Tag: Kurege Da Kura

  • Tatsuniyar Kurege Da Kura

    Tatsuniyar Kurege Da Kura

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Kurege da ƙawarsa Kura suka fita farauta. Suna cikin tafiya, sai suka tarar da inda hanya ta rabu biyu. Hanyar da ta yi dama, doguwa ce, wadda ta yi hagu kuma gajeriya. Sai Kurege ya ce da Kura: “Tun da ke ce babba, sai ki bi doguwar hanyar, watau ta dama, ni kuma ƙarami in bi gajeriyar, wadda ta yi hagun.”

    Kura ta ce: “A a, kai ƙarami ka bi babbar hanya, ni zan bi ƙaramar.” Sai ya ce: “To, shi ke nan mu tafi.” Kowa ya kama hanyarsa. Kura da ta bi gajeriyar hanya ba ta sami komai ba, sai wani ɗan ƙanzo. Da lokacin da za su haɗu ya matso, sai ta je inda suka shirya za su haɗu da Kurege, ta tsuguna tana jira.

    Shi kuwa Kurege mai doguwar hanya, sai ya yi ta tafiya har ya gaji. Sai ya sami inuwar wata bishiya ya zauna yana hutawa. Da sanyin inuwa ya ratsa shi, sai ya ce: “Kai, amma wannan inuwada daɗi take.” Sai kawai ya ji bishiya ta ce: “Ai ma sai ka ɗanɗana ganyena ka ji irin daɗinsa!” Sai Kurege ya tsinki ganyen bishiyar nan ya sa a baki ya tauna.

    Sai ya ce: “Kai, amma wannan ganye da daɗi yake!” Sai bishiya ta ƙara da cewa: “Ai don ma ba ka ɗanɗana cikina ka ji ba?” Sai Kurege ya tambaye ta ya ce: “Yaya zan yi in ɗanɗana cikinki?” Sai ta ce: “Idan kana so ka shiga cikina sai ka ce: ‘Buɗe bus’ sai ka shiga.

    Idan ka ce: ‘Rufe kif’ bayan ka sha zumar, za ta rufe.” Kurege ya yi godiya, ya matsa kusa da bishiya ya ce: “Buɗe bus.”Tana jin haka sai ta tsage, Kurege ya shiga ya tarar da zuma ya zauna ya sha, har ta yi masa karo. Ya ɗebi wata kuma ya cika jakarsa. Da ya fito daga cikin kogon bishiya, sai ya ce: “Rufe kif.”

    Sai bishiya ta rufe, ya yi godiya, ya kama hanyar zuwa inda suka shirya za su haɗu da Kura. Da ya isa inda suka yi alƙawarin haɗuwa da Kura sai ya tarar da ita tana barci. Ya shure ta, ta farka. Sai ta gan shi yana tanɗar baki, alamun ya ci daɗi, ta tambaye shi, “Kai, me ka samo ne mai daɗi haka?”

    A cikin yanga da burga, Kurege ya ce da Kura: “Na samo wani abu ne mai daɗi, ke kuma fa?” Cikin nadama da mairairaita ta ce: “Ni kam ban samo komai ba sai wani ɗan kanzo. Yunwa ma nake ji. Ɗan ba ni abin da ka samo in ɗanɗana mana.” Sai ya ce: “Idan na ba ki a cikin jaka, za ki cinye har da jakar, amma bari in dangwalo miki.”

    Kurege ya sa tsinke ya dangwalo zuma, ya miƙa wa Kura; ta karɓa ta sa a baki sai ta lumshe idanu da zaƙin zuma ya ratsa ta; sai ta cinye har da tsinken. Nan take fa sai kwaɗayinta ya motsa, ta ce da Kurege: “Gaya mini inda ka samo wannan zuma mai daɗi domin ni ma in je in samo.” Sai ya yi mata kwatancen bishiyar da ta ba shi zuma; Kura ta kama hanya.

    Da ta isa ko hutawa ba ta yi ba, sai kawai ta tsunki ganyen bishiya ta sa a bakinta. Sai daɗi ya sa ta ce: “Amma wannan ganye da daɗi yake.” Da bishiya ta ji haka sai ta ce: “Ai wannan ma kaɗan ne, ba ki ɗanɗana abin da ke cikina ba.” Kura ba tare da ta tambayi yadda ake shiga cikin bishiyar ba, sai kawai ta ce: “Buɗe cikin in shiga in ci daɗin da kika faɗa.”

    Nan take bishiya ta buɗe wa Kura cikinta, ta shiga ta fara warwason zuma, tana sha. Da daɗin zuma ya kwashe Kura sai ta fara wannan waƙar: “Buɗe bus, Rufe kif, Mu sha zaƙi, Kurege ba wayo, Nafi shi shan zuma, Zuma mai daɗi, Ke bishiya rufe kif.” Sai ko bishiya ta rufe.

    Bayan wani ɗan lokaci sai ta ce da Kura: “Ki yi maza ki gama, masu ɗakin nan fa sun kusa dawowa.” Amma saboda wauta irin ta Kura, sai ta ce da bishiya: “Ba komai ko sun zo, ai ina da ƙarfin da zan kore su. Idan sun gan ni ma za su gudu.” Sai ta ci gaba da shan zuma. Ta sha ta ƙoshi, amma kuma ta mance abin da za ta faɗa ƙofa ta buɗe.

    Tana cikin wannan hali ne fa kudan zuma suka dawo daga cin furanni. Suna shiga saƙarsu da ke cikin kogon bishiya suka tarar da Kura; nan take suka far mata da harbi, tana kuka da kugi irin wanda aka san ta da shi. Ta ruɗe, ta rinƙa cewa: “Kif, bishiya kif” maimakon ta ce: “Bus.” Can dai ta yi sa’a ta ce: “Buɗe bus.”

    Bishiya ta buɗe, Kura ta fito da ƙyar, duk jikinta ya kumbura saboda harbin zumar da ta sha; sai ta kama gudu, tana haɗawa da waiwaye, ta doshi inda Kurege ke jiranta. Da Kura ta matsa kusa Kurege ya ga yadda jikinta ya zama, sai ya nemi sanin abin da ya faru.

    Sai ta kwashe labari ta gaya masa; shi kuma ya ce da ita: “Kin cika mantuwa.”Haka dai Kura ta koma gida tana jinya.Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Rashin yin abu da kyakkyawar niyya shi yake sa yin nadama.
    • Yin abu da zuciya ɗaya zai kawo taimakon Allah.
    • Haɗama da rashin godiya ga Allah sukan sa a yi da-na-sani.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Biyu)

    Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Biyu)

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana ’ya’yan Kura sun je yawo gidan Kurege sai suka tarar an yi farfesun Biri. Sai aka ba su suka ci. Da babban cikinsu ya ji daɗin farfesu sai ya ɗebi romon ya shafa a kan gashin kansa ya tafi gida. Da suka koma gida, sai ya je wurin babansa Kure ya ce: “Baba ka dafa kaina mana. ”Da uban ya ji haka sai ya dube shi ya ce: “Ka taɓa jin an cewa uba ya dafa kan dansa ne?

    ”Sai ɗan ya nace shi dai uban ya dafa kansa. Sai ya dafa kan, ya ji danshin romo, ya sa harshe ya lashe. Da ya ji zaƙin romo, a nan take ya tambaye su a inda suka sami wannan abu mai daɗi. Suka amsa masa da cewa a gidan abokinsa Kurege aka ba su. Sai Kure ya sa takalminsa ya tafi gidan Kurege ƙwalama. Da ya isa gidan Kurege sai ya tarar saura kaɗan a tukunya.

    Kurege ya zuba masa ya ci. Da ya ji daɗi sai ya ce da Kurege: “Ina kake samo wannan nama mai daɗi haka?” Sai Kurege ya amsa masa da cewa: “Muna wasa ne a ruwa kullum tare da birrai, sai in daura tarko a ƙafata. Idan mun shiga mun fara kurme a ruwa sai in kama ƙarami a cikinsu, in danne a ruwa har sai ya sha ruwa sosai ya mutu. In sun tafi sun bar shi, sai in ɗauka in yanka mu yi farfesu a gidana.

    ”Da Kure sarkin kwaɗayi ya ji haka sai ya ce: “To in gari ya waye gobe zan bi ka.” Sai Kurege ya amince. Da Kure ya tafi gidansa sai ya kasa barci, ya ƙagara gari ya waye. Can dai da ya ga kamar gari ya ƙi wayewa, sai ya hura wuta ta haske ko ina. Daga nan ya je ya faɗa wa Kurege wai gari ya waye, sai Kurege ya ce: “Haba Kure, ka hura wuta a kan dakinka ka ce gari ya waye?

    Ai gara ka koma gida sai gari ya waye.” Bayan ya koma gida ya ɗan jima gari bai waye ba, sai ya kama zakara ya rinƙa matsa shi har ya rinƙa yin cara. Da Kurege ya fito sai ya ce: “Haba Kure yaya kake damun kanka haka ne? Na gaya maka sai gari ya waye.” Haka dai Kure ya haƙura ala tilas har sai da gari ya waye. Da sassafe ya shirya ya nufi ƙofar gidan Kurege.

    Suka kama hanyar rafi har suka isa, suka tarar da birrai a bakin rafi. Sai Kure da Kurege suka yanke shawarar su shiga cikin ruwa su yi wasan kurme. Da suka shiga tare da birrai sai Kurege ya faki ƙarami daga cikinsu ya danne a ruwa. Shi kuma Kure maimakon ya faki ɗan ƙarami, sai ya nufi kan babba, ya sa masa igiya ya danne shi. Da ya ji Kure zai halaka shi, sai ya yi ƙara, har sauran suka ji, suka watse da gudu.

    Kure da Kurege dai kowa ya kaso Biri daya, amma sai Kuregeya ce: “Kai kuma Kure da muka yi da kai za ka kama karami donkada su gane, sai ka kama babban cikinsu?” Sai Kure ya dubi Kurege ya ce masa ai ƙarami ba zai ƙosar da shi ba, shi ya sa ya kama babba wanda idan ya yi farfesu da shi zai sha ya ƙoshi ya more.

    Washe-gari da suka koma tun safe har yamma suna jira a bakin rafi babu Birin da ya fito bakin rafi. Sai Kurege ya dubi Kure yace da shi: “Kai ka yi mana wannan ɗanyen aiki.” Rannan dai haka suka koma gida, ba su sami nama ba. Sai Kurege ya gaya wa Kure gobe da safe za su je unguwar birrai su gaishe su domin rashin da suka yi na babbansu.

    Da ma birrai sun aika wa Kurege da Kure za su yi taro domin ba su sani ba cewa ko Kure da abokinsa Kurege ne suka kashe musu’yan’uwa. Da gari ya waye suka shirya, sai Kurege ya ce zai hau doki, shi kuma Kure ya hau ɓera. Sai Kure ya ƙi, ya ce tun da shi ne babba shi zai hau doki shi kuma Kurege ya hau ɓeran.

    Haka aka yi; suka kama hanya, kafin su isa sai Kurege yace in sun je shi zai ɗaure abin hawansa a jikin bishiya, sai Kure yace shi ne zai ɗaure a jikin bishiya, domin shi ne babba. Sai Kurege yace to shi zai ɗaure nasa a jikin ciyawa. Da suka isa garin birrai aka yi musu maraba, aka ba su masauki, shi Kure ya ɗaure abin hawansa a gindin bishiya, shi kuma Kuregeya ɗaure nasa abin hawan a jikin ciyawa.

    Suna zaune a masauki aka ce za a kawo musu giya don liyafar baƙunta. Kafin a kawo sai Kurege ya ce ya kamata su yi waƙa. Suka fara waƙa. Kurege yana rerawa yana cewa: “Ni da ƙananan nake wasa, Da ƙananan nake abota.” Shi kuma Kure yana waƙa yana cewa: “Ni da babban nake wasa, Babba na kama, A wasan ruwa mai daɗi” Sai manyan birrai suka ji abin da Kure yake faɗa, sai suka kawo musu giya a ƙwarya.

    Kure yana ta sha, Kurege kuma ya yi kamar tare suke sha amma in ya zuba a ƙoƙo sai ya kwara a jikin shinge, shi kuma Kure ya yi ta shan giya har ya yi tilis. Su kuma manyan birrai suna ta shiri don su rama abinda Kure da Kurege suka yi musu. Nan take birrai suka ƙwala ihu, suka ce a kawo sanduna za su ɗauki fansa. Suka ɗebo sanduna suka nufi kan Kurege da Kure.

    Shi kuma Kure ya riga ya yi tilis da giya ta yadda ba ya jin abinda ake faɗa. Sai ya tambayi Kurege ko me suke cewa a waje? Sai Kurege ya gaya masa cewa an ce a kawo musu farfesun ƙashi da nama. Da Kure ya ji haka sai ya gyara zama, yana dariya da murna wai za a kawo musu nama da ƙashi. A daidai lokacin da birrai suka shigo da sanduna za a fara ma Kurege da Kure, sai Kurege ya kutsa ta jikin shinge, inda yake kwarar da giya, ya gudu.

    Kure kuwa ba zai iya gudu ba, saboda haka suka yi ta jibgar sa. Bayan Kurege ya fita ta baya, kafin su biyo shi har ya hau kan ɓera. Yana taɓa shi sai ya fara gudu. Shi kuma Kure kafin ya fito ya kwance dokinsa daga jikin bishiya, ya rigaya ya sha sanduna har ya faɗi ya suma. Suka ɗauke shi, suka ɗora shi a kan dokinsa, suka kora shi gida. Ya isa gida a galabaice, ya yi ta jinya da kyar ya warke. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Son zuciya, ɓacin zuciya

    Wannan tatsunya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Daya)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Daya)

    Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Daya)

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Kurege da Kura suna yawo, sai suka tsinci ƙyallen fatari. Sai Kurege ya ce, bari ya je ya ɗinka musu riguna da shi. Ya je ya ɗinko riguna biyu, amma girmansu ɗaya. Ya bai wa Kura ɗaya. Da Kura ta saka sai rigar ta matse ta, ta shaƙe mata wuya saboda ta yi mata kaɗan.

    Sai Kurege ya ce da Kura tun da rigar nan ta yi mata kaɗan, sai ta bar masa ita. Da Kura ta ji haka sai ta ce masa: “Daman ka cuce ni ne tun da ka ɗinka rigata daidai da taka, sai ka ɗauka.” Kurege ya haɗa duka biyun, suka shiga jeji don su farauto abinda za su ci. Da suka kamo namun daji da yawa sai suka dawo gindin wata bishiya, suna hutawa.

    Kurege yana so ya cinye namanshi kaɗai, amma ya rasa yadda zai yi. Can sai ya hango wasu ‘yanmata a bakin rafi, sai ya dubi Kura ya ce: “Ga ‘yan mata can, mu je mu yi musu magana. “Sai Kura ta yarda, suka je suka tarar da ‘yan matan suna hira. Suka zauna suna sauraron hirar.

    Da Kurege ya ga hira ta fara yin daɗi sai ya ce da Kura su je su dafa naman nasu. Sai Kura tace ita tana nan a wurin hira, ba za ta je ba. Shi kuwa Kurege sai ya je domin ya dafa musu naman. Ashe ya sami abin da yake so, wato sai ya zaɓi nama mai kyau ya zuba a jakarsa, ya ɓoye. Sai ya samo naman mushe ya dafa, ya ajiye wa Kura. Bayan ta dawo sai ya miƙa mata nama.

    Kura ta hau ci ba ta san mushe ya dafa mata ba. Ta ci nama, irin cin haɗama, amma ta ɗan rage ta ɓoye a jakarta. Kura ba ta da masaniyar cewa Kurege ya ɓoye nama mai kyau, ya ba ta mushe. Saboda wayo irin na Kurege, sai ya dubi Kura ya ce: “Kura ki rage mini naman mana. Saboda haɗama irin ta Kura ita ma sai ta harari Kurege tace:
    Ni ba zan ba ka ba tun da kai ne ka dafa, na san sai da ka zaɓi inda ya fi ko ina daɗi ka ci ka ƙoshi, ba zan ƙara maka ba.

    Da rana ta faɗi, kuma dare ya yi sai suka samu wata bukka suka kwanta, can cikin dare sai zawayi ya kama Kura. Ta nemi Kurege ya raka ta, sai da rana ta faɗi, kuma dare ya yi sai suka sami wata bukka suka kwanta ki, ya ce in zawayin yana damunta, to ta fita waje. Ya ƙara da cewa: “Idan ma abin ya dame ki ai sai ki yi shi a kwance ba sai kin tashi ba.

    Amma idan na ji ihu to babu lafiya, idan kuma abin ya yi tsanani, idan kuma kin yi shiru to lafiya kenan. Sai Kura ta fita waje ta yi kwanciyarta. Jim kaɗan sai kunama ta harbe ta. Kura da raki sai ta ƙwala ƙara, haka dai ta kwana tana zawo. Wayewar gari ke da wuya, sai ta je ta faɗa wa Kurege cewa jiya da daddare kunama ta harbe ta.

    Sai Kurege ya ce: “Ai dama mun yi da ke idan na ji shiru lafiya ta samu, idan kuma na Ji ihu to ta yi tsanani sai in fita in taimaka miki. “Bayan Kura ta ji bayanin Kurege, sai ta ce: “To shi ke nan.” Da suka gama maganganunsu, sai Kurege ya rasa yadda zai yi ya ɗauki naman da ya ɓoye ya kai gida, domin ya sani idan Kura ta gani za ta ƙwace. Sai ya yi dabara ya ba Kura shawara ta je ta sha ruwa, ta wanke jikinta kafin su tafi gida.

    Ba tare da zaton wani abu ba, sai ta kama hanyar rafi. Da Kurege ya ga ta tafi rafi, sai ya ɗauko namansa a inda ya ɓoye, ya saka shi a jakar Kura, shi ma ya shiga cikin jakar. Da ta dawo daga wanka, sai ta ɗauki jakarta ta rataya. Ba ta san Kurege yana cikin jakar ba, sai ta kama hanya. Daɗin waƙa ya sa ta kama hanyar gida ta fara tafiya, ta manta da Kurege.

    Tana cikin tafiya sai ta fara yi wa Jakarta waƙa tana cewa. “Sai ni Kura durungu, Na yi farauta, Na cika jakata da nama, Nama sai mun ture, Ga shi a cikin jakata.” Haka ta rinƙa yi wa jakar waƙa. Sai da ta isa gida ta tuna ta bar cikin jakar Kura, riƙe da namansa ya gudu zuwa gidansa. Shi ya sa duk wanda ya je daji zai ga Kura tana ta yawon nema nai. Shi kuma da za ku je gidansa, za ku tarar da gidan cike yake da nama mai kyau, wanda yake ci ya more. Da babu Gizo da na yi muku ƙarya. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Karamin mai hankali ya fi babba mai wauta.
    • Wauta mai janyo wuya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kishiyoyi Biyu

    Edita@rumasau-kallamu