Tag: Huɗuba

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 31st Octoba 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 31st Octoba 2025

    Fassarar huɗubar Juma’a kai daga Masallaci mai alfarma, ta yau Juma’a 9 Jumadal Ula, 1447 H / 31 October, 2025 M

    Mai Huɗuba: Sheikh Dr. Mahir bin Hamad Almu’aiƙili

    Mai Fassara: Usman Muhammad Ahmad

    Huɗuba ta farko:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda Yake afuwa da yafiya kuma Yake gafarta zunubai, kuma Yake saka wa ma’abota kyautatawa, kuma Yake tunkuɗe musu tsanani da damuwowi, kuma Shi ne wanda Yake talala kuma Yake jinkirtawa don mai laifi ya tuba.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai Yake ba Shi da abokin tarayya, Tsarkakakke daga tawaya da aibuka Wanda Ya ce: ((Haƙiƙa kuma Mun halicci sammai da ƙasa da abin da yake tsakaninsu cikin kwana shida, kuma wata gajiya ba ta shafe Mu ba)).

    Kuma ina shaidawa lallai Annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa, ma’abocin tafkin nan da za a tuzga masa, da matsayin nan da za a masa baiwarsa, duk wanda ya masa biyayya ya tsira, kuma duk wanda ya saɓa masa za a jefa shi a wuta, Allah Ya yi salati a gare shi, da alayensa, da sahabbansa, da matansa, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar da halittu za su koma zuwa ga Ubangijinsu a cikinta, kuma Ya yi masa sallama mai yawa.

    Bayan haka:

    Ya ku taron muminai! Ina muku wasici da ni kaina da tsoron Allah, ku ji tsoron Allah Maɗaukakin Sarki kuma ku masa biyayya, kuma ku sani cewa a gaba gare ku akwai mutuwa da ƙabari, da tashi daga ƙabari da taron filin alƙiyama da sakamako, wasu za su kasance cikin ni’ima da farin ciki, wasu kuma za su kasance cikin azaba da halaka – Allah Ya tsare mu – ((Lallai masu taƙawa suna cikin gidajen aljanna da ƙoramu () A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko)).

    Ya ku al’ummar musulmi!

    Lallai zuciya ita ce abin da Ubangiji Yake la’akari da shi daga bawa, don haka, duk wanda ya haɗu da Allah da zuciya kuɓutacciya, to haƙiƙa ya rabauta kuma ya tsira, kuma duk wanda ya haɗu da Shi da zuciya mara lafiya, to haƙiƙa ya taɓe kuma ya yi asara, kuma cututtukan zukata suna da yawa, kuma daga cikin mafi hatsarinsu akwai cutar ƙeƙashewa, saboda ma’abocin ƙeƙasasshiyar zuciya, yana kawar da kai daga tuba da komawa zuwa ga Allah, har ma a lokacin saukar bala’i da masifa, sai zuciyarsa ta zama makiyaya ce ta Sheɗan, kuma ba ta karɓar wa’azozin Alƙur’ani.

    Allah Maɗaukaki Yana cewa: ((Kuma lallai Mun aika da (manzanni) zuwa ga al’ummomin da suka gabace ka, sai Muka ɗora musu tsananin talauci da cutuka ko sa ƙasƙantar da kai To me ya hana lokacin da musibarmu ta zo musu, su ƙasƙantar da kai? Sai dai kuma zukatansu ne suka ƙeƙashe, Shaiɗan kuma ya ƙawata musu abin da suka kasance suna aikatawa)), kuma Allah Mai girma da ɗaukaka Ya ce: ((To tsananin azaba ya tabbata ga masu ƙeƙasassun zukata da ba sa ambaton Allah. Waɗannan suna cikin ɓata mabayyani)).

    Kuma daga cikin sabuban tausasan zuciya da khushu’inta akwai dawwama a kan ambaton Allah, da tuntuntuni cikin ayoyinsa, da tuna mutuwa da magaginta, da ƙabari da matsansa da duhunsa, da ziyartar maƙabartu, da nazari game da lamuran ranar alƙiyama, ya zo a cikin littafin Ɗabaƙatul Hanabila cewa, wani mutum ya ce wa Imamu Ahmad: “Ta yaya zuciyata za ta yi taushi?”, sai ya ce: “Ka shiga maƙabarta, kuma ka shafa kan maraya”.

    Ya ku ‘yan’uwa masu imani!

    Ita rayuwa gajera ce duk yadda ta yi tsawo, kuma kwanakinta ‘yan kaɗan ne ko yaya suka yawaita, mai dace shi ne wanda ya rayu a cikinta a kan biyayya ga Ubangijinsa, kuma ya yi guzuri a cikinta don ranar haɗuwa da Mahaliccinsa, asararre kuwa, shi ne wanda ya bi son zuciyarsa, kuma ya yi burace-buracen samun kyakkyawar sakamako a wajen Allah, har mutuwa ta afka masa alhali yana cikin gafalarsa.

    Kuma bai mata shiri da aiki nagartacce da zai zama sababin kuɓutarsa ba, kuma masu barin wannan duniya iri biyu ne: Mamaci da zai huta daga wahalar wannan gida ta duniya, ya isa zuwa ga hutu a gidan matabbata, da kuma mamaci da bayi da ƙasa za su huta daga sharrinsa, kuma zai tafi ne zuwa ga mammunan makoma, kuma tur da makwanci.

    Hadisi ya zo a Sahihu Muslim, daga Abu Ƙatada Allah Ya ƙara masa yarda cewa: Lallai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya bi ta wajen wata gawa, sai ya ce: (Wanda zai huta, da wanda za a huta daga gare shi), sai suka ce: Me kake nufi da wanda ya huta da wanda aka huta daga gare shi? Sai ya ce: (Bawa mumini zai huta daga cutarwar duniya da wahalarta zuwa rahamar Allah, shi kuma fajirin bawa bayi da ƙasa, da bishiyoyi, da dabbobi za su huta daga gare shi).

    Ya ku ‘yan uwa masu imani!

    Idan mutum ya mutu, to haƙiƙa alƙiyamarsa ta tsaya, domin ƙabari shi ne farkon matakan lahira, Allah Ya sanya shi ya zama wa’azi da izina, wacce zuciya za ta tausasa da ita, kuma ta tunkuɗe gafala, ta kuma taimaka wurin ƙoƙarin aikata ɗa’a, don haka, babu abin da zai amfanar da mutum a ƙabarinsa face aikinsa, hadisi ya zo a Bukhari da Muslim cewa: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Abubuwa uku ne suke bin mamaci, sai biyu su dawo, ɗaya kuma ya wanzu tare da shi: Iyalansa da dukiyarsa da aikinsa za su bi shi, sai iyalansa da dukiyarsa su dawo, sai aikinsa ya tsaya tare da shi)).

    Don haka ne Usman Allah Ya ƙara masa yarda ya kasance idan ya tsaya a kan ƙabari, sai ya yi kuka, har sai ya jiƙa gemunsa, sai aka ce da shi: Kana tuna aljanna da wuta ba ka kuka, amma kana kuka saboda wannan? Sai ya ce: Lallai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ƙabari shi ne farkon matakan lahira, idan ya tsira a cikinsa, to abin da yake bayansa ya fi shi sauƙi, idan kuwa bai tsira ba, to abin da yake bayansa ya fi shi muni). Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ban taɓa ganin wani abu mai firgitarwa ba face ƙabari ya fi shi firgitarwa). Tirmizi ne ya rawaito a Sunan ɗinshi.

    Ƙabari ya fi shi firgitarwa; saboda mutum yana kasancewa a cikinsa shi ɗaya tilo, ba tare da aboki, ko masoyi, ko mai ɗebe kewa, ko abokin zama ba, kuma akwai matsa a cikinsa, da akwai wani da zai kuɓuta daga wannan matsar, da Sa’adu ɗan Mu’azu ya kuɓuta daga gare ta.

    Ƙabari ya fi shi firgitarwa; saboda akwai fitina a cikinsa, kamar fitinar Dujal koma wacce ta fi ta tsanani, ƙabari ya fi shi firgitarwa; saboda shi ko dai ya zama dausayi ne daga cikin dausayoyin aljanna, ko kuma rami ne daga cikin ramukan wuta – Allah Ya tsare mu – saboda haka, duk wanda ya kasance mai kyautatawa, to ƙabarinsa zai zama yalwa da farin ciki a gare shi, duk kuwa wanda ya kasance mai mummunan aiki, to zai zama kewa da baƙin cikin da damuwa a gare shi.

    Hadisi ya zo a Bukhari da Muslim, Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Shi bawa idan aka sanya shi a ƙabarinsa, kuma abokansa suka juya suka tafi suka bar shi, har ma zai na jin ƙaran takun takalmansu, sai mala’iku biyu su zo masa, sai su zaunar da shi, sai su ce da shi: Me ka kasance kana cewa game da wannan mutumin, wato Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi?

    Sai ya ce: Na shaida cewa shi bawan Allah ne kuma Manzonsa, sai a ce da shi: Ka duba mazauninka a wuta, Allah Ya musanya maka shi da wani mazauni a aljanna), Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare ya ce: (Sai ya gan su gaba ɗaya, amma kuma kafiri ko kuma munafiki sai ya ce: Ban sani ba, na dai kasance ina faɗin abin da mutane suke faɗi ne, sai a ce da shi: Ba ka sani ba, kuma ba ka karanta ba, sannan sai a dake shi da guduma ta ƙarfe da ƙarfi a tsakanin kunnuwansa biyu, sai ya yi ihu da ƙarfi ihun da duk wanda yake kusa da shi zai ji ban da mutane da aljanu).

    Don haka ne ya zama daga cikin shiriyar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai neman tsari daga azabar ƙabari a kowace salla, kamar yadda ya zo a Sahihu Muslim, daga hadisin Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda cewa: Lallai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Idan ɗayanku ya yi tahiya, ya nemi tsarin Allah daga abubuwa guda huɗu, ya ce: Ya Allah ina neman tsarinka daga azabar wutar jahannama, da azabar ƙabari, da fitinar rayuwa da mutawa, da sharrin fitinar Dujal).

    A’uzu billahi minsh-shaiɗanir-rajim: ((Har sai idan da mutuwa ta zo wa ɗayansu zai ce: “Ubangijina, Ku mai da ni (duniya) mana  “Don in yi aiki na gari game da abin da na bari (a rayuwata).” Ina! Lalle wannan kalma ce da yake faɗin ta (da bakinsa). A gabansu kuwa akwai shamaki har zuwa ranar tashinsu Sannan idan aka busa ƙaho to fa babu wata dangantaka (mai amfani) a tsakaninsu a wannan ranar, kuma ba za su tambayi juna ba

    To waɗanda ma’aunansu suka yi nauyi waɗannan su ne masu babban rabo. Waɗanda kuwa ma’aunansu suka yi sakayau waɗannan su ne waɗanda suka yi asarar kawunansu, suna masu dawwama a cikin (wutar) Jahannama)). Allah Ya albarkace mu da Alƙur’ani da sunna, kuma Ya amfanar da mu abin da ke cikinsu na ayoyi da hikima, ina faɗin abin da kuke sauraro, kuma ina nema mana gafarar Allah daga kowane zunubi da laifi, don haka ku nemi gafararsa, lallai Shi Ya kasance Mai gafara ne Mai jin ƙan.

    Huɗuba ta biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, dukkan yabo ya tabbata ga Allah Mai tabbatar da zukata, Mai gafarta zunubai, ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah Shi, kaɗai Yake ba Shi da abokin tarayya, Mai yaye damuwa, kuma ina shaidawa lallai Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da Alayensa da Sahabbansa, da aminci mai yawa.

    Bayan haka, ya ku taron muminai!

    Lallai a cikin ziyartar maƙabartu akwai wa’aztuwa da ɗaukan izina da suke zaburar da mutum a kan tsoro da fargaba, da kuma gaggawa wurin ɗa’a da aiki, kuma duk wanda ya ji tsoro zai yi gaggawa, kuma duk wanda ya yi gaggawa zai kai ga matsayin da yake fata, saboda haka ne Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya kwaɗaitar game da ziyartar maƙabartu don wa’aztuwa da ɗaukar izina, ya zo a cikin Musnad na Imamu Ahmad cewa: Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Na kasance ina hana ku ziyartar ƙaburbura.

    to ku ziyarce su domin za su tunatar da ku lahira), kuma ziyartar maƙabartu yana da hukunce-hukunce da ladubba, daga cikinsu akwai yin addu’a ga mamata, domin ƙaburbura cike suke da duhu, amma Allah yana haskaka su sakamakon addu’ar salihai daga cikin bayinsa, ya zo a cikin Sahihu Muslim daga hadisin Abu Huraira Allah ya ƙara masa yarda cewa: “Wata mata baƙa ta kasance tana hidima a masallacin Annabi, sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya daina ganinta, sai ya tambayi inda take, sai suka ce: ta rasu, sai ya ce: (Me ya sa ba ku sanar da ni ba?)

    Kamar dai sun raina lamarinta, sai ya ce: (Ku nuna min ƙabarinta), sai suka nuna masa, sai ya yi mata salla, sannan ya ce: (Waɗannan ƙaburbura a cike suke da duhu ga ma’abotansu, kuma lallai Allah Maɗaukaki yana haskaka musu sakamakon addu’ata gare su), kuma ya kasance daga cikin shiriyarsa tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi, idan ya zo maƙabarta, yana cewa: (Assalamu ala ahlid diyari minal muminina wal musulmin, wa yarhamullahul mustaƙdimina minna wal musta’akhirin, wa inna insha Allahu bikum lalahiƙun), Muslim ne rawaito shi.

    Ya ku taron ‘yan-uwa!

    Lallai ƙaburbura suna da alfarma, don haka ba ya halatta ga mutum ya taka su, ko ya zauna a kansu, ya zo a cikin Sahihu Muslim cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Mutum ya zauna a kan wuta ta ƙone tufafinsa har ta kai ga fatarsa, shi ya fi alheri gare shi sama da ya zauna a kan ƙabari).

    Haka kuma, Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya hana fuskantar ƙaburbura yayin salla, da riƙar maƙabartu a matsayin wurin salla, ya zo cikin Bukhari da Muslim daga Aisha Allah ya ƙara mata yarda cewa: “lallai Ummu Habiba da Ummu Salama Allah ya ƙara musu yarda sun ambaci wani coci da suka gani a Habasha mai ɗauke da hotuna a cikinsa, sai suka ba da labarinsa wa Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi, sai ya ce: (Lallai su waɗannan mutanen idan wani mutumin kirki ya mutu a cikinsu sai su gina masallaci a kan ƙabarinsa, sannan su zana waɗancan hotunan, kuma waɗannan su ne mafiya sharrin halitta a wurin Allah a ranar alkiyama).

    Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Ku saurara! lallai waɗanda suka gabace ku sun kasance suna riƙar ƙaburburan annabawansu da salihansu a matsayin masallatai, lallai na hane ku daga yin hakan). Muslim ne ya rawaito shi.

    Ya ku bayin Allah! Kuma hakan ya kasance ne saboda lallai shi wuce iyaka game da ƙaburburan salihai yana kai mutum ga yin shirka da Allah, ga babban malamin tafsirin nan, Abdullah ɗan Abbas Allah ya ƙara musu yarda, yana faɗi a ƙarƙashin fassarar faɗin Ubangiji Maɗaukaki: ((Kuma suka ce: kada ku bar ababen bautarku, kuma kada ku bar Wadda da Suwa’a da Yagusa da Ya’uƙa da Nasra)), ya ce:

    “Waɗannan sunaye ne na wasu mutane salihai daga cikin mutanen Annabi Nuhu, yayin da suka mutu, sai Shaiɗan ya yi wahayi ga mutanensu cewa su kafa hotunansu a wuraren da suke zama, kuma su sa musu sunayensu, sai suka yi haka, ba tare da suna bauta musu ba, har sai da waɗannan suka mutu, kuma ilimi ya bace, sai aka fara bauta musu”. Bukhari ne ya rawaito shi.

    Saboda haka, ya kai bawan Allah! ba ya halatta a girmama ƙaburburan salihai, ko a yi gini a kansu, bare kuma a riƙa kewaye su da ɗawafi, ko yanka ko bakance dominsu, ko kiran ma’abotansu, ko neman agaji a wajensu, a neman biyan buƙatu ko yaye damuwa, don haka mu ji tsoron Allah ya ku Musulmi, kuma mu taƙaita da abin da aka shar’anta ziyartar ƙaburbura saboda su, na wa’aztuwa da ɗaukan izina, da sallama ga mamata, da yi musu addu’a, kuma kada mu ƙirƙiro wani abu da zai fusata Ubangiji a wurin.

    Haƙiƙa ya zo cikin Musnad na Imām Ahmad cewa, Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Na hana ku ziyartar ƙaburbura, to ku ziyarce su, amma kada ku faɗi abin da zai fusata Ubangiji), a wata ruwayar kuma: (Amma kada ku faɗi magana marar kyau), wato: maganar banza, kuma bai dace ga wanda ya je maƙabarta ya shiga cikin zancen duniya ba, ko yin dariya da barkwanci, bari dai, abin da ya dace shi ne ya yi tunani game da halin ma’abota ƙaburburan, haka kuma, ana so ya yi tunani a kan halinsa da makomarsa, da kuma cewa shi ma mai tafiya ne zuwa wurin da suka tafi.

    Sannan ku sani, ya ku taron muminai cewa, lallai Allah Ya umarce ku da wani umarni mai daraja wanda Ya fara da kansa, sai Ya ce: ((Lallai Allah da mala’ikunsa suna yin salati wa Annabi. Ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah Ka yi salati ga Annabi Muhammad da matansa da zuriyarsa kamar yadda Ka yi salati ga iyalin Annabi Ibrahim, kuma Ka yi albarka ga Annabi Muhammad da matansa da zuriyarsa kamar yadda Ka yi albarka ga iyalan Annabi Ibrahim, lallai Kai ne Sha-yabo Mai girma.

    Ya Allah, Ka ƙara yarda da halifofi shiryayyu, Abubakar da Umar da Usman da Ali, da sauran sahabbai da tabi’ai, da waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar alkiyama, kuma Ka haɗa mu tare da su cikin afuwarka da karamcinka da kyautarka, ya Mafi tausayin masu tausayi.

    Ya Allah, Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmai, Ka sanya wannan ƙasa ta zama mai aminci da kwanciyar hankali da wadatar arziki da yalwa, da sauran ƙasashen Musulmai.

    Ya Allah, Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu da majiɓinta al’amuranmu, kuma Ka ƙarfafi shugabanmu kuma jagoranmu da gaskiya.

    Ya Allah Ka datar da shugabanmu hadimin masallatai biyu masu alfarma da gaskiya, tare da magajinsa amintacce zuwa ga abin da ɗaukaka ne ga Musulunci da gyaruwar Musulmai, da kuma abin da alheri ne ga ƙasa da mutane, tare da dukkan shugabannin musulmai.

    Ya Allah, Ka kiyaye mana addininmu, da shugabancinmu da tsaronmu, ya Allah Ka datar da jami’an tsaronmu da sojojinmu masu tsaro a kan iyakoki da fagage.

    Ya Allah, Ka tabbatar da aminci da zaman lafiya da kwanciyar hankali da nutsuwa ga ‘yan-uwanmu a Falasɗinu.

    Ya Allah Ka kiyaye Masallacin Ƙudus, kuma Ka sanya shi ya kasance mai ɗaukaka har zuwa ranar alkiyama.

    Ya Allah, Ka yaye damuwar masu damuwa daga cikin musulmai, Ka kwaranye baƙin cikin masu bakin ciki, Ka biya bashin waɗanda ake bi bashi, kuma Ka warkar da marasa lafiya daga cikinmu da na sauran musulmai.

    Ya Allah, Ka sanya ƙaburburanmu su zama mafi alherin masauƙanmu bayan mutuwa, Ka sanya su su zamto dausayi daga cikin dausayoyin aljanna, saboda rahamarka, ya Mai ni’imtarwa, ya Ma’abocin ɗaukaka da girma.

    Ya Allah, Ka gafarta wa Musulmi maza da mata, da muminai maza da mata, rayayyunsu da matattu.

    ((Ya Ubangijinmu! Ka ba mu mai kyau a duniya da mai kyau a Lahira, kuma Ka tsare mu daga azabar wuta!).

    ((Ya Ubangijnmu! Ka karɓa daga gare mu, lallai Kai Mai ji ne kuma Masani. Kuma Ka karɓi tubanmu lallai Kai ne Mai yawan karɓar tuba kuma Mai jin ƙai)).

    ((Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka Ubangijin buwaya game da abin suke siffanta Shi da shi () Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni () Kuma dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai)).

    Karanta Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Edita @rumasau-kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Huɗubar Juma’a daga Masallaci mai alfarma:21 Safar 1447
    15 August 2025
    Mai huɗuba: Sheikh Dr. Bandar bin Abdul-Aziz Badila
    Mai fassara: Dr. Usman Muhammad Ahmad
    Shugaban sashi: Dr. Abdulkarim Tahir Abdullahi

    Huɗuba ta farko:
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Ya halicci halittu kuma Ya ƙaddara ƙaddarori, Ya rarraba arziki kuma Ya rubuta ajali, muna yaba masa tsarki ya tabbata a gare Shi kuma muna gode masa, Ya fari halittar rayuwa kuma Ya gudanar da ƙoramu, Ya shimfiɗa ƙasa kuma Ya tsaga tekuna.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Ya hore rana da wata, da dare da yini. Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa, kuma zaɓaɓɓen Annabinsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da alayensa tsarkaka, da sahabbansa nagartattu, da waɗanda suka biyo su da kyautatawa a dukkan darare da yini.

    Bayan haka:
    Ya ku mutane! Ina muku wasici da ni kaina da tsoron Allah, ku ji tsoron Allah, Allah Ya muku rahama, kuma ku sani cewa babu abin da ke faruwa a cikin wannan rayuwa face sai da ƙaddarar Allah da kuma nufinsa, da hikimarsa da iradarsa; na dare da yini, da iska da ruwan sama, da sanyi mai tsanani da zafi, da sauye-sauyen yanayi da maimaituwarsa, abin da zai sa mumini ya tabbatar da cewa wannan duniya ba gidan dawwama ba ce.

    Kuma wannan gaba ɗayansa yana daga cikin ayoyin Allah na halitta masu nuna girman ƙarfinsa da ikonsa, da yalwar iliminsa da hikimarsa, da zurfin nufinsa da rahamarsa, da kuma cewa kowane abu a wurinsa tsarki ya tabbata a gare Shi yana da iyaka.
    ((Lallai a cikin halittar sammai da ƙasa da sassaɓawar dare da rana, tabbas akwai ayoyi ga ma’abota hankula Su ne waɗanda suke ambaton Allah a tsaye da kuma zaune da kuma kishingiɗe, suna kuma tunani a kan halittar sammai da ƙasa (suna cewa: “Ya Ubangijinmu, ba Ka halicci wannan a banza ba, tsarki ya tabbata gare Ka, Ka tsare mu daga azabar wuta)).

    Ya ku bayin Allah!
    Waye a cikinmu da zafin rani bai taɓa cutar da shi ba? Kuma waye a cikinmu da ƙunar rana ba ta taɓa ƙona fuskarsa ba? Dukanmu mun samu rabonmu daga wannan, ko dai kaɗan ko ko dayawa, lallai wannan shi ne zafin rani, mai wa’azin nan da Allah Yake tunatar da bayinsa zafin taron alƙiyama da azabar wuta da shi.

    An rawaito daga Miƙdad ɗan Aswad Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: (Za a kusanto da rana ga halittu a ranar alƙiyama har ta kasance kamar tazarar mil daga gare su). Sulaim ɗan ‘Amir ya ce: Na rantse da Allah ban san me yake nufi da mil ba, yana nufin na tazarar ƙasa, ko ko mil da ake amfani da shi wajen sanya kwalli a ido? Ya ce: (Sai mutane su kasance cikin zufa gwargwadon ayyukansu; daga cikinsu akwai wanda zufa za ta kai masa idanuwan sawu, akwai kuma wanda za ta kai masa gwiwoyi, akwai wanda za ta kai masa zuwa ga kwuiɓinsa, akwai kuma wanda zufa za ta yi wa bakinsa linzami sosai). Sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi nuni zuwa ga bakinsa da hannunsa. Muslim ne ya rawaito shi.

    Ya ku musulmi!
    Lallai tsananin zafi yana daga cikin ayoyin da Allah yake aiko wa bayinsa don tsoratarwa da tunatarwa, da zama wa’azi da ɗaukan izina, kamar yadda Allah Ya ce: ((Kuma ba Ma aiko da ayoyi sai don tsoratarwa)).

    An rawaito aga Abu Huraira Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Wuta ta kai kokenta ga Ubangijinta, ta ce: Ya Ubangiji, sashina na cin sashi, sai Ya ba ta izinin numfasawa sau biyu; numfasawa a lokacin sanyi, da numfasawa a lokacin zafi, to wannan shi ne mafi tsananin zafin da kuke ji a lokacin rani, da kuma mafi tsananin sanyi da kuke ji a lokacin hunturu). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

    To, ya ku muminai! Mai rabo, shi ne wanda ya yi guzuri daga zafin duniya domin kuɓuta daga zafin lahira, da kuma wanda ya yi haƙuri da ibada a lokacin tsananin zafi, domin ya more ni’imar da ba ta ƙarewa a ranar da za a tona ɓoyayyun sirrikan zukata.
    ((Ya ku waɗanda kuka yi imani, ku kare kanku da iyalanku daga wuta, wacce makamashinta mutane ne da duwatsu, masu kula da ita mala’iku ne masu kaushin hali, masu tsananin gaske, ba sa saɓa wa Allah abin da Ya umarce su, kuma suna aikata abin da aka umarce su da aikata shi)).

    An rawaito daga Abu Sa’id Alkhudri Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: (Duk wanda ya yi azumin yini ɗaya saboda Allah, Allah zai nesanta fuskarsa daga wuta na tsawon shekara saba’in). Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.

    Kuma Abu Darda Allah ya ƙara masa yarda ya kasance yana cewa: “Ku azumci yini mai tsananin zafin rana saboda kuɓuta daga zafin ranar tashin alƙiyama, kuma ku yi raka’a biyu cikin duhun dare saboda ku kuɓuta daga duhun ƙaburbura”. Abu Nu’aim ne ya rawaito shi a Hilya.

    Kuma ku sani Allah Ya jiƙan ku cewa dukkan abin da zai samu mumini a cikin zafi na tsanani da wahala, da gajiya da ƙosawa, to, dukkansu za a rubuta su, za a kiyaye su kuma za a ƙididdige su, a wajen Wanda ayyukan ƙwarai ba sa tozarta a wajensa, kuma ba a rasa ayyukan ɗa’a a wajensa, da su za a kankare zunubai, kuma a ninka kyawawa, kuma a ɗaga darajoji.

    An rawaito daga Abu Sa’id da Abu Huraira Allah Ya ƙara musu yarda, sun ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Babu wani abu da zai samu musulmi, na ciwo, ko wahala, ko jinya, ko bakin ciki, har ma da damuwa da za ta sauko masa, face sai an kankare masa zunubansa da shi). Muslim ne ya rawaito shi.

    Kuma lallai ayyuka ana ninninka ladansu, kuma ana ƙara sakamakonsu, kuma ma’auninsu na nauyaya, da gwargwadon abin da ya tabbata na niyya da ikhlasi da juriya da haƙuri a zukatan ma’abotansu. Ibnul Asir Allah Ya yi masa rahama ya ce: “Kuma neman lada a cikin ayyuka nagartattu da kuma lokacin da ake ƙi, shi ne gaugawa zuwa ga neman lada da kuma samun sa ta hanyar miƙa wuya da haƙuri”. Ƙarshen maganarsa kenan.

    Kuma yana daga cikin rahamar Allah ga bayinsa shar’anta musu abin da za su iya yi na ayyuka da ya yi, kuma bai ɗaura musu abin da zai wahalar da su ba, an rawaito daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda, daga Annabi tsirda da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Idan zafi ya tsananta, to ku sanyaya sallarku, saboda tsananin zafi daga hucin Jahannama yake). Bukhari da Muslim ne suka rawaito. Abin da ake nufi da sanyaya salla, shi ne jinkirta ta zuwa ƙarshen lokacinta, lokacin da zafin garji zai yi sauƙi, kafin shigar lokacin sallar da za ta biyo bayanta.

    Kuma za a gwama dukkan wata ibada da ke cikin jinsinta da ita, cikin abin da ya halatta a jinkirta shi, don haka, duk wanda ake bin shi azumi na watan Ramadan, ko kuma kaffara ta azumi ko makamancin haka, to, ya halatta a gare shi ya jinkirta shi zuwa ga lokutan sanyi, idan biyansa a lokacin zafi zai ba shi wahala, akwai hadisin A’isha Allah Ya ƙara mata yarda da yake nuni a kan haka, ta ce: “a kan samu wani lokaci da ake bi na azumi da na sha tun a watan Ramadan, amma na kasa samun daman biya sai a watan Sha’aban”. Bukhari da Muslim ne suka rawaito. Amma gaggauta biya shi ya fi,

    Don haka, ya ku bayin Allah!
    Ku gode wa Allah a bisa dukkan hali da yanayi, kuma ku gade masa a kan abin da Ya tanada muku na hanyoyi da sabuba, waɗanda Ya sauƙaƙe muku wahalar zafi da tsananinsa da su, da ƙunarsa da hucinsa, da na’urorin sanyayawa da wuraren hutu a lokacin zafin rani, kuma ku riƙa bincikan halin ‘yan uwanku talakawa da marasa abin hannu, kuma ku sauƙaƙa musu abin da suke fama da shi na tsananin zafi da ƙunar rana, kowa ya yi dai dai ƙarfinsa da ikonsa, kuma daga cikin haka akwai shayar da ruwa mai sanyi a waɗannan lokuta na zafi, saboda hakan yana daga cikin sadokoki mafiya falala, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ba mu labarin hakan.

    Kuma ku riƙa tunawa da wasu ‘yan’uwanku a Addini, waɗanda raɗaɗin rashi da tawaya ta dukiya da rayuka da ‘ya’yan itacuwa suka ƙaru a gare su a kan abin da suke fama da shi na tsananin zafi, ya Allah Ka yaye musu abin da ya sauko musu, ya Allah Ka sauya tsoronsu da aminci, biƙin cikinsu da farin ciki, yunwarsu da ƙoshi, kuma Ka taimake su a kan maƙiyanka kuma maƙiyansu ya Mai ƙarfi ya Mabuwayi.

    Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina nema wa kaina gafarar Allah, da ku da sauran musulmi, daga kowane zunubi, don haka ku nemi gafararsa, lallai Shi Mai yawan gafara ne kuma Mai jinƙai.

    Huɗuba ta biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda dukkan al’amura suke samuwa daga aikinsa da nufinsa, muna yaba masa tsarki ya tabbata a gare Shi kuma muna gode masa a bisa falalarsa mai yalwa da ni’imominsa, da kyakkyawar afuwarsa da gafararsa, tsira da amincin Allah su ƙara tabbata ga mafificin Manzanninsa kuma zaɓɓaɓensa, da alayensa, da sahabbansa da tabi’ai, da waɗanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar rarrabewa da tashin alƙiyama.

    Bayan haka: Ku sani, Allah Ya muku rahama, cewa lallai bayyana fushi da raki don tsananin zafi yana daga cikin suka ga hukuncin Allah da ƙaddararsa, da nufinsa da ganin damansa, da kuma cewa lallai babu abin da zai auku a wannan duniya face sai da wata hikima da maslaha da fa’ida da amfani, daga cikin haka akwai yadda muke ganin dayawa daga cikin shukoki da ‘ya’yan itatuwa ba sa yin daɗi kuma ba sa daidaituwa har sai lokacin da rani ya kai maƙurarsa, haka kuma dayawa daga cikin cututtuka da annoba ba sa ɓacewa har sai lokacin da zafi ya kai ƙololuwar matakinsa, Ibnul Ƙayyim Allah Ya masa rahama ya ce:

    “A lokacin rani, iska na rikiɗewa ta yi zafi sosai, sai ‘ya’yan itatuwa su nuna, kuma sauran ababe marasa amfani da ababen da suka cakuɗu da jiki su gushe a lokacin hunturu, kuma sai sanyi ya kutsa ya shiga cikkuna, don haka ne ma maramaren ruwa da rijiyoyi suke yin sanyi”. Ƙarshen maganarsa kenan.

    Saboda haka, ku ji tsoron Allah, ya ku bayin Allah, kuma ku kiyaye zukatanku da harsunanku daga dukkan abin da zai rage imaninku, ya lalata tauhidinku, domin yana daga cikin cikar tauhidi yarda da kuma miƙa wuya ga dokokin Allah na shari’a da tsarinsa na gudanar da duniya.

    Sannan ku yi salati da sallama ga mafi alherin halittun Allah, Muhammadu bin Abdullahi, domin Ubangijinku Ya umarce ku da hakan, sai Ya ce: ((Lallai Allah da mala’ikunsa suna salati ga Annabi; ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah, Ka yi salati da sallama, da ƙarin daraja da albarka ga bawanka kuma ManzonKa, Annabinmu Muhammadu, kuma ka ƙara yarda da sahabbai baki ɗaya, da tabi’ai, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
    Ya Allah, ka ɗaukaka Musulunci da Musulmai, Ka kiyaye shingen addini, Ka taimaki bayinka muminai masu tauhidi.

    Ya Allah, ka yaye damuwar masu damuwa daga cikin musulmai, ka kwaranye baƙin cikin masu baƙin ciki, Ka biya bashin wadanda ake bi bashi, Ka warkar da marasa lafiya daga cikinmu da na sauran musulmai.

    Ya Allah Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu kuma jagororinmu, Ka ƙarfafi Shugabanmu kuma jagoranmu Hadimin Masallatai Biyu Masu alfarma da gaskiya da dace da gamonkatar, Ya Allah, ka tsawaita rayuwarsa cikin waraka da ƙoshin lafiya, da ni’ima mai yalwa kuma cikakkiya, kuma Ka datar da shi da magajinsa amintacce ga abin da alheri ne ga ƙasa da mutane, da ɗaukaka ga Musulunci da musulmi ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka kasance Mai ƙarfafawa da kawo ɗauki da agazawa da taimako ga ’yan’uwanmu masu rauni, ya Allah, Ka taimake su a ƙasar Falasɗinu a kan yahudawa ‘yan ƙwace, ya Allah, Ka ƙididdige adadin yahudawa, Ka halaka su ɗaya bayan ɗaya, kuma kada Ka bar ko ɗaya daga cikinsu.

    Ya Allah Ka kiyaye dakarunmu masu dako a kan iyakoki da fagage, Ya Allah, Ka kiyaye su da idonka da ba ya barci, Ka tsare su da ƙarfinka da ba a iya rinjayarsa ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka azurta mu da haƙuri akan jarrabawa, da yarda da ƙaddara, da godiya a lokacin yalwa, kada Ka ɗora mana abin da ya fi ƙarfinmu, domin aminci daga gare Ka shi ya fi yalwa a gare mu ya Mafi tausayin masu tausayi.

    Ya Allah Ka tsare mu daga azabarka a ranar da Za Ka tashi bayinka, ya Allah Ka tsare mu daga azabarka a ranar da Za Ka tashi bayinka.
    ((Ubangijinmu, Ka ba mu alheri a duniya, da alheri a lahira, kuma Ka tsare mu daga azabar wuta))
    ((Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin buya daga abin da suke sifantaShi da shi () Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni () Kuma dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai)).

    Karanta Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya 1st August 2025

    Edita@rumasau-kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 11/7/25

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 11/7/25

    Mai huɗuba: Sheikh Dr. Bandar bin Abdul-Aziz Badila

    Mai fassara: Dr. Usman Azzuhree

    Huɗuba ta farko:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Mai jin ƙai, Mai rahama, Mai karamci, Mai yawan baiwa. Ina yaba Masa tsarki ya tabbata a gare Shi kuma ina gode Masa, Mai yawan afuwa, Mai yalwar yafiya.

    Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya; tausayinSa ya game dukkan halittu, kuma rahamarSa ta yalwaci mutane da aljanu. Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa, Ubangijinsa ya aiko shi a gabanin Ƙiyama da gaskiya da ma’auni, da afuwa da kyautatawa, tsira da aminci da albarkar Allah su ƙara tabbata a gare shi, da alayensa da Sahabbansa ma’abota tuba da komawa ga Allah.

    Bayan haka:

    Ya ku mutane! Ina yi muku wasici, da ni kaina da tsoron Allah, ku ji tsoron Allah, Allah Ya jiƙan ku, kuma kada ku ɗebe tsammanin samun rahamar Allah, kuma kada ku yanke ƙaunar samun jinƙai daga Allah: (Saboda lallai Allah Maɗaukaki yana shimfiɗa hannunSa da dare domin wanda ya yi laifi da rana ya tuba, kuma yana shimfiɗa hannunSa da yini domin wanda ya yi laifi da dare ya tuba, har sai rana ta fito daga mafaɗarta).

    Muslim ne ya ruwaito.

    Ya ku bayin Allah! Lallai Allah Maɗaukaki ya sanya ɗabi’u na sha’awa da karkata zuwa ga ababen so a cikin zukatan ‘ya’yan Adam, wanda hakan ya sa suka zama tushen umurni da hane-hane da aka ɗaura musu, kuma ya rubuta musu rabonsu daga saɓo domin gwaji da jarrabawa: ((Domin Allah ya san wanda ke tsoronSa a bayan ido)).

    Suratul Ma’ida (94).

    An ruwaito daga Anas ɗan Malik Allah Ya ƙara masa yarda, ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Dukkan ɗan Adam mai kuskure ne, kuma mafi alheri cikin masu kuskure su ne masu tuba). Imam Ahmad ne ya rawaito a Musnad.

    Manufar hakan kuwa ita ce; masu tuba su koma gare Shi, kuma masu komawa su fuskance Shi, kuma masu tsoron Sa su rusuna a gabanSa, an rawaito daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda, ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ina rantsuwa da Wanda raina ke hannunSa, da ba ku yi zunubi ba, da Allah ya kawar da ku, ya kawo wasu mutane waɗanda za su yi zunubi, sannan su nemi gafara daga Allah, kuma Allah Ya gafarta musu).

    Muslim ne ya ruwaito.

    Kuma lallai daga cikin manyan siffofin Allah Maɗaukaki akwai siffar rahama, Allah Maɗaukaki Ya ce: ((Rahamata ta yalwaci komai)). Suratul A‘rāfi (156).

    Kuma lallai daga cikin mafi girman sunayenSa akwai Ar-Rahmān da Ar-Rahīm, wato Mai rahama Mai jinƙai, kamar yadda Ya ce: ((Kuma abin bautarku abin bauta ne guda, babu abin bautawa bisa cancanta sai Shi, Mai rahama Mai jinƙai)). Suratul Baƙara (163).

    Kuma Ya kwaɗaitar da bayinSa da su kasance masu jin ƙai ga halittu. An ruwaito daga Usāma ɗan Zaid Allah Ya ƙara masa yarda, cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Lallai waɗanda Allah Yake tausayin su cikin bayinSa su ne masu tausayi). Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

    Kuma an rawaito daga Abdullah ɗan Amr Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Allah Mai rahama yana jinƙan masu jinƙai, ku ji ƙan waɗanda ke bayan ƙasa, Wanda yake sama Zai jiƙan ku). Ahmad ne ya rawaito a Musnad ɗinsa.

    Kuma daga cikin rahamarSa tsarki ya tabbaya a gare Shi ga bayinSa akwai saukar musu da littattafai da Ya yi, kuma Ya aiko musu Manzanni, kuma bai gaggauto musu da uƙuba ba, ((Idan da Allah Yana (saurin) damƙar mutane saboda laifin da suka aikata, to, da bai bar kowane mai rai ba a bayan ƙasa, sai dai kuma Yana saurara musu ne zuwa wani lokaci ƙayyadajje)). Suratu Faɗir (45).

    Kuma Ya kwaɗaitar da su zuwa ga tuba, kuma ya kira su zuwa ga dawowa gare Shi, sai Ya ce: ((Ka ce: Ya ku bayiNa waɗanda suka lalata kawunansu (da kafirci da saɓon Allah), kada ku ɗabe ƙauna daga rahamar Allah. Lallai Allah Yana gafarta dukkan zunubai. Lallai Shi Mai gafara ne, Mai jin ƙai)). Suratuz Zumar (53).

    Sannan Allah tsarki ya tabbata a gare Shi Ya yi musu alkawarin gafarar zunubai da kuma kankare munanan laifuka, sai Ya ce: ((Kuma waɗanda idan suka aikata alfasha ko suka zalunci kawunansu, nan take sai su tuna da Allah, sai su nemi gafarar zunubansu. Kuma wa ya ke gafarta zunubai in ba Allah ba? Kuma ba sa dogewa a kan abin da suka aikata alhali suna sane)). Suratu Ali Imran (135).

    Kuma Allah tsarki ya tabbata gare Shi Ya lamunce wa duk wanda ya tuba kuma ya koma gare Shi cewa zai mayar da miyagun ayyukansa su zama kyawawa kamar yadda Ya ce: ((Sai dai wanda ya tuba, kuma ya yi imani, kuma ya aikata aiki nagari, to, waɗannan ne Allah zai mayar da munanan ayyukansu su zama kyawawa. Kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai)). Suratul Furƙan (70).

    Kuma Ya umarci AnnabinSa da ya tausaya wa mutane, ya ji ƙansu, kuma ya karɓa daga gare su, sai Ya ce da shi: ((To, Saboda rahama ta musamman daga Allah, sai ka zama mai tausayawa a gare su; in da kuwa ka kasance mai kaushin mu’amala, mai ƙeƙasasshiyar zuciya ne, to, da sun watse sun barka. Saboda haka, ka yi musu afuwa, kuma ka roƙa musu gafara, kuma ka shawarce su cikin dukkan lamura; amma idan ka riga ka ƙulla niyya, to, ka dogara ga Allah. Lallai Allah yana son masu dogaro a gare Shi)). Suratu Ali Imran (159).

    Bari dai, Tausayinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana isa har zuwa ga waɗanda suka yi masa adawa daga cikin mushirikai, saboda girman abin da ke jiran su a Ranar Alƙiyama, yana fatan su shigo Musulunci, don tsoron kada su mutu a kan shirka, sai su cancanci azabar wuta, Allah Mai ɗaukaka da buwaya Ya ce yana Mai bayyana hakan a wurare da dama cikin littafinsa: ((To ko mai yiwuwa ne za ka kashe kanka da baƙin ciki, in ba su yi imani da wannan zancen ba (watai Alƙur’ani)). Suratul Kahfi (6).

    Kuma ya ce: ((Ko za ka kashe kanka ne don ba su zama muminai ba?)). Suratush-Shu’ara’ (3). Kuma ya ce: ((Kada ka kashe kanka saboda bakin ciki a kansu. Lallai Allah Masani ne ga abin da suke aikatawa)). Suratul Faɗir (8). Malaman tafsiri suka ce: Ma’ana: Kana shirin halakar da kanka saboda baƙin ciki a kansu.

    To, ya ku bayin Allah! Ku ji tsoron Allah, ku kasance masu tausayi ga bayin Allah, kuma ku kyautata musu, ku tausasa musu, ku yi koyi da halin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, an rawaito daga Abū Huraira Allah Ya ƙara masa yarda cewa: lallai wani baƙauye ya yi fitsari a cikin Masallaci, sai mutane suka tashi don su afka masa, sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da su: (Ku bar shi, ku zuba guga na ruwa ko bokiti na ruwa a in da ya yi fitsarin, domin an aiko ku ne masu sauƙaƙawa, ba masu tsanantawa ba). Bukhari ne ya ruwaito.

    Kuma an rawaito daga Abu Musa Allah Ya ƙara masa yarda, ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan zai aika wani daga cikin Sahabbansa zuwa ga wani lamarinsa, sai ya ce: (Ku yi bishara, kada ku yi kora; ku sauƙaƙa, kada ku tsananta). Muslim ne ya rawaito.

    Ku yi hattara sosai! Kada mumini ya zama katanga a kan tafarkin Allah, ko mai koran mutane daga addinin Allah, ko shinge da ke hana mutane samun kusanci da Allah, alhali bai sani ba, domin zukata suna hannun Allah tsarki ya tabbata a gare Shi, kuma Shi ne Yake sanin abin da ke cikinsu na imani, da yaƙini, da gaskiya, da ƙauna ko ya ya kuwa bawa ya dulmiya cikin zunubai, kuma ko ma waɗanne irin munanan laifuka ya aikata.

    Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina nema wa kaina gafarar Allah, da ku da dukkan Musulmi daga kowane zunubi, don haka, ku nemi gafararSa, domin Shi Mai gafara ne, kuma Mai jin ƙai.

    Huɗuba ta biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Yana karɓar tuba daga bayinSa, kuma Yana yin afuwa ga laifuka masu yawa. Ina yaba Masa, tsarki ya tabbata gare Shi, kuma ina gode masa, Yana yafe tuntuɓe, kuma Yana suturce aibuka, kuma Yana ƙarfafa masu rauni.

    Ina shaidawa lallai babu abin bautawa bisa cancanta sai Allah Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya, idan aka yi aiki kaɗan Yana ba da sakamako mai yawa. Kuma Ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa, mai bishara, da kuma gargaɗi, kuma fitila mai haskakawa, tsira da aminci da albarkar Allah su ƙara tabbata a gare shi, da Alayensa da Sahabbansa masu rangwame da kuma sauƙaƙawa.

    Bayan haka:

    Ya ku bayin Allah!

    Kishi a kan addini, da yin fushi idan aka taɓa Shari’ar Allah, na iya jawo wasu jama’a daga cikin Musulmi ko wasu gungun Muminai, idan sun ga ana aikata mummunan aiki, ko suka samu ana aikata saɓo, su wuce gona da iri wajen yin hani da kuma ƙetare iyaka wajen inkari, wataƙila ma har wasu daga cikinsu Allah Ya kiyaye mu su shiga cikin abin da yake haƙƙin Allah Mahalicci ne, kuma abubuwan da Ubangiji kaɗai Ya keɓanta da su.

    Wannan kuma, ina rantsuwa da Allah babban kuskure ne, kuma tuntuɓe ne mai haɗari.

    An rawaito daga Damdamu ɗan Jaus al-Yamami ya ce: Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda ya ce da ni: “Ya kai Yamami, kada ka ce wa wani mutum: ‘Wallahi, Allah ba zai gafarta maka ba’ ko kuma ‘Allah ba zai shigar da kai Aljanna ba har abada”. Na ce: “Ya Abu Huraira, wannan magana ce da ɗaya daga cikinmu yake faɗa wa abokinsa idan ya fusata”.

    Sai ya ce: “Kada ka faɗa”. Domin na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: (A cikin Banu Isra’ila akwai wasu mutane biyu, ɗaya daga cikinsu ya kasance mai ƙoƙari wurin ibada, ɗayan kuwa mai yawan zunubi ne, kuma sun kasance abokan juna.

    Mai ibadar yana yawan ganin ɗayan cikin aikata zunubi, sai ya ce masa: “Kai wane, ka daina”. Sai shi kuma ya ce masa: “Ka bar ni ni da Ubangijina, shin an aiko ka ne don ka sa ido a kaina?” Ya ce: Har wata rana ya gan shi a cikin wani zunubi, sai ya ga girman hakan, sai ya ce masa: “Kaitonka! Ka daina”. Sai ya ce: “Ka bar ni ni da Ubangijina, shin an aiko ne don ka sa ido a kaina?”. Sai mai ibadar ya ce masa: “Wallahi, Allah ba zai gafarta maka ba”, ko “ba zai shigar da kai Aljanna ba har abada”.

    Ya ce: Sai Allah Ya aiko da mala’ika zuwa gare su, sai ya karɓi rayukansu, suka haɗu a wurinSa, sai Ya ce wa mai aikata laifin: Je ka shiga Aljanna da rahamaTa. Sai ya ce wa ɗayan: Shin ka san abin da ke cikin ilimiNa ne? Shin kana da wani iko a kan abin da ke hannuNa ne? Ku tafi da shi zuwa wuta. Ya ce: Na rantse da wanda rayuwar Baban Ƙasim ke hannunSa, lallai ya furta kalmar da ta hallaka masa duniyarsa da lahirarsa”. Imam Ahmad ne ya rawaito a cikin Musnad da Abu Dawud a cikin Sunan.

    Kuma ku sani, ya ku bayin Allah cewa: Lallai ƙin saɓo da kuma inkarin mummunan aiki, ba sa cin karo da tausasa wa wanda ya aikita laifi, ko kuma tausayi ga mai aikata saɓo, bari dai, haɗuwar duka biyun dalili ne na cikar imani, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance a kai.

    Sannan ku yi salati da salama ga mafi alherin halittun Allah, Muhammadu ɗan Abdullahi, kamar yadda Ubangijinku ya umarce ku, sai Allah Maɗaukaki Ya ce: ((Lallai Allah da Mala’ikunSa suna yi wa Annabi salati. Ya ku waɗanda kuka yi imani! Ku yi salati a gare shi da salama mai yawa)).

    Ya Allah! Ka yi daɗin tsira da aminci da albarka ga bawanKa kuma ManzonKa, Annabinmu Muhammadu.

    Kuma ya Allah Ka ƙara yarda da Halifofinsa guda huɗu, jagorori kuma tsayayyu a kan addini: Abubakar da Umar da Usmanu da Ali, Ka kuma ƙara yarda da sauran sahabbai goma da aka musu albishir da Aljanna, da waɗanda suka yi mubaya’a a ƙarƙashin bishiya, da sauran Sahabbai gabaɗaya, da Tabi’ai, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

    Ya Allah! Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmi. Ka kare shingen addini. Ka taimaki bayinKa masu tauhidi, ya Ubangijin halittu. Ya Allah! Ka yaye damuwar masu damuwa daga cikin Musulmi, kuma Ka sauƙaƙa wa waɗanda ke cikin ƙunci, kuma Ka biya bashin waɗanda ake bi bashi, Ka warkar da marasa lafiyar mu da na sauran Musulmi gabaɗaya.

    Ya Allah! Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu da majiɓinta lamuranmu, kuma Ka karfafi Shugabanmu kuma majiɓincin lamurammu, Hadimin Masallatai biyu masu alfarma, da gaskiya, da dace, da aikata daidai.

    Ya Allah! Ka tsawaita rayuwarsa cikin lafiya da kwanciyar hankali, da ni’ima mai yalwa, kuma Ka datar da shi da magajinsa amintacce zuwa ga abin da ke da amfani ga ƙasa da bayinKa, da ɗaukaka ga Musulunci da Musulmi, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah! Ka kare sojojinmu, masu tsaron iyakokinmu da fagagenmu, Ya Allah Ka kiyaye su da idonKa da baya barci, Ka lulluɓe su da karfinka wanda ba a rinjayar sa, ya Ma’abocin girma da karamci.

    Ya Allah! Ka kasance Mai taimako da ƙarfafawa da goyon baya ga ‘yan’uwanmu masu rauni, Ya Allah! Ka kasance tare da su a ƙasar Falasdinu da duk inda suke, Ka mayar da rauninsu ya zamo ƙarfi, tsoronsu ya koma aminci, talaucinsu ya zama yalwa da jin daɗi, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah! Ka yi maganin Yahudawa ‘yan ƙwace ‘yan mamaya, Ka kare mu da sauran duniya daga sharrinsu, ya Mai ƙarfi. Ya Allah! Ka sanya mu daga cikin mafiya tausayin bayinKa ga halittunKa, kuma mafiya tausasawa da kyatatawa a gare su, ya Mai Rahama Mai jinƙai.

    ((Ya Ubangijinmu! Ka ba mu kyakkyawa a duniya, kyakkyawa a lahira, kuma Ka tsare mu daga azabar wuta)). ((Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin buwaya daga abin da suke sifanta Shi da shi, aminci ya tabbata ga Manzanni, kuma dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Ubangijin talikai)).

    Domin karanta Rubutacciyar Fassarar Idin Ƙarmara Sallah danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Rubutacciyar Fassarar Huɗubar Idin Ƙaramar Sallah (Eid Kabir) Daga Masallaci mai Alfarma

    Rubutacciyar Fassarar Huɗubar Idin Ƙaramar Sallah (Eid Kabir) Daga Masallaci mai Alfarma

    Mai Huɗuba: Sheikh Dr Abdurrahman bn Abdur’aziz Sudais

    Mai Fassara: Dr Abdulkareem Tahir Abdullahi

    Transcribe: Aminu Bashir

    Shugaban Shashi: Dr Abdurrahman Muhammad Sani Yakubu

    Huɗuba ta farko:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, muna gode Maka – ya Ubangijina – kuma muna neman taimakonKa da gafararKa, muna tuba gare Ka, kuma muna yaba Maka da dukkan alheri.

    Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar Kabiran, walhamdu lillahi kasiran, wa subhanallahi bukratan wa asilan.

    Allah Shi ne Mafi girma, kuma dukkan yabo mai daɗin furtawa da kyawu naSa ne, Allah Shi ne Mafi girmam muddin zukatan masu kaɗaitawa za su ambace Shi kuma su Masa tasbihi mai tsawo.

    Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Ya shar’anta mana lokuta masu daraja da bukukuwan idi, don tabbatar da amfani ga bayi a duniya da lahira, kuma ina shaidawa lallai Annabinmu Muhammadu bawan Allah ne kuma ManzonSa, mafi alherin bayi kuma mafi darajan masu bauta, Allah Ya masa salati, shi da Alayensa, da Sahabbansa, da Tabi’ai, da waɗanda suka bi bayansu da kyautatawa, kuma Ya masa sallama mai yawa har zuwa ranar sakamako.

    Bayan haka:

    Ku kiyaye dokokin Allah – ya ku bayin Allah – in kun kasance masu biɗan maƙurar ɗaukaka, da ƙololuwar rahamar shiriya, ((Kuma duk wanda ya bi Allah da ManzonSa kuma yake tsoron Allah kuma yake kiyaye dokokinSa, to, waɗannan su ne masu rabauta)).

    Duk wanda ya kiyaye dokokin Allah, to, zai sanya tsananinsa ya koma sauƙi, kuma Allah Zai girmama ladansa saboda taƙawa.

    Ya ku taron Musulmi na gabashin duniya da yammacinta: Shin kun san wane yini ne wannan? Shin kun san wane lokaci ne wannan? Lallai wannan lokaci ne na bikin idin ƙaramar Salla mai albarka, ina taya ku murnar idi mai albarka, kuma ina roƙon Allah Ya karɓa mana kyawawan ayyukan mu tare da ku, Ya kuma maimaita mana da shugabanninmu da ƙasashenmu da al’ummar Musulunci da alheri da yalwa da albarka.

    Ga shi Allah Ya muku ni’ima da riskar wannan yini mai daɗi, don haka ku yi farin ciki da idinku kuma ku yi murna, domin farin ciki da idi sunnar Musulmi ne, kuma alama ne daga cikin alamomin Addini, an shar’anta bayyana farin ciki da murna a bikin idi, ba bayyana baƙin ciki da damuwa ba, don haka ku yaɗa farin ciki, kuma ku bayyana murmushi, ku yaɗa jindaɗi da murna, ku kwantar da hankali, kuma ku kiyaye ƙaunar juna, don tutocin farin ciki su kaɗa a gidaje da unguwanni, da kasuwanni da hanyoyi, kuma ku kawar da dundumin baƙin ciki, ku hutar da jikkuna.

    Kuma duk wanda ya hango jindaɗi na haƙiƙa da fata da albishir da farin ciki na har abada a furuci da magana da kyakkyawar hangensa, to, wani mashaya da ya fi ruwan girgije garɗi kuma haskenshi ya fi tataccen zuma ƙyalli zai bayyana gare shi, kuma wannan mashaya ba komai ba ne face wasu gwalagwalai masu ƙyalli, daga tarihin mai kyakkyawar ɗabi’u da siffofi, mai tarin albarka, mafi alherin halittu, Annabinmu Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, mafi darajan salati da mafi tsarkakar jinjina su tabbata a gare shi, wanda ya zo mana da shiriya mai haske da ƙyalli.

    Ya zo a Bukhari da Muslim, daga Uwar Muminai A’isha Allah Ya ƙara mata yarda cewa, lallai Abubakar ya shiga wajenta, alhali a tare da ita akwai kuyangu guda biyu suna rera waƙa kuma suna buga ganga, a wannan lokacin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana lulluɓe cikin tufafinsa, sai Abubakar ya musu tsawa, sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yaye fuskarsa, sai ya ce: (Ka ƙyale su ya Abubakar, saboda waɗannan kwanakin idi ne).

    Kuma an rawaito daga Uwar Muminai A’isha Allah Ya ƙara mata yarda ta ce: (Wallahi haƙiƙa na ga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana tsayuwa a kan ƙofar ɗakina, alhali Habashawa suna wasa da masunsu a Masallacin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana suturce ni da tufafinsa don na kalli wasansu, sannan sai ya tsaya don ni har sai na kai lokacin da ni da kaina zan tafi).

    Ya ku Muminai!

    A wannan yini na farinciki mai albarka, ku yalwata wa kawunanku da ‘ya’yanku, kuma ku shigar da farin ciki ga iyalanku da maƙoftanku da makusantanku, haƙiƙa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Yana daga mafi falalar aiki, shigar da farin ciki ga Mumini). Baihaƙi ne ya rawaito shi.

    Ku tsarkake zukatanku daga ƙeta da ƙullata da hassada da ƙiyayya da tsana da gaba, kuma ku karɓi uzuri, ku gyara kuskure, kuma kada ku juya wa juna baya, kada ku yi gaba, kada ku yi hassada, ku zama bayin Allah ‘yan’uwan juna.

    Idinmu mu Musulmi, idin murna da farin ciki da sada zumunci ne, ba idin yanke zumunci da ƙullata ba, ku sada zumuntanku, ku ziyarci juna, kuma ku kira wanda yake nesa da ku ta hanyar kafafen sada zumunta na zamani, wannan rana ce ta zumunci da ziyara da tausayi da sasanta juna da kau da kai, ku yafe wa wanda ya yi tuntuɓe ko kuskure, ku yi afuwa ga wanda ya yi zalunci kuma ya munana muku.

    Wannan rana ce ta ‘yan’uwantaka da haɗin kai, da curewa da dunƙulewa da tausayi, kuma waɗannan su ne alamomi da Musulunci ya ba wa muhimmanci matuƙar gaske sai ya ƙarfafa su, ya tabbatar da su kuma ya kafa su, ashe ba su ne ginshiƙan ƙarfi da tabbatawu ba bayan tauhidi da saboda shi ne aka aiko Manzanni kuma aka saukar da littaffafai, Allah Maɗaukaki ya ce: ((Ban halicci aljani da mutum ba sai don su bauta mini)).

    Kuma Maɗaukakin Sarki ya ce: ((Ku yi riƙo da igiyar Allah gabaɗaya, kada kuma ku rarrab. Kuma ku tuna ni’imar Allah da Ya yi muku yayin da kuka zamo abokan gaban juna sai Ya haɗa tsakanin zukatanku, sai kuka zamo ‘yan’uwan juna a sakamakon ni’imarsa)). Haka kuma ya kasance ne saboda abin da yake samuwa ta dalilin haɗin kai na so da ƙauna, da tunɓuke ƙeta da ƙullata.

    Allahu Akbar, Allahu Akbar, la’laha illallah, wallahu akbar, Allahu Akbar, wa lillahilhamd.

    Ya ku Musulmi! Wannan idin Allah Ya shar’anta mana shi ne bayan ibadar azumi don mu yi farin ciki da shi bayan cikar azumi da doguwar tsayuwar dare, kuma haƙiƙa kun ba da zakkar fidda kai kuna masu son haka a zukatanku, ita kuma tsarkaka ce ga mai azumi daga maganar wargi da batsa, kuma abinci ne ga miskinai, Allah Maɗaukaki Ya ce: ((Don ku cika adadin (kwanakin Ramadan), kuma domin ku girmama Allah bisa ga shiryar da ku da Ya yi, don ku yi godiya)).

    Kuma daga cikin shiriyarsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai cewa lallai yana sanya mafi kyawun tufafi da yake da shi ranar idi, kuma ya kasance tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana fita a idin ƙaramar Salla da na layya yana mai ɗaga sautinsa da hailala da kabbara, kuma Ibnu Umar Allah Ya ƙara masa yarda ya kasance idan ya wayi gari ranar idi yana bayyana kabbara har sai ya iso filin Salla kuma liman ya zo.

    Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, la’laha illallah, Allahu akbar, Allahu Akbar, wa lillahilhamd.

    Kuma an rawaito daga Ummu Aɗɗiya Allah Ya ƙara mata yarda ta ce: (Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya umurce mu da mu fitar da zawarawa da ‘yan mata, da masu haila ranar idin ƙaramar Salla da ranar Sallar layya, su halarci alheri da addu’ar Musulmi). Ahmad ne ya rawaito shi a Musnadinsa.

    Allahu Akbar Kabiran!

    Wannan shi ne Addininmu tsarkakakke, kuma wannan ita ce shari’armu mai haske, shari’ar sauƙi da rahama da tsakatsakiya da daidaito Allah Ya ce: ((Kuma kamar haka ne Muka sanya ku al’umma tsakatsaki)), lallai ita ce haske mai ƙyalli da haskakawa, Ubangijin talikai Ya yi gaskiya da ya ce: ((Ba mu aiko ka ba face don ka zama rahama ga talikai)).

    Ya ku ‘yan’uwa Musulmi!

    Taya juna murnar idi yana ƙara ƙauna, da ƙarfafa soyayya, kuma an shar’anta a riƙa cewa a lokacin taya murna na idi: (Taƙabbalallahu minna wa minkum). An rawaito daga Wasilatu ɗan Asƙa’ ya ce: Na haɗu da Manzon Allah tsirda da amincin Allah su tabbata a gare shi a wata rana ta idi, sai na ce: (Taƙabbalallahu minna wa minka), sai ya ce: (Na’am, Taƙabbalallahu minni wa minka). Baihaƙi ne ya rawaito shi.

    Ya ku al’umma masu imani!

    Musulunci Addini ne na yalwa da yafiya da sassauci da sauƙi, da fahimtar juna da rayuwa tare da tattaunawa da ɗan’adamtaka, saboda haka ne hujjarsa ta bayyana, matsayinsa ya haskaka a cikin talikai, saboda ya ƙunshi maƙuran sassauci da sauƙi, da nisantar wahalarwa da tsanantawa, don haka, ku bayyana hakan ta hanyar furuci da aiki- Allah Ya kiyaye ku -, ku zama masu kira na gaskiya ta hanyar kyakkyawan furuci ((Kuma ku faɗa wa mutane magana mai kyau)), da aiki nagari, ku yaɗa fata nagari da daddaɗar kalma don koyi da Manzonku mai girma.

    Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana son kyakkyawan fata da daddaɗan zance, an rawaito daga Anas Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Alfa’alu yana birge ni), suka ce: Mene ne Fa’alu ya Manzon Allah? Ya ce: (Daddaɗar kalma). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

    Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan zai aiki wani sashe daga cikin Sahabbansa tare wani al’amari yana musu wasici da faɗinsa: (Ku yi albishir kada ku kori mutane, kuma yi sassauci kada ku tsananta). Muslim ne ya rawaito.

    Kuma an rawaito daga Ubayyu ɗan Ka’ab Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ka yi albishir ga wannan al’umma da ɗaukaka da matsayi da nasara da tabbatuwa a bayan ƙasa). Imamu Ahmad ne ya rawaito shi a Musnadinsa da isnadi ingantacce.

    Ya ku al’ummar Musulmi!

    Kada ku guji ayyukan ɗa’a bayan watan Ramadana, ku riƙe karsashinku na Ramadana har zuwa bayansa, kuma ku raba kawunanku da kasala da rauni da nawa, ku yi riƙo da sabuban rabauta da tsira, na tawakkali da himma da ƙoƙari, saboda manyan burace-burace ba a samun su da nawa, to dama ta ya ya mai nauyin jiki ƙasƙantacce zai samu maɗaukakan darajoji!

    Kuma lallai tabbatuwa a kan ayyukan ɗa’a da taƙawa yana daga alamomin karɓar aiki, Imamu Aliyu ɗan Abu Ɗalib Allah Ya ƙara masa yarda yana cewa: “Ku zama masu ba da muhimmanci ga karɓar aiki sama da ba da muhimmanci ga yin aiki”.

    Kuma haƙiƙa Imamu Muslim ya rawaito a Sahihinsa cewa lallai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Duk wanda ya azumci watan Ramadana, sannan ya bi bayanshi da azumin kwanaki shida na watan Shawwal, to, zai samu lada kamar wanda ya azumci shekara).

    Domin karanta Yadda Ake Yin Umara Dalla-dalla danna nan

    Don haka, ku kwaɗaitu wurin azumtarsu, kuma ku yi wasici wa juna da hakan, ku sadar da aikin ɗa’a da aikin ɗa’a, za ku kasance daga cikin karɓaɓɓu da izinin Allah.

    Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, la’ilaha illahu, Allahu Akbar, Allahu Akbar, wa lillahil hamd.

    Ya ku ‘yan’uwa mata masu daraja! Matsayinku a cikin addinin Musulunci kamar lu’ulu’u ne killatacce, ko kayan alatu mai daraja, kuma kun fi ma lu’ulu’u tsada, ku ɗabi’antu da kunya gwargwadon iyawarku, kuma ku yi riƙo da ɗabi’ar kamun kai da saka hijabi da rufe jiki, kuma ku kame ganinku, ku riƙa sadaka, ku yawaita istighfari, ku dena butulce wa ni’ima, ku kasance mafiya alherin mataimaka ga mazajenku a kan ayyukan ɗa’a, ku ƙara ƙaimi wurin tarbiyyantar da ‘ya’yanku ababen ƙaunarku, ku kange su daga fitintinu, domin su fuskanci kalubale da sauye-sauyen rayuwa da imani mai ƙarfi da azama tabbatatta.

    Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, la ilaha illallah, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Wa lillahil’hamd, Allahu Akbar kabira, Wa-lhamdulillahi kathira, Wa subhanallahi bukratan wa asila.

    Allah Ya albarkace mu da Alkur’ani da Sunna, Ya amfanar da mu da abin da ke cikinsu na ayoyi da hikima, ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah gare mu da dukkan Musulmi daga dukkan kuskure da saɓo, saboda haka, ku nemi gafararSa kuma ku tuba zuwa gare Shi, lallai Shi Mai yawan karɓar tuba ne.

    Huɗuba ta biyu:

    Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, La ilaha illallah, wallahu Akbar, wa lillahil’hamd.

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Ya kwararo mana ni’imomi masu yawa kuma masu girma, ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Ya tsarkaka da daraja da ɗaukaka, kuma ina shaidawa lallai Annabinmu Muhammadu Bawan Allah ne kuma ManzonSa, wanda aka zaɓe shi a cikin talikai da manzanci da matsayi.

    Ya Allah Ka yi daɗin tsira ga Annabinmu kuma masoyinmu abin koyinmu Muhammadu ɗan Abdullahi, da Alayensa wanda suka kai maƙura wurin ƙaunarsa, da Sahabbansa masu bin sunnarsa suna masu lizimtar ta da riƙo da ita, da Tabi’ai da waɗanda suka bi su da kyautatawa matuƙar rana da wata na bibiyar juna kuma suna nan.

    Bayan haka:

    Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah! Ku yi riƙo gaba ɗayanku da Littafin Ubangijinku, da Sunnar Annabinku Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, domin mafi alherin shiriya ita ce shiriyar Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma mafi sharrin al’amura su ne ƙirƙirarrunsu.

    Ya ku al’ummar Musulmi! Lallai daga cikin alamomin shiriya, akwai lazimtar tabbatattun abubuwa na shari’a, da kyawawan ɗabi’u, da riƙo da haɗinkai da kasancewa tare da jama’ar Musulmi, da abin da hakan ke lizimtawa na ji da biyayya ga shuwagabanni, an karɓo daga Ibnu Umar Allah Ya ƙara musu yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Al’ummata ba za ta taɓa haɗuwa a kan ɓata ba, saboda haka, ku lizimci jama’a, domin taimakon Allah yana tare ne da jama’a). Tirmizi da Ɗabarani ne suka rawaito shi da isnadi mai kyau.

    Lallai jama’a igiyar Allah ne ga mai addini saboda haka, ku yi riƙo da igiyar mai ƙarfi.

    Sau Nawa ne Allah Yake tunkuɗe bala’i ta dalilin shugaba.

    A cikin lamuran addini da na duniya don rahama daga gare shi.

    Ba don shugabanci ba da ba a amintar mana da hanyoyi ba.

    Kuma da masu ƙarfinmu sun danne masu rauni daga cikinmu.

    Da kasancewa tare da jama’a da biyayya ga shugaba ne aminci da zaman lafiya ke tabbata, kuma ababen guda biyu, ni’imomi ne da babu ni’imar da ta kai su girma, kuma kyauta ne da falala da babu abu mai daraja kamar su.

    Kuma haƙiƙa Allah Maɗaukakin Sarki Ya fifita ƙasa mai tsarki da ni’imar aminci da zaman lafiya, sai Ya ce tsarki ya tabbata a gare shi: (Ashe ba su ga cewa lallai Mu mun sanya garin Makka mai alfarma ya zamto mai aminci ba, alhali ana fauce mutane a garuruwan da ke kewayensu).

    Saboda haka, wanzuwar zaman lafiya a ƙasa mai tsarki aƙida ce tabbatatta, tushenta na kafe cikin ƙasa, rassanta kuma su na sama, kuma hakan ya tabbata kuma ya ƙarfafu tun lokacin kafuwar wannan ƙasa har zuwa zamanin shugaban da ya haɗa sassan ƙasar, nagartaccen Sarki – Allah Ya kyautata makomarsa – cikin inuwa mai faɗi na tutar haɗinkai da ɗinkewa, da nesantar sharrin rarrabuwa da saɓani.

    Kuma a wannan zamani na bunƙasawa da hangen nesa da kyakkyawan tsari na shugabanci da cigaba da ginawa da rayawa da haɓɓakawa da daɗin rayuwa da kyawunta, da cin ma manufofinta ta hannun matasanta maza da mata, da tabbatar da kishin ƙasrsu da jinginuwarsu gare ta, wannan ƙasa tamu maɗaukakiya tana da daraja ta ɓangaren abin da ya shafi haɗinkan mutanen cikinta, da sauƙin rayuwa da riƙo da al’adu da tafiya kafaɗa da kafaɗa da zamani da cigaba da bunƙasa, kuma dama – da falalar Allah – ita ce ƙasar da take da girman tasiri ga Musulmi da Larabawa da duniya, da mahimmancin wurin da take da girman tarihinsa, da matsayinta mai girma a idon duniya, ga Allah kaɗai godiya da falala suka tabbata, Allah Ya ƙara mata haɗinkai da dunƙulewa da wadata, kuma Ya ƙare mata aƙidarta da shugabancinta da amincinta lumanarta, lallai Shi Mai yawan kyauta ne Mai karamci.

    Kuma bayan haka: Albishirinku ya ku waɗanda kuka yi azumi da tsayuwar dare, albishirinku ya ku waɗanda kuka yi Tahajjudi kuma kuka yi sadaka, haƙiƙa gajiya da wahala sun gushe, lada kuma ya tabbata in Allah Ya yarda, domin wannan rana ce ta kyaututtuka.

    Kuma daga cikin falalar Allah ga ƙasarmu, akwai abin da Allah Ya ɗaukaka ta da shi na hidimar Masallatai biyu masu alfarma, da abin da Ya ni’imta wa masu Umra da maniyyata na samar musu da wani yanayi na imani mai girma, da manyan hidindimu masu ban-ƙaye, saboda haka, ga Allah kaɗai yabo da godiya suka tabbata, kuma Allah Ya saka wa Hadimin Masallatai biyu masu alfarma da magajinsa amintacce da mafi alherin sakamako kuma mafi cikarsa a kan ƙoƙari da suke yi na gabatar da ayyuka masu girma na hidima ga Masallatai biyu masu alfarma da maziyartarsu, da taimako cikin lamuran da suka shafi Musulunci da Musulmi, na gaba daga ciki, shi ne lamarin da ya shafi Falsɗinu da Masallacin ƙudus, da ƙoƙarin wajen samar da aminci da zaman lafiya a duniya.

    Allah Ya karɓa mana kyawawan ayyuka, kuma Ya sa a kowace shekara ku cigaba da ni’imtuwa da alkhairai da jin daɗi, cikin aminci da lumana da natsuwa da kwanciyar hankali.

    Wannan kena! Allah Ya muku rahama, Ku yi aiki da umarnin Ubangijinku da Yake sakanta muku da lada mai girma a kansa, da matsayi maɗaukaki, sai Allah Madaukaki Ya faɗi magana mai daraja: ((Lallai Allah da Mala’ikunSa suna salati ga Annabi, ya ku waɗanda kuka yi imani ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah Ka yi daɗin tsira ga Annabi Muhammadu, da Alayensa nagartattu tsarkaka, da Sahabbansa masu hasken fuska masu albarka, da Halifofinsa shirayayyu, Abubakar da Umar da Usman da Ali, da sauran Sahabbai baki ɗaya, da Tabi’ai da waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa Ranar sakamako.

    Ya Allah ya ma’abocin girma da ɗaukaka, Ka daidaiata tsakanin Musulmi, Ka azurta su da shiriya da tsoron Allah da kamewa da wadatar zuci, ya Allah Ka datar da su ga haɗin kai da ƙaunar juna, Ka nesanta su daga sharrori da laifuka don falalarKa, Ka shiryar da su hanyoyin tsira.

    Ya Allah Ka datar da shugabanmu Hadimin Masallatai biyu masu alfarma ga ayyuka na ƙwarai da tsoron Allah, da aikin da Ka yarda da shi, kuma Ka yalwata masa tufafin waraka da lafiya, Ka datar da shi da magajinsa ga abin da yake ɗaukaka ne ga Musulunci da Musulmi, Ka azurta su da mashawarta nagari, waɗanda za su riƙa nuna musu alheri su riƙa kwaɗaitar da su a kan shi, ya Allah Ka game su da baiwarwaki masu kyawu, Ka ƙawata su da siffofin karamci, Ka kasance Mai taimako da agazawa da ƙarfafawa da ba da nasara a gare su cikin ayyukan alheri, Ka sanya su su zamto masu taimako ga Musulunci da Musulmi.

    Ya Allah Ka wanzar da aminci da zaman lafiya a garuruwanmu, Ka sanya su su rabuta da alheri da albarkoki, su kuɓuta daga sharrori da masifu.

    Ya Allah Ka datar da shugabannin Musulmi ga hukunci da shari’arKa, da bin Sunnar AnnabinKa Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, Ka shiryar da su bisa tafarkin kyawawan ayyuka da tsira.

    Ya Allah Ka taimaki ‘yan’uwanmu masu rauni a kowane wuri.

    Ya Allah Ka ceto Masallacin ƙudus daga ta’addancin ‘yan ta’adda, da yahudawa ‘yan share wuri zauna, ya Allah Ka sanya shi ya zamto mai ɗaukaka da buwaya har zuwa Ranar sakamako.

    Ya Allah Ka taimaki ‘yan’uwanmu a ƙasar Falasɗinu, ya Allah Ka darkake maƙiyansu, Ka tarwatsa taronsu, Ka sanya su su zamto abin lura ga masu lura.

    Ya Allah Ka zartar wa wannan ƙasa wani al’amari na shiriya da za a ɗaukaka masu yi maka ɗa’a da shi, a shiyar da masu saɓa maka da shi, a yi umurni da kyakkyawan aiki da shi, a yi hani daga mummunan aiki da shi, ya Ma ji roƙo.

    Ya Allah Ka datar da jami’an tsaronmu, da masu dako a fagage da iyakokinmu.

    ((Ya Ubangijinmu Ka ba mu kyakkyawa a duniya, Ka ba mu kyakkyawa a lahira, kuma tsare mu daga azabar wuta)).

    Ya Allah Ka sanya Idinmu ya zamto mai daɗi, rayuwarmu ta zamto mai yalwa, aikinmu ya zamto daidaitacce, kuma Ka maimaita mana shi cikin shekaru masu yawa, da zamuna masu tsawo, muna cikin alheri da lafiya da rayuwa mai daɗi, ya Allah Ka maimaita mana shi tare da shugabanninmu da ƙasarmu da Musulmi cikin alheri da jin daɗi da albarka, ya Mafi alherin Wanda ake roƙo, kuma Mafi ɗaukakar Wanda ake fata.

    Ya Ubangijinmu Ka karɓa mana lallai Kai Mai ji ne kuma Masani.

    Ka karɓi tubarmu, lallai Kai Mai yawan karɓar tuba ne kuma Mai jinƙai.

    Ka gafarta mana da iyayenmu da dukkan Musulmi, rayayyu daga cikinsu da matattu, don tausayinKa ya Mafi tausayin masu tausayi.

    Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, la ilaha illallah, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Wa lillahil’hamd.

    Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin buwaya daga abin da suke siffantawa).

    Aminci ya tabbata ga Manzanni. Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai.

    Danna nan don karanta Addu’ar Fita Daga Masallaci

    Edita@rumasau-kallamu

     

     

     

     

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 14th March 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 14th March 2025

    Mai Huɗuba: Sheikh Dr Abdurrahman bin Abdul-Aziz Assudais

    Mai Fassara: Malam Salisu Alhaji Abdullahi

    Transcribe: Aminu Bashir

    Shugaban Sashi: Dr Abdurrahman Muhammad Sani Yakubu

    Huɗuba Ta Farko:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, muna gode Masa tsarki ya tabbata gare Shi, muna neman taimakonSa da gafararSa, Ya keɓance mu da lokaci na ayyukan ɗa’a, madalla da tafki irinsa, duk wanda ya yi gaggawa zuwa gare shi zai kai ga samun ƙololuwar yardar Allah.

    Godiya ta tabbata gare Ka godiya dawwamammiya a bisa ni’imomin da ba su da adadi bare su kare. Kuma muna roƙon Sa datarwa da godiyarSa lallai ita godiya ta kasance mai bayyana ni’imomin abin bauta ce. Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai Yake ba Shi da abokin tarayya, shaidar da za mu samu mazauni a gidan Aljanna ta dalilinta.

    Kuma ina shaidawa lallai Annabinmu kuma abin koyinmu Muhammad bawan Allah ne kuma ManzonSa, mafi alherin wanda ya yi azumi da sallar dare, sai ya kasance ɗaya tilo wurin falala. Ya Allah ya Ubangijinmu Ka yi daɗin tsira ga Annabi Muhammad, a matsayinsa na shayabo kuma abin yabo, da Alayensa tsarkaka nagartattu, waɗanda suka kai ga samun daraja da jagoranci a watan taƙawa, da Sahabbansa masu daraja waɗanda suka ƙarar da watan Ramadana suna masu ruku’u da sujjada, da Tabi’ai da waɗanda suka bi su da kyautatawa suna masu fatan samun kyakykyawar ƙarshe, da aminci mai yawa, muddin mutum zai wayi gari ko ya yini cikin kyautatawa.

    Bayan haka;

    Ya ku bayin Allah!

    Ku ji tsoron Allah Ubangijinku, domin tsoron shi ne ƙashin bayan azumi da manufarsa, kuma shi ne haƙiƙaninsa da ma’anarsa, Allah Ya ce: ((Ya ku waɗanda kuka yi imani an wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabta wa waɗanda suka gabace ku don ku samu taƙawa)).

    Ya kai ɗan Adam ka yi sauri wurin neman taƙawa, kuma ka yi gaggawa zuwa ga aikata alheri matuƙar an saurara maka. Me yafi taƙawa kyawu! kuma me yafi hanyarta zama shiriya!, da ita ne mutum yake samun ɗaukaka da aikinsa.

    Ya ku taron Muminai!

    A yayin da al’ummar Musulmi suke ni’imtuwa da dawwamammen ƙamshin watansu mai albarka, da kwanakinsa masu yalwa da asali, kuma suke shiga ƙarƙarshin inuwarsar alkhairansa mai faɗi, wanda aka ƙawata shi da mafi kyawun mayafi, kuma suke kwankwaɗar ruwansa garɗi, suke shan ruwansa mai ƙosarwa, suke haskaka da haskensa, kuma suke more kwanakinsa masu banƙaye, kwatsam sai ga shi watan ya raba, watan alheri da kyauta da kyautatawa, watan da ƙoramunsa suka gudana da ayyukan ɗa’a, furannin alheri da ayyukan nagarta suke hudowa daga cikinsa, kuma Musulmi suke sauraron manufofinsa da sirrorinsa cikin shauƙi, kuma suke yi shiru suna masu sauraron manufofinsa tabbatattu da labaransa cikin nutsuwa, kwanakinsa kuma suna kwararowa da ayyukan neman kusanci ga Allah da farin ciki, dararensa suna haskaka da ayoyin da ake karantarwa da haske, wani lokaci ne da Allah Mai rahama Ya sanya albarka a cikinsa, kuma Alƙur’ani ya wanzar da shi ((Watan Ramadana wanda aka saukar da Alƙur’ani a cikinsa, shiriya ne ga mutane kuma ayoyi ne bayyanannu na shiriya, kuma mai rarrabewa)).

    Ya ku taron Musulmi!

    Haƙiƙa Allah Maɗaukakin Sarki Ya shar’anta azumi don Musulmi ya sabunta kyawawan ɗabi’unsa na bauta, kuma ya sake motsa yunƙurinshi na ayyukan alheri, sai ya samu ɗaukaka a cikin darajojin imani, ya kuma siffantu da siffofin ma’abota nagarta da kyautatawa, ta yadda Shari’a mai hikima ba ta tsaya game da azumi a kan abin da yake fili ba, bari dai, ta ƙetare haka zuwa ɗaukakar ruhi da ɗaukakan rai da kiyaye shi da tsakake gaɓɓai, da ɗaukaka shi daga lamari na zahiri zuwa sasannin matsayi da ɗaukaka na imani, don haka ne ma Allah Maɗaukakin Sarki Ya keɓance wannan bauta ban da sauran ibadu, kamar yadda ya zo a Sahihaini cewa: (Dukkan ayyukan ɗan Adam nasa ne, ban da azumi, domin shi Nawa ne, kuma Ni ne Zan ba da sakamakonsa).

    (Watan Ramadana) wani wata ne da Allah Ya ba shi matsayi, don Allah Ya ji tausayin wanda hanyoyi suka ƙuntata gare shi. (Allah) Shi ne Mai tausayin mu, shin akwai wani ma’abocin buƙata da ya kira Allah Mai rahama da zuciya mai cike da kunya sannan ya taɓe.

    Ya ku al’ummar Muminai!

    Waɗannan kwanaki masu albarka dama ce mai kyau da za a amfana da ita wajen bibiyan rai da gyara aiki, da yin watsi da saɓani da rarrabuwar kai, da alƙalantar da hankali da harshen tattaunawa, da taimakekeniya a kan ayyukan nagarta da taƙawa, saboda abin da wannan wata mai karamci yake ɗauke da shi na darusa masu girma na rigegeniya wajen yin alherai da kyawawan ayyuka, Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce: ((Ku yi gaggawar aikata alheri)).

    Imami Ibnul-Ƙayyim Allah Ya masa rahama ya ce: “Shiriyar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ita ce mafi cikar shiriya a cikin watan Ramadan, kuma mafi girma wajen tabbatar da manufa, sannan mafi sauƙi ga rayuka, kuma daga cikin shiriyarsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a cikin watan Ramadana akwai: Yawaita nau’uka mabanbanta na ibadu, kuma Jibrilu amincin Allah ya tabbata a gare shi ya kasance yana taya shi muraja’ar Alƙur’ani, kuma ya kasance yana Yawaita sadaka da kyautatawa a cikinsa, da karatun Alƙur’ani, da Salla, da zikiri, da i’itikafi, kuma ya kasance yana keɓance shi da wasu ibadu da ba ya keɓance wani watan na daban da su”.

    Ya ku bayin Allah! Ku gaggauta tattara ƙoƙarinku, ku tafke ɗaurin ɗamararku, ku bayyana wa Allah alheri daga gare ku, ku farkar da zukatanku daga angajen munanan tunani, kuma ku kame idanuwanku daga kallon ababen da aka hana ku kallo, Mai rabo shi ne wanda ya ƙawatu da adon ayyukan ɗa’a, kuma ya gyastu daga hasken jama’a.

    Ya ku taron masu azumi, masu salla, kuma masu kyauta! ((Haƙiƙa kuna da kyakkyawan abin koyi daga Manzon Allah)). Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance ya fi kowa yawaita kyauta a cikin mutane, kuma yafi yawaita kyauta a watan Ramadana (Ya kasance ya fi yawaita kyauta sama da sakakkiyar iska). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

    Don haka ku yawaita kyauta da baiwa a wata mai daraja, lallai ku yi kyauta ya ku masu karamci da daraja, daga cikin abin da Allah Ya kwararo muku na arziki, ku shimfiɗa hannayenku da kyauta da baiwa, don ku gusar da damuwowin waɗanda ake bi ba shi da hakan, da talaucin mabuƙata, da rashin ma’abota baƙin ciki, da fitar da garƙamammu da suke jiran taimakonku kuma suke hangen agajinku da kyautatawarku daga gidajen yari ((kuma duk abin da kuka ciyar (don Allah), to Shi ne zai ba ku madadinsa, Shi ne kuwa Fiyayyen masu arzutawa)).

    Ya zo a Sahihaini daga Hadisin Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda, lallai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Babu wani yini da bayi za su wayi gari a cikinsa face Mala’iku biyu sun sauko a cikinsa, sai ɗayansu ya ce: Ya Allah Ka maye wa duk wanda ya ciyar gurbin abin da ya ciyar, ɗayan kuma sai ya ce: Ya Allah Ka lalata dukiyar duk wanda ya ƙi ciyarwa). Su kuma mutane ɗayan biyu ne, wanda aka datar da shi kuma aka jiƙanshi, da kuma marowaci da aka haramta wa rahamar Allah, don haka ku saki hannayenku da alheri don amfanar da wani.

    Sannan ayyukanku na alheri ya zama ƙarƙashin amintacciyar inuwa, da cibiyoyi nagartattu, kuma Cibiyar Sarki Salman na ayyukan agaji da taimakon mutane, da Dandalin Ihsan na ayyukan agaji misalai ne masu kyau a kan matsayan wannan ƙasa mai albarka, da kwaɗaituwar shugabanninta wajen ƙarfafa ayyukan agaji da taimakon mutane, a nan za a jinjina wa gidauniyar ƙasa ta ayyukan agaji ta hanyar Dandalin Ihsan, da ƙarfafawa mai girma da yake samu daga shugabanni Allah Ya kiyaye su, wanda hakan yake nuna ƙoƙarin wannan ƙasa mai albarka tun daga lokacin kafa ta wajen taimakon ayyukan agaji da ƙarfafa su, wanda hakan zai wajabta taimakawa da ƙarfafawa wajen isar da saƙonsu na Addini, da karantarwa, da zamantakewa, da agaji, da kiwon lafiya, da ayyukan agaji da taimakon mutane a mataki na duniya a bisa tsarin cigaba na zamani.

    Kamar yadda kuma hakan zai taimaka wajen dakile ɗabi’ar barace-barace wacce mabaraci da wanda ake roƙa suke cutuwa da ita, domin ita ɗabi’a ce mummuna, wacce cutarwata take bayyane, mai yaɗa laifuka, kuma tana hana aiki da ƙoƙarin neman na kai, kamar yadda kuma ta saɓa wa tsare-tsare da aka gindaya, da gamammun ladubba, da tsarin cigaba, kuma tana zaburarwa a kan kasala da zaman banza, sannan kuma tana ɓata kyawawan ɗabi’u a cikin al’ummomi.

    Madalla da ibada da aikin neman kusanci na fitar zakka da ta wajaba da bayar da sadaka, a cikin waɗannan kwanuka masu albarka. Allah Ya ce: (Ka karɓi wata sadaka daga dukiyarsu, kana mai tsarkake su da ita).

    Madalla da yawaita baiwa da ciyarwa da kula da waƙafi da wasiyyoyi da kiyaye tsarin gudanar da waƙafi cikin ayyukan alheri, don ta bambanta da wanzuwa da ƙayataccen tsari, da fayyacewa da amana, da lura da abin zai tabbatar da gamammiyyar maslaha, kamar gina asibitoci da cibiyoyin maganin ciwon ƙoda, da samar da hanyoyi, da gina sabbin gidaje, da haƙan rijiyoyi, da shayar da ruwa, da yaɗa ilimi mai amfani, kamar Tauhidi, da taimakon tsangayoyin Alƙur’ani, da sadaukar da Alƙur’anai, da Litattafan Sunna da hukunce-hukunce, da sadakoki masu gudana bayan rai, na daga dukkan abin da zai haifar da gamammen amfani, da fagage na bunƙasawa, kuma masu hannu da shuni da manyan ‘yan kasuwa su kasance su ne ababen koyi cikin haka, kuma bayyana sadaka da fito da ita fili zai iya kasancewa shi ne ya fi falala a wasu lokuta, domin koyi da kwaikwayo, abin da zai girmama lada ya wanzar da tasiri, Allah Ya ce: (Duk abin da kuka bayar na alheri, to, za a cikashe muku ladansa kuma ku ba za a zalunce ku ba).

    Saboda haka, ya ku bayin Allah!

    Ku ɗaura ɗamarar aiki, matuƙar kuna da ragowar kwanaki, kuna masu ribatar abin da ya yi saura na ayyukan alheri cikin wannan watan, musamman kwanaki goman ƙarshe, don samun mafi girman lada, Allah Maɗaukakin Sarki Yana cewa: (Allah Yana nufin sauƙaƙa wa gare ku, kuma ba Ya nufin tsananta muku, kuma don ku cika ƙirge kuma ku girmama Allah saboda abin da Ya shiryar da ku a kai, kuma don ku gode Masa).

    Allah Ya albarkace mu da Alƙur’ani da Sunna, Ya amfanar da mu kuma Ya ɗaukaka darajarmu da abin da ke cikinsu na ayoyi bayyannu da hikima, ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah Mai girma da ɗaukaka gare mu da sauran Musulmi daga dukkan wani laifi da zunubi, saboda haka, ku nemi gafararSa kuma ku tuba zuwa gare Shi, lallai Ubangijina tabbas Mai yawan gafara ne Mai jinƙai.

    Danna nan don karanta Azumi

    Huɗuba Ta Biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, muna gaggawa da sauri wajen neman kusanci gare Shi da azumi, ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, muna fatan Ya tunkuɗe mana sharri daga gare mu.

    Kuma ina shaidawa lallai Annabinmu Muhammadu bawan Allah ne kuma ManzonSa, mafi girman mutumin da ya amfanar da talikai, Allah Ya masa daɗin salati da albarka, da Alayensa da Sahabbansa, mafi alherin waɗanda azumi ya gyara halayensu da ɗabi’unsu, da Tabi’ai da waɗanda suka bi bayansu da kyautatawa, muddin Ramadana zai kwaranyo da hawaye daga idanuwan masu tuba, kuma Ya masa ƙarin sallama mai yawa.

    Bayan haka:

    Ku kiyaye dokokin Allah ya ku bayin Allah, ku yawaita kyawawan ayyuka da fatan karɓuwarsu a watan rahama da gafara da kyatatawa, kuma ku bi bayansu da godiyar Ma’abocin ni’ima da ba ta yankewa, saboda da yardarsa za ku rabauta, kuma izuwa ga ni’imominsa za ku tafi.

    Ya ku taron Muminai!

    Watan Ramadana wata ne na ƙoƙari da himma da aiki, watan samun nasarori da tabbatar da su, domin a cikin watan Ramadana ta shekara ta biyu bayan Hijira ne Musulmi suka ci nasarar a yaƙinsu na farko mafi girma, wato yaƙin Badar, sannan sai nasarorin Musulmi suka cigaba da samuwa a gabashin duniya da yammacinta, kuma dayawa daga cikin waɗannnan nasarorin sun kasance ne a wannan wata mai albarka, don haka ya ku bayin Allah ku jefar da kasala da rauni da nawa daga gare ku, ku yi riƙo da sabuban samun rabauta da nasara, na tawakkali da ƙoƙari da himma, kuma ku fuskanci goman ƙarshe da himma mai ƙarfi matsananciya, don koyi da Annabinku mai daraja.

    An rawaito daga Uwar Muminai A’isha Allah Ya ƙara mata yarda, ta ce: “Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana ƙoƙari a kwanaki goma na ƙarshe irin ƙoƙarin da ba ya yi a waninsu”. Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

    Kuma ya zo a Hadisi ingantacce: “Cewa lallai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan goman ƙarshe ya shigo sai ya ɗaure ɗamararsa, kuma ya raya darensa, kuma ya farkar da iyalansa”. Don haka kuma ku ɗaure ɗamara kuma ku raya dararensa, idanuwanku su zubar da hawayen nadama. Saboda Ubangijina Mai gafara ne Mai jinƙai Mai ƙaunarmu, Mai haƙuri, Mai karamci, kuma Mai yawan ni’ima.

    Ya ku masu azumi kuma masu tsayuwar dare!

    Ina muku albishir da ni’imomi da za ku samu a waɗannan ‘yan kwanaki kaɗan masu albarka, ku yi ƙoƙarin neman kusanci zuwa ga Ubangijinku ta hanyar ayyuka na farillai da nafiloli, ku kuma riski abin da ya kuɓuce muku na manyan ayyuka, kuma ku kwankwaɗi zumar ƙulla alaƙa da Ubangijinku da kyawawan salloli da i’itikafi da roƙon Allah da addu’a, domin har yanzu dama ba ta gushe ba, kuma kasuwanci bai gushe ba yana mai albarka, ga wanda ya salwantar da kwanakin Ramadana kuma ya tozarta su, ya bi da ransa hanyoyin sakaci sai ya halakar da shi.

    Kuma a cikin wannan wata mai girma kuma watan alkhairai, ana so a yawaita kyawawan addu’o’i, domin haƙiƙa Allah Ya sanya addu’a a tsakiyar ayoyin azumi kamar yadda Ya ce: (Kuma idan bayiNa suka tambaye ka game da Ni, to, ka ce Ina kusa, Ina karɓar addu’ar mai addu’a idan ya roƙe Ni).

    Saboda haka, ku ɗaga hannayenku sama kuna masu ƙasƙantar da kai gare Shi ta hanyar addu’a ga kawunanku da iyalanku da ƙasarku da al’ummarku, kuma ku yi wa Allah Tsarkakakken Sarki magiya ta hanyar addu’a, ku kai Masa kokenku da roƙonku, a kan Ya taimaki ‘yan’uwanku masu rauni da waɗanda annoba ta sauka musu, da waɗanda suke ƙarƙashin zalunci a ko’ina, ku roƙi Allah Ya yaye baƙincikinsu da damuwarsu, Ya kwaranye tsananinsu da ƙuncinsu, lallai Shi Maji roƙo ne kuma Mai karɓar addu’a.

    Wannan kenan:

    Ku yi salati da sallama – Allah Ya muku rahama – ga Annabin rahama da shiriya, mafificin masu azumi, kuma mafi darajar masu tsayuwar dare, kamar yadda Ubangijinku Ubangijin talikai Ya umurce ku, sai Ya ce kuma dama Shi ne Mafi gaskiyar masu zance: ((Lallai Allah da Mala’ikunSa suna salati ga Annabi, ya ku waɗanda kuka yi imani ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Kuma ya zo a Hadisi ingantacce cewa: (Duk wanda ya yi salati a gare ni sau ɗaya, to, Allah Zai masa salati sau goma). Ya Ubangiji Ka yi daɗin tsira a gare shi a duk lokacin da taurari suka haskaka a duhun dare da ƙarshen dare. Ka haɗa da Alayensa da dukkan Sahabbai gaba ɗaya, waɗanda suka dace da falala kuma suka kasance mafiya kyawun tarihi

    Ya Allah Ka yi salati da sallama ga Annabinmu Muhammad da Alayensa nagartattu tsarkaka, da Sahabbansa masu hasken fuska masu albarka, da Halifofinsa shiryayyu – Abubakar da Umar da Usman, da Ali – da sauran Sahabbai bakiɗaya, da Tabi’ai da waɗanda suka bi bayansu da kyautatawa har zuwa Ranar sakamako, Ka haɗa mu tare da su cikin falalarKa da kyautarKa da karamcinKa, ya Mafi karamcin masu karamci.

    Ya Allah Ka ɗora mu a bisa tafarkin masu taƙawa kuma mutanen kirki, kuma Ka sanya mu daga cikin bayinKa na ƙwarai zaɓaɓɓu, kuma Ka yi mana tagomashi da ‘yantuwa daga wuta gabaɗayanmu, don tausayinKa ya Mabuwayi ya Mai yawan gafara. Ya Allah Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmai, Ka kare shingen addini, Ka sanya wannan ƙasa ta zamto mai aminci da kwanciyar hankali, da yalwa da wadata, da sauran ƙasashen Musulmai.

    Ya Allah, Ka amintar da mu a cikin ƙasashenmu, ka datar da shuwagabanninmu da jagororinmu, Ka ƙarfafi Shugabanmu kuma Jagoranmu da gaskiya da dace.

    Ya Allah Ka datar da Shugabanmu Hadimin Masallatai biyu masu alfarma da Magajinsa ga abin da yake ɗaukaka ne ga Musulunci da kuma gyaruwa ne ga Musulmi, da kuma abin da yake alheri ne da shiriya ga mutane da ƙasa, Ka saka musu da mafi alherin sakamako bisa abin da suka gabatar da wanda suke gabatarwa na hidindimu masu girma da mafi kyawun kula ga Masallatai biyu masu alfarma da maniyyata da masu umara da maziyarta.

    Ya Allah ka datar da dukkan shuwagabannin Musulmi. Ya Allah Ka datar da jami’an tsaronmu da masu dako a iyakokinmu. Ya Allah duk wanda yake nufatarmu da Musulunci da Musulmi da wani sharri, Ka sa ya shagala da kansa, Ka mayar da mugun nufinsa a kansa, Ka sanya halakarsa cikin dabararsa, ya Maji roƙon bayi.

    Ya Allah, Ka haɗa kan al’umma akan Alƙur’ani da Sunna, ya Ma’abocin kyauta da falala da baiwa. Ya Allah ba a iya karya rundunarKa, kuma alƙawarinKa ba ya sauyawa, Ka tseratar da masu rauni daga cikin Musulmi a ko’ina, Ka taimaki ‘yan’uwanmu a Falasɗinu, Ka kare Masallacin ƙudus, ka sa zama mai ɗaukaka da buwaya har zuwa Ranar sakamako.

    Ya Allah kamar yadda Ka taimaki masoyanKa a ranar yaƙin Badar, ranar da aka rabe tsakanin ƙarya da gaskiya, Ka taimake su a kowane zamani da kowane wuri.

    Ya Allah Ka halakar da maƙiyansu, Ka tarwatsa taronsu, Ka sanya su su zamto izina ga masu ɗaukar izina. Ya Allah lallai Kai Mai afuwa ne Kana son afuwa, saboda haka, Ka yafe mana ((Ya Allah, Ka ba mu kyakkyawa a duniya Ka bamu kyakkyawa a Lahira, Ka tsare mu daga azabar wuta)). ((Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka Ubangijin buwaya daga abin da suke siffantawa, aminci ya tabbata ga Manzanni, godiya ta tabbata ga Ubangijin talikai).

    Don karanta Yaƙe-yaƙen Annabi SAW A Watan Ramadan danna nan

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Fassarar Huɗuba Daga Masallaci Mai Alfarma 10 Rajab 1446 AH 10 January 2025

    Fassarar Huɗuba Daga Masallaci Mai Alfarma 10 Rajab 1446 AH 10 January 2025

    Mai Huɗuba:
    Sheikh Dr Saleh Bin Abdullahi Bin Humaid

    Mai Fassara:
    Dr Abdullahi Yunusa Machina

    Shugaban Sashi
    Dr Abdurrahman Muhammad Sani Yakubu

    Transcribe
    Aminu Bashir

    Huɗubar Masallaci Mai Alfarma
    Sheikh Dr. Abdullah Awwad 12/06/1446H

    HUƊUBA TA FARKO
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, muna gode Masa, muna neman taimakonSa da gafararSa, kuma muna neman tsarinSa daga sharrin kawunammu da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah Ya shiryar, to, babu mai ɓatar da shi, kuma duk wanda Ya batar, to babu mai shiryar da shi.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa. (Ya ku waɗanda kuka ka yi Imani, ku ji tsoron Allah matuƙar tsoronsa, kuma kada ku mutu face kusa Musulmi)

    Ya ku mutane, ku ji tsoron Ubangijinku, Wanda Ya halicce ku daga rai guda ɗaya, kuma Ya halicci matars (Ya ɗaga shi, kuma ya yaɗa maza da mata masu yawa daga gare su, kuma ku ji tsoron Allah Wanda kuke yi wa juna magiya da Shi, kuma ku kiyaye yanke zumunci, lallai Allah Mai kula da ku ne)

    (Ya ku waɗanda kuka yi Imani, ku ji tsoron Allah kuma ku faɗi magana wacce take daidai, Zai kyautata muku ayyukanku, kuma Ya gafarta muku zunubbanku, kuma duk wanda ya yi ɗa’a ga Allah da ManzonSa, to haƙiƙa ya rabauta rabauta mai girma)

    Bayan haka:
    Lallai mafi gaskiyar zance shi ne Littafin Allah, kuma mafi alherin shiriya ita ce shiriyar Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma mafi sharrin lamura su ne ƙirƙirarru, kuma kowane ƙirƙirarren abu bidi’a ne, kuma kowace bidi’a ɓata ce.

    Bayan haka:
    Ya ku mutane! Lallai Allah Wanda hikimarSa ta ɗaukaka, Ya halicce ku ne domin ku bauta Masa, kuma Ya kallafa muku ayyukan da za ku iya, don haka, ku aikata su. Ku ji tsoron Allah ta hanyar bin umarninsa, da nisantar abin da ya hana da manyan zunubai, kuma ku yi la’akari da abin da ke cikin Alƙur’ani mai girma na ababen lura, haƙiƙa Allah ya saukar da shi a gare ku don ku bi shi, domin lallai yana daga cikin mafi girman tanadi na samun tsira.

    Saboda abin da yake ƙunshe da shi na farillai da mustahabbai da halacci da haramci da wa’azozi da jan kunne, to me ya sa zukata ba sa bin umarninsa, kuma ba sa barin abin da ya hana kuma ya tsawatar, kuma ba sa jin tsoron wanda ya san bayyane da ɓoyayye cikin ayyukan bawa, da sirrikansa da kuma zahirinsa!

    Haƙiƙa gafala ta yi musu katutu, kuma sha’awace-sha’awacen zukata sun kautar da su daga lura da ababen suka saɓa musu, sai su ka ji daɗin ɗanɗanon ɓarnarsu, kuma suka jahilci ɗacin sakamako da za a musu a lokacin mutuwarsu, don haka, sai suka doge a kan saɓonsu, ba su ji tsoron yini da za a damƙe su ta ƙafafunsu da makwarkwarɗarsu ba.

    Ranar da za a ninka azaba ga wanda ya bar salla kuma ya tozarta ta, wanda ya yi sakaci game da lamarin zakka kuma ya ƙi ba da ita, wanda ya keta alfarmar watan Ramadana ya sha azumi a cikinsa, wanda ya jinkirta faralin Hajji alhalin yana da ikon yi kuma ba tare da wani uzuri ba.

    Ranar da za a shayar da mashayin giya da ruwan ɗiwa, a kwankwaɗa masa abin da zai ɗanɗani kaito da kuɗarsa da shi daga ruwan mugunyar ‘yan wuta. Ranar da za a sako harasan wuta ga mazinata da fajirai, kuma a dake su da bulalunta ta gabansu da bayansu.

    Maciyin riba kuma ya ci daga bishiyar zaƙƙum, lallai zina da cin riba ba su taɓa bayyana a cikin wasu mutane ba face sai sun sakko wa kansu da azabar Allah, muna neman tsarin Allah daga fushinsa da azabarsa, kuma azzalumai za su wanzu a cikin iska mai tsananin zafi da kuma tafasasshen ruwa, da kuma inuwa ta turnuƙun hayaƙi.

    Ku saurara! Lallai duk wanda ya shagala da kansa, to, ba zai samu lokacin aibata waninsa ba, kuma duk wanda gazawarsa ta dame shi, to, idanuwansa za su makance daga ganin gazawar waninsa da abin da yake aikatawa, don haka, ku kame harsunanku daga keta mutuncin mutane- Allah ya muku rahama- saboda lallai Allah Yana kusa da harshen duk wani mai magana, kuma duk wanda ya keta mutuncin ɗan’uwansa kuma ya cutar da shi da magana ko da aiki, to, Allah Shi ne Abokin husumarsa.

    Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce: ((Waɗanda suke cutar da muminai maza da muminai mata ba tare da sun yi laifi ba, to, haƙiƙa sun ɗauki nauyin ƙage da kuma zunubi bayyananne)).
    Babban malami Ibnu Usaimin Allah Ya masa rahama ya ce: “Wato suna jifansu da abin da ba su aikata ba, to, haƙiƙa sun ɗauki nauyin ƙage, wato ƙarya.

    Ƙage kuma, shi ne ka ambaci ɗan’uwanka da abin da bai tare da shi; don haka ne ma lokacin da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi tambaya game da yi da wani, sai ya ce: “Shi ne ka ambaci ɗan’uwanka da abin da yake ƙi”. Ya ce: Ya Manzon Allah! Idan ɗan’uwana yana tare da abin da nake faɗi fa? Ya ce: “Idan yana tare da abin da kake faɗi, to haƙiƙa ka ci namansa, idan kuma ba ya ɗauke da shi, to, haƙiƙa ka masa ƙage”. Muslim ne ya rawaito.

    Sannan Allah Ya masa rahama ya ci gaba da cewa: Kuma cutar da mumini yana kasancewa da magana da kuma aiki, kuma hanyoyinsa na da yawa, lallai waɗanda suke cutar da muminai ba tare da sun yi laifin komai ba, to, haƙiƙa sun ɗauki nauyin ƙage wa kawunansu, kuma shi ne ƙarya, da kuma laifi bayyananne, shi ne uƙuba mai girma, Allah Ya amintar da mu”.

    A nan maganarsa ta ƙare, Allah Maɗaukakin Sarki Ya masa rahama kuma Ya saka masa da alheri bisa hidimarsa ga Musulunci da Musulmi. Ya Ubangijinmu, Ka sanya harsunanmu su kasance masu tsarki, zukatanmu su kasance masu ƙaunar muminai. Ya Ubangijinmu, Kada Ka sanya ƙiyayyar waɗanda suka yi imani a cikin zukatanmu. Ya Ubangijinmu, lallai Kai Mai tausayawa ne, Mai jinƙai.

    Ya Allah Ka tsare mu daga son zuciya, da kuma bin zuciya mai yawan umarni da mummuna, sannan Ka tsare mu daga shaiɗan la’ananne. Ku ji tsoron Allah, ya ku bayin Allah! Kuma ku yi gaggawar yin amfani da damar da aka ba ku matuƙar tana nan. Ku ci gaba da ingantattun ayyukanku muddin ana karɓar su, kuma ku kakkaɓe kawunanku daga aikata laifi matuƙar igiyar rayuwa bata katse ba.

    Kuma ka rage buri, ya kai wanda ya ruɗu, domin rayuwa gajeriya ce. Ka tsarkake aikinka ga Allah domin Mai duba aikin Mai gani ne, kuma ka bar kusakuranka, domin lissafin mai tsauri ne. Kuma ka gyara laifukanka ta hanyar tuba, domin makoma ta yi maka daɗi.

    Imam Ahmad Allah Ya yi masa rahama, da Imamul Bukhari Allah Ya yi masa rahama a cikin “Al-Adabul-Mufrad”, da kuma Albaihaƙi da isnadi mai kyau, sun rawaito daga Abdullahi bin Amr Allah ya yarda da su: cewa Annabi tsira da amincina Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ku yi jin ƙai, za a jiƙanku, ku yi gafara, za a gafarta muku.

    Kaicon waɗanda suke zama kamar masakin magana. Bone ya tabbata ga masu dogewa da yin abin da suka sani cewa mummuna ne). Ma’anar “Masakin magana”: su ne waɗanda suke sauraron magana amma ba sa fahimtar ta, kuma ba sa aiki da ita.

    A’uzubillahi minash shaiɗanir rajim, bismillahir Rahmanir Rahim: (Sai ka yi bushara ga bayina () Su ne waɗanda suke sauraron magana kuma su bi mafi kyawun ta, Waɗannan ne waɗanda Allah ya shiryar, kuma waɗannan su ne ma’abota hankula). Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah gare mu da kuma dukkan Musulmi, don haka, ku nemi gafaranSa, lallai Shi Mai yawan gafara ne kuma Mai jin ƙai.

    HUƊUBA TA BIYU
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo mai ɗorewa tare da wanzuwarSa. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo da ba ya ƙarewa sai idan Ya nufa. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo na dindindin, ba abin da zai samu wanda ya faɗe shi sai yardarSa.

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo dawwamamme a kowane ƙiftawar ido da numfashin abu mai rai. Tsira da aminci su tabbata ga Annabinmu Muhammad da Alayensa da Sahabbansa da waɗanda suka bi shiriyarsa kuma suka yi kira irin kiransa.

    Bayan haka:
    Ku ji tsoron Allah ya ku Musulmi don ku rabauta, ku fargar da kawunanku daga gafala, kuma ku bi hanyar tsira, idan ba ku aikata haka ba kuka tsaya, to fa ku sani cewa shi ajali tafiya yake da ku, kyawawan ranaku na wucewa, ita mutuwa kuma tana farke a farfajiyarku, kuna nufin samun duniya Shi kuma Allah Yana nufin Lahira.

    Ya ku bayin Allah!
    Ku yawaita salati da sallama ga mafakar mutane a babbar matsaya Ranar Alƙiyama, Annabinmu kuma mai cetonmu Muhammadu tsira da amincin Allah mai yawa su tabbata a gare shi da Alayensa. Ya Allah ka ƙara yarda da Halifofi shiryayyu da sauran Sahabbai gabaɗaya, da waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

    Ya Allah Ka amfanar da mu da son su, kuma Ka tashe mu cikin tawagarsu, kuma kada Ka karkatar da mu daga bin tafarkinsu da hanyarsu ya Mafi karamcin masu karamci.
    Ya Allah! Ka ƙarfafa Musulunci da Musulmi, Ka ɗaukaka Kalmar gaskiya da Addini da falalarka.

    Ya Allah! Ka ƙarfafa Shugabanmu kuma Majiɓincin lamuranmu da gaskiya da yin daidai da dace, Ka yi riƙo da hannunshi ga ayyukan nagarta da taƙawa, Ka azurta shi da mashawarta nagari, Ka ɗaukaka AddininKa da kalmarKa da shi, Ka sanya shi ya zama mai taimako ne ga Musulunci da Musulmi, kuma Ka haɗa kan Musulmi da shi a kan gaskiya da shiriya ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah! Ka datar da shi da Yarimansa da ‘yanuwansa da mataimakansa zuwa gaskiya da shiriya da kuma duk abin da yake akwai gyara ga al’umma da ƙasa a cikinsa, Ka saka musu da alheri saboda kulawarsu da Masallatai biyu masu alfarma da daraja, da kuma duk abin da suke gabatarwa saboda cigaban Musulunci da Musulmi.

    Ya Allah! Ka datar da masu jagorancin Musulmi ga yin aiki da Littafinka da Sunnar Annabainka Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, Ka sanya su su zama rahama ga bayinKa Muminai, Ka haɗa kansu akan gaskiya ya Ubangijin talikai, Ka kuma datar da duk jagororin Musulmi ga duk abin da yake gyara ne ga ƙasa da mutanen.

    Ya Allah! Ka saki labulan suturtawarka akan ƙasarmu da kuma dukkan ƙasashen Musulmi.
    Ya Allah! Muna kamun ƙafa da yardarKa kada Ka yi fushi da mu, kuma muna kamun ƙafa da amincinKa kada Ka yi mana uƙuba, kuma muna nema tsarinka daga azabarKa, ba mu iya kaiwa matuƙa wurin yaɓonKa kamar yadda Ka yabi kanKa.

    Ya Allah! kada ka yi mana azaba da munanan ayyukanmu, kuma kada Ka kama mu da abin da wawayen cikinmu suka aikata, Ka isar mana duk wani abin da ya dame mu, kuma Ka kasance Mai ƙarfafawa da ba da nasara a gare mu. Ya Allah! Lallai mu muna roƙon Ka farin ciki da zai lulluɓe zukatanmu da ‘yantuwar Masallacin Ƙudus daga hannu Yahudawa ‘yankwace.

    Ya Allah Ka jefe su da kibiyarKa da ba ta kure, Ka saukar musu da uƙubarKa mai tsanani, ya Majiɓincin masu rauni, ya Ma’boci ƙarfi mai tsanani! Ya Mai gudanar da giragizai! Ya Mai rusa rundunonin maƙiya! Ka saukar wa ‘yan ta’adda azaba mafi tsanani, Ka sanya su abin ɗaukar izina ga masu hankali. Ya Allah! Muna roƙon Ka farin ciki saboda samun nasarar Musulmi a kan abokan gabansu azzalumai.

    Ya Allah! Lallai mu muna roƙon gafararKa, saboda lallai Kai Ka kasance Mai yawan gafara ne, don haka Ka saukar mana da ruwan sama mamako, ya Allah! Ka saukar mana da ruwan sama, ya Allah! Ka saukar mana da ruwan sama, ya Allah! Lallai mu wata halitta ce cikin halittunKa, don haka kada Ka hana mu falalarKa saboda zunubanmu.

    Ya Allah! Ka karɓa daga gare mu lallai Kai Mai ji ne kuma Masani, kuma Ka karɓi tubarmu lallai Kai Mai yawan karɓar tuba ne Mai tsausayi. Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka Ubangijin buwaya daga abin da suke siffantawa, aminci ya tabbata ga Manzanni, godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai.

    Don karanta falalar tafiya masallacidanna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma

    Mai Huɗuba:
    Sheikh Dr Saleh Usama Bn Abdullahi Alkhayyaɗ

    Mai Fassara:
    Dr Usman Muhammad Ahmad (Azzuhri)

    Shugaban Sashi
    Dr Abdurrahman Muhammad Sani YYakubu

    Huɗubar Juma’a ta Masallaci Mai Alfarma 3/7/1446H
    Dr. Usama bin Abdullahi Khayyaɗ

    (Kiyaye Rassa Tare Da Tozarta Asali)
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, wanda ya yi wa bayinSa ni’ima da Musulunci, ina gode masa tsarki ya tabbata a gare Shi, idanuwa ba sa riskar Sa kuma hankula ba sa kewaye Shi da fahimta.

    Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Mai cikakken sarauta da tsarkaka da aminci. Kuma ina shaidawa lallai Shugabanmu kuma Annabinmu Muhammadu Bawan Allah ne kuma ManzonSa, Ya bayyana wa al’umma asalin wannan Addini da rassansa, da manyan ginshiƙansa.

    Ya Allah Ka yi daɗin tsira da aminci ga BawanKa kuma ManzonKa Muhammadu, da Alayensa da Sahabbansa manyan jagorori masu taƙawa da nagarta, da waɗanda suka bi bayansu da kyatatawa muddin darare da yini na bibiyan juna.
    Bayan haka:

    Ya ku bayin Allah!
    Ku ji tsoron Allah, saboda tsoron Allah shi ne tafarkin ankararrun mutane, kuma hanyar ma’abota hankali, sannan kuma gwadaben ma’abota basira. Cikinsa akwai aminci daga faɗawa kuskure, da rabauta da Aljanna, da kuɓuta daga wuta, ((Kuma duk wanda ya yi wa Allah da ManzonSa biyayya, kuma yake tsoron Allah kuma yake kiyaye dokokinSa, to waɗannan su ne masu rabauta)).
    Ya ku Musulmi!

    A lokacin da matsaloli suke mamaya, illoli suke yaɗuwa, kuma cututtuka suke yawaita, to, hankula za su ɗimauce, zukata kuma za su rikice, fahimtu za su ruɗe, sai hakan ya nisantar da mutum daga bin miƙaƙƙiyar hanya, ya karkatar da shi daga tafarki, ya kawo ɓarna mai girma a cikin tsarin rayuwa, saboda matsaloli za su yaɗu, karkata kuma za ta bazu, ma’aunan rayuwa su lalace, lamura su babbauɗe, sai a wayi gari an fara gabatar da na baya, kuma a jinkirta na gaba, a ƙasƙantar da manya, kuma a girmama ƙasƙantattu, a kiyaye ƙananan rassa, tare da tuzarta asali.

    Ya ku bayin Allah!

    Lallai a duniyarmu ta yau akwai misalai mabambanta da ba za su ƙirgu ba na kiyaye rassa da tozarta ginshiƙai, sai ka ga wani cikin mutane yana ƙoƙari wajen aikata ayyuka masu kusantarwa zuwa ga Allah dare da yini, don ya samu kusanci zuwa ga Majiɓincinsa Allah da su, kuma ya samu matsayi mai girma da ni’ima dawwamammiya a wajenSa, amma kuma za ka same shi yana haɗa hakan da abin da zai ɓata masa ƙoƙarinsa da wahalarsa, da abin da zai lalata masa aikinsa da jajircewarsa, a lokacin da zai yi wa Allah shirka da waninSa, a addu’a, ko neman taimako, ko neman agaji, ko yanka, ko bakance, ko karkatar da wani abu cikin nau’ikan bauta, wanda haƙƙi ne keɓantacce ga Allah, ba ya halatta a karkatar da wani abu cikinsu ga waninSa tsarki ya tabbata a gare Shi.

    A lokacin da zai je wajen wani boka ko ɗan duba ya tambaye shi kuma ya gaskata shi, da kuma lokacin da yake rataya laya ko ɗanwuri, yana riya cewa zai tunkuɗe cuta daga kansa da iyalinsa ko ‘ya’yansa, alhali kuwa Allah Maɗaukaki Ya bayyana wa bayinSa a cikin LittafinSa da fayyataccen bayani cewa: Lallai sakamakon wannan shirka shi ne lalacewar aikin mutum da rushewarsa, kuma ba zai amfani ma’abocinsa ba a Lahira, da kuma haramta masa shiga Aljanna, da kuma sanya wuta ta zama makomarsa.

    Allah Maɗaukaki Ya ce: Haƙiƙa kuma an yi maka wahayi kai da waɗanda suka gabace ka cewa: “Tabbas idan ka yi shirka, to, lalle aikinka zai ɓaci, kuma tabbas za ka kasance daga cikin asararru. (Suratuz-Zumar: 65).

    Bayani mai daraja wanda ba ya buƙatar wani ƙari, ya zo daga Annabi a cikin ingantaccen Hadisi game da makomar wannan lamari. Haƙiƙa Imam Ahmad ya rawaito a cikin Musnadinsa, da Hakim a cikin Mustadrak ɗinsa da isnadi ingantacce daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda cewa: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Duk wanda ya je wurin mai duba ko boka, kuma ya gaskata shi a kan abin da yake faɗa, to, lallai ya kafirce wa abin da aka saukar wa Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).

    Haka kuma Imamu Ahmad ya rawaito a cikin Musnadinsa, da Al-Hakim a cikin Mustadrak ɗinsa da isnadi ingantacce daga Uƙba ɗan Amir Allah ya ƙara masa yarda, cewa: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Duk wanda ya rataya laya, to, lallai ya yi shirka).

    Daga cikin misalan kiyaye rassa da kuma tozarta ginshiƙan addini, akwai abin da za ka ga wasu daga cikin masu mayar da hankali wajen karanta AlƘur’ani da Tajwidinsa da kyautata sautinsu wajen tilawa, sannan kuma suna yin sakaci wajen kiyaye iyakokin da aka gindaya a cikinsa, kuma suna yin sakaci wajen aiki da abin da aka saukar game da su, kuma suna kau da kai daga yin tuntuntuni a cikin ma’anoninsa, da tasirantuwa da wa’azozinsa, da ɗaukar darasi daga labarai da misalai da ke cikinsa.

    Haka nan, cikin mutane akwai wanda yake nisantar najasa don kada ta taɓa tufafinsa, amma ba ya kauce wa yin gulma da annamimanci da yin karya. Akwai kuma wanda yake yawaita yin sadaka, amma ba ya nisantar dukiyar haram. Haka kuma, cikin mutane akwai wanda zai tashi ya yi sallolin dare yayin da mutane ke barci, amma yana jinkirta sallar farilla a kan lokacinta.

    Akwai kuma wanda yake azumtar yini, amma yana cutar da makwabtansa, yana take haƙƙoƙinsu, yana cin mutuncinsu, har maƙwabtaka da shi ya zama damuwa matsananciya, da sharri mai yawa, da bala’i mai girma a gare su. Akwai kuma wanda yake faranta wa abokan hulɗarsa da danginsa na nesa ta hanyar ƙulla alaƙoƙi masu ƙarfi da su, amma kuma sai ka ga yana munana wa iyayensa da ‘yan’uwansa, yana yanke zumunci, yana nisantar makusantansa da mutan gidansa.

    A cikin mutane, akwai wanda yake sakin hannu ga talaka na nesa, amma yana barin iyalinsa cikin yunwa, suna neman taimako a hannun mutane, ko kuma yana ƙuntata musu a kan kuɗin da ya zama wajibi ya ba su, kuma ba ya kyautatawa wajen ba su abin da zai ishe su. Akwai wanda kuma yake tsare tufafinsa da abin hawansa da shimfidarsa daga datti da ƙazanta, amma ba ya kiyaye kunnuwansa da idanuwansa daga gani ko jin abin da aka haramta masa.

    Haka nan, akwai wanda yake bin ƙananan lamura, amma yana yin sakaci game da manyan lamura, kuma yana bin abin da yake masa sauƙi, amma ba ya bin abin da yake da nauyi a gare shi. Ibnul Jauzi Allah Ya masa rahama ya ce: “Abubuwan da muka gani daga mutane a wannan babi, wato dangane da kiyaye ƙananan lamura da kuma tozarta manya, akwai ababen al’ajabi waɗanda za a shafe lokaci mai tsawo wajen ambatonsu”.
    Ya ku bayin Allah!

    Lallai babu shakka cewa tushen wannan karkacewa da asalin wannan kaucewa yana cikin barin muhimman tushe da kiyaye ƙananan rassa. Wannan kuwa ba komai ba ne face tsagwaron rinsinawa ga al’adu da kuma bin ɗabi’un gargajiya, nesa da hasken wahayi biyu wato Alƙur’ani da Sunna, kuma nesa da ƙa’idojinsu, tare da bin son zuciya ba tare da shiriya daga Allah ba, da kuma rashin ilimi game da Addinin Allah, da ƙarancin masu nasiha, da rashin tallafin masu taimako.

    Ku saurara! Lallai mafita daga duk waɗannan abubuwa, ba ta samuwa sai da magani na ilimi da kuma aiki. Game da ilimi kuwa, yana nuna wa ma’abocinsa ƙa’idoji da tushe da kuma ginshiƙai da ake gina rassa a kansu, ƙananan sassa kuma su samu ginuwa daga su. Hakan yana ba shi tsararren tunani mai kyau sai ya dinga sanya abubuwa a inda suka dace, kuma ya fahimci matsayi da darajar ayyuka.

    Shi kuma aiki a ɓangarensa, yana kasancewa mai inganci daidai da abin da Allah ya shar’anta, yana tafiya a bisa tafarkin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma mai rabauta da samun karɓuwa a wajen Allah, tare da kaiwa ga dukkan burin da ake fata.

    Haka kuma, lallai ƙin bin son zuciya da ƙoƙarin tsara al’adu da ɗabi’un gargajiya bisa dokokin shari’a yana daga cikin abin da ake fatan za a gyara wannan karkacewa da tsayar da wannan kaucewa da shi, wanda zai dawo da Musulmi zuwa ga tafarkin Addininsa madaidaici.

    Allah ya amfanar da mu da shiriyar LittafinSa da Sunnar ManzonSa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah mai girma da ɗaukaka a gare mu da dukkan Musulmi daga kowanne zunubi, lallai shi ne Mai gafara, Mai jin ƙai.

    Huɗuba ta biyu:
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Mai hukunci, Mai adalci, Mai tausasawa, Mai cikakken sani. Ina gode Masa -tsarki ya tabbata a gare Shi, Shi ne Mamallakin duniya da Lahira, kuma zuwa gare Shi ne makomar ƙarshe take.

    Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu BawanSa ne kuma ManzonSa, mai bishara da kuma gargaɗi, fitila mai haskakawa. Ya Allah, ka yi daɗin salati da sallama ga BawanKa kuma ManzonKa Muhammad, da Alayansa da Sahabbansa. Bayan haka:

    Ya ku bayin Allah!
    Lallai babbar asarar da wanda ya tsare ƙananan rassa ya bar muhimman tushe zai samu, musamman idan waɗannan tushen sun kasance Tauhidi da Imani ne, ya dace ya sanya masu hankali su ba da cikakkiyar kulawa a kan wannan al’amari, su nisanci faɗawa cikin raminsa, su kuma nisanci kowace hanya da ke kaiwa gare shi..

    Ya ku bayin Allah!
    Wace iriyar asara ce mafi girma fiye da lalacewar aikin mai aiki, ko rage ladansa, ko ninka laifinsa? Ku ji tsoron Allah, ya ku bayin Allah, ahir ɗinku da barin muhimman tushe, ku san ƙimar kowane abu, ku ajiye shi a matsayinsa, al’amuranku za su daidaita, rayuwarku za ta inganta, kuma ku samu yardar Ubangijinku.

    Kuma a kodayaushe, ku tuna cewa lallai Allah Ya umurce ku da salati da sallama ga Mafi alherin talikai, a inda Maɗaukakin Sarki Yake cewa, ((Lallai Allah da Mala’ikunSa suna salati ga Annabi, ya ku waɗanda kuka yi imani ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah Ka yi daɗin tsira da aminci ga BawanKa kuma AnnabinKa Muhammdu, Kuma Ka ƙara yarda da Halifofinsa guda huɗu shiryayyu, Abubakar da Umar da Usman Ali, da sauran Alaye da Sahabbai da Tabi’ai, da Matansa iyayen Muminai, da waɗanda suka bi bayansu da kyautatawa har zuwa Ranar Sakamako, ka haɗa mu tare da su cikin afuwarKa da karamcinKa da kyautatawarKa ya mafi karamcin masu karamci.

    Ya Allah Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmi, Ka kiyaye shingen addini, Ka taimaki bayinKa masu Tauhidi, Ka haɗa kawunan Musulmi da zukatansu, Ka daidaita sahunsu, Ka gyara Shugabanninsu, Ka haɗa kalmarsu a kan gaskiya ya Ubangijin talikai, kuma Ka sanya wannan ƙasa ta zamto mai aminci da lumana da sauran ƙasashen Musulmi.

    Ya Allah Ka amintar da ƙasashenmu Ka gyara shugabanninmu da masu jagorancin mu, Ka taimaki shugabanmu Hadimin Masallatai biyu masu alfarma, Ka sanya masa nagartattun mashawarta, Ka datar da shi a kan abin da Kake so kuma Ka yarda da shi Ya Maji roko.
    Ya Allah Ka datar da shi da Magajinsa ga abin da alheri ne ga Musulunci da Musulmi, da abin da yake gyara ne ga ƙasa da kuma bayinKa, ya Wanda komai zai dawo gare shi a Ranar ƙarshe.

    Ya Allah Ka kare wannar ƙasa, Ka ba ta kowane irin alheri Ka tsare ta daga kowane irin sharri, da sauran ƙasashen Musulmi. Ya Allah, ka ‘yanta Masallacin Ƙudus, Ka kiyaye Musulmi a Falasdinu. Ya Allah Ka kiyaye su ta gabansu da bayansu, da damansu, da hagunsu, da kuma samansu, kuma muna neman tsarinKa kada a shammace su ta ƙarƙashinsu.

    Ya Allah Ka kasance musu Mai taimako kuma Mai goyon baya, Mai ƙarfafa su kuma Mai basu nasara, Ya Allah Ka sauko wa maƙiyanKa kuma maƙiyansu da bala’i, ya Ma’abocin ɗaukaka da karamci. Ya Allah Ka inganta mana Addininmu wanda shi ne kariyar lamuranmu, Ka kyautata mana duniyarmu wacce a cikinta muke rayuwa, kuma Ka gyara mana Lahirarmu wacce zuwa gare ta za mu koma, Kuma Ka sanya rayuwa ta zama ƙari ga duk wani alheri a gare mu, Ka sanya mutuwa ta zama hutunmu daga dukkan wani sharri.

    Ya Allah Ka sanya wa zukatanmu tsoranKa, Ka tsarkake su Kai ne Mafi alherin Mai tsarkakewa, Kai ne Masoyinsu kuma Majiɓincinsu. Ya Allah Ka kyautata ƙarshen lamuranmu gabaɗaya, Ka tsare mu daga kunyar duniya da azabar Lahira. Ya Allah muna neman tsarinKa daga gushewar ni’imarKa da sauyawar amincinKa, da uƙubarKa ta bazata, da kuma dukkan fushinKa.

    Ya Allah, muna roƙon Ka Ka bamu ikon yin ayyuka nagartattu, da barin munanan ayyuka, da ƙaunar talakawa. Kuma Ka gafarta mana, Ka yi mana rahama, kuma idan Ka ƙaddara aukuwar wata fitina ga bayinKa, Ka karɓi rayukanmu ba tare da mun shiga cikin fitinar ba.
    Ya Allah, Ka isar mana kan maƙiyanKa kuma maƙiyanmu da abin da Ka ga-dama, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah, Ka yi maganin maƙiyanKa kuma maƙiyanmu, kuma muna neman tsarinKa daga sharrinsu. Ya Allah ka warkar da marasa lafiyanmu, Ka ji ƙan mamatanmu, kuma ka cika mana burikanmu cikin abin da Ka yarda da shi, kuma Ka sa ayyukanmu na ƙarshen su zama kyawawa.

    ((Ya Ubangijinmu! Mun zalunci kawukammu, idan ba Ka gafarta mana kuma Ka yi mana rahama ba, to, tabbas za mu kasance cikin hasararru)).
    ((Ya Ubangijinmu! Ka ba mu kyakkyawa a duniya da kuma Lahira kuma ka tsare mu daga azabar wuta)).

    Tsira da aminci su tabbata ga BawanKa kuma ManzonKa Annabi Muhammadu da Alayensa, da Sahabbansa baki ɗaya.
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai.

    Don karanta Tarihin Dutsen Dala danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu