ci nama an rasa yadda za a yi”. Sai ya kama yankan naman jikinsu yana tarawa, har ya kashe su duka. Sai ya jide naman ya kai gida aka soya masa, ya ci ya ƙoshi, ya ajiye sauran, yana ci lokaci-lokaci.

    Ƙurunƙus.

    Domin karanta Tatsuniyar Ɗankaɗafi danna nan.

    Domin karanta Tatsuniyar Gizo Da Giwa danna nan.

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Gizo Da Giwa

    Tatsuniyar Gizo Da Giwa

    Ga ta nan ga ta nan ku

    Tatsuniya! Tatsuniya!! Tatsuniyar!!!

    Tatsuniya! Wani mutum ne dai ya ba wani malami kuɗi don a yi masa asiri. Sai malamin ya ce, “Sai an samo hauren giwa domin ya haɗa maganin da shi”.

    Sai mutumin ya je cikin jama’a ya ce, “Wa zai iya samo min hauren giwa in ba shi kuɗi?’

    Aka rasa wanda zai iya.
    Sai Gizo ya ce, “Shi zai iya”.
    Sai mutumin ya ce, “To shi ke nan, sai ka samo ka kawo”.

    Shi ke nan, sai Gizo ya tafi gida, ya daka nakiya mai zaƙin gaske. Sai ya je gidan giwa da ɗan ƙunshin nakiyar a hannunsa, ya ce, “Gafaya dai masu gida”.
    Sai giwa ta ce, “Maraba da Gizo”.
    Ya ce, “Yauwa, Wata nakiya ce na kawo miki da na samo a pa”.
    Shi ke nan sai giwa ta ce, “To”.

    Ta gutsiri nakiya ta kai bakinta. Da ta ji zaƙin nakiyar, sai ta ce, “Don Allah Gizo, ni ma ka raka ni in je in samo?”
    Sai ya ce, “Haba yaya! Me zai hana in raka ki? Ki zo gobe in kai ki”.
    Shi ke nan, sai ta zo washegari, suka je wajen kan pa. Sai ya ce da ita, “Idan kika doka bakinki sau ɗaya, kika doka sau biyu, a na ukun sai ki ga nakiya ruɓus a bakinki”.

    Shi ke nan, sai giwa ta doka bakinta sau ɗaya fas a kan pa. Ta kuma dokawa. Da ta doka na ukun, sai haƙorinta ya ɓalle ya faɗo ƙasa.
    Sai jini shar.
    Sai Gizo ya ce, “Assha, assha! Yaya aka yi haka kuma?” Ya yi maza ya ɗauki haƙorin giwar, ya sa a aljihunsa. Ita ba ta gani ba. Tana ta kanta.
    Shi ke nan sai gizo ya bar giwa a nan. Ya yi sauri ya kai wa mutumin nan haƙorin.

    Mutumin ya ba shi ladansa.

    Sai gizo ya je daji ya tattara namun daji, suka je gidan da giwa take a kwance, suka tarar kanta ya kumbura, suntum.

    Gizo ya gaya wa namun dajin cewa, “In na ce, “Babbanmu da giɓi”, ku ce, Ɓurum ɓaɓurka”.
    Sai ya fara waƙar:
    Babbanmu da giɓi,
    Sai suka amsa:
    Ɓurum ɓaɓurka.
    Shi ke nan sai suka gama, suka koma. Gizo ya bar giwa a wahala, shi kuwa ya karɓe kuɗinsa.
    Shi ke nan.
    Ƙurunƙus.

    Domin karanta Tatsuniyar Yarinya Da Dodanni danna nan

    Domin karanta Hausawa Da Al’adunsu danna nan

  • Tatsuniyar Yarinya Da Dodanni

    Tatsuniyar Yarinya Da Dodanni

    Ga ta nan ga ta nan ku.

    Tatsuniya : Wata yarinya ce dai mai tsananin kyau, duk garinsu babu mai kyanta, ta ce ba ta son kowa sai marar tabo. Sai dodanni suka ji labari.

    Sai suka yi wanka a gidan tururuwa. sai suka zama samari kyawawa da su.
    Da ta gan su, sai ta ce, “Ta sami mazajen aure”. sai duk ta duba jikinsu, sai ta ga jikin wannan da ɗan tabo ɗan mitsitsi, sai ta ce, “Ba ta son sa”. Da ta duba jikin ɗayan ta gan shi sumul, ba ko ɗigon tabo a jikinsa, sai ta ce, “Shi take so”.
    Shi ke nan, sai aka shirya aka yi biki.

    Sai suka ce, “Za su tafi da ita garinsu, su ba mazauna ba ne”, sai aka ce; “To za a ba ta ƙanwarta ta taya ta zaman ɗaki”. Sai ta ce, “Ita ba ta so, ta zauna ita kaɗai”. Shi ke nan, aka yi aka yi su tafi da ƙanwarta ta ƙi; sai ƙanwar ta zama ƙuda ta maƙale mata.

    Shi ke nan, da suka je gidan dodanni; sai dare ya yi suka shiga ɗaka suka rufe ƙofa, sai ta ga ƙanwarta, sai ta rufe ta da faɗa, ta ce, “Ke wa ya kawo ki nan?”

    Ita kuwa ƙanwar sai ta yi shiru.
    Shi ke nan sai yar ta ƙyale ta.
    Ita yar kamar sokuwa take. In dare ya yi, sai ta yi ta shirgar barci. Ita kuwa ƙanwar, sai ta zauna tangar har gari ya waye.

    Sai uwar mijinta ta zo da tsakar dare ta ce:
    “Sarma-sarma duf-duf”.
    Sai ƙanwar ta ce:
    “Wane ne nan ya ke mana
    Sarma-sarma duf-duf?”
    Sai uwar mijin ta ce:
    “Uwar miji ce take muku
    Sarma-Sarma duf-duf”.
    Sai yarinya ta ce:
    “Me kike so kike mana
    Sarma-sarma duf-duf?”
    Sai ta ce:”Wuta nake so nake muku
    Sarma-sarma duf-duf”.
    Sai yarinya ta ce:
    “Iya ga wuta nan.
    Ki bar mana
    Sarma-sarma duf-duf”

    Sannan yarinya ta watso mata wutar. Tsohuwa ta je ta kashe wutar ta kuma dawo musu. Nan kuwa ashe ba wuta take so ba. So take yi ta cinye su idan ta tarar sun yi barci.
    Kullun haka, kullum haka. Duk sa’ad da yarinyar ta gaya wa yayarta game da uwar mijin mai zuwa ɗiban wuta da daddare, sai yayar ta ce, “Ƙarya take yi”.
    Ana nan a haka sai, ran nan yarinya ta ce da yayarta, “To, yau dai ki zauna kada ki yi barci don ki ji yadda muke yi da tsohuwar da kunnenki”.

    Shi ke nan, yayar ta zauna.
    Sai ita uwar mijin ta zo ta yi musu irin yadda take yi kullum.
    Shi ke nan, sai ya ta ji da kunnenta.
    Shi kuma mijin nata yana wani ɗaki suna kwance tare da abokansa. Idan an yi abinci na aikin gona an kai musu, sai su yi haƙa su bunne. Sai su yi ta cin kwaɗi. Ita kuwa ƙanwar, wadda ta kai musu abincin, sai ta ce da su:
    Mijin yayata, ci kwaɗi.
    Mijin yayata, ci kwaɗi.
    Mazan-wazata, ci kwaɗi
    Sha da kwaɗi, ci kwaɗi
    Sha da kwaɗi, ci kwaɗi.

    Su kuma idan sun ji wannan waƙar, sai su yi ta rawa suna cin kwaɗi.
    Shi ke nan. Da sun ga ƙanwar ta dawo daga gida, sai su zama mutane su ce, “Ga kwanukanki nan. ki ce muna yi mata sannu da aiki”.
    Shi ke nan, sai yarinya ta ɗebi kwanuka ta tafi da su gida.
    Kullum haka, kullum haka.
    Sai rannan yayar ta yi shawara da ƙanwarta don su gudu gida.
    Sai suka yi ta haƙa rami, tun daga nan gidan har ya zuwa hanyar ƙofar garinsu. Suna ta bin rami da ita da ƙanwarta har suka je gida.
    Iyayenta suka ce da ita, “Lafiya?”.
    Sai ta ce wa iyayenta, “Ashe dodanni ne? Ni zato nake mutane ne”.
    Shi ke nan.
    Ƙurunƙus kan ɗan ɓera.
    Ba don ƙarya ce ba, wa zai zuba ruwa a jallo, jallo ya fashe kuma ruwan bai zube ba?

    Domin karanta tasuniyar gizo da giwa danna nan

    Domin karanta bayani akan Ra’in Bincike Hausawa danna nan