Tag: Falala

  • Hadisi Na Biyar A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musa

    Hadisi Na Biyar A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musa

    An karɓo daga Aliyyu (Radiyallahu Anhu) ya ce: “Maganar ƙarshe da Manzon (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi ita ce: “Ku kula da sallah, ku kula da sallah, ku ji tsoron Allah ku kula da haƙƙoƙin waɗanda suke a ƙarƙashinku”.

    Abu Dawud da Ibn Majah ne suka rawaito shi.

    ƘARIN BAYANI

    Wannan hadisi yana daga cikin wasiyyoyin da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya bar wa al’ummarsa dab da wafatinsa. Ya yi wasiyyar a kula da sallah kuma a kula da haƙƙoƙin bayi da barori da duk waɗanda suke ƙarƙashin mutum.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu A kan Shugabanci) wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi domin karanta cikaken Littafin danna nan.

  • Yadda Falalar Suratul Ƙulhuwallahu Ahad Take

    Yadda Falalar Suratul Ƙulhuwallahu Ahad Take

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) yace: “Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce: “Ku taru zan karanta muku ɗaya bisa ukun al-ƙur’ani, sai waɗanda suka haɗu suka haɗu, Sai Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya fito sai ya karanta “Ƙulhuwallahu Ahad”.

    Sannan ya shiga gida, sai muka ce da junanmu mu zaton wahayi ne ya zo masa daga sama, shi ya sa ya shiga gida, sai ya fito ya ce haƙiƙa na ce da ku zan karanta muku ɗaya bisa ukun al-ƙur’ani, ku faɗaka haƙika ita (ƙulhuwallahu tana daidai da ɗaya bisa ukun al-ƙur’ani”. (Muslim 812)

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Suratul Falaƙi Da Nasi Ta Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sahihin Sirrin Ƙulhuwallahu Ahad danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Yadda Falalar Karanta Amanar Rasulu Take

    Yadda Falalar Karanta Amanar Rasulu Take

    An karɓo daga abu Mas’ud Albadri (Radiyallahu Anhu) haƙiƙa Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Wanda ya karanta ayoyi biyu na ƙarshen Baƙara a cikin dare sun isar masa” (Bukhari: 3786, muslim 807).

    Malamai sun bayyana ma’anar “sun isar masa” da cewa; za su zama garkuwa a gareshi daga dukkan sharri; ko kuma za su tsaya a masa a matsayin ƙiyamul laili”.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Ayoyi Goma Na Farko Ko Ƙarshen Suratul Kahfi Ta Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Karatun Surah A Cikin Sallah danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Falalar Watan Dhul-Hajj (BABBAR SALLAH)

    Falalar Watan Dhul-Hajj (BABBAR SALLAH)

    Dukkan godiya da ɗaukaka Ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai, tsira da aminci su tabbata a kan Manzonmu Annabi Muhammad SAW, tare da Alayensa da sahabbansa masu girma.

    Haƙiƙa ‘yan Uwa Musulmai; babu wani abu da zamu yi wa Ubangiji sai dai godiya bisa ni’imominsa da ya yi mana masu yawa, daga ciki sun haɗa da wannan wata mai Albarka wanda ake aiwatar da wasu muhimmun ibadu kamar Haka:

    i. Akwai kwanaki goma na farkon wata wanda Allah SWT ya yi rantsuwa da su domin girmansu inda yake cewa:

    “Na rantse da Alfijir, Da kuma kwanaki goma (na farkon watan Dhul-Hajj.)”

    Sannan ya tabbata daga Ibn Abbas (R.A) yace “Babu wasu kwanaki da ake aikin alheri a cikinsu (Aikin lada) wanda ya fi soyuwa a gurin Allah SWT fiye da waɗannan kwanaki goma na Farkon Wannan wata (Dhul-HaJJ) Sai sahabbai suka ce: Har yaƙi don ɗaukaka kalmar Allah? Sai yace: Har yaƙi don ɗaukaka Addinin Allah, sai dai mutumin da ya fita da kansa da dukiyar sa, sannan bai dawo da ɗaya daga cikinsu ba (Dukiya ta ƙare; shi kuma ya yi shahada). Bukhari.

    ii. Daga cikin falalan wannan watan babbar Sallan (Dhul-Hajj) akwai Ranar Arfa wanda ya zo a hadisin Manzon Allah SAW yace: “Duk wanda ya yi Azumin ranar Arfa; Allah zai gafarta masa zunubansa na shekara biyu (shekarar da yake ciki da kuma shekara mai zuwa). Bukhari

    iii. Yawaita ‘yanta bayi daga wuta zuwa aljanna. An karbo daga Nana Aisha (R.A) tace: Manzon Allah SAW yace: ‘Babu wata rana da Ubangiji SWT ya fi ‘yanta bayi daga cikin wuta kamar ranar Arfa” Muslim.

    YANKAN LAYYA

    Manzon Allah SAW yace: Dabbar da ɗaya daga cikinku zai yanka saboda layya yana da Hasana ga kowanne gashi. Saboda haka ‘yan uwa musulmai mu yawaita aiki na ƙwarai a cikin waɗannan kwanaki Musamman ranar Arfa, sannan mu yawaita Addu’a da neman gafara da shiriya da neman arzikin duniya da Lahira. Sannan mu roƙawa ƙasarmu zaman Lafiya da kuma shugabanni na kwarai.

    KWAƊAITARWA A KAN LAYYA

    Layya sunna ce mai ƙarfi, sannan ta samo asali ne tun daga zamanin Annabi Ibrahim, inda Allah ya yi masa Umurni (a cikin Mafarki) ya yanka dansa (Annabi Isma’il) wanda ya daɗe yana neman Haihuwa Allah bai ba shi ba, sai daga baya ya samu wannan ɗan (Annabi Isma’il). Ku duba irin soyayyar da ke tsakanin ɗa da uba, amma don cika umurnin Allah, sai ya faɗawa ɗan; sai ɗan yace: Ya baba ka cika Umurnin da Allah Yayi maka. Annabi Ibrahim ya kama ɗansa (Annabi Isma’il) ya kwantar da shi, ya sa wuƙa zai yanka shi. Sai Allah ya canza mashi da Rago.

    Danna nan don karanta Gudumawar Iyaye Wajen Gina Al’umma

    Edita@rumasau-kallamu

  • Falalar Ayoyi Goma Na Farko Ko Ƙarshen Suratul Kahfi

    Falalar Ayoyi Goma Na Farko Ko Ƙarshen Suratul Kahfi

    An karɓo daga Abu Darda’i (Radiyallahu Anhu)

    Haƙiƙa Annabin Allah (Sallallahu alaihi wasalam) ya ce: “Wanda ya haddace ayoyi goma na farkon Suratul Kahafi, Za a kare shi daga Dujal” (Muslim 809) A wata ruwayar ayoyin goma na Ƙarshen suratul kahfi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Suratul Tabarakallazi Biyadihil Mulku Ta Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Raka’o’in Ɗawafi danna nan.

    Don karanta cikakken bayani a kan Kalmomi Guda Biyar Masu Amfani A Duniya Da Lahira danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Falalar Gaggauta Shan Ruwa

    Falalar Gaggauta Shan Ruwa

    Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasalla) ya koya mana amfanin gaggauta shan ruwa ga mai azumin farilla da nafila, saboda irin alheri da ke cikinsa, kamar yadda wannan hadisin ya nuna mana;

    حدثنى يحي عن مالك عن أبى حازم بن دينار عن سهل بن سعد الساعدى, أن رسول الله صلى الله عليه وسلم قال” لا يزال الناس بخير ما عجلواالفطر”

    An ruwaito daga Yahaya daga Malik daga Abi–Hazim bin Dinari daga Sahlu bin Sa’adu Assa’ida, haƙiƙa ba su gushe ba da cikin alheri ba matuƙar suna gaggauta buɗe baki (shan ruwa).

    Ma’ana akwai dalili masu matuƙar amfani a cikin wannan hadisin, wanda yake koyarwa kamar haka; saɓawa yahudawa da Nasara, saboda sun kasance suna jinkirta shan ruwa idan sun yi azumi, haka ma gaggauta shan ruwa sunnar annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasalla) ce. Kamar yadda ya zo a cikin wannan hadisin;

    حدثنى مالك عن عبدالرحمن بن حرملة ألأ سلمى عن سعيد بن مسيب, أن رسول الله صلى الله عليه وسلم قال ” لا يزال الناس بخير ما عجلواالفطر”

    An ruwaito daga Malik daga Abdulrahman bin Hurmal Al-assalami daga Sa’idul bin Musayyib (shugaban maruwaita), haƙiƙa Monzan Allah (Sallallahu alaihi wasalla) yace: “mutane ba za su gushe ba da aikin aheri, matuƙar suna gaggauta buɗe baki (shan ruwa)”.

    حدثنى مالك عن إبن شهاب عن حميد بن عبدالرحمن أن عمربن الخطاب و عثمان بن عفان كانا يصليان المغرب حين تنظر إلى اليل الأسود ,قيل أن يفطر ثم يفطر أن الصلاة وذلك في رمصان .

    An ruwaito daga Malik daga ibin shihabi daga Humidu bin Abdullah (yace) haƙiƙa Umar bin khaɗɗab da Usman bin Affan (R.A) sun kansance suna yin sallar Magriba a lokacin da dare ya yi baƙi (duhu) kafin su sha ruwa, sannan sai su sha ruwa bayan sun yi sallah (Magariba) wannan kuma ya kasance a cikin watan Ramadan ne.

    Amma magana mafi shahara wanda kuma babban malamin nan ya tafi a kai (Imam Malik bin Anas) shi ne gaggauta shan ruwa kafin a yi sallar Magariba, Saboda haka ne ya kamata a ce a cikin masallatan mu a dinga bari mintuna biyar (5) bayan an kira sallah, saboda mutane su samu falalar aikata sunnar annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasalla), ba wai kawai ana gama kiran sallah ba, sai a tayar da sallah, amma idan an yi hakan, sallah ta yi sai dai ba a aikata sunnar annabi ba ga me azumi da sauransu.

    Domin karanta Dalilan Wajabcin Ramadan danna nan 

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Falalar Suratul Baƙara

    Falalar Suratul Baƙara

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) Haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “kada ku mayar da gidajenku kamar maƙabarta; Haƙiƙa Shaiɗan yana gudu daga gidan da ake karanta Suratul Baƙara a cikinsa”. (Muslim 708).

    An karɓo daga Abu Umamah (Radiyallahu Anhu) haƙiƙa ya ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) yana cewa; “ku riƙa karanta suratul Baƙara saboda riƙo da ita albarka ne, barinta nadama ne; kuma matsafa ba sa iyawa da ita”. (Muslim 804).

    Wato karanta suratul baraƙa yana maganin sihiri da tsafi da kuma sharrin shaiɗanu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Falalar Karanta Ayatul Kursiyyi Ya Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Wajibcin Karatun Fatiha A Cikin Sallah danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’ar Neman Falala

    Addu’ar Neman Falala

    Wannan addu’a ana yin ta domin neman falala da buɗi akan abinda ka sa a gaba, karatu ko kasuwanci.

    Akan so ka zama mai yawan salatul-duha; kamar yadda aka ruwaito daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) yace; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya min wasicci da abubuwa guda uku (3) su ne salatul-duha, sallah raka’ah huɗu lokacin da rana ta fito (da ƙarfe 9 zuwa 10 na safe); Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) yace; ta fi duniya da abunda ke cikinta da kuma yin azumi uku a kowane wata; da kuma salatul-witr, shafa’i da witr kafin a kwanta bacci.

    A yi sa’a ma’abocin yin salatul-duha ne kafin ka fita harkokin ka ka yi sallar raka’ah biyu ko huɗu. Bayan ka yi sallama, kayi salatin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) da hailala sai ka karanta wannan addu’ar kamar haka;

    “Allahummaj al awwala hazan nahar salaahan, wa ausadahu falaahan, wa akhiruhu najaahan, as aluka khaira dunya wal akhira, ya arhamur rahimin. Labbaika lahumma labbaik, wa sa’daika wal khairu fi yadaka, wa minka ilaika”

    Wannan Addu’ar Neman Falala; An samo ta ne daga littafin DUA’U YARFA’U BALA’I, shafi na 49.

    Don karanta bayani akan Falalar Tafiya Masallaci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’ar Da Abi Zaril Gaffari Yake Yi danna nan.

  • Falalar Yaɗa Sallama A Cikin Al’umma

    Falalar Yaɗa Sallama A Cikin Al’umma

    Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Ba za ku shiga aljanna ba sai kun yi imani, kuma ba za ku yi imani ba sai kun so juna. Shin ba na nuna muku wani abu da in kun yi shi za ku so juna ba? Ku yaɗa sallama tsakaninku’.

    Ammar, Allah ya yarda da shi, ya ce: Abubuwa uku, wanda duk ya haɗa su, ya haɗa imani; mutum ya yi adalci ga kansa, da yaɗa gaisuwar sallama a cikin al’umma, da yin kyauta a cikin rashin wadata’.

    Daga Abdullah ibn Umar, Allah ya yarda da shi, ya ce: wani mutum ya tambayi Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam); wane abu ne a cikin musulunci ya fi alheri? Sai ya ce; Ka ciyar da abinci, kuma ka yi sallama ga wanda ka sani da wanda ba ka sani ba’.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Amsa Wa Kafiri Idan Ya yi Sallama danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Nafilolin Sallah. danna nan.

    Don karanta cikakken bayani a kan A Ina Mahaifiyar Annabi muhammad (S.A.W) Ta Rasu? danna nan.

  • Hadisi Na Goma Sha Biyu A Kan Falalar Adalci Da Tausaya Wa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Hadisi Na Goma Sha Biyu A Kan Falalar Adalci Da Tausaya Wa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Ibn Abi Aufa (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Haƙiƙa Allah yana tare da alƙali matuƙar bai yi zalunci ba. Idan kuwa ya yi zalunci, sai Allah ya rabu da shi, sai shaiɗan ya naniƙe masa.
    Tirmizi da Ibn Majah da Ibn Hibban da Hakim ne suka rawaito shi. Sai dai a ruwayar Hakim ya ce: “Idan ya yi zalunci sai Allah ya yi watsi da shi”.

    ƘARIN BAYANI
    Allah Ta’ala yana taimaka wa shugabanni da alƙalai masu adalci, yana kuma ba su kariya, yana rufa musu asiri, ya ɗaukaka su. matuƙar sun kama hanyar zalunci da rashin gaskiya, sai Allah ya yi watsi da su, ya bar su da dabararsu, su yi ta ɗimuwa da shirme, ga rashin ƙima a idon mutane, sannan in suka tafi a haka, a lahira su haɗu da matsananciyar azaba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Hadisi Na Goma Sha Uku Kan Falalar Adalci Da Tausaya wa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu A kan Shugabanci) wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi domin karanta cikaken Littafin danna nan.