Tag: Fassara

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Huɗubar Juma’a daga Masallaci mai alfarma:21 Safar 1447
    15 August 2025
    Mai huɗuba: Sheikh Dr. Bandar bin Abdul-Aziz Badila
    Mai fassara: Dr. Usman Muhammad Ahmad
    Shugaban sashi: Dr. Abdulkarim Tahir Abdullahi

    Huɗuba ta farko:
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Ya halicci halittu kuma Ya ƙaddara ƙaddarori, Ya rarraba arziki kuma Ya rubuta ajali, muna yaba masa tsarki ya tabbata a gare Shi kuma muna gode masa, Ya fari halittar rayuwa kuma Ya gudanar da ƙoramu, Ya shimfiɗa ƙasa kuma Ya tsaga tekuna.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Ya hore rana da wata, da dare da yini. Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa, kuma zaɓaɓɓen Annabinsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da alayensa tsarkaka, da sahabbansa nagartattu, da waɗanda suka biyo su da kyautatawa a dukkan darare da yini.

    Bayan haka:
    Ya ku mutane! Ina muku wasici da ni kaina da tsoron Allah, ku ji tsoron Allah, Allah Ya muku rahama, kuma ku sani cewa babu abin da ke faruwa a cikin wannan rayuwa face sai da ƙaddarar Allah da kuma nufinsa, da hikimarsa da iradarsa; na dare da yini, da iska da ruwan sama, da sanyi mai tsanani da zafi, da sauye-sauyen yanayi da maimaituwarsa, abin da zai sa mumini ya tabbatar da cewa wannan duniya ba gidan dawwama ba ce.

    Kuma wannan gaba ɗayansa yana daga cikin ayoyin Allah na halitta masu nuna girman ƙarfinsa da ikonsa, da yalwar iliminsa da hikimarsa, da zurfin nufinsa da rahamarsa, da kuma cewa kowane abu a wurinsa tsarki ya tabbata a gare Shi yana da iyaka.
    ((Lallai a cikin halittar sammai da ƙasa da sassaɓawar dare da rana, tabbas akwai ayoyi ga ma’abota hankula Su ne waɗanda suke ambaton Allah a tsaye da kuma zaune da kuma kishingiɗe, suna kuma tunani a kan halittar sammai da ƙasa (suna cewa: “Ya Ubangijinmu, ba Ka halicci wannan a banza ba, tsarki ya tabbata gare Ka, Ka tsare mu daga azabar wuta)).

    Ya ku bayin Allah!
    Waye a cikinmu da zafin rani bai taɓa cutar da shi ba? Kuma waye a cikinmu da ƙunar rana ba ta taɓa ƙona fuskarsa ba? Dukanmu mun samu rabonmu daga wannan, ko dai kaɗan ko ko dayawa, lallai wannan shi ne zafin rani, mai wa’azin nan da Allah Yake tunatar da bayinsa zafin taron alƙiyama da azabar wuta da shi.

    An rawaito daga Miƙdad ɗan Aswad Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: (Za a kusanto da rana ga halittu a ranar alƙiyama har ta kasance kamar tazarar mil daga gare su). Sulaim ɗan ‘Amir ya ce: Na rantse da Allah ban san me yake nufi da mil ba, yana nufin na tazarar ƙasa, ko ko mil da ake amfani da shi wajen sanya kwalli a ido? Ya ce: (Sai mutane su kasance cikin zufa gwargwadon ayyukansu; daga cikinsu akwai wanda zufa za ta kai masa idanuwan sawu, akwai kuma wanda za ta kai masa gwiwoyi, akwai wanda za ta kai masa zuwa ga kwuiɓinsa, akwai kuma wanda zufa za ta yi wa bakinsa linzami sosai). Sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi nuni zuwa ga bakinsa da hannunsa. Muslim ne ya rawaito shi.

    Ya ku musulmi!
    Lallai tsananin zafi yana daga cikin ayoyin da Allah yake aiko wa bayinsa don tsoratarwa da tunatarwa, da zama wa’azi da ɗaukan izina, kamar yadda Allah Ya ce: ((Kuma ba Ma aiko da ayoyi sai don tsoratarwa)).

    An rawaito aga Abu Huraira Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Wuta ta kai kokenta ga Ubangijinta, ta ce: Ya Ubangiji, sashina na cin sashi, sai Ya ba ta izinin numfasawa sau biyu; numfasawa a lokacin sanyi, da numfasawa a lokacin zafi, to wannan shi ne mafi tsananin zafin da kuke ji a lokacin rani, da kuma mafi tsananin sanyi da kuke ji a lokacin hunturu). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

    To, ya ku muminai! Mai rabo, shi ne wanda ya yi guzuri daga zafin duniya domin kuɓuta daga zafin lahira, da kuma wanda ya yi haƙuri da ibada a lokacin tsananin zafi, domin ya more ni’imar da ba ta ƙarewa a ranar da za a tona ɓoyayyun sirrikan zukata.
    ((Ya ku waɗanda kuka yi imani, ku kare kanku da iyalanku daga wuta, wacce makamashinta mutane ne da duwatsu, masu kula da ita mala’iku ne masu kaushin hali, masu tsananin gaske, ba sa saɓa wa Allah abin da Ya umarce su, kuma suna aikata abin da aka umarce su da aikata shi)).

    An rawaito daga Abu Sa’id Alkhudri Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: (Duk wanda ya yi azumin yini ɗaya saboda Allah, Allah zai nesanta fuskarsa daga wuta na tsawon shekara saba’in). Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.

    Kuma Abu Darda Allah ya ƙara masa yarda ya kasance yana cewa: “Ku azumci yini mai tsananin zafin rana saboda kuɓuta daga zafin ranar tashin alƙiyama, kuma ku yi raka’a biyu cikin duhun dare saboda ku kuɓuta daga duhun ƙaburbura”. Abu Nu’aim ne ya rawaito shi a Hilya.

    Kuma ku sani Allah Ya jiƙan ku cewa dukkan abin da zai samu mumini a cikin zafi na tsanani da wahala, da gajiya da ƙosawa, to, dukkansu za a rubuta su, za a kiyaye su kuma za a ƙididdige su, a wajen Wanda ayyukan ƙwarai ba sa tozarta a wajensa, kuma ba a rasa ayyukan ɗa’a a wajensa, da su za a kankare zunubai, kuma a ninka kyawawa, kuma a ɗaga darajoji.

    An rawaito daga Abu Sa’id da Abu Huraira Allah Ya ƙara musu yarda, sun ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Babu wani abu da zai samu musulmi, na ciwo, ko wahala, ko jinya, ko bakin ciki, har ma da damuwa da za ta sauko masa, face sai an kankare masa zunubansa da shi). Muslim ne ya rawaito shi.

    Kuma lallai ayyuka ana ninninka ladansu, kuma ana ƙara sakamakonsu, kuma ma’auninsu na nauyaya, da gwargwadon abin da ya tabbata na niyya da ikhlasi da juriya da haƙuri a zukatan ma’abotansu. Ibnul Asir Allah Ya yi masa rahama ya ce: “Kuma neman lada a cikin ayyuka nagartattu da kuma lokacin da ake ƙi, shi ne gaugawa zuwa ga neman lada da kuma samun sa ta hanyar miƙa wuya da haƙuri”. Ƙarshen maganarsa kenan.

    Kuma yana daga cikin rahamar Allah ga bayinsa shar’anta musu abin da za su iya yi na ayyuka da ya yi, kuma bai ɗaura musu abin da zai wahalar da su ba, an rawaito daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda, daga Annabi tsirda da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Idan zafi ya tsananta, to ku sanyaya sallarku, saboda tsananin zafi daga hucin Jahannama yake). Bukhari da Muslim ne suka rawaito. Abin da ake nufi da sanyaya salla, shi ne jinkirta ta zuwa ƙarshen lokacinta, lokacin da zafin garji zai yi sauƙi, kafin shigar lokacin sallar da za ta biyo bayanta.

    Kuma za a gwama dukkan wata ibada da ke cikin jinsinta da ita, cikin abin da ya halatta a jinkirta shi, don haka, duk wanda ake bin shi azumi na watan Ramadan, ko kuma kaffara ta azumi ko makamancin haka, to, ya halatta a gare shi ya jinkirta shi zuwa ga lokutan sanyi, idan biyansa a lokacin zafi zai ba shi wahala, akwai hadisin A’isha Allah Ya ƙara mata yarda da yake nuni a kan haka, ta ce: “a kan samu wani lokaci da ake bi na azumi da na sha tun a watan Ramadan, amma na kasa samun daman biya sai a watan Sha’aban”. Bukhari da Muslim ne suka rawaito. Amma gaggauta biya shi ya fi,

    Don haka, ya ku bayin Allah!
    Ku gode wa Allah a bisa dukkan hali da yanayi, kuma ku gade masa a kan abin da Ya tanada muku na hanyoyi da sabuba, waɗanda Ya sauƙaƙe muku wahalar zafi da tsananinsa da su, da ƙunarsa da hucinsa, da na’urorin sanyayawa da wuraren hutu a lokacin zafin rani, kuma ku riƙa bincikan halin ‘yan uwanku talakawa da marasa abin hannu, kuma ku sauƙaƙa musu abin da suke fama da shi na tsananin zafi da ƙunar rana, kowa ya yi dai dai ƙarfinsa da ikonsa, kuma daga cikin haka akwai shayar da ruwa mai sanyi a waɗannan lokuta na zafi, saboda hakan yana daga cikin sadokoki mafiya falala, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ba mu labarin hakan.

    Kuma ku riƙa tunawa da wasu ‘yan’uwanku a Addini, waɗanda raɗaɗin rashi da tawaya ta dukiya da rayuka da ‘ya’yan itacuwa suka ƙaru a gare su a kan abin da suke fama da shi na tsananin zafi, ya Allah Ka yaye musu abin da ya sauko musu, ya Allah Ka sauya tsoronsu da aminci, biƙin cikinsu da farin ciki, yunwarsu da ƙoshi, kuma Ka taimake su a kan maƙiyanka kuma maƙiyansu ya Mai ƙarfi ya Mabuwayi.

    Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina nema wa kaina gafarar Allah, da ku da sauran musulmi, daga kowane zunubi, don haka ku nemi gafararsa, lallai Shi Mai yawan gafara ne kuma Mai jinƙai.

    Huɗuba ta biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda dukkan al’amura suke samuwa daga aikinsa da nufinsa, muna yaba masa tsarki ya tabbata a gare Shi kuma muna gode masa a bisa falalarsa mai yalwa da ni’imominsa, da kyakkyawar afuwarsa da gafararsa, tsira da amincin Allah su ƙara tabbata ga mafificin Manzanninsa kuma zaɓɓaɓensa, da alayensa, da sahabbansa da tabi’ai, da waɗanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar rarrabewa da tashin alƙiyama.

    Bayan haka: Ku sani, Allah Ya muku rahama, cewa lallai bayyana fushi da raki don tsananin zafi yana daga cikin suka ga hukuncin Allah da ƙaddararsa, da nufinsa da ganin damansa, da kuma cewa lallai babu abin da zai auku a wannan duniya face sai da wata hikima da maslaha da fa’ida da amfani, daga cikin haka akwai yadda muke ganin dayawa daga cikin shukoki da ‘ya’yan itatuwa ba sa yin daɗi kuma ba sa daidaituwa har sai lokacin da rani ya kai maƙurarsa, haka kuma dayawa daga cikin cututtuka da annoba ba sa ɓacewa har sai lokacin da zafi ya kai ƙololuwar matakinsa, Ibnul Ƙayyim Allah Ya masa rahama ya ce:

    “A lokacin rani, iska na rikiɗewa ta yi zafi sosai, sai ‘ya’yan itatuwa su nuna, kuma sauran ababe marasa amfani da ababen da suka cakuɗu da jiki su gushe a lokacin hunturu, kuma sai sanyi ya kutsa ya shiga cikkuna, don haka ne ma maramaren ruwa da rijiyoyi suke yin sanyi”. Ƙarshen maganarsa kenan.

    Saboda haka, ku ji tsoron Allah, ya ku bayin Allah, kuma ku kiyaye zukatanku da harsunanku daga dukkan abin da zai rage imaninku, ya lalata tauhidinku, domin yana daga cikin cikar tauhidi yarda da kuma miƙa wuya ga dokokin Allah na shari’a da tsarinsa na gudanar da duniya.

    Sannan ku yi salati da sallama ga mafi alherin halittun Allah, Muhammadu bin Abdullahi, domin Ubangijinku Ya umarce ku da hakan, sai Ya ce: ((Lallai Allah da mala’ikunsa suna salati ga Annabi; ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah, Ka yi salati da sallama, da ƙarin daraja da albarka ga bawanka kuma ManzonKa, Annabinmu Muhammadu, kuma ka ƙara yarda da sahabbai baki ɗaya, da tabi’ai, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
    Ya Allah, ka ɗaukaka Musulunci da Musulmai, Ka kiyaye shingen addini, Ka taimaki bayinka muminai masu tauhidi.

    Ya Allah, ka yaye damuwar masu damuwa daga cikin musulmai, ka kwaranye baƙin cikin masu baƙin ciki, Ka biya bashin wadanda ake bi bashi, Ka warkar da marasa lafiya daga cikinmu da na sauran musulmai.

    Ya Allah Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu kuma jagororinmu, Ka ƙarfafi Shugabanmu kuma jagoranmu Hadimin Masallatai Biyu Masu alfarma da gaskiya da dace da gamonkatar, Ya Allah, ka tsawaita rayuwarsa cikin waraka da ƙoshin lafiya, da ni’ima mai yalwa kuma cikakkiya, kuma Ka datar da shi da magajinsa amintacce ga abin da alheri ne ga ƙasa da mutane, da ɗaukaka ga Musulunci da musulmi ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka kasance Mai ƙarfafawa da kawo ɗauki da agazawa da taimako ga ’yan’uwanmu masu rauni, ya Allah, Ka taimake su a ƙasar Falasɗinu a kan yahudawa ‘yan ƙwace, ya Allah, Ka ƙididdige adadin yahudawa, Ka halaka su ɗaya bayan ɗaya, kuma kada Ka bar ko ɗaya daga cikinsu.

    Ya Allah Ka kiyaye dakarunmu masu dako a kan iyakoki da fagage, Ya Allah, Ka kiyaye su da idonka da ba ya barci, Ka tsare su da ƙarfinka da ba a iya rinjayarsa ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka azurta mu da haƙuri akan jarrabawa, da yarda da ƙaddara, da godiya a lokacin yalwa, kada Ka ɗora mana abin da ya fi ƙarfinmu, domin aminci daga gare Ka shi ya fi yalwa a gare mu ya Mafi tausayin masu tausayi.

    Ya Allah Ka tsare mu daga azabarka a ranar da Za Ka tashi bayinka, ya Allah Ka tsare mu daga azabarka a ranar da Za Ka tashi bayinka.
    ((Ubangijinmu, Ka ba mu alheri a duniya, da alheri a lahira, kuma Ka tsare mu daga azabar wuta))
    ((Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin buya daga abin da suke sifantaShi da shi () Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni () Kuma dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai)).

    Karanta Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya 1st August 2025

    Edita@rumasau-kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 7th March 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 7th March 2025

    1. Mai Huɗuba: Sheikh Dr Abdullahi Bin Awwad Aljuhani

    Mai Fassara: Dr Usman Muhammad Ahmad

    Shugaban Shashi: Dr Abdurrahman Muhammad Sani Yakubu

    Huɗuba Ta Farko

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Mai yawan baiwa, Mai yalwar falala da kyautatawa, Ya wajabta azumin watan Ramadana ga bayinSa Muminai. Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Majiɓincin masu taƙawa da bayinSa nagartattu, Ya karrama al’ummar Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah masu yawa su tabbata a gare shi da watan Ramadana.

    Kuma ina shaidawa lallai Shugabanmu kuma Annabinmu Muhammadu BawanSa ne kuma ManzonSa, Mafi alherin wanda ya yi Salla da azumi, kuma ya yi ɗawafi a ɗakin Allah, daɗin tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da Sahabbansa, taurarin shiriya kuma fitulu a cikin duhun ɓata.

    Bayan haka:

    Ina muku wasici da kiyaye dokokin Allah Maɗaukakin Sarki, da Masa biyayya a kowane waje da lokaci, kuma ku sani cewa ɗan ƙanƙanin aiki da yawa yake a wajen Allah idan ya haɗu da tsoron Allah Maɗaukakin Sarki, mai yawansa kuma ɗan kaɗan ne idan bai haɗu da tsoron Allah ba, kuma ku yi riƙo da rukunen Addini da rassan Imani, saboda ba za ku tsira ko ku rabauta a cikin rayuwarku da mutuwarku ba sai da jin tsoron Allah Maɗaukakin Sarki da Imani da Shi.

    Kuma ku yi Amfani da damar da kuke da ita a cikin wannan rayuwa kafin ta kuɓuce muku, sannan ku yi rigegeniya izuwa ga ayyukan ɗa’a, saboda ku fa kuna cikin mafi ɗaukakan lokutansu ne. Shi mutum a wannan rayuwa ta duniya ba za a ba shi rayuwa da ba ta ƙarewa ba, kuma ba zai wanzu ba, bari dai, shi samamme ne daga babu, kuma mutuwa ita ce ƙarshensa, kuma lallai lokuta da suke gittawa ga mutum a wannan rayuwar duniya kamar ƙiftawar ido suke, ƙiftawa bayan ƙiftawa, haka mutum zai ta rayuwa har zuwa lokacin da zai isa zuwa ƙarshen rayuwarsa, kuma wannan lamari ne da kowane ɗaya daga cikinmu yake ji a jikinsa.

    Kuma a kodayaushe mu riƙa tuna ‘yan uwanmu da suka kasance tare da mu a shekarar bara, suna jiran watan Ramadana watan alheri da albarka, amma sai dai ajalinsu ya cimmu su, kuma ayyukansu sun yanke, sai suka samu kansu a cikin wasu ramuka na ƙasa da babu komi tare da su a cikinsa face ayyukansu, kuma ba su bar wa kawunansu komi a bayansu ba face wata sadaka mai gudana, ko wani ilimi da ake amfanuwa da shi, ko wani ɗa nagari da yake musu addu’a, kuma mu masu tafiya ne izuwa ga wajen da suka tafi.

    Kamar haka ne kuma zamani ya juyo, kuma watan Ramadana ya dawo a wannan shekara, ya dawo bayan mun yi mantuwa mai yawa, bayan mun kutsa muna masu ninƙaya a cikin al’amuran duniyarmu ninƙaya mai zurfi, to, watan Ramadana ya dawo, kuma muma an ƙaddara mana dawowa tare da shi don mu shaida kwanakinsa masu haske kuma mu raya dararensa masu ƙyalli.

    Ya ku Musulmi!

    Lallai yana daga cikin mafiya girman ni’imomin Allah Maɗaukakin Sarki a kan bayinSa Muminai, ni’ima da Ya yi musu a cikin waɗannan kwanaki na riskar wani lokaci cikin lokutan alhairai, wanda shi ne watan Ramadan, ma’abocin rahama da albarkatu, watan da masu azumi suke farin ciki a cikinsa, kuma masu aiki suke samun riba a wajen Allah, watan da ake ruɓanya ladan farillai a cikinsa sama da ladan farillai a waninsa, watan da nafilolinsa kamar farillai suke a wani wata da ba shi ba, watan kyauta da sadaka, watan da ake yafe kurakurai a cikinsa, kuma ake kankare zunubai, Allah ya wajabta mana azumtar sa, shi kuma Manzon Allah tsira da amincin Alah su tabbata a gare shi ya sunnanta mana tsayuwa a dararensa.

    Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana albishir wa Sahabbansa yana cewa: (Watan Ramadana ya zo muku, watan albarka, Allah Yana saukar da rahama a cikinsa, kuma Yana yafe laifuka, Yana amsa addu’a, kuma Allah Yana alfahari da ku ga Mala’ikunSa, don haka ku bayyana wa Allah alheri daga gare ku; saboda taɓaɓɓe shi ne wanda aka haramta masa rahamar Allah a wannan wata). Haisami ya dangana shi ga Ɗabarani a littafin Maj’ma’uzzawa’id.

    Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Idan watan Ramadana ya shigo ana buɗe ƙofofin Aljanna, kuma ana rufe ƙofofin wuta, sannan kuma ana ɗaure shaiɗanu). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

    Haƙiƙa yana daga cikin shiriyar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi wanda shi ne mafi cikar shiriya, Yawaita mabanbantan ibadu, haƙiƙa ya kasance ya fi kowa yawaita kyauta a cikin mutane, kuma yafi yawaita kyauta a watan Ramadana, yana yawan sadaka a cikinsa, da kyautatawa, da karatun Alƙur’ani, da zikiri, da i’itikafi, kuma ya kwaɗaitar a kan yin Umara a watan Ramadana.

    Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce wa wata mata cikin Mutanen Madina: (Me ya hana ki yin aikin Hajji tare da mu?), sai ta ce: “Mun kasance muna da wani raƙumi mai bayin ruwa, sai baban wane da ɗansa- wato mijinta da ɗanta- sai ya bar wani raƙumin muna bayi da shi”, sai ya ce: (To, yin Umara a watan Ramadana kamar aikin Hajji ne tare da ni). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

    Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana keɓance watan Ramadana da wasu ibadu da ba ya keɓance sauran watanni da su, don haka ku gode wa Allah a bisa ni’imar riskarsa, kuma ku gode Masa ta hanyar ƙara himma da ƙoƙari da raya lokutansa da ayyukan ɗa’a mabanbanta, kuma ku fuskance shi ta hanyar kiyaye shi daga kurakurai da laifuka, Allah Ya muku rahama.

    Waɗannan lokuta ne masu falala, ina masu amfana da su? Waɗannan lokuta ne na kasuwanci mai ba da riba, to, ina masu nema?

    Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce: (Dukkan ayyukan ɗan Adam nasa ne, Sai dai azumi, domin shi Nawa ne, kuma Ni ne zan ba da sakamakonsa, Azumi garkuwa ne, idan ya zama ɗayanku na azumi a wani yini, to, kada ya yi yasasshen zance, kuma kada ya yi hayaniya, idan wani ya zage shi ko ya nemi yin faɗa da shi, to, ya ce: Ni ina azumi. Ina rantsuwa da Wanda ran Muhammadu ke hannunSa, warin bakin mai azumi ya fi ƙamshi a wajen Allah fiye da ƙamshin almiski. Mai azumi yana da farin ciki guda biyu da zai yi, idan ya sha ruwa zai yi farin ciki, haka kuma idan ya haɗu da Ubangijinsa zai yi farin ciki da azuminsa).

    Allah Ya taimake ni tare da ku a kan azumtar sa da tsayuwa a dararensa muna masu Imani da fatan samun lada, kuma Ya gafarta mana kurakurai gaba ɗaya, Ya suturce mana dukkan laifuka, kuma Ya mana yafiya a ranar tambaya da hisabi.

    A’uzu billahi minash-shaiɗanir-rajim. Bismillahir-Rahmanir- Rahim: (Ya ku waɗanda kuka yi Imani an wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabta wa waɗanda suka shuɗe gabaninku don ku samu taƙawa).

    (Waɗansu kwanaki ne ƙididdigaggu. To duk wanda ya kasance marar lafiya a cikinku ko yake halin tafiya, to, (idan ya sha azumi) sai ya rama a waɗansu kwanakin na daban. Kuma waɗanda za su yi azumi da wahala su ba da fansa ta ciyar da miskini; to, duk wanda ya ƙara (a kan abincin miskini), to hakan alheri ne gare shi, amma ku yi azumin shi ne ya fi muku alheri, in har kun kasance kun sani).

    Domin Karanta Shakku a Cikin Sallah danna nan

    (Watan Ramadana shi ne wanda aka saukar da Alƙur’ani a cikinsa, shiriya ne ga mutane kuma ayoyi ne bayyanannu na shiriya, kuma mai rarrabewa. Don haka, duk wanda ya riski wannan wata daga cikinku, to, ya azumce shi, kuma wanda ya kasance marar lafiya ko yake halin wata tafiya, to, (idan ya sha azumi) sai ya rama a wasu kwanakin na daban. Allah yana nufin sauƙi a gare ku, Kuma baya nufin tsanani a gare ku, don ku cika adadin (Kwanakin Ramadana), kuma domin ku girmama Allah bisa ga shiryar da ku da Ya yi, don ku yi godiya).

    Allah Ya albarkace mu da Alkur’ani, kuma Ya amfanar da mu da abin da yake cikinsa na bayani. Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah Mai girma gare ni tare da ku da dukkan Musulmi daga dukkan zunubi, don haka, ku nemi gafararSa, lallai Shi ne Mai yawan gafara, Mai jinƙai.

    Huɗuba Ta Biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda Ya lulluɓe zukatan bayinSa da ni’imominSa, kuma Ya raya zukatansu da hasken Addini da hukunce-hukuncensa, kuma Ya musu wasici da riƙo da abin da Ya shar’anta musu daga hikimarSa da hukunce-hukuncenSa.

    Ina shaidawa lallai babu abin bautawa bisa cancanta sai Allah Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya a zatinSa da siffofinSa da aikinSa. Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa, Ya aiko shi ga dukkan mutane don Ya rinjayar da shi a kan dukkan addinai. Tsira da aminci su tabbata a gare shi da Alayensa da Sahabbansa masu riƙo da igiyarsa.

    Bayan haka:

    Ina yi mana wasiyya da jin tsoron Allah, da yin gaggawa wajen neman gafarar Allah da kuma neman Aljanna wadda faɗinta yake daidai da sammai da ƙasa, wadda aka tanade ta ga masu taƙawa.

    Kuma ku sani cewa watanmu mai albarka, watan falala da alheri, kuma lokacin ayyukan ibada da kyawawan ayyuka, wasu ranaku sun shuɗe daga cikinsa, kuma kwanakinsa suna ci gaba da tafiya, kuma nan ba da daɗewa ba za su ƙare. Marabauci a cikinsa shi ne wanda ya yi tunani cikin lamarinsa, ya yi takatsan-tsan, kuma ya yi amfani da wannan damar kafin ta wuce, kuma ya ribaci falalar Ubangijinsa Ma’abocin kyauta da karamci da kyautatawa.

    Saboda haka, ku yawaita karatun Alƙur’ani, da ciyar da abinci, da sadaka ga talakawa da marayu, kuma ku kiyaye gaɓɓanku daga aikata laifuka da zunubai a cikinsa. Kuma ku yawaita salati da sallama ga Shugaban halittu kuma cikakken haske. ((Lallai Allah da Mala’ikunSa suna yi wa Annabi salati. Ya ku waɗanda kuka yi Imani! Ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah Ka yi salati da salama ga Shugaban dukkan halittu, Shugabanmu kuma Annabinmu Muhammadu, da Alayensa nagartattu tsarkaka, da Sahabbansa masu haske da albarka, amintattu a kan da’awarsa, kuma komondojin rundunarsa, waɗanda duk wanda ya roƙa musu rahama, kuma ya yi musu addu’a, sannan babu ƙiyayyarsu a cikin zuciyarsa, to lallai shi ne wanda Allah Maɗaukaki ya nufa da faɗinSa:

    (Waɗanda suka zo bayansu suna cewa: “Ya Ubangijinmu Ka gafarta mana mu da ‘yan’uwanmu waɗanda suka riga mu yin Imani, kuma kada ka sanya wata ƙullata a zukatanmu game da waɗanda suka yi Imani. Ya Ubangijinmu! Lallai Kai Mai tausayawa ne, Mai jinƙai).

    Da kuma waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar Alƙiyama. Ka yarda da mu tare da su, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah, ya Mai kawar da damuwa, Mai yaye baƙin ciki, Mai karɓar addu’ar waɗanda ke cikin matsanancin hali, Mai Rahama Mai jinƙai a duniya da lahira, Kana bayar da su ga wanda Ka so, kuma Kana hanawa ga wanda Ka so, Ka yi mana rahama wacce za ta wadatar da mu daga neman rahamar waninKa, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah muna neman tsarinKa daga talauci da rashi da ƙasƙanci, kuma muna neman tsarinKa kada a zalunce mu ko mu yi zalunci. Ya Allah! Ka wadatar da mu da halal daga barin haram, kuma Ka wadatar da mu da falalarKa daga falalar waninKa, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah, Ya Wanda zunubin masu zunubi ba ya cutar da Shi, kuma biyayyar masu biyayya ba ta amfanar da Shi, Ka yi mana rahama, Ka yi falala ga waɗanda suka miƙa hannayensu gare Ka suna masu ƙanƙan da kai, suna neman Ka ‘yanta su daga wuta ma’abociya tsanani da muni.

    Ya Allah muna roƙon Ka Ka sanya mu daga cikin waɗanda za Ka ‘yanta daga wuta a cikin wannan wata mai albarka, kuma daga cikin masu tsira daga gidan halaka gidan wuta, daga cikin waɗanda za su dawwama a gidan tabbata Aljanna. Lallai Kai Mai rahama ne, Mai yawan gafara, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah lallai Muna roƙon Ka a cikin wannan wata mai albarka, muna kamun ƙafa da fuskarKa mai girma, da LittafinKa mai hikima, kada Ka bar mana wani zunubi a wannan lokaci face Ka gafarta mana, kuma kada Ka bar mana wani aibi face Ka suturce shi, ko wata damuwa face Ka kawar da ita, ko wata cuta face Ka warkar da ita, ko wata matsala face Ka yaye ta, ko wani Imani face Ka tabbatar da shi, ko wata zuciya face Ka yalwata ta, ko wani ɓatacce face Ka shiryar da shi, ko wani marar lafiya face Ka warkar da shi, ko wani mamaci face Ka yi masa rahama, ko wani da ake tambaya cikin ƙabari face Ka datar da shi, ko wani da ke tsoron azabarKa face Ka amintar da shi.

    Ya Allah, Ka gafarta mana abin da muka riga muka aikata da abin da zamu aikata, da abin da Ka ƙididdige na zunubammu mu kuma muka manta, da abin da Ka sani amma muka jahilta.

    Ya Allah, kada Ka bar mana buri face Ka cika mana shi, ko wata buƙata face Ka sauƙaƙa mana ita, ko wani alheri face Ka ba mu shi, ko wani sharri face Ka nisantar da mu daga gare shi, ya Mafi alherin Wanda bawa ya dogara da Shi kuma ya yi fatan samun alheri daga gare Shi, Ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah, Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu da masu jagorancinmu, Ka ƙarfafi Hadimin Masallatai biyu masu alfarma Sarki Salman bin Abdulaziz da Magajinsa amintacce Muhammad bin Salman da ɗaukaka da nasara bayyananniya.

    Ya Allah, Ka kiyaye su cikin cikakken lafiya da kariya, Ka saka musu da mafificin alheri game da hidimar Masallatai biyu masu alfarma da wurare masu daraja ga Musulunci da Musulmi.

    Ya Allah, Ka datar da dukkan shugabannin Musulmi kuma ka shiryar da su zuwa ga abin da yake alheri ne ga Addini da ƙasashensu. Ya Allah, Ka kare sojojinmu, Ka kare iyakokinmu da sansanoninmu, Ka kare jami’an tsaronmu, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah, muna neman gafara daga gare Ka, lallai Kai ne Mai gafara, Ka saukar mana da ruwan sama mai albarka. Ya Allah, Ka saukar mana da ruwa ya Allah, Ka saukar mana da ruwa ya Allah, Ka saukar mana da ruwa. Ya Allah, mu halittu ne daga cikin halittunKa, kada Ka hana mu falalarKa saboda zunubanmu.

    (Tsarki ya tabbata ga Ubangijininka Ubangijin buwaya daga abin da suke siffantawa. Aminci ya tabbata ga Manzanni, kuma godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin talikai).

    Danna nan don karanta Falalar Salati Ga Annabi SAW

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Fassarar Huɗuba Daga Masallaci Mai Alfarma 10 Rajab 1446 AH 10 January 2025

    Fassarar Huɗuba Daga Masallaci Mai Alfarma 10 Rajab 1446 AH 10 January 2025

    Mai Huɗuba:
    Sheikh Dr Saleh Bin Abdullahi Bin Humaid

    Mai Fassara:
    Dr Abdullahi Yunusa Machina

    Shugaban Sashi
    Dr Abdurrahman Muhammad Sani Yakubu

    Transcribe
    Aminu Bashir

    Huɗubar Masallaci Mai Alfarma
    Sheikh Dr. Abdullah Awwad 12/06/1446H

    HUƊUBA TA FARKO
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, muna gode Masa, muna neman taimakonSa da gafararSa, kuma muna neman tsarinSa daga sharrin kawunammu da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah Ya shiryar, to, babu mai ɓatar da shi, kuma duk wanda Ya batar, to babu mai shiryar da shi.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa. (Ya ku waɗanda kuka ka yi Imani, ku ji tsoron Allah matuƙar tsoronsa, kuma kada ku mutu face kusa Musulmi)

    Ya ku mutane, ku ji tsoron Ubangijinku, Wanda Ya halicce ku daga rai guda ɗaya, kuma Ya halicci matars (Ya ɗaga shi, kuma ya yaɗa maza da mata masu yawa daga gare su, kuma ku ji tsoron Allah Wanda kuke yi wa juna magiya da Shi, kuma ku kiyaye yanke zumunci, lallai Allah Mai kula da ku ne)

    (Ya ku waɗanda kuka yi Imani, ku ji tsoron Allah kuma ku faɗi magana wacce take daidai, Zai kyautata muku ayyukanku, kuma Ya gafarta muku zunubbanku, kuma duk wanda ya yi ɗa’a ga Allah da ManzonSa, to haƙiƙa ya rabauta rabauta mai girma)

    Bayan haka:
    Lallai mafi gaskiyar zance shi ne Littafin Allah, kuma mafi alherin shiriya ita ce shiriyar Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma mafi sharrin lamura su ne ƙirƙirarru, kuma kowane ƙirƙirarren abu bidi’a ne, kuma kowace bidi’a ɓata ce.

    Bayan haka:
    Ya ku mutane! Lallai Allah Wanda hikimarSa ta ɗaukaka, Ya halicce ku ne domin ku bauta Masa, kuma Ya kallafa muku ayyukan da za ku iya, don haka, ku aikata su. Ku ji tsoron Allah ta hanyar bin umarninsa, da nisantar abin da ya hana da manyan zunubai, kuma ku yi la’akari da abin da ke cikin Alƙur’ani mai girma na ababen lura, haƙiƙa Allah ya saukar da shi a gare ku don ku bi shi, domin lallai yana daga cikin mafi girman tanadi na samun tsira.

    Saboda abin da yake ƙunshe da shi na farillai da mustahabbai da halacci da haramci da wa’azozi da jan kunne, to me ya sa zukata ba sa bin umarninsa, kuma ba sa barin abin da ya hana kuma ya tsawatar, kuma ba sa jin tsoron wanda ya san bayyane da ɓoyayye cikin ayyukan bawa, da sirrikansa da kuma zahirinsa!

    Haƙiƙa gafala ta yi musu katutu, kuma sha’awace-sha’awacen zukata sun kautar da su daga lura da ababen suka saɓa musu, sai su ka ji daɗin ɗanɗanon ɓarnarsu, kuma suka jahilci ɗacin sakamako da za a musu a lokacin mutuwarsu, don haka, sai suka doge a kan saɓonsu, ba su ji tsoron yini da za a damƙe su ta ƙafafunsu da makwarkwarɗarsu ba.

    Ranar da za a ninka azaba ga wanda ya bar salla kuma ya tozarta ta, wanda ya yi sakaci game da lamarin zakka kuma ya ƙi ba da ita, wanda ya keta alfarmar watan Ramadana ya sha azumi a cikinsa, wanda ya jinkirta faralin Hajji alhalin yana da ikon yi kuma ba tare da wani uzuri ba.

    Ranar da za a shayar da mashayin giya da ruwan ɗiwa, a kwankwaɗa masa abin da zai ɗanɗani kaito da kuɗarsa da shi daga ruwan mugunyar ‘yan wuta. Ranar da za a sako harasan wuta ga mazinata da fajirai, kuma a dake su da bulalunta ta gabansu da bayansu.

    Maciyin riba kuma ya ci daga bishiyar zaƙƙum, lallai zina da cin riba ba su taɓa bayyana a cikin wasu mutane ba face sai sun sakko wa kansu da azabar Allah, muna neman tsarin Allah daga fushinsa da azabarsa, kuma azzalumai za su wanzu a cikin iska mai tsananin zafi da kuma tafasasshen ruwa, da kuma inuwa ta turnuƙun hayaƙi.

    Ku saurara! Lallai duk wanda ya shagala da kansa, to, ba zai samu lokacin aibata waninsa ba, kuma duk wanda gazawarsa ta dame shi, to, idanuwansa za su makance daga ganin gazawar waninsa da abin da yake aikatawa, don haka, ku kame harsunanku daga keta mutuncin mutane- Allah ya muku rahama- saboda lallai Allah Yana kusa da harshen duk wani mai magana, kuma duk wanda ya keta mutuncin ɗan’uwansa kuma ya cutar da shi da magana ko da aiki, to, Allah Shi ne Abokin husumarsa.

    Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce: ((Waɗanda suke cutar da muminai maza da muminai mata ba tare da sun yi laifi ba, to, haƙiƙa sun ɗauki nauyin ƙage da kuma zunubi bayyananne)).
    Babban malami Ibnu Usaimin Allah Ya masa rahama ya ce: “Wato suna jifansu da abin da ba su aikata ba, to, haƙiƙa sun ɗauki nauyin ƙage, wato ƙarya.

    Ƙage kuma, shi ne ka ambaci ɗan’uwanka da abin da bai tare da shi; don haka ne ma lokacin da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi tambaya game da yi da wani, sai ya ce: “Shi ne ka ambaci ɗan’uwanka da abin da yake ƙi”. Ya ce: Ya Manzon Allah! Idan ɗan’uwana yana tare da abin da nake faɗi fa? Ya ce: “Idan yana tare da abin da kake faɗi, to haƙiƙa ka ci namansa, idan kuma ba ya ɗauke da shi, to, haƙiƙa ka masa ƙage”. Muslim ne ya rawaito.

    Sannan Allah Ya masa rahama ya ci gaba da cewa: Kuma cutar da mumini yana kasancewa da magana da kuma aiki, kuma hanyoyinsa na da yawa, lallai waɗanda suke cutar da muminai ba tare da sun yi laifin komai ba, to, haƙiƙa sun ɗauki nauyin ƙage wa kawunansu, kuma shi ne ƙarya, da kuma laifi bayyananne, shi ne uƙuba mai girma, Allah Ya amintar da mu”.

    A nan maganarsa ta ƙare, Allah Maɗaukakin Sarki Ya masa rahama kuma Ya saka masa da alheri bisa hidimarsa ga Musulunci da Musulmi. Ya Ubangijinmu, Ka sanya harsunanmu su kasance masu tsarki, zukatanmu su kasance masu ƙaunar muminai. Ya Ubangijinmu, Kada Ka sanya ƙiyayyar waɗanda suka yi imani a cikin zukatanmu. Ya Ubangijinmu, lallai Kai Mai tausayawa ne, Mai jinƙai.

    Ya Allah Ka tsare mu daga son zuciya, da kuma bin zuciya mai yawan umarni da mummuna, sannan Ka tsare mu daga shaiɗan la’ananne. Ku ji tsoron Allah, ya ku bayin Allah! Kuma ku yi gaggawar yin amfani da damar da aka ba ku matuƙar tana nan. Ku ci gaba da ingantattun ayyukanku muddin ana karɓar su, kuma ku kakkaɓe kawunanku daga aikata laifi matuƙar igiyar rayuwa bata katse ba.

    Kuma ka rage buri, ya kai wanda ya ruɗu, domin rayuwa gajeriya ce. Ka tsarkake aikinka ga Allah domin Mai duba aikin Mai gani ne, kuma ka bar kusakuranka, domin lissafin mai tsauri ne. Kuma ka gyara laifukanka ta hanyar tuba, domin makoma ta yi maka daɗi.

    Imam Ahmad Allah Ya yi masa rahama, da Imamul Bukhari Allah Ya yi masa rahama a cikin “Al-Adabul-Mufrad”, da kuma Albaihaƙi da isnadi mai kyau, sun rawaito daga Abdullahi bin Amr Allah ya yarda da su: cewa Annabi tsira da amincina Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ku yi jin ƙai, za a jiƙanku, ku yi gafara, za a gafarta muku.

    Kaicon waɗanda suke zama kamar masakin magana. Bone ya tabbata ga masu dogewa da yin abin da suka sani cewa mummuna ne). Ma’anar “Masakin magana”: su ne waɗanda suke sauraron magana amma ba sa fahimtar ta, kuma ba sa aiki da ita.

    A’uzubillahi minash shaiɗanir rajim, bismillahir Rahmanir Rahim: (Sai ka yi bushara ga bayina () Su ne waɗanda suke sauraron magana kuma su bi mafi kyawun ta, Waɗannan ne waɗanda Allah ya shiryar, kuma waɗannan su ne ma’abota hankula). Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah gare mu da kuma dukkan Musulmi, don haka, ku nemi gafaranSa, lallai Shi Mai yawan gafara ne kuma Mai jin ƙai.

    HUƊUBA TA BIYU
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo mai ɗorewa tare da wanzuwarSa. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo da ba ya ƙarewa sai idan Ya nufa. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo na dindindin, ba abin da zai samu wanda ya faɗe shi sai yardarSa.

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo dawwamamme a kowane ƙiftawar ido da numfashin abu mai rai. Tsira da aminci su tabbata ga Annabinmu Muhammad da Alayensa da Sahabbansa da waɗanda suka bi shiriyarsa kuma suka yi kira irin kiransa.

    Bayan haka:
    Ku ji tsoron Allah ya ku Musulmi don ku rabauta, ku fargar da kawunanku daga gafala, kuma ku bi hanyar tsira, idan ba ku aikata haka ba kuka tsaya, to fa ku sani cewa shi ajali tafiya yake da ku, kyawawan ranaku na wucewa, ita mutuwa kuma tana farke a farfajiyarku, kuna nufin samun duniya Shi kuma Allah Yana nufin Lahira.

    Ya ku bayin Allah!
    Ku yawaita salati da sallama ga mafakar mutane a babbar matsaya Ranar Alƙiyama, Annabinmu kuma mai cetonmu Muhammadu tsira da amincin Allah mai yawa su tabbata a gare shi da Alayensa. Ya Allah ka ƙara yarda da Halifofi shiryayyu da sauran Sahabbai gabaɗaya, da waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

    Ya Allah Ka amfanar da mu da son su, kuma Ka tashe mu cikin tawagarsu, kuma kada Ka karkatar da mu daga bin tafarkinsu da hanyarsu ya Mafi karamcin masu karamci.
    Ya Allah! Ka ƙarfafa Musulunci da Musulmi, Ka ɗaukaka Kalmar gaskiya da Addini da falalarka.

    Ya Allah! Ka ƙarfafa Shugabanmu kuma Majiɓincin lamuranmu da gaskiya da yin daidai da dace, Ka yi riƙo da hannunshi ga ayyukan nagarta da taƙawa, Ka azurta shi da mashawarta nagari, Ka ɗaukaka AddininKa da kalmarKa da shi, Ka sanya shi ya zama mai taimako ne ga Musulunci da Musulmi, kuma Ka haɗa kan Musulmi da shi a kan gaskiya da shiriya ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah! Ka datar da shi da Yarimansa da ‘yanuwansa da mataimakansa zuwa gaskiya da shiriya da kuma duk abin da yake akwai gyara ga al’umma da ƙasa a cikinsa, Ka saka musu da alheri saboda kulawarsu da Masallatai biyu masu alfarma da daraja, da kuma duk abin da suke gabatarwa saboda cigaban Musulunci da Musulmi.

    Ya Allah! Ka datar da masu jagorancin Musulmi ga yin aiki da Littafinka da Sunnar Annabainka Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, Ka sanya su su zama rahama ga bayinKa Muminai, Ka haɗa kansu akan gaskiya ya Ubangijin talikai, Ka kuma datar da duk jagororin Musulmi ga duk abin da yake gyara ne ga ƙasa da mutanen.

    Ya Allah! Ka saki labulan suturtawarka akan ƙasarmu da kuma dukkan ƙasashen Musulmi.
    Ya Allah! Muna kamun ƙafa da yardarKa kada Ka yi fushi da mu, kuma muna kamun ƙafa da amincinKa kada Ka yi mana uƙuba, kuma muna nema tsarinka daga azabarKa, ba mu iya kaiwa matuƙa wurin yaɓonKa kamar yadda Ka yabi kanKa.

    Ya Allah! kada ka yi mana azaba da munanan ayyukanmu, kuma kada Ka kama mu da abin da wawayen cikinmu suka aikata, Ka isar mana duk wani abin da ya dame mu, kuma Ka kasance Mai ƙarfafawa da ba da nasara a gare mu. Ya Allah! Lallai mu muna roƙon Ka farin ciki da zai lulluɓe zukatanmu da ‘yantuwar Masallacin Ƙudus daga hannu Yahudawa ‘yankwace.

    Ya Allah Ka jefe su da kibiyarKa da ba ta kure, Ka saukar musu da uƙubarKa mai tsanani, ya Majiɓincin masu rauni, ya Ma’boci ƙarfi mai tsanani! Ya Mai gudanar da giragizai! Ya Mai rusa rundunonin maƙiya! Ka saukar wa ‘yan ta’adda azaba mafi tsanani, Ka sanya su abin ɗaukar izina ga masu hankali. Ya Allah! Muna roƙon Ka farin ciki saboda samun nasarar Musulmi a kan abokan gabansu azzalumai.

    Ya Allah! Lallai mu muna roƙon gafararKa, saboda lallai Kai Ka kasance Mai yawan gafara ne, don haka Ka saukar mana da ruwan sama mamako, ya Allah! Ka saukar mana da ruwan sama, ya Allah! Ka saukar mana da ruwan sama, ya Allah! Lallai mu wata halitta ce cikin halittunKa, don haka kada Ka hana mu falalarKa saboda zunubanmu.

    Ya Allah! Ka karɓa daga gare mu lallai Kai Mai ji ne kuma Masani, kuma Ka karɓi tubarmu lallai Kai Mai yawan karɓar tuba ne Mai tsausayi. Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka Ubangijin buwaya daga abin da suke siffantawa, aminci ya tabbata ga Manzanni, godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai.

    Don karanta falalar tafiya masallacidanna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu