Tag: Wanzanci

  • Yadda Sana’ar Wanzanci Take A Zamanin Baya

    Yadda Sana’ar Wanzanci Take A Zamanin Baya

    Wannan babi ya duba sana’ar wanzanci a jiya wato yadda aka gudanar da wannan sana’a kafin al’ummar Hausawa su sami shigar al’adun wasu baƙi cikin al’adunsu. A nan an yi bayani a kan matsayin sana’ar wanzanci a al’adar Hausawa da kayan aikin wanzanci da kuma yadda ake gudanar da ayyukan wanzanci waɗanda suka haɗa da aski da gyaran fuska da cire belun-wuya da na mata da kaciya da tsaga da bayar da magungunan gargajiya.

    Matsayin Sana’ar Wanzanci a Al’adar Hausawa

    Kowane irin al’amari wanda ya danganci yadda ɗan Adam yake tafiyar da rayuwarsa ta yau da kullum yana da irin nasa matsayi a idanun masu yin sa da waɗanda ake yi wa. Wannan ne ya sa aka ga ya dace a duba matsayin sana’ar wanzanci a al’adance da irin yadda al’ummar Hausawa suke kallon wannan sana’a da masu yin ta.

    Sana’ar wanzanci tana da babban matsayi a al’adar Hausawa, wannan kuwa ya faru ne saboda ire-iren muhimman ayyukan da wanzamai suke aiwatarwa. Haka kuma al’ummar Hausawa suna girmama wanzamai, wannan ne ya sa Alhaji Sale Gambara a cikin bakandamiyarsa yake cewa, a duk gari akwai manya uku waɗanda su ne kamar haka; shugaban da yake jagorancin mutanen garin, sai limamin garin daga nan sai wanzamin garin.

    Haka kuma a fannonin adabin Hausawa akwai wurare da dama waɗanda aka bayyana muhimmancin wannan sana’a. Misali, a cikin littafin da Alhaji Nuhu Bamalli ya rubuta mai sunan “Mungo Park Mabuɗin Kwara”, wanda aka yi bayani a kan tafiye-tafiyen Mungo Park a sassan Afrika ta Yamma a shafi na 42-43 an yi bayyanin inda wannan matafiyi ya bayyana ya zama wanzami.

    Haka su ma makaɗan ƙasar Hausa suna bayyana muhimmancin wanzami a idon Hausawa. A iya ganin haka a waƙar da Ɗan’anace ya yi wa Shago inda yake cewa:

    “Ɗan Abdu Gazaguru,

    Ai na faɗa maka goga,

    Wanga kashi da kay yi ba dawa ne ba,

    Kar ka kashe Na’ila wanzami na,

    Ai shi ka yo muna gyara,…”

    Kuma kasancewar wanzaman gargajiya masana tsubbace-tsubbace da sihirce-sihirce ne masu ban mamaki da al’ajabi da ban tsoro ya sa al’ummar Hausawa suke ɗaukar su kamar wasu dodanni ko wasu mutane da ake tsoro. Wannan ne ma ya sa ba a yi wa wanzamai gardama ko gatse ko shisshigi dangane da yadda suke aiwatar da ayyukansu, don tsoron kar su yi wa mutum wani abu da zai cuce shi.

    Haka kuma al’ummar Hausawa sun ɗauki wanzamai a matsayin wasu mutane masu bayar da taimako idan wata lalura ta rashin lafiya ko bukatar maganin gargajiya ta taso. A nan ma makaɗan Hausawa sun bayyana irin rawar da wanzamai suke takawa wajen yin ire-iren waɗannan tsatsube-tsatsube.

    Misali, a waƙar da Alhaji Mamman Shata Katsina ya yi wa Ciroman Aski na Jalingo ya bayyana irin yadda wanzamai suke harbin ‘yan uwansu a lokacin da suka zo yin aski sai su riƙa yin kyarmar hannu wadda take yin dalilin a riƙa yankar wanda ake yi wa aski. Ga irin yadda ya bayyana haka cikin wannan waƙa:

    “Ga wani ya zo aski,

    Sun harbai hannu nai na karkarwa,

    Da ya zo gun aski,

    Sai na ga jini na ta zubowa…”

    Haka kuma karin maganar Hausawa ya ƙara fito da matsayin wanzami a idon Hausawa kamar haka:

    Kowa ya ci ladar kuturu, dole ya yi masa aski.

    Kushekarar jaki sai wanzamin kura.

    Wanzami ba ya son jarfa.

    Waɗannan dalilai ne suka sa al’ummar Hausawa suke matuƙar kyautata wa wanzamai da dukkan abin da ya dace na kyautatawa, kuma kowane mutum ya yarda da dukkan ayyukan wanzanci, ana yi masa da dukkan iyalinsa. Idan bukatar aikin wanzami ta kama matuƙar bai zo lokacin da ake buƘatar ya zo ba, ana tarar da shi har gidansa don a gani ko lafiya? Wannan dalili ya sa yin ayyukan wanzanci a wurin Hausawa a jiya wani al’amari ne wanda ya zama dole a yi shi.

    Kayan Aikin Yin Wanzanci

    Wanzamai suna amfani da kayayyaki iri daban-daban domin yin ayyukan wanzanci. Ire-iren waɗannan kayayyaki sun haɗa da askar aski da kwanon aski da kalaba da ƙoshiya da ‘yaR tsaga da hantsaki da tankolo da zabira da ƙaho da kura ta cire haƙori da sauransu.

    Askar Aski

    Askar da ake amfani ita wajen yin aski ƙarama ce madaidaiciya kuma ba ta da tsawo sosai. Akwai bambanci tsakanin wadda ake askin jarirai da wadda ake yi wa manya aski.Ta askin jarirai ba ta kai girman wadda ake yi wa manya aski ba. Da kuma askar aski ake amfani wajen yin kaciya, ana amfani ne da irin wadda ake yi wa manya aski wato mai kaifi da nauyi wajen yin kaciya. Kafin zuwan wannan zamani ana amfani da askar baƙin ƙarfe wajen yin aski da kaciya, irin wannan aska ita wanzamai suka gaji amfani da ita, kuma maƙeran Hausawa ne suke samar ta ita ga wanzamai.

    Wani muhimmin abu da ya kamata a sani a nan shi ne, askar baƙin ƙarfe ta fi kowace irin aska riƙe kaifi. Idan wanzami ya wasa askar baƙin ƙarfe sai ya yi wa mutane da yawa aski ko gyaran fuska ba tare da ya sake wasa ta ba. Akwai maƙera na daban waƙanda suke ƙerawa da kuɗar asaken aski.

    Dutsin Washin Asaken Aski

    Dutsin washin asaken aski dutsi ne ƙarami mai sulɓi da ake amfani da shi domin yin washin asaken aski idan kaifinsu ya dakushe, wato idan kaifinsu ya ragu. Idan kuwa kaifinsu ya dakushe duka, to sai a kai ga maƙeri domin a sake koɗa su. Ana amfani da dutse ta hanyar goga askar bisa dutsen sannu a hankali har sai an tabbata askar ta wasu.

    Hanyar da ake gane aska ta wasu ita ce, sai a ɗan fera fatar hannu, idan askar ta fere fatar sosai aska ta wasu ke nan. Kafin zuwan wannan zamani duwatsu iri biyu da ake amfani da su wajen wasa asaken aski. Na farko shi ne na gatarin aradu, watan dutsen da yake faɗowa idan an yi tsawa lokacin ruwan damina.

    Hanyar da ake bi domin samun dutsen gatarin aradu ita ce, da zarar an yi tsawa, aka kuma yi dacen ganin wurin da ta faɗi, sai a yi gaggawa a je a zuba madara ko nonon shanu a wurin da tsawar ta faɗi. Idan an tona sai a tarar da dutsin da ya faɗo, don kuwa madara ko nonon da aka zuba zai hana shi yin ƙasa da nisa. Dutsi iri na biyu da ake amfani da shi domin washin asaken aski shi ne na ƙanƙara mai sulɓi da ake samu a kogi ko wurin da yake da duwatsu. 

    Fatar Washin Asaken Aski

    Fatar wasa asaken aski fatar dabbobi ce ake samu daga wajen dukawa wadda aka jeme. Ana amfani da mai faɗin misali inci ɗaya da rabi, tsawonta kuma misalin inci goma sha biyar zuwa ashirin. An fi amfani da mai kauri irin ta manyan dabbobi domin kuwa ta fi inganci da ƙara wa aska kaifi.

    Amfanin fatar washin asaken aski shi ne, idan aka wasa askar da dutsi kaifinta ba zai kai sosai ba, sai an wasa da fata. A nan ne sai a shafa ruwa ga fatar a bi da askar ana shafawa bisa fatar sannu a hankali. Wannan ne zai daidaita kaifin askar yadda idan an zo yin aski askar za ta tuje gashin da sauƙi. Mafi yanwancin wanzamai suna ɗaura fatar wasa asaken askin wurin zabira daga gefe.

    Kwanon Aski

    Kwanon aski ana amfani da shi ne domin zuba ruwan da za a riƙa amfani da shi wajen yin aski da gyaran fuska da kaciya da tsaga. A da can kafin zuwan Turawa wanzamai suna amfani da ƙoƙo domin zuba ruwan aski. Wannan ne ma ya sa ake kiran wanzaman da suke yin aski da gyaran fuska da sunan ‘wanzaman ƙoƙo’. A halin yanzu ana amfani da kofin roba ko na ƙarfe domin zuba ruwan aski

    Kalaba

    Kalaba ƙarfe ne ƙarami wanda tsawonsa misalin inci shida zuwa bakwai, kuma ba shi da kauri sosai. Maƙera ne suke ƙera kalaba, ba kuma dukkan maƙeri ne yake ƙirar kalaba ba, akwai maƙera na daban masu ƙera ta. Ana yin ta ne da kaifi a gefe ɗaya na kanta sai a lanƘwasa kan ya zamo kaifi ciki. Ana yi wa gindinta kauri domin a ji daɗin riƙewa idan za a yi aiki da ita. Amfanin kalaba wajen ayyukan wanzanci shi ne a riƙa cire belin- wuya da ita.

    Ƙoshiya

    Ƙoshiya itace ne ƙarami ake sassaƙawa da ɗan faɗi ga kai da kuma kauri ga gindi. Tsawon ƙoshiya misali inci shida ne zuwa bakwai, faɗin kanta kuma bai kai inci ɗaya ba. A taƙaice tsawon ƙoshiya ɗaya yake da na kalaba. Ana amfani da ƙoshiya wajen wanzanci domin taushe harshen jariri a lokacin da za a cire belun-wuya. Ita ƙoshiya masassaƙa ne suke samar da ita ga wanzamai, akwai kuma wasu wanzamai da suke iya sassaƙa ƙoshiya.

    ‘Yar Tsaga

    Yartsaga aska ce ƙarama da maƙera suke ƙerawa, tsawonta ya kai misalin inci huɗu zuwa biyar, kanta kuma ana yin sa da faɗi da tsini da kaifi. Ana amfani da ‘yartsaga wajen ayyukan wanzanci domin yin wasu ayyukan da wanzamai suke yi a farjin mata kamar cire angurya da yanke linzami da cire haƙoran shuwa.Ana kuma amfani da ita domin yin tsagar gado da ta magani da kuma ta kwalliya.

     Hantsaki

    Hantsaki ƙarfe ne da maƙera suke ƙerawa da baki a gindi da kuma tsini a kai. Ba shi da kauri sosai, kuma tsawon sa misalin inci huɗu ne. Ana amfani da hantsaki wajen wanzanci domin cire angurya a farjin mata.

    Ƙaho

    Wanzamai suna amfani da ƙahon sa ne domin yin ƙaho. Ana amfani da ƙaho madaidaici wanda ba babba ba ƙwarai, ba kuma ƙarami ba, ana yanka misalin tsawon inci biyar ko shida. Ana yi wa wajen tsininsa ‘yar ƙaramar ƙofa. Ana amfani da ƙaho ne domin yin ƙaho. Mahauta ne suke samar da ƙaho ga wanzamai, su ne suke fitar da shi daga kan sa da aka yanka sai su sayar wa wanzaman da suke yin ƙaho.

     Jijiya

    Wanzamai suna amfani da jijiyar agarar ƙafar akuya ko tunkiya domin a riƙa liƙe ƙofar tsinin ƙahon da aka kafa wa mutum domin ya liƙe a wurin da aka kafa shi a jikin mutum. Wanzamin zai sanya wannan jijiya a cikin bakinsa yana taunawa sai ya liƙa ta a wurin ƙofar, da an liƙa shi ke nan sai ƙahon ya liƙe a wurin da aka kafa shi, ba zai fita ba sai in an cire wannan jijiya. Ita ma jijiya mahauta ne suke samar da ita ga wanzamai.

    Kura ta Cire Haƙori

    Ita kura ƙarfe ne ake samu domin cire haƙori, yanayinta ya yi kama da abin da kafintoci suke cire ƙusa a wannan zamani, amma ita kura ba ta kai girman abin cire ƙusa ba. Wanzamai suna amfani da kura ne domin cire haƙori. Wanzami yana amfani da kura ne ya kama haƙori mai ciwo ko mai girgiɗa sai ya cire shi daga wurin da yake.

    Tankolo

    Tankolo ‘yar jaka ce wadda dukawa suke ɗinkawa da fatar akuya ko tinkiya domin wanzamai su riƙa sanya askar aski ɗaya ko kuma babba wadda za a sanya asaken aski masu yawa.

    Zabira

    Zabira jaka ce babba mai aljihuna da yawa misali uku ko huɗu. Ana yi mata maratayi domin a riƙa ratayawa. Ita ma dukawa ne suke ɗinka ta da fatar akuya ko tinkiya domin yi wa wanzamai jakar da za su riƙa sanya dukkan kayan aikin wanzanci waɗanda aka yi bayaninsu a baya.

    Don karanta Matsayin Hausawa A Yau danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

     

     

  • Sana’ar Wanzanci Da Sauye-sauyen Zamani Jiya Da Yau (Shimfiɗa)

    Sana’ar Wanzanci Da Sauye-sauyen Zamani Jiya Da Yau (Shimfiɗa)

    Wannan babi ya yi bayani kan hasashe da bagiren wannan bincike da manufarsa da ƙunshiyarsa da kuma dabaru da hanyoyin da aka yi amfani da su wajen tattara bayanan wannan nazari da wuraren da aka samo su.

    1.1 Hasashe da Bagiren Bincike

    Hasashe na kai tsaye da aka kalla a kan wannan bincike ya haɗa da:

    • Nazarin wanzanci a wajen Hausawa don gano tsantsar al’adun wanzanci ba tare da sun sami wata gurɓata ba.
    • Gano nauyin sauye-sauyen zamani da suka yi kaka-gida a wanzancin Hausawa tare da fito da yanayin rawar da al’adun wasu al’ummu suka taka a wannan sana’a ta wanzanci. Shin sauye-sauyen zamani sun taimaka wajen bunƙasa wanzanci ko kuwa sun taimaka wajen dankwafe shi?
    • Shin wanzanci da al’adun da suke zagaye da shi suna nan da kadarinsu har a wannan lokaci da muke ciki?

    Muhimmin hurumi na wannan bincike shi ne sana’ar wanzanci a ƙasar Hausa tare da duba yadda sauye-sauyen zamani suka shiga cikin wanzancin Hausawa daga al’ummomin Fulani da Barebari da Buzaye da Nufawa da Yarabawa. Sannan kuma da abubuwan da Hausawa suka samu na wanzanci daga al’ummar Larabawa da Turawa.

    Akwai wasu ayyuka da aka fara yi a kan wanzancin Hausawa da suka haɗa da Musa (1983) da Suleman (1990) da Sallau (2000). Shi wannan ɗoriya ne a kan abubuwan da aka fara tattarawa tare da shigo da wani sabon bincike inda aka duba sauye-sauyen zamani waɗanda wanzancin Hausawa ya ci karo da su daga al’adun wasu al’ummomi.

    Wannan bincike an karkasa shi yadda zai shafi manyan garuruwan ƙasar Hausa da kuma wasu sassa da suke maƙwabtaka da ƙasar Hausa na kusa da na nesa. Garuruwan da wannan nazari ya duba su ne kamar haka:

    (i) Rukuni na ɗaya ya ƙunshi garuruwan ƙasar Hausa a arewacin Nijeriya waɗanda suka haɗa da Argungu da Birnin-Kabi da Daura da Gusau da Kano da Katsina da Sakkwato da Yawuri da Zariya.

    (ii) Rukuni na biyu ya ƙunshi garuruwan da suke maƙwabtaka da ƙasar Hausa ta kusa ko ta nesa a Nijeriya waɗanda suka haɗa da Bauchi da Bida da Ibadan da Ilori da Jos da Kaduna da Kafanchan da Kagoro da Lafiyar-Barebari da Maiduguri da Kwantagora da Minna da Gwambe da Potiskum da Shagamu da Keffi da Yola da Wase da Lagos da Wamba da Zuru.

    (iii) Rukuni na uku ya ƙunshi garuruwan da suke cikin Jamhuriyar Nijar waɗanda suka haɗa da Maraɗi da Tassawa da Agades da Birnin-Ƙwanni da Yamai.

     1.2 Manufar Wannan Bincike

    Kafin shiga bayani a kan manufar wannan bincike yana da matuƙar muhimmanci a san ma’anar kalmar manufa. A ƙamus na Turanci (Hornby, 2000:804) an fassara kalmar manufa ‘objective’ a “matsayin wani abu ko buri da ake son cimma”. Abin nufi a nan shi ne, manufa na nufin tsara wasu hikimomi don samun biyan buƙata kan abin da aka sa gaba. Misali, babbar manufar duk wani malamin makaranta ita ce, bayan ya kammala darasinsa ɗaliban da yake koyarwa su fahimci abubuwan da ya koya masu.

    Idan muka juyo kan manufar wannan bincike za a ga bisa la’akari da ayyukan da mutane suka yi na rayuwar yau da kullum an fahimci kowane mutum yana da manufar da take cikin ransa da yake son ya cim mata. Masana da manazarta sun gabatar da ayyuka gwargwado kan al’adun Hausawa.

    Yawanci a waɗannan nazarce-nazarce an fi mayar da hankali kan fito da abubuwan da suka danganci al’adun aure da haihuwa da mutuwa da nazarin addinin gargajiya waɗanda suka shafi sihirce-sihirce da tsubbace-tsubbacen Hausawa. Bisa dukkan alamu ba a gudanar da wani bincike mai zurfi kan sana’o’in gargajiya na Hausawa ba, in ban da aikin Sharifai (1990) shi ma wanda ya yi game da kirari da take na sana’o’in Hausawa na gargajiya da kuma na Sallau (2000) wanda ya yi game da sana’ar wanzanci.

    Haka kuma ire-iren waɗannan ayyukan ba a faye duba rawar da sauye-sauyen zamani suka taka a wajen bunƙasa sana’o’in gargajiya na Hausawa ko daƙushe su ba. Saboda haka babbar manufar wannan bincike ita ce nazarin ƙaura da shigowar baƙi da tasirin al’adunsu a kan wanzancin Hausawa. Amma a rarrabe, wannan bincike ya fuskanci waɗannan abubuwa kamar haka:

    (i) Ƙaura da shigowar baƙi ƙasar Hausa tun daga farkon ƙarni na goma sha huɗu zuwa yau.

    (ii) Matsayin sana’ar wanzanci a idon Hausawa da kuma maƙwabtan Hausawa na kusa waɗanda suka haɗa da Fulani da Barebari da Buzaye da Nufawa da Yarabawa da sauran ƙananan ƙabilun sassan kudancin jihar Kaduna da wasu sassan jihohin Bauci da Gwambe da Filato da Nasarawa da Neja. Sai kuma maƙwabtan Hausawa na nesa waɗanda suka haɗa da Larabawa da Turawa.

    (iii) Sauye-sauyen zamani irin waɗanda al’adun maƙwabtan Hausawa na kusa da na nesa suka yi a kan sana’ar wanzanci.

    1.3 Ƙunshiyar Bincike

    Wannan bincike ya ƙunshi babi shida. An fara da yin shimfiɗa a inda aka bayyana hasashen wannan bincike da wuraren da aka samo bayanan da aka yi amfani da su wajen gabatar da wannan nazari.

    Sannan kuma aka yi bitar ayyukan da suka gabata waɗanda suka taimaka wajen sanin wuraren da wannan bincike ya sa gaba. Bayan haka an yi waiwaye kan ƙasar Hausa da ɓunƙasarta da yadda baƙi suka shigo da dalilan shigowarsu da garuruwan da suka zauna. An kuma yi bayani dangane da tasirin addinin Musulunci kan wasu al’adun Hausawa waɗanda suka shafi dabbar suna da askin ranar suna da al’adun kaciya da kaciyar mata, da sauran wasu ayyuka da wanzamai suke yi a ƙasar Hausa.

    An ci gaba da kawo bayanan da suka danganci wasu al’adun Turawa cikin sana’ar wanzanci waɗanda suka haɗa da aski da kaciya da cire haƙori da gudummuwar ba da jini da matakan da ake bi don kula da mai ciki da iren-iren hanyoyin da ake bi don tanadin abin da aka haifa da kuma irin yadda magungunan Turawa suka yi tasiri a kan ire-iren waɗanda wanzamai suke bayarwa.

    Daga ƙarshe an kawo bayani kan nason da al’adun wasu baƙi waɗanda suke zaune a cikin ƙasar Hausa da kuma na wasu al’ummomi maƙwabta waɗanda Hausawa suke zaune a cikin ƙasashensu suka yi a kan wanzanci.

    1.4 Dabarun Aiwatar da Bincike

    A wajen aiwatar da wannan aiki an bi wasu dabaru da hanyoyi don gabatar da shi waɗanda suka haɗa da:

    (i) Hanyar nazarin zaune inda aka bi ɗakunan ajiye littattafai da kundaye digiri na uku da na biyu da na ɗaya da littattafai na ɗab’i aka karanta waɗannan ayyuka aka taƙaita su. Daga cikin ɗakunan karatun da aka ziyarta akwai na Jami’ar Bayero ta Kano da na Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo ta Sakkwato da na Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya da Jami’ar Maiduguri da Babbar Kwalejin Ilimi ta Abdullahi Augie ta Argungu da Babbar Kwalejin Ilimi ta Gwamnatin Tarayya a Kwantagora da Babbar Kwalejin Ilimi ta Gwamnatin Tarayya a Zariya da Babbar Kwalejin Ilimi ta Jihar Kaduna a Gidan-Waya Kafanchan. Haka kuma an ziyarci ɗakunan karatu na Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Hassan Usman a Katsina da Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kaduna.

    (ii) Hanyar ziyartar ɗakunan ajiye kayan tarihi na jihohi waɗanda suka haɗa da Hukumomin Binciken Tarihi da Kyautata Al’adu na Jihohin Kano da Katsina da Zamfara da Sakkwato da Kabi da Neja da Nasarawa da Kaduna da Yobe da Borno da Adamawa da Bauci da kuma Gwambe. An kuma ziyarci Hukumar Adana Kayan Tarihi ta Ƙasa da take Kaduna. Haka kuma an ziyarci Cibiyar Binciken Tarihin Arewacin Nijeriya wadda take ƙarƙashin Sashen Koyar da Tarihi na Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya. An kuma ziyarci Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya ta Jami’ar Bayero Kano da kuma Cibiyar Al’adun Gargajiya ta Jami’ar Ahmadu Bello Zariya.

    (iii) Hanyar amfani da takardun tambayoyi da aka rubuta da harshen Hausa waɗanda aka rarraba wa wasu Hausawa a sassa daban-daban na ƙasar Hausa da wasu garuruwan da suke maƙwabtaka da wannan ƙasa. Akwai kuma wadda aka rubuta da harshen Turanci aka rarraba wa musamman waɗanda ba Hausawa ba mazauna ƙasar Hausa da maƙwabtanta. An rarraba waɗannan takardu ga maza da mata, matasa da dattawa.

    iɓ) Hanyar yin hira da mutane daban-daban musamman wanzamai su kansu da ungozomomi da masana da manazarta da sauran jama’a waɗanda suka bayar da ra’ayoyinsu. Haka kuma an zauna cikin waɗannan wanzamai aka yi nazarin yadda suke aiwatar da aikace-aikacen wanzanci, musamman a garuruwan da ba a ƙasar Hausa ba.

    An gudanar da waɗannan hirarraki a garuruwan:

    Akwanga da Arugungu da Bauchi da Bida da Birnin-Kabi da Birnin-Ƙwanni da Damagaram da Damaturu da Daura da Gusau da Gwambe da Ibadan da Ilori da Jega da Jos da Kaduna da Kafanchan da Kagoro da Katsina da Keffi da Koko da Kwantagora da Lafiyar-Barebari da Lagos da Maiduguri da Manchok daMaraɗi da Minna da Potiskum da Sakkwato da Tassawa da Wase da Yamai da Yawuri da Yola da Zariya da Zuru.

    A taƙaice kamar yadda aka gani wannan babi na share fage ne don kuwa bayanan da suke cikinsa an yi su ne inda aka fito da hasashen binciken da manufofinsa da abubuwan da nazarin ya ƙunsa da kuma dabarun da aka yi amfani da su wajen tattara bayan da suka haifar da wannan kundi.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundi mai taken SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU: NA BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU

    KUNDIN BINCIKE WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI, SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA, JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

     MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu