Tag: tatsuinya

  • Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Uku)

    Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Uku)

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Kurege ya je gidan Kura ya ce su tafi farautar kayan daɗi a jeji. Kura ta amince. Suka shirya suka kama hanyar daji. Da suka isa bakin rafi sai Kura ta ce, to su rabu a nan. Ta ce tunda shi Kurege ƙarami ne ya bi cikin ciyawa, ita kuma Kura da yake babba ce, za ta bi kan hanya.

    Da fari Kurege ya ƙi yarda, amma daga baya ya haƙura, ya bi cikin ciyawa yana tafiya har ya kai ga gidan zuma, ya tarar ƙudan Zuma suna ciki. Sai ya saurare su ya ji duk sanda za su fita sukan ce: “Buɗe bus,” sai ƙofar gidan ta buɗe, su fita. Idan sun dawo sai su ce: “Rufe kif,” sai kuma ƙofar ta rufe.

    Da ya gane yadda suke yi, sai ya laɓe har ƙudan Zuma suka fita sarai. Da ya ga haka sai ya matsa kusa yace: “Buɗe bus,” sai ƙofa ta buɗe. Sai Kurege ya shiga ya kwashi zuma ya sha, ya cika jakarsa da ita, ya fito, ya dubi ƙofa ya ce: “Rufe kif,” sai ƙofa ta rufe, ya kama hanya ya dawo inda suka yi alkawari za su haɗu da Kura.

    Ita kuma Kura da ta kama hanyarta, ta rinƙa tafiya ba ta ga komai ba, ga shi ta fara jin yunwa. Can dai ta hango zawayi a malale a gindin bishiya, ta je ta kama shan zawo har ta ƙoshi. Daga nan ta ɗebi sauran zawayin nan ta zuba a jakarta, ta kama hanyar inda suka yi alƙawari za su haɗu da Kurege.

    Da ta iso sai ta tarar ashe Kurege ya riga ta dawowa. Kurege ya dubi Kura, ya ce: “Kura ga shi kin ciko jakarki da kayan daɗi, sai ki ɗan ɗebo mini abin da kika samo.” Da Kura ta ji haka sai ta ƙi, ta ce ina nasa? Sai ya ce to zai ɗan ɗebo mata, ita ma ta ɗebo masa nata, amma idan na Kurege ba daɗi, zai biya ta nata.

    Kurege ya yarda. Da Kura ta buɗe jaka sai Kurege ya fara jin warin kashi, ya dubi Kura ya ce mata ya fasa shan abin da ta zo da shi. Da ta ji haka, sai ta ce to shi ke nan, amma ya ɗan ba ta nasa. Kurege ya buɗe jakarsa ya ɗeba mata, ya ba ta. Da ta ji zaƙi sai ta jefar da jakarta ta kuma ce sai Kurege ya nuna mata inda ya samo wannan zumar.

    Kurege ya ce to su tafi ya nuna mata. Suka kama hanya, har suka je gidan Zuma, ya gaya mata yadda za ta buɗe ƙofar gidan Zuma. Nan take Kura ta je ta buɗe gidan zuma, ta fara shan zuma har ta ƙoshi, ta cika jakarta. Amma kuma sai ta manta yadda za ta buɗe ta fita, sai ta rinƙa cewa: “Rufe kif.”

    Ta dai kasa fita har Ƙudan Zuma suka dawo daga cin furanni, suka faɗa Kura da harbi, duk jikinta ya kumbura. Kurege ya gudu ya bar ta, daga baya ta koma gida duk fuskarta a kumbure. A gida aka tambaye ta me ya same ta, sai ta ce: “Ai na yi yaƙi ne da wasu namun daji, amma duk na kashe su sai dai jikina ya kumbura.”

    Da ta je gidan Kurege sai ya buya, ya ce: “A gaya mata ba na gida.” Kura ta ce: “Idan ya dawo a gaya masa in bakinsa ya yi masa ƙaiƙayi, to ya daka da dutse kafin mu haɗu,” sai ta yi tafiyarta. Da ba don Gizo ba da na yi muku ƙarya. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Natsuwa maganin kuskure.
    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Cin Kasuwar Sama

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Yarinya Da Dodanni

    Tatsuniyar Yarinya Da Dodanni

    Ga ta nan ga ta nan ku.

    Tatsuniya : Wata yarinya ce dai mai tsananin kyau, duk garinsu babu mai kyanta, ta ce ba ta son kowa sai marar tabo. Sai dodanni suka ji labari.

    Sai suka yi wanka a gidan tururuwa. sai suka zama samari kyawawa da su.
    Da ta gan su, sai ta ce, “Ta sami mazajen aure”. sai duk ta duba jikinsu, sai ta ga jikin wannan da ɗan tabo ɗan mitsitsi, sai ta ce, “Ba ta son sa”. Da ta duba jikin ɗayan ta gan shi sumul, ba ko ɗigon tabo a jikinsa, sai ta ce, “Shi take so”.
    Shi ke nan, sai aka shirya aka yi biki.

    Sai suka ce, “Za su tafi da ita garinsu, su ba mazauna ba ne”, sai aka ce; “To za a ba ta ƙanwarta ta taya ta zaman ɗaki”. Sai ta ce, “Ita ba ta so, ta zauna ita kaɗai”. Shi ke nan, aka yi aka yi su tafi da ƙanwarta ta ƙi; sai ƙanwar ta zama ƙuda ta maƙale mata.

    Shi ke nan, da suka je gidan dodanni; sai dare ya yi suka shiga ɗaka suka rufe ƙofa, sai ta ga ƙanwarta, sai ta rufe ta da faɗa, ta ce, “Ke wa ya kawo ki nan?”

    Ita kuwa ƙanwar sai ta yi shiru.
    Shi ke nan sai yar ta ƙyale ta.
    Ita yar kamar sokuwa take. In dare ya yi, sai ta yi ta shirgar barci. Ita kuwa ƙanwar, sai ta zauna tangar har gari ya waye.

    Sai uwar mijinta ta zo da tsakar dare ta ce:
    “Sarma-sarma duf-duf”.
    Sai ƙanwar ta ce:
    “Wane ne nan ya ke mana
    Sarma-sarma duf-duf?”
    Sai uwar mijin ta ce:
    “Uwar miji ce take muku
    Sarma-Sarma duf-duf”.
    Sai yarinya ta ce:
    “Me kike so kike mana
    Sarma-sarma duf-duf?”
    Sai ta ce:”Wuta nake so nake muku
    Sarma-sarma duf-duf”.
    Sai yarinya ta ce:
    “Iya ga wuta nan.
    Ki bar mana
    Sarma-sarma duf-duf”

    Sannan yarinya ta watso mata wutar. Tsohuwa ta je ta kashe wutar ta kuma dawo musu. Nan kuwa ashe ba wuta take so ba. So take yi ta cinye su idan ta tarar sun yi barci.
    Kullun haka, kullum haka. Duk sa’ad da yarinyar ta gaya wa yayarta game da uwar mijin mai zuwa ɗiban wuta da daddare, sai yayar ta ce, “Ƙarya take yi”.
    Ana nan a haka sai, ran nan yarinya ta ce da yayarta, “To, yau dai ki zauna kada ki yi barci don ki ji yadda muke yi da tsohuwar da kunnenki”.

    Shi ke nan, yayar ta zauna.
    Sai ita uwar mijin ta zo ta yi musu irin yadda take yi kullum.
    Shi ke nan, sai ya ta ji da kunnenta.
    Shi kuma mijin nata yana wani ɗaki suna kwance tare da abokansa. Idan an yi abinci na aikin gona an kai musu, sai su yi haƙa su bunne. Sai su yi ta cin kwaɗi. Ita kuwa ƙanwar, wadda ta kai musu abincin, sai ta ce da su:
    Mijin yayata, ci kwaɗi.
    Mijin yayata, ci kwaɗi.
    Mazan-wazata, ci kwaɗi
    Sha da kwaɗi, ci kwaɗi
    Sha da kwaɗi, ci kwaɗi.

    Su kuma idan sun ji wannan waƙar, sai su yi ta rawa suna cin kwaɗi.
    Shi ke nan. Da sun ga ƙanwar ta dawo daga gida, sai su zama mutane su ce, “Ga kwanukanki nan. ki ce muna yi mata sannu da aiki”.
    Shi ke nan, sai yarinya ta ɗebi kwanuka ta tafi da su gida.
    Kullum haka, kullum haka.
    Sai rannan yayar ta yi shawara da ƙanwarta don su gudu gida.
    Sai suka yi ta haƙa rami, tun daga nan gidan har ya zuwa hanyar ƙofar garinsu. Suna ta bin rami da ita da ƙanwarta har suka je gida.
    Iyayenta suka ce da ita, “Lafiya?”.
    Sai ta ce wa iyayenta, “Ashe dodanni ne? Ni zato nake mutane ne”.
    Shi ke nan.
    Ƙurunƙus kan ɗan ɓera.
    Ba don ƙarya ce ba, wa zai zuba ruwa a jallo, jallo ya fashe kuma ruwan bai zube ba?

    Domin karanta tasuniyar gizo da giwa danna nan

    Domin karanta bayani akan Ra’in Bincike Hausawa danna nan