Tag: Gizo

  • Tatsuniyar Sarki, Gizo Da Kwarkwata

    Tatsuniyar Sarki, Gizo Da Kwarkwata

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana a can kusa da garin da Gizo ke sarauta, wani tsoho yana cikin gonarsa yana kashe kwarkwata, sai ya ga wata ƙatuwar kwarkwata, har ya haɗa manyan yatsunsa zai murtsuke ta, sai ta ce da shi: “Kada ka kashe ni, zan yi maka tsaro a gonarka, kada ka kashe ni.”

    Sai ya tambaye ta: “Idan na bar ki, me za ki yi mini?” Sai Kwarkwata ta ce: “Kai dai ka sake ni a cikin gonarka ka gani.” Mamaki ya kamaTsoho, sai ya sake ta a cikin gonarsa. Ya yi kamar ya tafi gida, amma sai ya sami wuri ya ɓuya. Yana maƙe, sai ga wasu fadawan Sarki Gizo sun zo gonar sata.

    Da suka je za su yanki harawar wake sai Kwarkwata ta fara waƙa tana cewa:

    “Caca bille, caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawan Sarki Gizo,

    Sun zo satar harawar wake,

    Su kai wa dokin Sarki.”

    Waƙar Kwarkwata da ta ratsa fadawan Sarki sai suka fara rawa. Da Sarki Gizo ya ga shiru, sai ya tura dogarawansa, watau su Kiyashi da Kyankyaso da Fara su kamo fadawan da ya tura don su yanko harawar wake. Dogarawa na zuwa suka ce da fadawa: “Yaya Sarki ya tura ku ciyawa kuka yi zamanku?

    To, an ce mu kama ku.” Sai fadawan nan suka ce da dogaran Sarki: “Ku taɓa waken ku ma ku gani.” Da dogaran suka taɓa waken kamar za su yanki harawar, sai Kwarkwata ta shiga abin da ta saba:

    “Caca bille, Caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawa sun zo,

    Dogarawa sun zo,

    Satar harawar wake,

    Su kai wa dawakin Sarki.”

    Su ma dogarawa suka kama rawa. Ba damar komawa fada, balle Sarki Gizo ya san me ake ciki. Da daɗewar ta yi yawa, sai Sarki Gizo ya taso baradensa, wato manyan mayaƙansa, irin su Kudan zuma da Kunama da Sari-kutuf da Macizai da Rina da Kwarkwasa domin su kamo masa fadawa da dogarawa saboda sun yi wa Sarki ƙyuya.

    Suna isa suka fara daka wa fadawa da dogarawa tsawa, suna cewa: “Sarki ya aiko ku yankan harawar dawakinsa, ba ku koma ba. Kun raina Sarki ke nan ko?” Fadawa da dogarawa ba su tsaya wani wuni-wuni ba, suka ce da sojojin nan: “Ku taɓa waken nan kamar za ku yanki harawar ku ga abin da zai faru.”

    Sai suka taɓa; sai Kwarkwata ta rera waƙarta:

    “Caca bille, Caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawa sun zo,

    Dogarawa sun zo,

    Sojoji sun zo,

    Garin satar harawar wake,

    Su kai wa dawakin Sarki.”

    Sai su ma suka kama rawa. Da Sarki ya ji shiru, sai ya je gonar shi da kansa a fusace. Yana isa sai ya ga baradensa da dogarawansa da fadawansa suna ta dirkar rawa ba ƙaƙƙautawa a wannan gonar. Sai ya faɗa su da faɗa. Da suka ga ran Sarki Gizo ya ɓaci, sai wasu daga cikinsu suka ce: “Ranka ya daɗe, taɓa waken nan kamar za ka yanki harawar ka gani.”

    Gaya wa Sarki haka ke da wuya, sai ya ƙara harzuƙa, sai ya ce: “Zan sa a fille muku kawuna.” Baki ɗayansu sai suka ce: “Don girman ikon da ke hannunka ka taɓa waken ka ga abin damaki.” Sai Sarki ya taɓa wake, hannunsa na sauka a kan waken nan sai Kwarkwata ta shiga aikinta:

    “Caca bille, Caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawa sun zo,

    Dogarawa sun zo,

    Barade sun zo,

    Sarki ya zo satar wake,

    Ya kai wa dawakinsa.”

    To, Sarki Gizo bai yi rawar ba, saboda shirinsa ya fi na Kwarkwatar. Wato hatsabibancin Sarki ya fi na Kwarkwata ƙarfi. Sai ya ce da fadawansa: “Kai wannan gonar ta wace ce?” Tsoho da ke maƙe bai mabari fadawa sun yi wa Sarki jawabi ba sai furut ya fito ya faɗi a gaban Gizo ya ce: “Mai duniya ka daɗe, ni ne mai gonar nan.”

    Sai Sarki Gizo ya ce: “Wane aiki ka yi wa gonarka take yin haka?” Sai Tsohon nan ya ba Sarki labarin yadda suka yi da Kwarkwata. Sai Sarki Gizo ya ce: “Tana ina?” Nan da nan ya ɗauko ta ya je gaban Sarki ya miƙa masa ita. Sai Sarki ya ce da Tsoho yana son ya bar masa Kwarkwatar nan, kuma ya sa ta saki fadawansa da dogarawansa da baradensa da ta sa su rawa.

    Da ya roƙe ta sai ta sake su, suka daina rawar, kuma ya mallaka wa Sarki Kwarkwata. Sarki Gizo saboda jin daɗi ya kawo kuɗi masu yawa ya ba Tsoho, shi kuma ya tafi fada da wannan Kwarkwatar. Duk sanda yake cikin nishaɗi sai ya sa ta zo ta rera masa waƙoki iri daban-daban.

    Duk sanda yake cikin raha kuma sai ya tsokani dogarawansa da fadawansa da sojojinsa ya ce: “Na gaban Sarki waɗanda Kwarkwata ta ci ku da yaƙi.” Sai duk a fashe da dariya. Haka dai Sarki Gizo ya ci gaba da tafiyar da mulkinsa tare da fadawansa da dogarawansa cikin jin daɗi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Tausaya wa halittar Ubangiji yakan yi sanadin samun nasara.
    • Adalci shi ne sinadarin samun nasarar kowane shugabanci; azzalumin shugaba kuma ƙarshensa nadama.
    • Kula da kaya, ya fi ban cigiya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kogi Mai Cinye Maƙaryata

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Gizo Da Damon Sarki

    Tatsuniyar Gizo Da Damon Sarki

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Sarki ya kawo Damo babba. Sai ya kai shi gonarsa bayan gari. Bayan ‘yan kwanaki kaɗan ya sake kawo wasu don kiwo, kuma yasa aka yi shela a gari cewa kada a taɓa su, tare da bayanin cewa duk wanda ya yanka ya ci zai mutu.

    Ana nan, sai wata rana kwaɗayin nama ya kama Gizo, sai ya zagaya inda Damon Sarki suke. Ba tare da jin wani tsoro ba ya kama ɗaya ya yanka, ya kawo wa matarsa ta dafa masa ya cinye. Da ya ji daɗi sai kullum ya zagaya ya kama ɗaya ya yanke, har sai da ya gama Damon Sarki duka shi kaɗai.

    Da ya ƙarasa cinye naman Damo sarai, rannan sai ciwo ya kwantar da shi. Sai ya aika wa Ƙoƙi domin ta zo ta kai shi wurin magani. Da Ƙoƙi ta ɗauki Gizo suka kama hanya za su neman magani, suna cikin tafiya sai suka haɗu da Kura a cikin jeji. Sai Kura ta ce: “Ke Ƙoƙi ina za ki?” Sai ta ce: “Zan kai Gizo ne gidan magani.”

    Sai Kura ta ce: “In kin je ki gaya masa ba zai yi rai ba don ya ci Damon Sarki.” Sai Ƙoƙi ta ce: “Wai, wai ashe cutar ba ta warkewa ba ce. Gwanin zafi, gwanin zaƙi.” Haka dai suka ci gaba da tafiya. Can kuma sai suka haɗu da Zaki. Sai Zaki manyan dawa ya dubi Ƙoƙi ya ce: “Ke Ƙoƙi ina za ki?” Sai ta ce: “Mai girma Manyan Dawa zan kai Gizo ne gidan magani.”

    Sai Zaki ya ce: “In kun je ku gaya masa Gizo ba zai yi rai ba.” Sai Ƙoƙi ta yi salati, ta ce: “Ashe cutar ta fitar rai ce. Gwanin daɗi, gwanin zafi.” A nan ne fa Ƙoƙi ta sauke Gizo daga bayanta, ta yar da shi ta ce: “Tunda ka ci Damon Sarki, ka ci mutuwarka. Bari in bar ka a nan idan ka mutu kada ka yi musu wari a gari.” Sai Ƙoƙi ta koma gida, ta bar mijinta Gizo a cikin ciwon ajali. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wanda bai ji bari ba ya ji hoho.
    • Ba a karya dokar Sarki a kwana lafiya.
    • Kowa ya ɗebo da zafi, bakinsa.

    Karanta Tatsuniyar Talipaku Da Kurciya

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ‎Gizo Da Giwa

    Tatsuniyar ‎Gizo Da Giwa

    ‎‎Ga ta nan ga ta nan ku.

    Wani mutum ne dai ya ba wani malami kuɗi don a yi masa asiri. Sai malamin ya ce sai an samo hauren giwa domin ya haɗa maganin da shi. Sai mutumin ya je cikin jama’a ya ce, ‘Wa zai iya samo min hauren giwa in ba shi kuɗi? ’Aka rasa wanda zai iya. Sai Gizo ya ce shi zai iya.

    Sai mutumin ya ce, ‘To shi ke nan sai ka samo ka kawo.’ Shi ke nan, sai Gizo ya je gida ya daka nakiya mai zaƙin gaske. Sai ya je gidan giwa da ɗan ƙunshin nakiyar a hannunsa, ya ce, ‘Gafaya dai.’ Sai giwa ta ce, ‘Maraba da Gizo.’

    ‎Ya ce, ‘Yauwa. Wata nakiya ce na kawo miki da na samo a pa.’ Shi ke nan sai giwa ta ce, ‘To’. Ta gutsiri nakiya ta kai bakinta. Da ta ji zaƙin nakiyar, sai ta ce, ‘Don Allah Gizo, ni ma ka raka ni in je in samo?’

    ‎Sai ya ce, ‘Haba yaya! Me zai hana? Ki zo gobe in kai ki.’ Shi ke nan, sai ta zo washegari suka je wajen kan pa. Sai ya ce da ita, ‘Idan kika doka bakinki sau ɗaya, kika doka sau biyu, a na ukun sai ki ga nakiya rubus a bakinki.’ Shi ke nan, sai giwa ta doka bakinta sau ɗaya fas a kan pa. Ta kuma dokawa.

    Da ta doka na ukun sai haƙorinta ya balle ya faɗo ƙasa. Sai jini shar. Sai Gizo ya ce, ‘Assha, assha. Yaya aka yi haka kuma?’ Ya yi maza ya ɗauki haƙorin giwar ya sa a aljihunsa. Ita ba ta gani ba. Tana ta kanta.

    ‎Shi ke nan sai gizo ya bar giwa a nan. Ya yi sauri ya kai wa mutumin nan haƙorin. Mutumin ya ba shi ladansa. Sai gizo ya je daji ya tattara namun daji suka je gidan da giwa ta ke a kwance. Suka tarar kanta ya kumbura, suntum.

    Sai gizo ya gaya wa namun dajin, ‘In na ce, “Babbanmu da giɓi,” ku ce, “Ɓurum ɓaɓurka.”’ Sai ya fara waƙar: Babbanmu da giɓi. Sai suka amsa: Ɓurum ɓaɓurka. Shi ke nan sai suka gama, suka koma. Gizo ya bar giwa a wahala. Shi kuwa ya karɓe kuɗinsa.

    Shi ke nan. Kurunk us.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Barewa Ta Auri Mutum

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Gizo Da Ɓaure

    Tatsuniyar Gizo Da Ɓaure

    ‎Ga ta nan ga ta nan ku.

    ‎Wata rana ne dai wani sarki yana zance a zuci, yana cewa, ‘Gonata ta ɓaure ta yi kyau. Ɓauren yanzu duk ya nuna. Gara in sami wani ya je ya tsinke mini duk ɓauren, kar in bar shi ya ruɓe a banza. Amma fa wanda zai tsinke ɓauren ba zai sha ba, ko da ɗaya ma.

    Idan ya gama bai sha ba, zan ba shi ‘yata tare da gararta baki ɗaya’. ‎Shi ke nan. Kashegari sai sarki ya sa duk a yi shela a gaya wa mutanen gari sarki yana kiran su a ƙofar fada.

    ‎Mutane suka taru a ƙofar gidan sarki. Sai sarki ya ce, ‘Da ma ba wani abu ya sa na yi kiran ku ba. Gonar ɓaurena ce na ke so a tsinke min, amma ba za a sha ko ɓaure ɗaya ba. Sai dai zan ba wanda ya tsinke ɗin ladan tsinkewar. Watau zan ba shi ‘yata da gararta baki ɗaya.’

    ‎Sai kowa ya ce ba zai iya ba, domin bauren ya cika kyau, ga kuma ƙanshi da zaƙi. Ba wanda zai iya ba tare da ya sha ba. Can, sai Gizo ya zo; ya ce wa sarki, ‘Zan iya. ‎Shi ke nan, sai sarki ya ce, ‘To. Gobe ka yi shiri ka tafi’.

    ‎Da gari ya waye, sai Gizo ya dura ruwa a jallo, ya ɗauki madubi da kuma tsinkensa na sakace. Ya je gonar sarki ya kama tsinkar ɓaure. In yana cikin yi mutane suka zo suka ce, ‘Gizo barka da aiki’; sai ya tsiri tofar da yau, yana cewa, ‘Tuf! Kai wannan ɓaure! Ko warinsa ba na so’.

    ‎Idan sun wuce, sai ya ci gaba da tsinkar ɓauren, yana sha yana zubo wani a ƙasa. Shi ke nan, ashe bai sani ba, wata ‘yar tsuntsuwa tana kallon sa. Da ya gama tsinkar ɓauren tas. Ya sauko zai tafi gida, sai ya ɗauko jallon ruwansa ya kurkure bakinsa, ya ɗauko madubin nan da tsinken sakace, duk ya ciccire ɓauren da ya maƙe masa a haƙorinsa.

    Bakinsa ya yi tas, kamar bai ci kome ba. Sai sarki ya aiko mutane don su debe ɓauren da Gizo ya tsinke. Suka zo suka sami Gizo suka ce, ‘Sannu da aiki, Gizo’. ‎Ya ce, ‘Yauwa’. ‎Suka ce, ‘Har ka gama? Sai ya ce, ‘I. Amma da ƙyar’.

    ‎na gama. Kamar na yi amai, saboda warin ɓauren nan. Warin duk ya cika mini ciki’. ‎Sai suka zuzzuba ɓauren a buhunhuna suka tafi su kai wa sarki. Da suka je gida, sai sarki ya tambaye su labarin Gizo da tsinkar ɓaure. Suka ce, ‘Ai, yallaɓai, Gizo bai sha ɓauren nan ba, domin mun ga muna zubawa a buhu yana tofad da yau..

    Kuma da muka ce da shi, ‘Me ya sa ka ke zubad da yau?’ Sai ya ce warin ɓauren ne ya cika masa ciki. Sun gama faɗin haka ke nan, sai ga Gizo ya zo gidan sarki. Sarki ya ce da shi, ‘To, Gizo. Ka yi aiki mai kyau. Sai kuma ka je gida ka gyaggyara, za a kawo amarya da gararta.’

    ‎Shi ke nan. Gizo ya je gida ya gyaggyara sarai. Aka ɗauko amarya da gara aka zo da ita gidan Gizo. Kafin ‘yan ɗaukar amarya su tafi gida, sai suka ji tsuntsuwa tana waƙa tana cewa: ‘Kai Gizo, kai Gizo, A can ka ci ɓaurenka, Har ka kurkure bakinka, Har ka manto jallonka…’

    ‎Tana ta faɗar haka har sai mutanen suka ce, ‘Kai, ku tsaya mu ji abin da tsuntsuwar can take faɗa. ‎Sai Gizo ya ce da su, ‘Kai, ku rabu da ita don Allah, shirmenta ta ke yi’. ‎Sai mutanen suka ce, ‘Wane irin a rabu da ita? Kai! Mu tsaya mu ji’.

    ‎Shi ke nan, sai ‘yan kawo gara da amarya suka ji tana cewa: ‘Kai Gizo kai Gizo, A can ka ci ɓaurenka, Har ka kurkure bakinka, Har ka manto jallonka…’‎Sai suka ce, ‘La’ila! Ashe da ma ka ci ɓauren ka ce ba ka ci ba?’

    ‎Sai suka yi ta surutu da hayaniya. Shi ke nan. Sai suka mayad da amarya da gararta gida su ka gaya wa sarki abin da ya faru.

    ‎Shi ke nan. Ƙurunƙus

    ‎Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafi mai suna TATSUNIYOYI DA WASANNI wanda Ibrahim Yaro Yahaya ya wallafa.

    Danna nan don karanta ‎Tatsuniyar Barewa Ta Auri Mutum

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ‎Gizo Da Namun Daji

    Tatsuniyar ‎Gizo Da Namun Daji

    ‎Ga ta nan ga ta nan ku.

    ‎Gizo ne dai yana son ya ci nama, amma ba shi da shi. Ya rasa yadda zai yi. Sai ya ce a ransa, ‘Bari dai in yi wata dabara. Sai ya sayo goro ya rarraba wa namun daji da tsuntsayen gida.

    ‎Sai ya fara kai wa kaza, ya ce, ‘Ga shi. Goron wasa ne wanda za a yi a cikin daji. Naki ne wannan. ‎Sai kaza ta ce, ‘To. Amma fa kada ka kai wa muzuru. Sai ya ce, ‘Haba, me zai sa in kai masa?’

    ‎Da gizo ya fita, sai ya shiga gidan muzuru, ya kai masa goro. Sai shi ma muzurun ya ce, ‘To, amma kada ka kai wa kare. ‎Sai gizo ya ce, ‘Haba me zai sa in kai masa? ‎Da dai gizo ya fita, sai ya shiga gidan kare ya ba shi nasa goron. Kare ya ce, ‘To, amma fa kada ka kai wa kura.’ Gizo ya ce, ‘Haba me zai sa in kai mata?’

    ‎Da ya fita, sai ya kai wa kura nata goron. Kura ta ce, ‘To, amma fa‎ kada ka kai wa Zaki.’ Ya ce, ‘Haba kura, me zai sa in kai wa Zaki? ‎Shi ke nan, sai ya kai wa Zaki nasa goron, ya ce, ‘Ranka ya daɗe. Wani ɗan wasa za a yi na kawo maka goro.’

    ‎Da Zaki ya karɓa, sai ya ce, ‘To Allah ya kai mu. ‎Shi ke nan. Da ya fita, sai ya shiga ya kai wa damisa. Damisa ta ce, ‘In ce ko dai ba ka kai wa Sarki Zaki ba? Sai Gizo ya ce, ‘Haba, haba. Wane ni da gayyatar Sarki? Sai damisa ta ce, ‘To, Allah ya kai mu.’

    ‎Da ya fito sai kuma ya shiga gidan giwa ya kai mata nata goron. Sai giwa ta ce, ‘To, in ce ko ba ka kai wa manyan dawa ba? ‎Ya ce, ‘Mhm. Yaya zan kai? Ko kai masa ne ma ai ke zan bai wa ki kai masa.’

    ‎Shi ke nan. Ana nan ana nan, sai ranar wasa ta zo. Gizo ya bayyana musu wurin da za su haɗu a yi wasan. Ya ce musu, ‘To, ku tafi zan same ku. Ni daga baya zan taho tare da makaɗa. Shi ke nan. Sai kaza ta fara tafiya. Ashe ba su sani ba, gizo ya riga su isa can. Sai kaza ta isa can. Gizo ya yi mata maraba. Ya ce, ‘To shiga wannan bukkar kafin su zo.’

    ‎Shi ke nan. Kaza ta shiga, ta zauna. Daga can sai ga muzuru ya taho. Sai Gizo ya gaya wa muzuru cikin raɗa, ‘Maraba. Shiga tana nan a ciki. Shi ke nan sai muzuru ya shiga ya tasar wa kaza zai cinye ta. Ya cinye ta.

    ‎Can kuma sai ga kare ya taho. Shi ma dai Gizo ya gaya masa kamar yadda ya gaya wa muzuru. Sai shi ma karen ya cinye muzuru. Daga nan kuma sai ga kura. Ita ma ya gaya mata kamar yadda ya‎ gaya wa kare da muzuru. Sai kura ta shiga ta cinye kare.

    ‎Kura kuma tana zaune a cikin rumfa. Sai ga Zaki ya taho. Shi ma Gizo ya gaya masa haka. Ya shiga ya cinye kura. ‎Daga nan sai ga giwa da damisa sun jero sun taho. Sai Gizo ya ce, ‘To. Ku shiga nan bukkar mana.’

    ‎Daga shigarsu, sai suka kaure da faɗa. Suka yi ta faɗa tun daga cikin rumfa har suka yiwo waje. Idonsu duk ya rufe, suna ta faɗa. Sai Gizo ya samo ganga, ya soma kiɗa yana waƙa:

    ‎Zaki bari, damisa bari.

    ‎Giwa bari.

    ‎Faɗanku na manya,

    ‎Wa yake shiga?

    ‎Sai wawa, sai mahaukaci.

    ‎Sai ko ni da ba ni da hankali.

    ‎Suna ta faɗa, can da giwa ta ga abin ba dama, sai ta fito ta yi‎ tafiyarta gida, ta bar zaki da damisa suna karawa. Sai Gizo ya ci gaba da yi musu waƙa. Ya yi ta yi, su kuma suna ta faɗa. Ashe Gizo da ma ya zo da yaji a ƙunshe. Sai ya ɗauko yajin nan ya barbada musu a idanunsu. Sai fa faɗa ya rincabe, idanunsu suka rufe ruf.

    ‎Daga can sai Gizo ya ɗauko wuƙa ya ce, ” ‘Yan banza. Ana so a ci nama an rasa yadda za a yi.” Sai ya kama yankan naman jikinsu yana tarawa, har ya kashe su duka. Sai ya jide naman ya kai gida aka soya masa, ya ci ya  ƙoshi, ya ajiye sauran, yana ci lokaci-lokaci.

    ‎Shi ke nan. Ƙurunƙus.

    ‎Wannan rubutu an ciro shi ne daga littafi mai suna TATSUNIYOYI DA WASANNI wanda Ibrahim Yaro Yahaya ya wallafa.

    Danna nan don karanta Ga Tsoro Ga Ban Tsoro

    Edita@rumasau-kallamu