Tag: Waƙar Ya’yan Alhazai

  • Waƙar Ya’yan Alhazai

    Waƙar Ya’yan Alhazai

    Ya’yan Alhazai laƙabi ne na Hausawa da Fulani da Bare-Bari (‘Yan Asalin Najeriya) waɗanda aka haife su a ƙasar Sudan, sakamakon tafiya aikin Hajji da iyayensu suka yi.

    1. Ganin ku ‘ya’yan Alhazai ya sa ina; 
    2. Ta tunatunin manya mazajen gaskiya. 
    3. Waɗanda ƙaunar Rabbana tsantsa ta sa; 

    Suka ƙaurace wa gida da daɗin duniya. 

    1. Ba kasuwanci koko noma za su je; 

    Ba bare a ce wannan bahaushe zai iya. 

    1. A a nufinsu kawai su keta duhun dare;  Su fice saharar nan kamar tatsuniya.
    1. Su je “Hijazu”4 Gabas su yo aiki Hajji;  Sannan su ga masu da sun ci burin duniya.
    1. Tun ma Bature bai yi ko da keke ba; 

    Balle su jirgi masu keta samaniya. 

    1. Sai dai su hau doki gami da su taguwa; 

    Koko su Alfadari da Jaki sha-wuya. 

    1. Ko Raƙumi ko ma su wanke ƙafafuwa; 

    Da ƙafarsu za su fito su doshi Sa’udiya! 

    1. Gaishe ku! Bayin Rabbana yaya kukai; 

    Da zama a zango inda babu gida ɗaya? 

    1. “Allahu Akbar” ya kuke a cikin Hama5

    Da lokacin rana kamar garwashiya. 

    1. Fatar jikunku kamar gasa ta ake ta yi; 

    Ina kukan samo ruwan sanyi niya. 

    1. Yaya kukai da harin ɓarayi masu son; 

    Su kashe mutum su fice da ɗimbin dukiya 

    1. Ko ko harin kura da kan yi cikin dare;

    4 Hijaz-Qasar Makkah da Kewaye. 

    5 Hamada – Sahara ke nan.

    Ku ko kuna tsaye tun daren har safiya. 

    1. Wata ma a sannan naƙuda kan zo mata: 

    Mata su je mata har ta haife lafiya. 

    1. Fallomi ga su Junaina har da Lubayya ma; 

    Dukkansu su shaida da kun yi gwagwarmaya. 

    1. Khartuumu Undurmana ga Madaninmu can; 

    Maƙil da ‘ya’yayen fataken gaskiya. 

    1. Maiwurno ga Sinari Sinja akwai su can; 

    A garin Damazin har zuwa ga “Isofiya” 

    1. A garin Gadarifu har zuwa Kasala da Bor

    Sudan Sawakin duk suna can bai ɗaya. 

    1. Haka nan kukai artabu ɗulin shekaru; 

    Kafin a ce kun je ku bakin Maliya. 

    1. Kogin da babu kamarsa ya haɗe duniya; 

    Zurfi da faɗi ga yawan ambaliya. 

    1. Sannan ku ajjari6 Murkaba wato kwami; 

    Don keta hamshaƙin ruwan nan Maliya. 

    1. Kukan yi kwanakki ɗari a cikin ruwa; 

    Wa ke batun girkin tuwo balle miya! 

    1. Amma a sannan kun yi fama, ba ta ma; 

    Kogi ake ba kawai, abokan taffiya. 

    1. Wani ba jimawa sai amai domin jiri; 

    Kullum yake yi har da tashin zuciya. 

    1. Wani ko gudawa in ta rafkake shi sai; 

    Dai ai ta biƙi nai da kiwon lafiya. 

    1. Shi ko matuƙin ba ruwansa gama mafi; 

    Yawan su ba su da tausayi ko da ɗaya. 

    1. Cewa yake yi ba ruwana ni idan; 

    Wani ya mace lallai a jefa Maliya. 

    1. Haka nan kukai har sai da kun ka haye ruwa; 

    Kuka je ku bautar Rabbana Sarki Ɗaya. 

    1. Haka nan kukai gumu a faɗin rayuwa;
    2. Gaishe ku jikoki da ‘ya’yan alhazai; 

    Ku kanku aya ce ta aikin gaskiya.

    Domin karanta cikekken littafin Danna nan