MA’ANAR AURE A ƘASAR HAUSA
Wata yarjejeniya ce, wacce ake ƙulla ta a tsakanin namiji da mace, wacce ta dace da shari’ar musulunci. A ƙasar Hausa, za mu iya cewa aure, wata hanya ce, wacce Bahaushe yake bi, don samun yaɗuwar iri, wanda yake zama da matarsa, kuma al’ada da shari’a suka amince da haka. Ƙasar Hausa, idan mutum zai auri mace, ana buƙatar ya;
1. Tuntuɓi iyayenta.
2. Amincewar yarinyar.
3. Sadakin aure.
4. Kayan aure.
5. Matsuguni.
6. Sana’a.
7. Goro.
Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

