Tag: Neman Mafita Da Riba Babba

  • Waƙar Neman Mafita Da Riba Babba

    Waƙar Neman Mafita Da Riba Babba

    1. Allah sarki ne mai yawaita

    Falala da tsari da kyauta

    Bismillah zan karanta

    Waƙar mafita da riba

    2. Zamanin nan ya ƙazanta

    Lamurra duk sun jirwanta

    Ayyuka da halin mugunta

    Ga cin amana bai tsaya ba.

    3.  Garkuwa don kuɗi da sata

    Ga yawan fyaɗe da ƙeta

    Ga rashin ladabin ‘yammata

    Duk ba zai mana mafita ba.

    4. Tur da sauyi maras nagarta

    Mai ɗorawa mutum kurumta

    Ayyukan sharri ko mugunta

    Mance Allah ba zai mana ƙa’ida ba

     

    5. Son kuɗi duk ya tsananta

    Burin kowa ya huta

    Da kuɗi mata da mota

    Babu cas, ko as dat ta’abba.

     

    6. Shi yasa ayyukan mugunta

    Munana, masu raba zumunta

    Ayyuka na rashin aminta

    Sun yawaita ba ma huta ba.

     

    7. Ga uwa ta saida ɗanta

    Ga uba ya haiƙewa ‘ƴar ta

    Ga ɗa yay fansa da wauta

    Ya subhanallahi ka tsare mu gaba

     

    8. Ran Hanan dai ya salwanta

    Malaminta ya ha’inta

    Ya aikata abin mugunta

    Aikin sa gareshi babu riba

     

    9. Aisha mai kasshe kanta

    Wani jami’i shi yai lahanta

    Cin zarafi mai muni na mata

    A zamanin nan ana yi ba da ƙa’ida ba

     

    10. Shugabanni da halin mugunta

    An sa talaka yana ragaita

    Daɗin haraji, tsada, duk an azabta

    Janye tallafin mai ba abu ne mai kyau ba

     

    11. Masu tsafi kun ƙazanta

    Masu caca kuna da wauta

    Luɗu da cin zali duk sun haramta

    Wanda duk bai bi Allah ba ba zai zauna lafiya ba

     

    12. Yau fasadi ya inganta

    Mai bin shaiɗan zai kafirta

    Ayyukan sa duk sun muzanta

    Annabin Allah ya hane mu da cin riba

     

    13. Masu shirka sun yawaita

    Masu kiran haram saboda wauta

    Ayyukan gaskiya ya ƙaranta

    Lalle masifa a duniya ba ta gushe ba

     

    14. A yau ƙarya ita ce mai tsafta

    Wasu ma sun ƙware a kanta

    Samun kuɗin su shi ne mafitta

    Ai kuwa hakan ba abu ne mai kyau ba

    15. Aikin ‘yan ta’adda ya ƙazanta

    Zubar jini a yankin mu ya yawaita

    Asalinsu akwai cin hanci da ƙeta

    Jami’ai masu cin amana ƙarshensu ba zai yi kyau ba

     

    16. ‘Ƴan siyasa ya kuke ta

    Yaudarar talaka da sata

    Kun hana arziƙi ya wadata

    Kawunan ku kuke so ba talaka mai wahala ba

     

    17. Ya kamata fa mu fahimta

    Arziƙi ko da ya tsananta

    Ko talauci in ya rabanta

    Ga bawa ƙaddara ce wadda ba a guje ba

     

    18. Tun gabannin yin halitta

    Rabbuna Allah ya hukunta

    Arziƙin ɗa, bawa ko jarrabta

    Duk abinda mutum zai yi ba zai keta ƙa’ida ba

     

    19. Yanzu menene mafitta?

    Ga zukata sun firgitta

    Rashin natsuwa ya yawaita

    Duk abinda mutum zai yi ba zai sake ba

     

    20. Fahimtata a rayuwa ta

    Sai mun sauya jigon nagarta

    Sai mun rage raɗaɗen masu jinta

    Sai muso juna da alheri banda gaba

     

    21. Jama’ar mu akwai nagarta

    A basu ilimi shi na fahimta

    Zai kawar da talauci mai kanta

    Duk mai aiki da hikima ba zai sha wuya ba

     

    22. Ilimi mai sa nagarta

    Mai gyara ayyuka da fahimta

    Jahilci kuwa idan ya yi kanta

    Dole ayyukan jama’a ba za su yi kyau ba

     

    23. Tarbiyya ko mafi inganta

    Turbar Islama binta

    Ba fasadi babu cuta

    Komai aka mayar ga Allah ba zai zama mai wuya ba

     

    24. Ladabi abu mai kyau ga mata

    Rufe tsiraicin su za su kuɓuta

    Bin iyaye da magabata

    Barin fariya, yin ɗagawa abu ne ba mai kyau ga lahira ba

     

    25. A koyar da yara jarumta

    Aiki tuƙuru shi ne za a huta

    Lalaci, sakaci ko sata

    Ayyuka ne haramtattu da ba za a yi su da ƙa’ida ba.

     

    26. Mu kalli Japan, Sin da Kolkata

    Matasa na fafutika, kai hatta

    Yara ƙananu da mata

    Kowa na son ceton ƙasarsa ba cutar da ita ba

     

    27. Neman halak abu ne mai tsafta

    Mai gyara ƙasa da zukata

    Idan zukata suka ladabta

    Ayyukan bayi da dama ba za su ƙetare ƙa’ida ba

     

    28. Wajibi zalinci ya huta

    Adalci shi ake buƙata

    Tsayar da haddi ga masu gata

    Matsawar kuɗi suka rinjayi adalci ba za mu zauna lafiya ba

     

    29. Ya Allah ka ba mu mafitta

    Ya Rahmanu sarkin Nagarta

    Ya man iza da aka fa ajibta

    Ya Laɗifu ka yaye mana  rashin aminci da gaba

     

    30. Ni Sadiq Gwarzo na yawaita

    Damuwa shi yasa na rubuta

    Waƙar ina kewa da buƙata

    Ina adduar samun tsira da rabo babba.

    ALHAMDULLAHI

    Karanta Tarihin Garin Rimin Gado

    Edita@rumasau-kallamu