Tag: Sallar Alwala

  • Zikiri Kafin (Gabanin) Da Bayan An Gama Alwala

    Zikiri Kafin (Gabanin) Da Bayan An Gama Alwala

    Zikiri Kafin (Gabanin) Alwala

    “Bismillaahi”.

    {Da sunan Allah}.

    Zikiri Bayan An Gama Alwala

    “Ashhadu an laa ilaha illallahu wah dahu laa sharika lahu wa Ashhadu anna Muhammadu abduhu wa rasuluhu”.

    {Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaɗai, babu abokin tarayya a gare shi, kuma ina shaidawa cewa Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) bawansa ne kuma manzonsa ne}.

    “Allahumma ja’alnii minat-tauwaabina waj’alnii minal mutaɗahhiriina”.

    {Ya Allah! Ka sanya ni a cikin masu yawan tuba, kuma ka sanya ni a cikin masu tsarkaka}.

    “Subhanakal-laahumma wabi hamdika Ashhadu an laa ilaaha illaa anta wa astagfiruka wa atubu ilaika”.

    {Tsarki ya tabbata gare ka ya Allah tare da yabo gare ka. Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai kai, ina neman gafararka kuma ina tuba gareka}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Zikiri Yayin Fita Daga Gida danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Ayyukan Gida Domin Taimako Juna danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Sallar Alwala Da Falalarta

    Sallar Alwala Da Falalarta

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu anhu ) ya ce: wata rana bayan sallar Asuba, sai Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya ce: da Bilal:

    “Ya kai Bilal , faɗa min aikin da ka fi sa rai da shi a Musulunci; saboda na ji ƙarar takalminka a gabana a Aljanna (Ma’ana yana yi wa Annabi zagi a Aljanna) sai ya ce, “Babu aikin da na fi sa rai da shi fiye da sallar da nake yi gwargwadon hali a duk lokacin da na yi alwala ko dare ko rana” .(Bukhari 1149, Muslim 910)

    Wannan ya nuna cewa Bilal ya sami matsayin zagin Annabi a Aljanna ne, Saboda sallar alwala da yake yi sai mu dage ‘yan uwa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sallar Tahiyyatul Masjid danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.