5 RUBUCE-RUBUCE
Dr. Magaji Ahmad Gaya shahararren malami ne a fannin harshen Hausa. Ya yi digiri na uku (PhD) a ɓangaren nazarin al’adu a jami’ar Umaru Musa “Yar Adua da ke Katsina. Haka kuma ya yi aikin koyarwa a wasu makarantun firamare da sakandare da kuma Kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kumbotso. A halin yanzu yana koyarwa a Jami’ar Northwest, Kano Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya.