Tag: Maƙala

  • Maƙala Mai Taken: Gurbin Makaɗa Sa’idu Faru a Sikelin Manazartan Ƙarni Na 21

    Maƙala Mai Taken: Gurbin Makaɗa Sa’idu Faru a Sikelin Manazartan Ƙarni Na 21

    Gurbin Makaɗa Sa’idu Faru a Sikelin Manazartan Ƙarni Na 21

     Daga

     Dr. Adamu Rabi’u Bakura

    Department of Languages and Cultures

    Federal University Gusau, Zamfara State, Nigeria

    Email: arbakura62@gmail.com

    Phone: 08064893336

     

    Da

     

    Abu-Ubaida SANI

    Department of Languages and Cultures,

    Federal University Gusau, Zamfara, Nigeria

    Email: abuubaidasani5@gmail.com | abu-ubaidallah@fugusau.edu.ng

    official@amsoshi.com | ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334

    Citation: Bakura, A. R., & Sani, A.-U. (2024, May 3–6). Gurbin Makaɗa Sa’idu Faru a sikelin manazartan ƙarni na 21. Paper presented at the International Conference on the Life and Songs of Alhaji Sa’idu Faru, Department of Languages and Cultures, Federal University Gusau, Zamfara State, Nigeria.

    Tsakure

    Masana suna la’akari da waɗansu alƙaluma yayin ayyana makaɗan Hausa a ƙarƙashin wani rukuni na musamman daga cikin tarin rukunonin makaɗa da ake da su a farfajiyar adabi da al’adun Hausawa. Waƙoƙin fada na daga cikin shahararrun rukunonin waƙoƙin baka. Wani abin lura shi ne, akan samu makaɗan da ke ƙarƙashin wannan rukuni da suke sauya sheƙa ko su kasance jemagu sakamakon tasirin zamani ko waɗansu dalilai masu alaƙa da tattalin arziki ko waninsa.

    Binciken nan yana da manufar bitar rayuwa da waƙoƙin Alhaji Sa’idu Faru domin ganin ko ya sauya sheƙa ko kuma ya kasance makaɗin sarauta kaifi ɗaya na tsawon zamanin kiɗansa? An yi amfani da dabarun ƙalailaice waƙoƙin makaɗin da kuma yin hira da masana a wannan fanni a matsayin hanyoyin tattara bayanai.

    Sakamakon binciken ya tabbatar da cewa, Sa’idu Faru ya tabbata makaɗin sarauta na yankan shakku, domin kuwa dukkannin waƙoƙinsa ba su fita daga da’irar sarauta da masarauta ba. Daga ƙarshe binciken ya ba da shawarwari da suka haɗa da nuna dacewar tattarawa da kundace waƙoƙin wannan shahararren makaɗi domin gudun salwantar su.

    Fitilun Kalmomi: Kiɗa, Waƙa, Waƙoƙin Fada, Waƙoƙin Sarauta, Makaɗan Fada, Makaɗan Sarauta

    1.0 Gabatarwa

    Allah ya arzurta mawaƙan Hausa da ɗimbin hikima da basira tare da fasahar sarrafa harshen Hausa wajen ƙaga waƙoƙi. Wannan ne ya sa sukan rera waƙoƙin da suka danganci fannonin rayuwar ɗan’adam daban-daban.

    A sakamakon haka ne masana da manazarta adabin Hausa suka karkasa makaɗan zuwa azuzuwa ta la’akari da rukunonin al’ummar da makaɗan ke yi wa kiɗa da waƙa. Masana kamar Bello (1982) da Yahaya (1983/85) da Mashi (1986) da Gusau (1996) sun raba mawaƙan zuwa rukuni-rukuni gwargwadon fahimtarsu, ta la’akari da abubuwa kamar haka:

    • Muhallin waƙoƙinsu
    • Kayan kiɗansu
    • Jigogin waƙoƙinsu

    Hasali ma kowane rukunin da makaɗan ke yi wa kiɗa da waƙa akwai kayan kiɗan da suka keɓanta da su wajen sarrafawa a yayin da suke aiwatar da sana’arsu ta waƙa. Bello (1982) da Ibrahim (1985) da Gusau (1996) sun raba mawaƙan Hausa ta la’akari da muhallin waƙoƙinsu, kamar haka:

    • Mawaƙan sarauta/Fada
    • Mawaƙan jama’a
    • Mawaƙan Sana’a
    • Mawaƙan ban dariya
    • Mawaƙan sha’awa

    Wannan aiki ya karkata kan binciko gurbin Makaɗa Sa’idu Faru a cikin makaɗan fada. Makaɗan fada sun shahara wajen luguden kalmomin Hausa ta fuskar salo, raha, ƙaƙale, yabo, zambo, habaici, shaguɓe, zuga da adana tarihi, da sauransu. Sukan sauya falsafar da suka gada kaka da kakanni sakamakon sauyawar zamani da ire-iren sauye-sauyen da ke wanzuwa a tsarin sarauta da raguwar ƙarfin ikon sarakunan ƙasar Hausa.

    Wannan ya sa wasu makaɗan suka zama bigi-sa-bigi-taiki domin neman tara abin duniya. Fahimtar haka ne ya sa wannan muƙalar ta yi azamar ɗora waƙoƙin Ɗan’umma Uban Kiɗi bisa sikelin bin diddigin gano ko makaɗin ya sauya sheƙa sakamakon sauyawar zamani, ko kuwa yana kamilin makaɗan sarauta har ya karɓa kiran Ubangijinsa?

    2.0 Bitar Muhimman Batutuwa

    2.1 Kiɗa

    Kiɗa Bahaushiyar kalma ce wadda Hausawa suke kiran ta kiɗaa. Kalmar tana cikin jerin kalmomi na suna jisin maza. Jam’in kalmar kuwa shi ne kaɗe-kaɗe. A wani karin harshen kuwa sukan ce kiɗe-kiɗe. Kalmar tana ƙunshe da ma’ana kamar haka:

    • Buga ganga ko kalangu da abin bugawa.
    • Bugun ƙwarya ko goge ko garaya da hannu ko da makiɗi ko da wani abu, kamar yadda Kano, (2006 p. 243) ya bayyana.

    Garba, (1990 p. 89) cewa ya yi kiɗa na nufin: “Yin amfani da abubuwa don ta da amo iri daban-daban.” A wata ma’anar kuwa cewa ya yi kiɗa na nufin, “Fasahar tsara amo na muryar mutum ko daga abubuwa ko duka a haɗe.” Yayin da aka dubi waɗannan ma’anonin za a iya cewa, kiɗa yana nufin buga wani abu a kan wani domin samar da wani amon sauti da ka iya jan hakalin mai saurare.

    2.2 Waƙa

    Kalmar waƙa tana cikin jerin kalmomin suna jinsi mace. Jam’inta kuwa waƙoƙi ko waƙe-waƙe. Kalmar tana ƙunshe da ma’anar: “Magana wadda akan rera da baki, aka tsara bisa wani zubi na musamman” kamar yadda Garba (1990 p. 152) ya nuna. Shi kuwa Kano, (2006 p. 466) ya bayyana ta da ma’anar, “Tsararriyar magana da ake rerawa a kan kari ko rauji.”

    Waƙa a bisa ma’anarta, tana nufin furta abin da ke cikin ƙwaƙwalwa. Sau da yawa akan ji Bahaushe na cewa:

    1. Na waƙa yi masa dukan fitar arziki.
    2. Na sha waƙa zuwa aikin Hajji.
    3. Na waƙa masa farashin kayan.
    4. To, Allah ya sa ba waƙa ba ce.

    A wata ma’anar kuwa, waƙa takan kasance wata murya ko zaƙin murya mai shiga zuciya da faranta rayuwa. Misali , Bahaushe kan ce:

    1. Ai na zaci waƙa ce.
    2. Ya matse sauti kamar mai waƙ
    3. Zaƙin murya sai ka ce zabiya.

    Ta wata fuskar kuwa, waƙa takan kasance wata magana wadda akan rera da baki, wadda kuma aka tsara bisa wani zubi na musamman.

    Dangane da ma’anar waƙa ta ɓangaren adabi kuwa, za a ga masana adabin baka da dama sun ba da ma’anarta a wurare mabambanta gwarwadon fahimtarsu. Daga cikin masanan, Gusau (1984 p. 3) cewa ya yi:

    Waƙar baka ita ce wani saƙo cikin zance na azanci da ake rerawa ba faɗa kurum ba, ta cikin hikima da fasaha da zaɓaɓɓun kalmomi, waɗanda suka dace da saƙon. Kuma tana zuwa gunduwa-gunduwa, dangane da sautin murya da kiɗa da amshi da gaɗa da taɓi ko zabiyanu mai saka zuciya jin daɗi.”

    Shi kuwa Umar (1987 p. 7) ya bayyana ma’anar da cewa:

    Waƙa ita ce nau’in sarrafaffen harshe da ake gabatarwa da sigar gunduwoyin zantuttukan da ake kira baitoci ko ɗiyoyi, waɗanda ake ginawa a kan kari ƙayyadadde, kuma ake rerawa da wani irin sautin murya na musamman.

    Yayin da aka nazarci waɗannan ma’anoni da masana suka bayyana, za a ga cewa, suna ƙoƙarin nuna cewa, waƙa na nufin tsararriyar magana da ke ƙunshe da fasaha da hikimar sarrafa harshe da ake rerawa gunduwa-gunduwa, cikin wani amo na musamman.

    2.3 Waƙoƙi Fada

    Su ne wasu manazarta kan kira da waƙoƙin sarauta. Waƙoƙi ne da ake yi wa duk wani da ya jiɓinci jinin sarauta ko aka ba shi wani matsayi na musamman a majalisar sarki, inda ake taro domin gudanar da mulkin al’umma cikin tsari irin na gargajiya. Masu aiwatar da waɗannan waƙoƙin su ake yi wa laƙabi da makaɗan sarauta ko mawaƙan sarauta.

    Ta fuskar ma’ana kuwa, Gusau (1988 p. 165) cewa ya yi:

    Waƙoƙin baka na fada su ne waɗanda makaɗa na musamman ke gudanarwa ga sarakunan gargajiya da iyayen ƙasa da hakimai da dagatai da masu unguwanni da ‘ya’yan sarakuna da fadawa da masu riƙe da da muƙaman sarauta da sauran ƙungiyoyin da suka jiɓinci sarauta.

    Waƙar fada na zuwa ne a rere cikin sautin murya da daidaita shi, wanda ya sa take zuwa gutsure-gutsure (gunduwa-gunduwa) tare da maimaita gindinta a tsakaninsu. Kowane gutsure kammalalle ne ga kansa, amma wani zubin ma’anarsa takan cika ta tumbatsa har ta tsallaka ga gutsuren da ke bi masa. Gutsuren nan ne ake kira ɗan waƙa, jam’insa kuwa, ɗiyan waƙa.

    Ana iya cewa, waƙar fada shiryayyen zance ne mai zuwa gaɓa-gaɓa bisa ƙa’idojin tsari da daidaitawa da ake yi wa wanda ya shafi sarauta domin a yabe shi, ko zuga shi ko kambama shi tare da fito da shi fili kowa ya san shi. Takan ƙunshi nakasa (aibanta) abokan hamayyar wanda ake yi wa waƙar ta hanyar yi musu zambo da habaici da shaguɓe da nuna hushi da tsoratarwa da firgitarwa da sauransu.

    2.3.1 Wanzuwar Waƙar Fada

    Ana kyautata zaton an soma waƙa ne a farfajiyar doron duniya a daidai lokacin aka ƙirƙiro farauta da samuwar addinin gargajiya. Gusau (1988 p. 167) ya nuna cewa, waƙa ta ƙara bunƙasa da haɓaka sanadiyyar yaƙe-yaƙe da bayyanar sana’o’i da wasannin motsa jiki da wasu lamurran da suka jiɓimci al’adun gargajiya. Masanin ya nuna cewa, a farfajiyar ƙasar Hausa farauta ta kasance daɗaɗɗiyar sana’a da aka fara aiwatarwa. Hasalima an sami waƙoƙin da suka dangance ta.

    Ana cikin irin wannan yanayi ne, sai sarautun gargajiya suka bayyana sakamakon taruwar al’ummar Hausa tsangaya-tsangaya. Wannan ya faru ne tun daga lokacin da suka kafa mazaunai don samar da wurin zama na dindindin, domin samun damar gudanar da sana’ar noma da kiwo da wasu abubuwan inganta rayuwa tare da kare kai daga farmakin namun daji.

    Ana kyautata zaton daga lokacin ne aka soma yi wa sarki waƙoƙi gajeru. Bayan bunƙasar waɗannan tsangayoyin mazaunin farko zuwa ƙauyuka da garuruwa da birane, sai yaƙe-yaƙe suka haddasu a tsakaninsu, domin ƙoƙarin tabbatar da mulkin danniya. Ana cikin irin wannan yanayi ne yaƙe-yaƙen ƙabilanci suka wakana a tsakanin ƙabilu da Hausawa domin son mulki da iko da kuma shugabanci na sarakuna da ke mulkin su, ko kuma don neman faɗaɗa ƙasa ta mulki domin ta zama babbar daula.

    Sakamakon irin waɗannan yaƙe-yaƙe da suka auku ne ya wanzar da samuwar wasu masu rauni da ke da kishin al’ummarsu; waɗanda ba su da ƙarfin karawa da dakarun yaƙi. Su ne suka dinga amfani da hikimarsu da basirarsu da zalaƙarsu wajen gudanar da kirari na yabon sarakunansu tare da zuga jarumansu domin ƙara musu ƙwarin guiwar fatattakar abokan adawa.

    A wani ƙaulin kuma, Gusau (1988 p. 167) ya nuna cewa, makaɗan da suka rinƙa yi wa sarakunansu guntayen waƙoƙi tun kafin a fara yaƙe-yaƙe ne suka cigaba da koɗa sarakunansu a fagen daga tun kafin a fita yaƙi ko bayan an dawo.

    A wani ƙaulin kuwa an bayyana cewa, a lokacin da ake kaɗa wasu kayan kiɗan yaƙi kamar: Tambari da kurya, sai Ɗanma’abba ya rinƙa aiwatar da kirari tare da zuga sarkinsu. Daga irin haka ne ‘Yanma’abban suka samu sukunin ɗinka ganguna da ƙudurin in an tafi yaƙi ko bayan an dawo su dinga cicciɓa sarki da jama’arsa.

    Hasali ma tare da su ake zuwa yaƙin. Ko an samu ɓacin rana, ba za a kashe su ba, sai dai su bi sarkin da ya samu nasara su dinga yi masa waƙoƙi suna zuga shi kan bajintarsa (Gusau, 1988 p. 168). A sakamakon haka ne wasu ƙasashe suka samu damar mallakar tamburran abokan hamayyarsu. Misali, kamar yadda ake hasashen cewa irin haka ne ya haifar da Gumawa suka mallaki tamburran Zamfarawan Anka.

    A tsakanin shekarar 1910 zuwa 1915 a daidai lokacin mulkin Sarkin Musulmi Muhammadu Maiturare aka daina kiɗan yaƙi, kamar yadda Gusau (1988 p. 170) ya nuna. Daga nan sai makaɗan suka koma ga aiwatar da waƙoƙin ga sarakuna suna yabon su ta hanyar bayyana musu irin bajintar da kakanninsu suka nuna a fagen fama.

    Wannan salon kiɗan shi ne ake yi wa laƙabi da kiɗan fada ko kuma a ce kiɗan sarauta ko na iko ko mulki. Hasali ma shi ne ya maye gurbin kiɗan yaƙi. Daga lokacin ne sarki kan gayyato mawaƙi ya yi masa waƙa a inda zai yabe shi, ya kuma zuga shi, kana kuma ya kushe abokin gabarsa. Yayin da mawaƙi ya gama rera waƙoƙinsa, sai sarkin ya yi masa gagarumar kyauta ta ƙasaita.

    A sakamakon wannan, mawakin yakan ji yana ƙaunar sarkin. Soyayyarsa takan sa ba wanda yake yi wa waƙa sai sarkin. Sakamakon haka ne sarakuna suka samu damar mallakar makaɗa da mawaƙa a fadojinsu, har suka zama makaɗan fada, kamar yadda Gusau (1988 p. 170) ya bayyana.

    2.3.2 Musabbabin Yin Waƙoƙin Fada

    Akwai abubuwa da dama da suka sabbaba ƙaga kiɗan fada. Ire-iren waɗannan abubuwan sun ƙunshi, nuna buwaya (gagara) da rinjaye (fifiko) da dawwama cikin samun nasara da galaba a kan maƙiya da soyayya da kyauta da sauransu.

    Sakamakon irin waɗannan abubuwa da mazaje suka keɓanta da su ne, ke sa a shirya musu waƙoƙi domin ƙara zuga su tare da fito da martabarsu da kwarjininsu a idon jama’a. Misali, ga abin da Malamin Kiɗa Sa’idu Faru ke bayyana wa Sarkin Kiyawa na Ƙaura Alhaji Abubakar, a inda yake cewa:

    Ni kiɗin yaƙi nay yi ma Abu na Isau,

    Ba ni son kana zaunawa banza,

    Ka ɗauki takobi da bindigogi da bakukuwa.

    Ba mu sansani sai bakin Tsabre,

    Kano da Katsina hak Kwantagora,

    Duk riƙon Namoda na, shi na ac can,

    Garba ka amshe riƙon duk da Umaru,

    Umaru yab bam ma.

    (Sa’idu Faru: Gwabron giwa na Shamaki, Baba Ubangandu)

    2.3.3 Makaɗan Fada/Sarauta

    Su ne makaɗan da ke yi wa sarakuna waƙa kawai. Ba kasafai suke yi wa sauran jama’a waƙa ba. Sun fi mayar da hankalinsu a kan uwayen gidansu. Sarakuna su ne iyayen gijinsu. A sakamakon haka, ba sa yi wa kowa waƙa sai da izinin sarkinsu. Wannan na faruwa musamman kasancewar sarakunan ne suke ɗaukar ɗawainiyarsu, kuma sun fi kowa ganin ɗaukaka da darajar sarakunansu. Makaɗa da dama da ke cikin rukunin farko na makaɗan sarauta suna da wannan falsafar a cikin zukatansu. Misali, Mu’azu Na’alalo cewa ya yi:

    Darajar kaza gashinta,

    Darajar makaɗi sarkinai,

    (Gital, 1984) a cikin Abba da Zulyadaini (2002)

    Haka shi ma Jankiɗi ya ce:

    Jumirin kwaram a kwana ana tafiya sai goga,

    Jaki bai kai nan ba,

    ‘Yan yara masu kurin waƙa ku bar wargi,

    Ma’ana ba ta zama ɗai ba.

    Ni ba ni kiɗin iska sai ga sarkina.

    Idan aka dubi waɗannan ɗiyan waƙa, mawaƙan fada suna nuni da cewa, yi wa sarakuna waƙa ya fi kome martaba, don haka suna kallon yi wa talaka waƙa kamar aikin banza ne. A ɓangaren sarakunan da ake yi wa waƙar kuwa, sukan ɗauki ɗawainiyarsu da ta iyalansu tun daga muhallinsu, har abin da za su ci da kuma suturarsu. Sa’idu Faru ma ya nuna yadda ubangidansa ke ɗauke da lalurarsa a cikin ɗiyan waƙoƙinsa. Misali, ga abin da yake cewa:

    Sarki zamaninka na ruhwa,

    Na ta da kaina,

    Kowag gane ni da Daudu,

    Ya san sarki garan gawurtacce.

    (Sa’idu Faru: Waƙar Abubakar Sarkin Kiyawan Ƙaura)

    A nan za a fahimci cewa, makaɗin na ishara ne da cewa shi makaɗin sarauta ne, don haka ne sarkinsa ke ɗauke da buƙatunsa.

    Haka kuma ya fito fili ya na bayyana wa al’umma cewa, shi ne kawai makaɗin sarauta da ya rage a wannan zamanin. Sauran makaɗa sun koma makaɗan jama’a sakamakon juyin zamani. Ga abin da yake cewa kamar haka:

    Sa’idu Faru ka waƙar iko,

    Komai kaj jiya ƙarya a kai,

    Sa’idu Faru ka waƙam mulki,

    Komai kaj jiya ƙarya a kai.

    (Sa’idu Faru: Turakin Kano Amadu)

    2.3.4 Rabe-Raben Makaɗan Sarauta

    A wannan rukuni na makaɗan sarauta (makaɗan fada) za a tarar cewa Gusau (1996) ya kasa su zuwa ɓangarori biyu. Kashi na ɗaya (1) da na biyu (2). Jerin makaɗan da suka faɗo ƙarƙashin kaso na farko su ne:

    1. Abdu Kurna
    2. Abubakar Akwara
    3. Alhaji Muhammadu Sarkin Taushin Katsina
    4. Aliyu Ɗandawo
    5. Buda Ɗantanoma
    6. Ibrahim Gurso
    7. Ibrahim Narambaɗa
    8. Idi Ɗangiwa Zuru
    9. Jibo Maituru
    10. Muhammadu Dodo Maitabshi
    11. Muhammadu Inyaga
    12. Salihu Jankiɗi

    Kashi na biyu kuwa ya ƙunshi makaɗan da suka haɗa da:

    1. Alhaji Ɗankurma Maru.
    2. Alhaji Musa Ɗankwairo Maradun.
    3. Alhaji Sa’idu Faru
    4. Alhaji Sa’idu Maidaji Sabon-Birni
    5. Alhaji Sani Aliyu Ɗandawo
    6. Muhammadu Ango Maitabshi
    7. Muhammadu Maidamma Sarkin Taushi
    8. Sarkin Taushi Muhammadu Ɗanbunguɗu
    9. Umaru Maisa’a Tubali

    2.3.5 Alaƙar Makaɗan Fada Da Sarauta

    Makaɗan fada na ɗaya daga cikin rukunin al’umma da sarakuna ke ɗauke da lalurorinsu na yau da kullun. Sarki yakan zama ubangidan makaɗi, shi yakan ɗauki lalurar cinsa da shansa, ya yi masa gida ya ba shi gona, ya kuma rinƙa yi msa sutura tare da iyalansa. Haka kuma yakan ba shi kuɗaɗen ɓatarwa.

    Sarki yakan amince wa makaɗinsa fiye da sauran fadawansa. Yakan zauna tare da shi su yi hira cikin sakin fuska sosai da zaman amana da taimakon juna. Shi kuma makaɗin zai dinga girmama sarkin da mutunta shi tare da yi masa ladabi da biyayya tamkar yadda al’ummar fada ke yi masa.

    A al’ada, makaɗin fada bai fita waje ya yi wa wani sarki ko jinin sarauta waƙa, sai da izinin ubangidansa. Yayin da ya je waƙa gun wani, zai nuna wa sarkinsa duk nau’in abin alherin da aka yi masa. Wani lokaci, yana iya bayyana masa a cikin sigar waƙa.

    3.1 Siffofin Makaɗan Sarauta Da Matsayin Sa’idu Faru

    Makaɗan sarauta suna da waɗansu siffofi da suka fi alaƙantuwa da su. Sun haɗa da:

    1. Makaɗin sarauta shi ne wanda kan samu wani basarake ya zauna a wajensa ya kasance ubangidansa da zai rinƙa yi masa yammaci (kiɗa daren Juma’a) ko daren salla. Sukan bi sarki a duk lokacin da zai fita rangadi (kewayar gundumar da ke ƙarƙashin mulkinsa).
    2. Sukan nemi izinin ubangidansu kafin su tafi yawon kiɗa gidan wani sarki ko alƙali ko bafade ko wani mai arziki da ke ɗasawa da ubangidansu.
    3. Akasarinsu sun gadi kiɗa da waƙa irin na sarauta idan aka cire Aliyu Ɗandawo Shuni, wanda ya kasance ɗan wani shahararren malami da aka yi a can Shuni ɗin da ake kira da suna Modibbo Aliyu, Kamar yadda Gusau (1984) ya nuna.
    4. Sun fi kowane Bahaushe sanya tufafin gargajiya, wato sanya manyan riguna da wandunan buje da taguwoyi masu manyan hannaye. Sukan kuma naɗa rawani. Suna riƙe wannan al’ada ce saboda irin wannan suturar sarakuna kan ba su. Abin la’akari shi ne, sarakuna ba sa rabuwa da sanya manyan suturu komi gumi ko zafi. Hasali ma sarki ba zai fito gidansa ba rawani a kansa ba. shi ya sa makaɗan sarauta suka riƙe wannan ɗabi’a domin kare martaba da alfarmar sarauta. Shi ya bambanta su da sauran makaɗa da mawaƙan ƙasar Hausa.

    Duban ire-iren waɗannan siffofi da aka ambata a sama da la’akari da irin sigar yanayin shigar Alhaji Sa’idu Faru za ka tabbatar shi cikakken makaɗin sarauta ne. A lokacin rayuwarsa ba ka raba shi da shiga irin ta iyayen gidansa.

    3.2 Kayan Kiɗan Makaɗan Fada Da Gurbin Sa’idu Faru

    Ta sigar kayan kiɗa kuwa, makaɗan sarauta sun sha bamban da sauran makaɗa da mawaƙan baka na ƙasar Hausa. Haka kuma sun kasu kashi-kashi dangane da kayan kiɗan da suke amfani da su, da nau’o’in waƙoƙin da kuma uwa-uba irin garuruwan da suke zaune da kuma inda suka ƙaurato. Ta fannin kayan kiɗa, za a iya kasa su zuwa kashi uku kamar haka:

    1. Masu kaɗe-kaɗe
    2. Masu bushe-bushe
    3. Bambaɗawa (masu kirari) (Ibrahim, 1983 p. 2).

    Ta wannan haujin kuwa, Alhaji Saidu Faru yana cikin sahun makaɗan fada da ke amfani da kayan kiɗa dangin na sarauta. Su ma kayan kiɗan sarauta sun karkasu kamar haka:

    (i) Tafshi

    (ii) Kotso[1]

    (iii) Jauje

    (iv) Tambari

    (v) Banga

    Waɗannan kayan kiɗa akan yi amfani da su wajen tsima sarki ta hanyar kambama shi da magabatansa.

    Kashi na biyu kuwa sun ƙunshi abubuwan busawa ne da suka danganci:

    (i) Algaita

    (ii) Kakaki

    (iii) Ƙaho

    (iv) Farai

    Waɗannan kayan busa suna ba wa talakawa labari ne cewa, sarauta tana nan daram ta kafu. Suna kuma jawo hankulan masoya sarki da cewa su zo su ji abin da za a faɗa game da masoyinsu.

    3.3 Sauya Sheƙar Makaɗan Sarauta Zuwa Na Jama’a

    Sauye-sauyen ubangida ga makaɗan fada yakan faru ne a zamanin da sarakuna ke da ƙarfin ikon gudanar da al’amuran tafiyar da ragamar mulkin al’ummominsu, kafin mulkin Jamhuriya ta farko. A waɗansu lokuta makaɗa na sauya ubangidansu, musamman saboda dalilai kamar haka:

    1. Yayin da ubangida (sarki) ya karɓa kiran Mahaliccinsa.
    2. Yayin da aka fitar da shi daga sarautarsa.
    3. Yayin da ya daina yi wa makaɗinsa alheri.

    4.1 Nau’o’in Waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru

    Sa’idu Faru ya yi wa sarakuna da jinin sarauta waƙoƙi da dama waɗanda shi ma kansa bai san adadinsu ba saboda yawansu. Hasali ma, dukkan waƙoƙin shi ne ya ƙaga su da kansa. Shi ba kamar sauran makaɗan sarauta ba ne da ke maimaita waƙoƙin da mahaifansu suka aiwatar ba. A ƙasa an kawo waɗansu sarakuna da hakimai da uwayen ƙasa da ya yi wa waƙa:

    1. Sarkin Yamman Faru Ibrahim
    2. Sarkin Yaƙin Banga Sule
    3. Sarkin Kiyawan Ƙaura Abubakar Garba
    4. Sarkin Gabas Na Mafara Muhammadu
    5. Sarkin Musulmi Abubakar III
    6. Sarkin Yawuri Alhaji Muhammadu Tukur
    7. Sarkin Sudan Na Wurno Alhaji Shehu Malami
    8. Sarkin Kano Ado Bayero
    9. Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo
    10. Sarkin Gabas Shehu Uban Ƙasar Talata Mafara
    11. Turakin Kano Amadu
    12. Muhammadu Muhammadu Maidabo Tudun Falale
    13. Alhaji Muhammadu Mode, Ɗan Alin Birnin Magaji
    14. Sarkin Zamfaran Zurmi, Suleiman Muhammadu Sambo
    15. Sarkin Zazzau Alhaji Dr. Shehu Idris, da sauransu

    Ta fuskar waƙoƙin da ya yi wa ubangidansa kuwa, ya yi wa Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo waƙoƙi da dama. Abin da hannaye suka samu nasarar dafawa su ne:

    1. Farin cikin Musulmi duk kai muka taƙama yau,

    Muhammadun Muhammadu ɗan Abdu mai darajja.

     

    1. Sai na zo in yi mai kiɗi in ƙaro ilmi,

    Mamman Bajinin Magaji mai takakkay yaƙi.

     

    1. Farin cikin Musulmin Duniya, mai martaba na Abubakar,

    Ci fansa Alhaji Macciɗo.

     

    1. Kana shire Baban Yan Ruwa,

    Na Bello Jikan Ɗanfodiyo.

     

    1. Bajinin gidan Bello Mamman Na Yari,

    Sarkin Kudu Macciɗo ci maraya.

     

    1. Shugaban sahun gabas riƙa ƙwarai,

    Muhammadun Amadu Uban Zagi.

     

    1. Hattara Bajinin gidan Bello Jikan Hassan maganin wargi.

     

    1. Ya yi Sarki daidai wada mai yanzu yar riƙa,

    Alhaji Macciɗo jikan Mamman mai dubun bara.

    1. Mai babban rabo ginshiƙin Sarkin Shariffai.

     

    1. Hattara mai martaba Bello ɗan Bubakar,

    Sarkin Kudun Hausa.[2]

    Yayin da aka kwatanta Alhaji Musa Ɗankwairo a matsayinsa na mawaƙin sarauta kuma Sarkin kiɗan ‘Yandoton Tsahe Alhaji Aliyu, da Alhaji Sa’idu Faru, za a iya cewa, Ɗanƙwairo ya canza sheƙa sakamakon juyin zamani.

    Hasali ma ana hasashen cewa, tun waƙar Shirya Kayan Faɗa ba wata waƙa da ya sake yi wa ubangidansa. A madadin haka, sai ya karkata ga yin waƙoƙin jama’a da suka ƙunshi ‘yan kasuwa da ‘yan siyasa da malamai da tajirai. Wannan ne ya sa mafi yawan waƙoƙinsa suka zama na gama-gari. Misalan waƙoƙin sun haɗa da ta:

    1. Alhaji Shehu Kangiwa
    2. Kanal Umaru Muhammad
    3. Alhaji Ahmadu Aruwa
    4. Alhaji Kabiru Mado
    5. Alhaji Ali na Malan Bawa
    6. Alhaji Garba A.D. Kano
    7. Alhaji Garba Nadama
    8. Alhaji Ahmad Muhammad
    9. Alhaji Bala Maiyafe
    10. Malan Lawal Ƙalarawi
    11. Alhaji Bala Salisu
    12. Alhaji Sikofiyo
    13. Alhaji Bature Dogon Tela
    14. Alhaji Ibrahim Maganinta
    15. Waƙoƙin Faɗakarwa
    16. Waƙoƙin Jam’iyyun Siyasa

    Ta la’akari da jerin waɗannan waƙoƙin, za su iya kawar da Ɗanƙwairo daga cikin sahun mawaƙan sarauta. Ta fuskar Sa’idu Faru kuwa, babu waƙar da ya aiwatar da za ta iya fitar da shi daga cikin sahun makaɗan sarauta.

    4.2 Turakun Waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru

    Kasancewar Sa’idu makaɗin sarauta ne na asali, bai sake juyin zamani da kwaɗayin tara abin duniya ya ruɗe shi ba. Shi ya sa ya tsaya wajen gina waƙoƙinsa a kan turakun da iyaye da kakanni suka assasa tushensu tun farkon fara kaɗe-kaɗen fada (sarauta).

    Binciken masana kamar Gusau (1996 p. 121) ya tabbatar da cewa, Makaɗa Sa’idu faru ba ya yi wa kowa waƙa sai sarki da wanda ya kasance jinin sarauta. Waƙar farko da ya fara aiwatarwa ita ce ta Sarkin Yamman Faru Ibrahim. Gindin waƙar shi ne:

    Bi da maza ɗan Joɗi na Iro,

    Iro magajin Shehu da Bello.

    Hasken hitila ba ɗai da wata ba,

    Tauraro haskenka subahin,

    Dawaya kora ɗimau na wakili,

    Uban sarkin zagi Bello na yari.

    Ruwa da kada ɗibgau na Magaji,

    Sai tsohon wawa ka shigar su.

    (Gusau, 1996 p. 119).

    Tun daga wannan waƙar sai ya ci gaba da yi wa sarakuna da ‘ya’yan sarakuna waƙoƙi. Yana cikin irin wannan yanayi ne, Allah cikin ikonsa da baiwarsa ya sada shi da Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo ɗan Sarkin Musulmi Abubakar na III, wanda ya sarauci ƙasar Talata Mafara daga 1953 zuwa 1956, kamar yadda Talata Mafara (2007 p. 17) ya nuna. Ya fara yi wa Sarkin Kudu Macciɗo waƙoƙi a daidai lokacin da yake riƙe da muƙamin Ubanƙasar Talata Mafara. Ga gindin waƙar da ya fara yi masa, a inda yake cewa:

    Kana shirye baban ‘Yanruwa,

    Na Bello jikan Ɗanfodiyo.

     

    Gardaye zo ka yi man iso,

    Faɗa mashi murna niz zaka,

    Ɗan Sardauna jikan Hassan.

     

    Babban ɗa ga Baura Sarkin Kudu,

    Na Alƙali baban zagi,

    Mai ja ma ya bari ɗan Adamu.

     

    Na Sarkin Gobir Amadu,

    Ci fansa ga wan Sarkin Ƙaya.

     

    Waƙag ga da nim maka Muhammadu,

    Na ji daɗin ta Mamman Sarkin Kudu,

    Tun dak Kabi hak Kano ham Masar,

    Hab birnin Legas hab Bici,

    Kowa ya ji waƙar Sarkin Kudu.

    (Gusau, 1996 p. 120).

    Sa’idu Faru fasihin mawaƙin sarauta ne da ya naƙalci harshen Hausa ga baiwar da Allah ya yi masa ta fasahar ƙulla waƙa yadda za ta yi daɗi ta kuma yi armashi da ma’ana. Sakamakon haka ne ya kira kansa da Malamin waƙa, a inda yake cewa:

    Sa’idu Malamin waƙa,

    Mai kwana ɗumi na Mamman na Balaraba×2

    Ban wuce gonata da irina ba,

    Inda Sarkin Kudu nat tsaya.

    Gindin Waƙa: Farin cikin Musulmin duniya.

    (Faru: Waƙar Sarkin Kudu Muhammadu Macciɗo)

    Sa’idu Faru bai taɓa yi wa talakka waƙa ba, komai tarin dukiyarsa. Hasali ma shi da kansa ya yi nuni da haka, a inda yake cewa:

    Ban zo gidan Ɗanbita niy yi roƙo ba,

    Ko ya raba lafiya ba ruwana.

    A wannan ɗiyan waƙar ya fito ƙarara ya tabbatar wa al’umma cewa shi bai taɓa yi wa talaka waƙa ba. Ya jaddada cewa ba zai yi haka ba ko da mutumin yana samar da kowane irin jin daɗi da ingancin jiki da kawar da ciwo daga jikin ɗan’adam. Shi bai damu da duk wannan ba, ballantana ya yi masa kiɗa da waƙa.

    Kalmar ɗanbita a nan tana nufin leburan da ke aikin gyaran hanyar mota. A daidai wancan lokacin, sarakuna ne ke bayar da waɗanda za su yi aikin hanya. Sukan zaɓo waɗanda suka dace da aikin hanyar daga cikin talakawansu. A daidai wancan lokacin akan ji tsofaffi na maganar aikin diga da ke nuni da aikin hanya. A sakamakon irin wannan aikin talakawa da dama sun tara abin duniya.

    Malamin waƙa ɗin ya bayyana dalilan da suka sa ba ya yi wa talaka waƙa da kiɗa kamar yadda Gusau (1996 p. 121) ya ruwaito su cewar:

    1. Ba wata hanya da zai bi ya ɓata wa talaka rai. A lokacin da talaka ya wulaƙanta makaɗi, to sai dai makaɗin ya yi na mai bara (haƙuri).
    2. Yayin da Sarki ko jinin sarauta ya yi wa makaɗi abin da ya ɓata masa rai, sai ya rama a cikin waƙa ta hanyar yi masa zambo ko habaici. Ba wani sarki ko jinin sarautar da yake son makaɗi ya yi masa su.

    Za a iya samun wasu rukunin al’umma su ce, idan haka ne wane dalili ne ya sa Makaɗa Sa’idu Faru ya yi wa Alhaji Shehu Kangiwa waƙa? Amsa a nan ita ce, an yi waƙar ne a shekarar 1976 bayan an naɗa shi Turakin Kangiwa. Sarauta ce da Masarautar Argungu ta ba shi, a ƙarƙashin Shugabancin Maimartaba Sarkin Kabin Argungu, Alhaji Muhammadu Mera.

    Ya zama ɗaya daga cikin jigajigan masarautar. Don haka, an yi masa waƙar ne a matsayinsa na ɗaya daga cikin masu riƙe da sarautun gargajiya a Msarautar Argungu. Idan aka yi la’akari da ma’anar makaɗan sarauta da lokacin da aka aiwatar da waƙar, za a iya tabbatar da cewa Makaɗa Sa’idu Faru bai taɓa yi wa talaka waƙa ba. Shi makaɗin sarauta ne tsantsa.

    4.3 Ƙananan Turakun Waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru

    4.3.1 Yabo

    Makaɗa Sa’idu Faru a cikin waƙoƙinsa yakan yabi ubangidansa ta haujin ambaton asalinsa. Yakan kuma danganta shi da asalinsa ta hanyar bayyana cewa ya gaji gidansu. Ta haka ne ya yabi Sarkin Kudu Macciɗo da irin wannan sigar a inda yake cewa:

    Allah ya ba ka albarkar nan ta Alu Babba,

    Ka gama da kyau cikin sa’a mun yi roƙon Allah,

    Allah shi ba ka albarkar nan ta Shehu, Amin.

    Ka gama da kyau cikin sa’a mun yi roƙo Allah.

    Allah shi ba ka albarkar nan ta Bello, Amin.

    Ka gama da kyau cikin sa’a mun yi roƙon Allah.

    Allah ya ba ka albarkar nan ta Bubakar na farko.

    Ka gama da kyau cikin sa’a mun roƙon Allah.

    Allah shi ba ka albarkar Bubakar na biyu,

    Ka gama lafiya da imani mun yi roƙon Allah.

    Allah ya ba ka albarkar nan ta Aliyu Babba,

    Ka gama da kyau da imani mun yi roƙon Allah.

    Allah ya ba ka albarkar nan ta Alu ƙarami,

    Ka gama da kyau cikin sa’a mun yi roƙon Allah.

    Allah shi ba ka albarkar Abdullahi,

    Ka gama da lafiya da imani mun yi roƙon Allah.

    Allah shi ba ka albarkar nan ta Hassan Dattijo.

    Ka kammale, ka ɗibo jama’arka.

    Duk ka shirya mu gaban Ma’aikin Allah,

    Mu yi farin ciki,

    Mu ji daɗin da yaf fi daɗi daɗi na Annabi.

    Mu ji ƙamshin da yaf fi ƙamshi, ƙamshi na Bubakar,

    Allah shi sa ka samun martabar kakanka.

    Yayin da aka dubi waɗannan ɗiyan waƙar, za a ga cewa, Sa’idu Faru na yi wa ubangidansa Sarkin Kudu Macciɗo fatan Allah ya ba shi albarkar waɗannan kakanni nasa ya kasance tamkarsu tare da samun martaba irin tasu.

    Ba nan kawai ya tsaya ba. Har ma ya yabi Sarkin Kudu Macciɗo ta haujin iya gudanar da mulki, a inda yake cewa:

    Shugaban duniya Alhaji Bello Sarkin Kudu,

    Jan damishi Shehu Sarkin Gabas,

    Baban su Alƙali.

    Gadangadan Shehu Sarkin duniya,

    Ba mai riƙo na ba.

    Ai! Ina ba magana ba ce yanzu gidan Bani,

    Ba mai kamar Macciɗon Hausa.

    Girmanka ya kai muƙaminka ya kai,

    Riƙon duniya wada Abubakar yak kai,

    (Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Kudu Macciɗo).

    A nan mawaƙin ya bayyana cewa, Macciɗo zai iya gudanar da mulkin wannan duniya sakamakon ƙwarewarsa a fagen mulki.

    Ta fuskar addini ma, ya yabi ubangidansa a inda yake cewa:

    Gindin Waƙa: Bajinin gidan Bello Mamman na Yari,

    Sarkin Kudu Macciɗo ci maraya.

    Jagora: Tsari gaskiya Bello kai Shefu yac ce,

    ‘Yan Amshi: Bari masu son dus su maishe ka yaro,

    Duk kyauta da ilmi da neman dalili,

    Da gode ma Allah da istingafari,

    Da su Bello ɓello ɗan Shehu yat tcarma kowa,

    Ka kai kamab Bello,

    Ka gadi Moyi,

    Saura ka kai inda mai Hausa yak kai.

    Yayin da aka dubi ɗiyan da suka gabata, za a ga yadda wannan turken ya ƙara tabbatar mana da kasancewar mawaƙin a gurbin makaɗin sarauta. Makaɗan fada ne suka yi fice wurin yabon uwayen gidansu ta fuskar addini. Hakan na faruwa ne kasancewar sarakunan ƙasar Hausa su ne shugabannin addinin Musulunci tun kafin jahadin Shehu. Jagorancin nasu ya ƙara bunƙasa ne bayan tabbatuwar jahadi. Da irin wannan yabon ne sarakuna suke alfahari da makaɗansu.

    A nan ya bayyana wasu siffofin da suka keɓanta ga sarakunan ƙasar Hausa, wato, kasancewarsu masu alheri ga al’ummarsu, da zamansu malamai masana dangogin ilmomin zaman rayuwar duniya, domin su ne tushen samun kyakkyawar makoma gobe kiyama. Ya kuma ƙara kawo abu da ya kasance tamkar ruwa da gishiri a fagen sarrafa abinci da sauran lamurran rayuwar duniya.

    A nan ya yi masa hannunka mai sanda ne da ya lizimci nuna godiya a kan ni’imomin da Allah ya yi masa da dagewa ga yin tuba game da kuskuren da yake aikatawa, domin ta haka magabatansa suka tsere tsara. Idan ya nace a kan haka, zai kai ga samun matsayin da Sarkin Musulmi Abubakar Sadik yake a kansa.

    4.3.2 Zuga

    A wannan haujin kuwa, Sa’idu Faru yakan harzuƙa ko tunzura sarkin da yake yi wa waƙa, ta hanyar kambama darajarsa. Dubi yadda yake cewa a waƙarsa da ya yi wa Sarkin Kudu Macciɗo mai take:

    Gindin waƙa: Kana shire baban ‘yan ruwa.

    Jagora: Wani taro da an ka zo Ikko na bariyac can,

    Da Turawa da kuma ministoci had da kansiloli,

    Sarkin Musulmi da Amdu Bello sun zo wurin dus sun ziyar tai,

    Tafawa Ɓalewa ya sauka ga Lamiɗo Barno,

    Nan kudu Shehu Talba,

    Sarkin Bidda ya sauka ga Sarkin Ilori,

    Kulluhinsu sarakunan majalisa sun taru Ikko,

    Muhammadu Bello jikan Hassan kai sun ka zaɓa,

    Don ka hi su kyawon shirin kawo dalillai.

    Idan aka dubi kwayar turken wannan ɗan waƙar, za a ga ya fito ne ƙunshe da zuga Sarkin Kudu Macciɗo tare da fifita shi a kan waɗanda suka halarci taron. A ɗaya ɓangaren kuwa, ya taskace tarihin taron da aka aiwatar a Ikko tare da fito da maigidan nasa fili domin waɗanda ba su san shi ba su san shi. Irin wannan zugar ke ƙara tabbatar wa masu nazari gurbin da mawaƙin ya kasance.

    4.3.3 Habaici

    A cikin waƙoƙinsa akwai wuraren da yakan yi wa abokan adawar ubangidansa habaici ba tare da faɗa masa wata muguwar magana ba. Wannan kan iya kasancewa a cikin sigar jifa a kasuwa ko kuma ya san da wanda yake. Hasali ma makaɗan fada sun fi shahara ta fuskar amfani da habaici domin ƙasƙantar da abokin hamayyar sarkinsu ko muzanta shi a bainar jama’a a fakaice. Misali Sa’idu Faru yana cewa:

    Zaki mai zama ga hilin Allah ga shi ga hili,

    To wak ka san ya far mashi,

    Kafin maza su shirya Mamman na Ali ya shirya.

    Sun dai yi ɓaɓɓakar dutsi,

    Sun yi gyangyaɗar dutsi,

    ‘Yan hannuwansu sun gaza.

    Na Audu ko da ƙarfin Allah kana shiga gidan.

    Na ce mai kama da ƙot,

    Haka nij ji gun Badakkare.

    Dogon sarki yana da ban sha’awa,

    Ko da anka zo taro ya fi kyau da riguna,

    Duk wanda ag gajere a aje shi gun rabon dawo,

    Shi kai ma wanga dunƙule.

    Aw wurin da mata ciki,

    Har tuman gada yakai.

    (Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Tudun Falale).

    Da duban waɗannan ɗiyan waƙar za a fahimci Sa’idu Faru ya yi wa wasu ‘ya’yan sarki habaici ne a kaikaice, domin ya fahimci suna son su yi jayayya da ubangidansa.

    4.3.4 Zambo

    A nan ma akan samu inda yakan yi wa abokan hamayyar ubangidansa wata mugunyar magana. Misali a cikin waƙar da ya yi wa Sarkin Kudu Macciɗo yana cewa:

    Gindin Waƙa: Gogarman gidan Moyi ci fansa niƙatau,

    Mai babban rabo ginshiƙin Sarkin Shariffai.

    Jagora: Na ishe dale tai ƙawa ga jama’at ta ba ƙawa.

    ‘Yan Amshi: Ya murɗe su duy ya zuba dogon akwati,

    Rana ta kewayo ya naɗe ya kai Ilori,

    Dac can yas sawo man kishe,

    Ya sai tabarau.

    Yayin da aka nazarci wannan ɗiyar za a ga cewa, ya yi wa wani ɗan sarki zambo ne ta hanyar siffanta shi da wata tsuntsuwa da ake kira dale. Ita dale akan gan ta ne lokacin kaka. Ta kasance nau’i biyu. Akwai ja mai baƙi-baƙi ga kai, akwai kuma mai launin ɗorawa da baƙi-baƙi ga kai.

    Ita dalen ba a ganin ta sai lokacin da amfanin gona ya kai. Saboda halayyarta ne ya kamanta ɗan sarkin da ita, domin bai amfana wa kowa komai. Hasali ma idan wani abun alheri ya zo da ya kamata ya ba al’ummarsa, sai ya yi sama-da-faɗi da shi.

    4.3.5 Roƙo

    Akan sami wasu ɗiyan waƙoƙinsa da Sa’idu Faru yakan yi bara ko ya roƙi ubangidansa wani abu kai tsaye cikin hikima. Wannan wata azaliyya ce da ta keɓanta ga makaɗan sarauta, wato su bayyana abin da suke so daga ubangidansu kai tsaye ba tare da wani sakaye-sakaye ba. Shi ma Malamin Waƙa ya aiwatar da shigen wannan a inda yake cewa:

    Manyan ma’aikatan gwamnati,

    Manyan ma’aikatan N.A.,

    Almajirinku na aike,

    Don bisa gare ku Allah ya shiya mana asiri,

    Na roƙe ku in da hali,

    Ku zam shirya muna kujera mui Haji.

    Na yi mafarki nai sallah Makka nai ɗawafi,

    Kuma na rungumo hirami

    Da makaru a fuskoki,

    An ce mani Alhaji baitul fasali kake,

    Wanga mafarki ya Allah ya nufa a shirya shi,

    Ya zam haka.

    (Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Kudu Macciɗo).

    A waɗannan ɗiyan waƙar, za a ga mawaƙin ya fito ƙarara ya nuna buƙatarsa tare da ayyana dalilinsa wanda ya kasance mafarkin da ya yi da yake son a taimaka masa ya zama gaskiya. Za a iya cewa, ma’aikatan gwamnati da ya roƙa ai suna cikin rukunin talakawa. Lamarin a wancan lokacin ba haka yake ba. A daidai lokacin ‘ya’yan ahalul falala ake damƙa wa aikin hukumar En-e da na gwamnati.

    4.3.6 Koɗa Kai

    Sa’idu Faru fasihin makaɗan fada ne, musamman idan aka yi la’akari da wuraren da yakan wasa kansa ta hanyar nuna ƙwarewarsa wajen tsara waƙa fiye da sauran makaɗan fada. Kuma yakan yi hakan ne a ciki ɗiyan waƙoƙin da ya ƙulla wa maigidansa Sarkin Kudu Macciɗo. Kasancewar sa makaɗin fada, ya shahara wajen amfani da wasu halaye da siffofi na ɗan’adam, ya ƙaga su ga wani abu wanda ba mutun ba, wato abin da ake kira mutuntarwa. A waƙar da ya yi wa Sarkin Kudu macciɗo cewa ya yi:

    Nan na bi Gusau sai niw wuce,

    Kuma nab bi Kwatarkwashi niw wuce,

    Kuma nib bi ta Tcahe ina gudu,

    Can na kusa kai wa Zariya,

    Sannan Daudu ni kau sai nit tsaya.

    Sai Sarkin Zazzau nig ga nay,

    Ya ce man Muhamman Sarkin Kudu.

    Sai nis saki hanya nig gabas.

    Can na taɓa ‘yar tafiya kaɗan,

    Sai ni ishe suda na kiwo,

    Tana barka Sarkin Kudu,

    Allah rai ya daɗe Sarkin Kudu,

    Allah sabbinane na Ahmadu,

    Allah shi ƙara mai nasara.

    Na ce suda waƙa akai,

    Ta ce lalle waƙa ni kai,

    Waƙar Mamman Sarkin Kudu,

    Waƙar nan da Ɗan’umma ya yi mashi.

    Baicin uwar tsuntsaye nike,

    In da kamar mulkina nikai,

    Da nai mai wasiƙa ya yi min kiɗi,

    San nan ni kau sai niw wuce,

    Can na taɓa ‘yar tahiya kaɗan,

    Sai ni iske burtu na kiwo,

    Yana barka Sarkin Kudu,

    Rai ya daɗe Sarkin kudu,

    Allah sabbinane na Amadu,

    Allah shi ƙara mai nasara,

    Na ce burtu waƙa akai,

    Ya ce lalle waƙa nakai,

    Waƙar Mamman Sarkin Kudu,

    Waƙar nan da Ɗan’umma ya yi mashi.

    In na yi ta za ni wurin kiwo,

    In na so abinci sai na rufe.

    A cikin waɗannan ɗiyan waƙar, za a fahimci cewa mawaƙin ya yi amfani da adon harshe ne domin jaddada cewa ba ya yi wa kowa kiɗa da waƙa sai sarakuna da waɗanda ke da alaƙa da fada. Ga shi har da tsuntsaye sun san da haka. A ɗaya ɓangaren kuwa yana ɗaukaka waƙar da ya yi wa Sarkin Kudu, wadda sakamakon yadda ta tsaru ta yi armashi, har tsuntsaye na maganar waƙar.

    Waƙar da ya yi wa Sarkin Sudan Na Wurno Alhaji Shehu Malami, ita ma wata hujja ce mai ƙarfi da ke tabbatar da kasancewarsa makaɗin sarauta ne na gani-da-faɗa wanda sauyin zamani bai juya shi ba. A wasu ɗiyan waƙar, yana cewa:

    Gindin Waƙa: Muzakkarin sarki ɗan Audu,

    Abin biya Shehu na Ali.

    Jagora: Ɗan talakka komai yac cika huska,

    Sa’idu ni ba ni kiɗa mai, .

    Jagora: Ɗan talakka komai ya aje ƙarhe,

    Sa’idu ni ba ni kiɗa mai.

    Da duban waɗannan ɗiyan waƙar za a ga ya fito fili yana jaddada cewa shi ba makaɗin talakawa ba ne, kuma komai bajintarsu da ƙwazo da kuma uwa-uba mallakar tamani (jikkunan kuɗaɗe) ba zai yi musu kiɗa da waƙa ba.

    4.4 Sarrafa Harshe a Cikin Waƙoƙin Saidu Faru

    4.4.1 Ƙarangiya ko Gagara-gwari

    Makaɗan fada, musamman waɗanda suka fito daga yankin da ke cikin farfajiyar tsohuwar Daular Zamfara, wato yakin da ke cikin Masarautar Bakura da Zurmi da abin da ya gangara Sabon Birnin Gobir har zuwa Dacaɗi da sauransu, sun fi takwarorinsu da ba ‘yan asalin yankin ba ne wajen mallakar harshen Hausa da iya sarrafa shi.

    Sa’idu Faru ya yi wa takwarorinsa da suka yi zamani ɗaya da shi fintinƙau ta fannin sarrafa sautukan Hausa masu bugun juna ta hanyar maimaita su a cikin ɗiyan waƙa domin nuna ƙwarewarsa a harshen da yake waƙa da shi (Hausa). Ana kyautata zaton cewa, sukan yi amfani da wannan hikimar ne domin kawar da wani lamarin da ke ci wa sarki tuwo a ƙwarya ta yadda zai koma ga hayyacinsa har ya yi ƙoƙarin fahimtar yadda aka yi luguden kalmomin da fahimtar ƙunshiyarsu. A duba misalin inda Sa’idu Faru ke cewa:

    Yaro in taƙamar salon magana kaka yi,

    Ce tsare tsara,

    Ta hi tsantsamin tsantsara,

    Ko tsattsame tsari,

    Tsaf ga tsamiya.

    Tunkuɗa tunku cikin tukar rukuɓu,

    Tukuɗin Tumba yai tuɓus,

    Tumba taho yau da ke da taɓo,

    Da taɓo da’yat tuɓus..

    (Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Kiyawa na Ƙaura).

    Yayin da aka duba waɗannan ɗiyan waƙar za a tarar cewa Sa’idu Faru ya yi luguden sautukan Hausa kamar: tsa, tu, ɓa, ɓo, ɓu, ɗa, ɗi, da kuma ɗu, domin ya nuna ya naƙalci harshen Hausa da yake waƙa da shi. Mai nazari zai iya yin tambaya game da hujjar kawo wannan dalili?

    Hujja ita ce, tun lokacin da addinin Musulunci ya shigo ƙasar Hausa, a fada ya soma zama da kafa harsashe. Wannan ne ya sa Sarakunan ƙasar Hausa suka kasance malamai musamman bayan jahadin Shehu. Hasali ma sun kakkafa makaratun ilimi (zaure) inda ake koyar da fannonin addini da luggar Larabci da ake fassarawa cikin harshen Hausa. Wannan ne ya sa har gobe tsofaffin kalmomi da hikimomin Hausa sun yanke cibiya a makarantun zaure, ta la’akari da irin hikimomin da ke ƙunshe cikin Muƙamatul Hariyri.

    4.4.2 Dangantakar Kalmomi

    Ta wannan haujin za a ga cewa makaɗan sarauta sun sha bamban da na jama’a ta fuskar zaɓen kalmomin da suka dace da ke da dangantaka da juna tare da tsara su wuri ɗaya cikin waƙarsu. Makaɗa Sa’idu Faru shi ne kan gaba a wannan fagen. Allah ya ba shi basira da hikimar zaɓen kalmomi masu dangantaka da juna. Yakan kuma tsara su a wuri ɗaya cikin waƙarsa. Misali, yana cewa:

    Ihihiya da kunkuru shawara guda sukai.

    Bushiya da beguwa shawara guda sukai.

    Kurciya da hasbiya shawara guda sukai.

    Bubukuwa da jinjimi shawara guda sukai.

    (Sa’idu Faru: Waƙar Muhammadun Muhammadu).

    Ta la’akarida waɗannan ɗiyan waƙar za a ga cewa ya kawo jerin halittu da suke da dangantaka da juna ta siffofin yanayin halittarsu.

    5.1 Sakamakon Bincike

    Daga abin da ya gabata dangane da wannan nazari, ya fayyace mana tabbatuwar Makaɗa Sa’idu Faru a matsayin sahihantaccen makaɗin sarauta na gwadi da ya tsayu wajen kiɗan sarauta da sarakuna a manyan gidaje sarauta har ma da ƙananansu da ke farfajiyar ƙasar Hausa. Sauye-sauye zamani da ɓullowar siyasar dimokuraɗiyya da kwaɗayin neman tara abin duniya bai sa ya bar turbar iyaye da kakanni ba.

    Irin wannan dogiya tasa, da ra’ayin mazan jiya sun bambanta shi da takwarorinsa da suka yi zamani tare har ya zamanto bai taɓa yi wa wani mutun waƙa ba idan ba jinin sarauta ba ne. Hasali ma ko jinin sarauta sai wanda ke riƙe da wani muƙamin sarautar gargajiya. Ya bambanta da mawaƙa irin su Alhaji Musa Ɗanƙwairo da suka kasance cikin zango guda da shi, wanda ya koma yana karɓar gayyatar jama’a domin rera musu waƙoƙi.

    Haka kuma, an fahimci sarakuna na rungume da makaɗansu ne sakamakon yadda suke tsara musu waƙoƙi, wanda ke zama sanadin daɗa ɗaukakuwarsu a idon duniya. Wannan kan auku ne, ta hanyar yadda makaɗan ke ambaton su da kyawawan halaye da ɗabi’u, waɗanda kan fito da sunayensu fili fiye da kima. Da haka ne sukan sami ƙwarin guiwar gudanar da harkokinsu na mulki ba tare da kasala ko tsoro ba, sakamakon zuga da kirarin da mawaƙansu ke yi musu, tare da tunatar da su tarihin iyaye da kakanninsu, musamman dangane da kyawawan halayensu kamar kyauta, haƙuri, ƙwazo da juriya.

    5.2 Kammalawa

    Waƙoƙin fada sun kasance wata maƙerar sarrafa harshe da luguden kalmomin fasaha. Haka kuma, suna mazaunin wata makaranta da ke koyarwa ko cusa waɗansu halayen ƙwarai da kuma ƙarfafa guiwa ga waɗanda ake yi wa waƙoƙin, da ma sauran masu sauraro. A ɓangare guda kuwa, suna da matsayin rumbun adana al’ada da tarihi. Makaɗa Sa’idu Faru ya shahara a waɗannan lamura a matsayinsa na makaɗin fada na yankan shakku. Hasali ma, shi ne babban misali lamba ta ɗaya idan ana batun kiɗan sarauta.

    Manazarta

    Abba, M. da Zulyadaini, B. (2000). Nazari Kan Waƙar Baka Ta Hausa. Zaria: Gaskiya Corpora-Tion LTD.

    Abubakar, A.T. (2015). Ƙamusun Harshen Hausa. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company Limited.

    Ammani, M.C. (2019). Nazarin Awon Baka Da Aiwatarwa Da Harshen A waƙoƙin Nafi’u Yakubu

    Baba Katsina. Juzu’i Na Biyu. (Ratayen Matanonin Waƙoƙin Da Aka Yi Nazari A Kansu). Kundin Bincike Da Aka Gabatar Domin Cikasa wata Ƙa’ida Ta Neman Digiri Na Adabin Hausa, A Sashen Harsunan Nijeriya Jami’ar Bayero Kano.

    Bango, A. & King, A.B. (1986). “An Introduction to Life and Works of Abubakar Akwara (C. –1876-1962)”. Seminer Paper. Zaria: Ahmadu Bello University.

    Bello, G. (1976). “Yabo, Zuga da Zambo a WaƘoƙin Sarauta”. Harsunan Nijeriya, Vol. VI: 21-34.

    Bunza, A.M. (2009). Narambaɗa. Lagos: Ibrash Islamic Publication Centre LTD.

    Bunza, A.M. (2014). In Ba ka San Gari Ba Saurari Daka: Muryar Nazari Cikin Tafashen Gambo. Cairo: Elkods Printing House.

    Ɗangambo, A. (1984 ). Rabe-Raben Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kano: Trimph.

    Funtuwa, A.I. da Gusau, S. M. (edt) (2011). Waƙoƙin Baka Na Hausa. Kano: Century Research And Publishing Limited.

    Gital, G. M. (1984). “Adabin Baka”. Maƙalar da aka gabatar a Kwalejin Kimiyya da Fasaha, Bauchi.

    Gusau, S. M. (1988). “Waƙoƙin Makaɗan Fada: Sigoginsu Da Yanayinsu, Musamman A Ƙasar Sakkwato. Juzi’i Na Ɗaya Da Sharhi. Kundin Binciken Da Aka Gabatar Domin Samun Shaidar Digiri na Ɗaya.

    Gusau, S. M. (1993). Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Kaduna: Fisbas Media Services.

    Gusau, S. M. (1996). Makaɗa Da Mawaƙan Hausa Na 1. Kaduna: Ɗab’in Fisbas Media Services.

    Gusau, S. M. (2002). Salihu JankiɗI Sarkin Taushi. Kaduna: Baraka Publishes Limited.

    Gusau, S. M. (2008). Waƙoƙin Baka A Ƙasar Hausa: Yanaye-Yanayensu da Sigoginsu. Kano: Benchmark Publishers Limited.

    Gusau, S. M. (2009). Diwanin Waƙoƙin Baka: Zaɓaɓɓun Matanoni na WaƙoƘin Baka na Hausa.Kano: Century Research and Publishing Limited.

    Gusau, S. M (2011). Adabin Hausa A Sauƙaƙe. Kano: Century Research and Publishing Limited.

    Gusau, S. M. (2014). Diwanin Waƙoƙin Baka, Juzu’i Na Biyu. Kano: Century Research and

    Publishing Limited.

    Gusau, S. M. (2014). Waƙar Baka Bahaushiya (The Hausa Oral Song). Kano: Published for Bay-Ero University.

    Gusau, S. M. (2015). Audu Karen Gusau. Kano: Century Research and Publishing Limited.

    Gusau, S. M. (2016). Makaɗa Da Mawaƙan Hausa. Littafi Na Biyu. Kano: Century Research and Publishing Limited.

    Gusau, S. M. (2018). Diwanin Waƙoƙin Baka: Matanonin Wasu Waƙoƙin Alhaji (Dr.) Mamman Shata Katsina. Kano: Century Research and Publishing Limited.

    Gusau, S. M. (2019). Diwanin Waƙoƙin Baka, Juzu’i Na Huɗu: Wasu Waƙoƙin Alhaji Musa

    Ɗankwairo Maradun (1909-1991) Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun Jahar Zamfara. Kano: Century Research and Publishing Limited.

    Gusau, S. M. (2020). Diwanin Waƙoƙin Baka Juzu’i Na Biyar: Matanonin Wasu Zaɓaɓɓun Waƙoƙin Makaɗan Baka. Kano: K.d.G.

    Ibrahim, M.S. (1983). Kowa Ya Sha Kiɗa. Ibadan: Longman Nigeria.

    Sa’id, B (edt) (2006). Ƙamusun Hausa. Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

    Yahaya, A. B. (1997). Jigon Nazarin Waƙa. Kaduna: FISBAS MEDIA SERVICE.

    Yahaya, A. B. (2001). Salo Asirin Waƙa. Kaduna: FISBAS MEDIA SERVICE.

     

    [1] Kotso abin kiɗa ne na makaɗan sarauta. Ya so ya yi kama da kalangu, amma shi fuska ɗaya kawai ake rufewa, a kuma kaɗa shi da hannu. Sa’idu Faru yana daga cikin sahun makaɗan da suka fi gwanancewa wajen kiɗan kotso. Ƙwararru kuwa sun haɗa da Ibrahim Narambaɗa da  Musa Ɗankwairo.

    [2] [Keɓantacciyar tattaunawa I. Muhammad, 14 ga watan Yuli, 2024] (A lokacin yana matsayin Ɗanmadamin Birnin Magaji)

    Danna nan don karanta Maƙala Mai Taken: Zamani Abokin Tafiya: Tasirin Kafafen Sada Zumunta ga Tashin Tashinar Zamfara

    Edita@rumasau-kallamu

  • Maƙala Mai Taken: Hoton Waibuwar Hausawa a Cikin Waƙoƙin Mamman Shata

    Maƙala Mai Taken: Hoton Waibuwar Hausawa a Cikin Waƙoƙin Mamman Shata

    Hoton Waibuwar Hausawa a Cikin Waƙoƙin Mamman Shata

     Yakubu Aliyu GOBIR

    Department of Nigerian Languages

    Usmanu Danfodiyo University, Sokoto

     &

    Abu-Ubaida SANI

    Department of Languages and Cultures

    Federal University Gusau, Zamfara

    Article Citation: Gobir, Y. A. & Sani, A-U. (2018). Hoton waibuwar Hausawa a cikin waƙoƙin Mamman Shata. Studies in the Songs of Dr. Mamman Shata Katsina. Katsina: Umaru Musa ‘Yar’adua University, 189-203. ISBN: 978-978-5588-2-4.

     Tsakure:

    Masana da manazarta sun tafi kan cewa, daga cikin adabin al’umma (na baka ko rubutacce), mutum na iya fahimtar salon rayuwar al’ummar na gaba ɗaya. Wannan ya haɗa da tunaninsu da imaninsu da fahimtarsu da al’adunsu da tsarin zamantakewa da sauransu. Mawaƙa na taka muhimmiyar rawa wurin fito da tunanin al’umma.

    A bisa wannan zaren tunani ne wannan takardar ta ginu, inda take ƙoƙarin hango waibuwar Hausawa daga bakin Mamman Shata. Shata yakan danganta mutum da aljani ko kuma ya ba shi wata siffa ko ɗabi’a ta aljani domin nuna shahara da buwayar mutumin. Haka ma yakan danganta magani da aljani a wasu daga cikin waƙoƙinsa.

    Wannan takarda ta bibiyi irin waɗannan waƙoƙi da suka haɗa da ‘Malam Babba na Ƙofar Gabas,’ da ‘Hassan Sarkin Dogarai,’ da ‘Mamman Sakkwato Kyaftin,’ da kuma ‘Waƙar Sarkin Bori Sule.’ Daga ƙarshe takardar ta fahimci cewa, Bahaushe ya yarda da wanzuwar aljani har ma ya ɗauke shi a matsayin halitta mai matuƙar hatsabibanci. A taƙaice, Bahaushe ya tafi kan cewa, ƙololuwar buwaya kan samu ga ɗan’adam yayin da ya yi cuɗanya da aljani.

    Muhimman Kalmomi: Hausaswa, Waibuwa, Aljani, Mamman Shata

     1.0 Gabatarwa

    Waƙa ba sabuwar aba ba ce da ake da buƙatar dogon bayani game da ma’anarta. Masana da manazarta da dama sun bayyana ma’anar waƙa a rubuce-rubuce da suka gabatar a matakan ilimi daban-daban. Daga cikin masana da marubuta da suka yi tsokaci kan ma’anar waƙa sun haɗa da: Gusau (1993) da Ƙaura (1994) da Bunza (1988) da Yahya (1996) da Habibu (2001) da Zurmi (2006) da Abdullahi (2017) da makamantansu.

    Kasancewar waƙa zance tsararre da ake rerawa cikin salo da raujin murya ta musamman tare da zaɓen kalmomi da jera su cikin tsari mai jan hankali, hakan ya sa waƙa ta kasance mai matuƙar tasiri ga zukatan al’umma. Masana da marubuta irin su: Furniss (1996) da Gusau (2009, 2014); Sani (2016) da Sani da Tsaure (2016) sun tabbatar da cewa, waƙa ta kasance aba mai matuƙar tasiri ga zukatan al’umma tun zamani mai tsawo da ya wuce.

    A taƙaice za a iya cewa, waƙa ta fara tasiri tare da samar da sauyi ga rayuwar Hausawa tun lokacin da suka fara ta’ammuli da ita. A wani ra’ayi mai kama da wannan, A’azamiyyun, 1962 da CNRS a cikin Science Daily, 2014 da Sani, 2016; duk sun tafi kan cewa, tasirin waƙa ba zai taɓa gushewa ba daga zukatan al’umma. Wannan ne ma ya sa, waƙa ta kasance babbar hanyar isar da saƙonni ga al’umma, kuma saƙonnin na yin tasiri ga rayuwarsu.

    Ƙudurin wannan takarda shi ne tsakuro ɗiyan waƙa da Dr. Mamman Shata ya kawo hoton waibuwar Hausawa cikin waƙoƙinsa.

    2.0 Taƙaitaccen Tsokaci Game Da Dakta Mamman Shata

    Dakta Mamman Shata ba ɓoyayyen mawaƙi ba ne. Yana ɗaya daga cikin makaɗan da suka fi kowa suna da ɗaukaka a duniyar waƙa a ƙasar Hausa. Waƙoƙinsa sun shiga duk lungu-lungu da saƙo-saƙo na ƙasar Hausa, haka ma sunansa. Wannan ya samo asali ne a dalilin zunzurutun fasaha da ke cikin waƙoƙinsa tare kuma da farin jini da yake da shi, wanda hakan ya zamar da shi wani zakara tsakanin mawaƙan lokacinsa.

    Hakan ne ma ya sa, har a yau mawaƙa da dama (cikinsu har da na zamani) suke ƙoƙarin danganta kansu da Shata. A taƙaice ke nan, inkiyar Shata da za a yi wa mawaƙi a yau na nuna ficen mawaƙin a fagen waƙa. Duniyar mawaƙan Hausa sun yi ittafaƙin Shata a matsayin sarkin waƙa. Nura M. Inuwa (Mawaƙin zamani) ya ambaci Shata a matsayin sarkin waƙa, inda yake cewa:

    Mai sautina kunno,

    Wani zance zan tono,

    Yaro na mawaƙa ne ni ba Shata ne ba,

    Matsayi ban kai a kira ni da sarkin waƙa ba.

    Daga baitin da ke sama, lallai mawaƙin yana nuna matsayinsa bai kai a kwatanta shi da Shata ba. Dalili kuwa shi ne, shi (mawaƙin) yaro ne kawai a cikin mawaƙa, amma bai kai matsayin sarkin waƙa ba. A taƙaice ke nan, Shata sarkin waƙa ne.

    Saboda fice da Shata ya yi a duniyar waƙa, ƙoƙarin kawo tarihinsa zai zama maimaici ne kawai na aikin da masana da marubuta suka daɗe da baje guminsu a kai. Saboda haka, a wannan gaɓa takardar za ta waiwaiyi irin ayyukan da aka yi ne game da Shata, wanda kuma ke ɗauke da tarihin rayuwarsa.

    Abdulƙadir (1975) shi ne aiki na farko na ilimi da aka yi a kan Mamman Shata da waƙoƙinsa. Sai Sheme da wasu (2000) sun kawo cikakken tarihin Shata a cikin littafinsu mai suna: Shata Ikon Allah. Haka kuma, Kankara, (2013) ya yi matuƙar ƙoƙari wurin tattaro cikakken tarihin Shata da kuma aikace-aikacensa masu tarin yawa.

    Ya tattara wannan tarihi cikin littafinsa mai suna: Mahadi Mai Dogon Zamani: Shata da Kundin Waƙoƙinsa. Wannan littafi yana ɗauke da tarihin rayuwar shata tun daga kan iyaye da kakanninsa. Sannan littafin ya kalato irin abubuwan mamaki da al’ajabi da Shata ya riƙa nunawa a lokacin rayuwarsa. Bayan waɗannan, akwai kuma wasu ayyuka da aka gudanar a kan Shata, da suka haɗa da Ɗangambo (1973) da Gusau (1996) da kuma Gusau (edita) (2003).

    3.0 Waibuwar Hausawa A Waƙoƙin Shata

    Mamman Shata ya kawo ire-iren waibuwar Hausawa a wasu daga cikin waƙoƙinsa. Ko bayan Shata ma, akwai mawaƙa da dama da suka nuna hoton waibuwar Hausawa cikin waƙoƙinsu. Wasu daga cikin waɗannan mawaƙa su ne: Gambo, (a cikin waƙarsa ta Tsoho Tudu) da Ɗan’anace (a cikin waƙarsa taShago) da Bage Ɗansala (a cikin waƙar ‘Yarkala) da Garba Ɗanwasa (a cikin waƙar Gojirgo) da kuma Sani Ɗanbalɗo (a cikin waƙarsa ta Ciran Rogo) da ma wasu mawaƙan na daban. Mawaƙan Hausa na fito da waibuwa bisa wasu tubalai cikin wasu gurabu na ɗiyan waƙoƙinsu. Sukan yi hakan ta amfani da wasu tubalai kamar:

    Kambamar zulaƙe

    Jarumta

    Tsafi

    Magani

    3.1 Tubalin Kambamar Zulaƙe

    Kambamar zulaƙe ta ƙunshi kurarawa da rurutawa tare da zuzutawa da kuma ɗaukaka abu sama da yadda yake a haƙiƙa. Ahmad (2010) da Fitri (2010) na da ra’ayin cewa, kambamar zulaƙe na samuwa ne yayin da aka yi amfani da wasu kalmomin da za su ɗaukaka wani mutum ko wani abu sama sosai da yadda ya kasance a haƙiƙa.

    Manazarta irin su Omosowone da Nelson (2003) da kuma Amaechi (2010) na da irin wannan fahimta, inda suka ƙara da cewa; kambamar zulaƙe ta ƙunshi ɗaukaka wani abu zuwa wani matsayin da bai kai wurin ba. Sai dai mai kambamar zulaƙe yakan yi ne dumin barkwanci ko dai gyaran zance ko kuma jan hankali zuwa ga abin da yake magana a kai.

    Bunza (2015) yana ganin cewa, kambamar zulaƙe shi ne mafi ƙololuwar salo da mawaƙi zai iya amfani da shi, domin ƙawata waƙarsa tare da jan hankalin mai sauraro da kuma ɗebe wa masu sauraro tantama dangane da wani abu da dai makamantansu.[1] Shata yakan danganta faruwar wasu abubuwa da waibuwa yayin da yake kambamar zulaƙe, domin fito da girman wani abu ko wani mutum. A cikin waƙar Sarkin Bori Sule, Shata ya yi amfani da kambamar zulaƙe wurin da yake cewa:

    Jagora: Shi ke kwana bakwai,

    Ba ci ba sha Sule,

    Kullum bori yake.

    ‘Yan Amshi:    Sarkin bori Sule.

    Binciken kimiyya ya tabbatar da ɗan’adam ba zai iya sama da kwana huɗu a raye ba tare da ruwa ba, balle har a ce yana aikata wani aiki, kuma mai wahala da buƙatar jijjiga jiki.

    A nan kuwa, sai ga shi Shata yana cewa, ai shi Sule na shafe har tsawon kwanaki bakwai ba tare da ci ko sha ba, sai dai zunzurutun bori. Haƙiƙa a nan kambamar zulaƙe ce Shata ya yi game da borin Sule.

    A cikin waƙar Hassan Sarkin Dogarai, Shata ya kawo kambamar zulaƙe dangane da girman shi Hassan.[2] Yayin da yake siffanta girman Hassan a cikin waƙar, sai yake cewa:

    Jagora: Mutuum huɗu da rabin mutum,

    ‘Yan Amshi: Hassan Sarkin Dogarai.

    Jagora: Mutuum huɗu da rabin mutum,

    ‘Yan Amshi: Hassan Sarkin Dogarai.

    Haƙiƙa wannan kambawa ce Shata ya yi dangane da girman Hassan Sarkin dogarai. Domin kuwa, ko kusa Hassan bai kai wannan girma da ake kwatanta shi da shi ba.

    Ko bayan Shata, akwai mawaƙan Hausa da ke amfani da hoton waibuwar Bahaushe wajen gina kambamar zulaƙe. Misali Gambu ya yi amfani da kambamar zulaƙe wajen bayyana yadda Tsoho Tudu ke da tsananin waibuwa. Ya yi hakan ne a cikin waƙarsa mai suna Tsoho Tudu. A cikin waƙar yake nuna cewa, saboda tsantsar ƙuƙuwa ta Tsoho Tudu, ko da furarsa ce ta zube ƙasa, to hatta ƙwaro ba ya iya taɓinta.[3]

    Jagora: “Don duk mai ku]i a Arewa

    Ko wa ya haihwai ɗan gaton’uwa

    Babu kamar guda mai ƙuƙuwat Tudu

    Sai dai a gwada mai tara jalli

    Duk da hura tai tat tuɗe ƙasa

    Tabbata ƙwaro bai taɓin ta

    Saboda mugunyar ƙuƙuwa tai”.

    3.2 Tubalin Jarumta

    Jarumta ta ƙunshi jajircewa da dagewa cikin zage damtse da taƙarƙarewa a kan duk wani abu da aka sanya a gaba. Wannan ya haɗa da fitar da tsoro da fargabar abin da aka tunkara tare da dakakkiyar zuciya da ƙarfin guiwar hangen nasara. Wannan ne ma ya sa, masana irin su: Becker da Eagly (2004) da kuma Blau da Zimbardo (2011) ke da ra’ayin cewa, jarumta ta ƙunshi aikata ayyuka da ke da matuƙar hatsari ga rayuwa.

    Wato dai, sau da dama jarumi kan cusa kansa ga halaka. Shi ya sa Bahaushe ke cewa: “Uwar rago ake yi wa barka, ta jarumi sai jaje.” Ke nan dai, rago ne ke tsira saboda karaya kan sa shi guje wa bacin rana. Shi ko jarumi, a koyaushe dagewa yake yi, “sai ya ga abin da ya ture wa Buzu naɗi.”

    Akan samu jarumai cikin al’umma, inda jarumtar ta danganta ga sana’o’i ko zamantakewa da dai sauransu. Misali, akan samu jarumai cikin manoma ko mafarauta ko sarkawa ko maharba da sauran sana’o’i da ke buƙatar jajircewa da nuna bajinta. Sai dai kuma, nuna jarumta bai tsaya ne ga kyawawan ayyuka ba kawai.

    Akan nuna jarumta har ga ɗabi’u da ayyuka da suka kasance ababan ƙi cikin al’umma. Sun haɗa da sata da fashi da sane da makamantansu. Douglas da Mathew (2012) na da wannan ra’ayi, inda suka nuna cewa, duk wata jajircewa da nuna bajinta akan iya kiran ta jarumta, ba wai sai ga abin ƙwarai ba.

    Waƙar Sarkin Bori Sule kyakkyawan misali ne na yadda Shata ke nuna dangantakar jarumta da waibuwa. Misali a cikin waƙar, Shata na nuna cewa, idan Sule ya faɗi magana bayan ya yi duba, to kuwa sai ta tabbata. Ke nan dai ya ƙware a kan sana’ar duba, wanda hakan ne ya zamar da shi jarumi da ya yi fice. Waibuwa ce ta zamar da Sarkin Bori Sule jarumi ga tunanin Shata. Ya ce:

    Jagora: Bugi ƙasa ka duba musu,

    Shidda shidda ka ɗauke uku,

    Ka ga idan ka haɗa su sun zama tara,

    Kowa aka gani cikin tara ɗin nan,

    Yai sha’ani nai shi ta rufa …

    Ka je Baba ya duba maka.

    Idan ya zana ƙasa ya duba maka,

    Ya ɗaga kai ya shaida maka,

    Ka ga kamar da shi ne a kai.

    ‘Yan Amshi: Malam Babba na Ƙofag Gabas.

    A wani baitin na daban, Shata ya nuna ficen Sarkin Bori Sule da cewa, nan take marar lafiya ke samun sauƙi idan dai har aka kai shi ga Sule. Shata yake cewa:

    Jagora: Yau wannan zamani,

    Wannan lokaci,

    Ko wani ke zazzaɓi,

    Ka ga ana gai da shi,

    Yana amsawa jika-jika,

    Ku kai mai borin Sule,

    Sarkin Bori Sule.

    Yan Amshi: Sarkin bori Sule.

    Jagora: Yanzu sai ka ga sun warware,

    Suna yawon duniya.

    ‘Yan Amshi: Sarkin bori Sule.

    Baya ga haka Shata ya nuna cewa, Sule ya yi matuƙar sanuwa a garuruwa daban-daban na ƙasar Hausa. Duk kuwa a dalilin bori ne. Ya bayyana hakan inda yake cewa:

    Jagora: Wurin rangadi Sule,

    Ya zo birnin Kano,

    Na Kazaure sun sani,

    Katsinawa sun sani,

    Ya je Kukar Bauɗe Shiɗe,

    Ya nemo bori duka.

    ‘Yan Amshi:    Sarkin bori Sule.

    A wani baiti makamancin wannan, Shata ya kawo wasu muhimman mutane masu manyan matsayi da muƙamai a cikin Hausawa tare da cewa su ma sun san Sule a dalilin bori. Daga cikinsu har da sarki da alƙali da magajin gari da kantoma da DPO da razdan har ma da gwamna. Shatan yake cewa:

    Jagora: Sarki ya sani,

    Alƙali ya sani,

    Magajin gari ya sani,

    Kantoma ya sani,

    D.P.O. ya sani,

    Kuma Razdan ya sani,

    Kuma gwamna sun sani,

    Duka sun san borin Sule.

    ‘Yan Amshi:  Sarkin bori Sule.

    aƙiƙa baitukan da ke sama, suna nuna mana yadda Shata ke danganta waibuwa da shahara. Ya nuna yadda Sule ya shahara a sanadiyyar bori. Sai dai yana da kyau a tuna ba Shata ba ne kaɗai ke da irin wannan ra’ayi a cikin mawaƙan Hausa. Misali, Ɗan’anace ya danganta shahara da buwayar Shago[4] da hulɗa da aljani. Ya kawo hakan ne cikin waƙarsa mai suna: Shago Mai Hagun Mai Dama, inda yake faɗin:

    Jagora: Ɗan Audu duk da idanunka ba awa na mutum ba,

    Ɗan Audu ya hau bori, borin da ba shi da girka,

    … ba a gyara maka iskoki ba.

    ‘Yan Amshi:    Arne ba a gyara maka iskoki ba.

    A nan yana nuna cewa, hatta siffar Shago na jirkicewa yayin fafatawa. Wato dai yakan koma tamkar ba mutum ba. A nan ya ƙara da kwatanta wannan yanayi da hawan bori, wanda kuma ba a yi wa girka ba. Ma’ana dai, tamkar mutum da ke ta’ammuli da aljanu alhali ba a yi masa girka domin daidaita su a kansa ba.

     3.3 Tubalin Tsafi

    Tsafi ya shafi hulɗa da aljani tare da biya masa wasu buƙatunsa domin shi kuma aljanin ya riƙa taimaka wa mai hulɗa da shi wajen yin abubuwan ban mamaki, da kuma biya masa wasu buƙatun da zai iya buƙata yau da gobe. Za a iya kallon tsafi a matsayin mafi ƙoluluwar mataki da mutum zai taka a matsayin hanyar waibuwa. Matsafi kan yi abubuwan ban mamaki waɗanda ga al’ada, ɗan’adam ba shi da damar gudanar da su ba tare da taimakon iskoki ba. Wannan ya haɗa da:

    1. Rikiɗa zuwa wasu halittu
    2. Ci ko shan wani abu da ya saɓa hankalin al’ada kamar allurai ko ƙaya ko wani ƙarfe ko fasasshiyar kwalba da makamantansu.
    3. Ɓacewa nan take
    4. Sanya wani abu marar motsi motsawa, kamar zabira ko garma/galma da makamantansu.
    5. Bayyanar da wani abu nan take wanda a farko matsafi ba ya tare da shi

    Sai dai yana da kyau a lura da cewa, akwai abubuwan bammamaki makamantan waɗannan da ɗaiɗaikun jama’a ke yi, wanda ya shafi siddabaru ne ba tsafi ba.[5] Matsafa kuwa na amfani da ƙarfin tsafinsu domin kare kai, ko nuna bajinta ko ma cutarwa a wasu lokuta.

    A cikin waƙar Shata ta Hassan Sarkin Dogorai, an ga yadda Shata ya nuna Hassan a matsayin mai waibuwa, inda yake cewa:

    Jagora: Nan na ga al’ajabi, Ranar tafiya Ɗorayi.

    ‘Yan Amshi: Hassan Sarkin Dogarai.

    Jagora: Ran hawa zuwa Ɗorayi.

    Yan Amshi: Hassan Sarkin Dogarai.

     

    Jagora: Ranar hawan Ɗorayi,

    In sarki yah hawo,

    Hassan kuwa ya yo hawa,

    Ko hadari ya taho,

    Ana ta ruwa yaf-da-yaf,

    Hassan ya ja yai gaba,

    Yai gaba sai yats tsaya,

    Na ɗauko doki guje,

    Na zo ciki na rakuɓe,

    Zatona rumfa a kai,

    Wanda sarki zai shiga,

    A ƙasa sai na ga kofatai,

    Kuma na ga idon mutum,

    Sai na ruga guje.

    Nai zaton ifiritu ne,

    Na kwalba

    ‘Yan Amshi: Hassan Sarkin Dogarai.

    Kamar yadda yake cikin ɗiyoyin waƙar da ke sama, tsananin waibuwar Hassan, ruwan sama da ake yi ba ya zuba a daidai wurin da yake tsaye tare da sarki. Wannan ne ma ya sa har Shata yake tunanin ko rumfa ce aka yi a wurin, domin a tare wa sarki ruwan saman, gudun kada ya jiƙe. Sai dai kuma yayin da Shata ya je wurin, sai ya ga kofatai, sannan da idanun mutum a ƙasa. A nan ma za a ga cewa, Shata ya danganta waibuwar Hassan da cuɗanya da aljani. Da ma dai a tunanin Bahaushe, kofoto na ɗaya daga cikin siffofin aljannu.

    A waƙar Malam Babba na Ƙofar Gabas, Shata ya sake bayyana waibuwar Malam Babba, inda yake nuna cewa, yayin da shi Malam Babba ya yi duba, sannan ya faɗi sakamakon; to kuwa abin zai kasance tamkar yana wurin aka shirya. Ke nan dai Shata na nufin cewa, Malam Babba yana iya faɗin abin da zai faru. Ya ce:

    Jagora: Malam na ga kana yin yaushi,

    Je ka Babba ya duba maka.

    Ya zana ƙasa ya duba maka…

    Ya ɗaga kai ya shaida maka,

    Ka ga kamar da shi ne akai.

    ‘Yan Amshi:    Malam Babba na Ƙofar Gabas.

    A wata waƙa mai suna: Mamman Sakkwato Kyaftin, Shata ya nuna yadda Kyaftin Mamman ke da waibuwa, musamman a daji. Waibuwar tasa har ta kai matsayin da, ko da mutum ya san shi, to idan ya kalle shi a daji, zai ga ya zama wani abin tsoro, wanda ba siffar mutane ba. Irin wannan waibuwa ta filin daga kuwa, ba sabon al’amari ba ne ga tunanin Bahaushe. Ma’ana, yana ɗaya daga cikin abin da Bahaushe ya yi amanna da su. Shata ya ce:

    Jagora: Ko ka san shi mutum kauce mashi,

    Kiyayi Mamman Sakkwato daji …

    Ya ce min, Shata mai waƙa,

    Sarkin waƙa,

    Lallai a daji Sakkwato Kyaftin,

    Wannan abin tsoro ya koma.

    ‘Yan Amshi: Sannu Mamman Sakwkato Kyaftin.

    4.4 Tubalin Magani

    Magani dai na nufin duk wani abin da ake amfani da shi domin samun waraka daga wata cuta. Bunza, (1995) ya nuna cewa, magani ga Bahaushen tunani na iya kasancewa sassaƙe ne ko saiwa ko ruwa ko allura ko ma wasu hanyoyin riga-kafi na daban. Tarihin Hausawa na ƙunshe da wasu hanyoyin waraka da Hausawan suka yi amfani da su, waɗanda suka haɗa da bori da ma sauran hanyoyin hulɗa da aljannu domin samun magani.

    Sai dai kuma yana da kyau a tuna, dalilan da kan sa Bahaushe ya nemi magani ba ciwon jiki ba ne kawai, har ma da na zuciya. Bahaushe kan nemi magani domin neman waraka ko kariya ko ɗaukaka da buwaya ko ma domin cutar da abokin gaba (Bunza, 1995; Sarkin Sudan, 2008; Gobir, 2012). Ke nan dai kalmar ‘magani’ na da faffaɗar ma’ana ga Bahaushen tunani.

    A cikin waƙar Mamman Sakkwato Kyaftin, Shata ya bayyana Mamman a matsayin mai waibuwar magani a filin daga. Waibuwarsa ta sanya, ko da ana musayar wuta, harsashe na zirya, to shi ba ya kwantawa ko ya duƙa domin gudun kada harsashi ya same shi. A maimakon haka, zai ci gaba da kutsawa ne kawai riƙe da sandarsa. Ke nan dai Shata na nuna Mamman a matsayin wanda yake da maganin harsashi. Ya ce:

    Jagora: In dai an ce bakin daga,

    Muddin an je bakin fama,

    Ga harsashi na warici,

    Ga harsashi na yawo nai,

    Malam Mamman Sakkwato Kyaftin,

    Bai kwantawa,

    Bai duƙawa,

    Ya riƙe sanda,

    Kui gaba yaran Sakkwato Mamman.

    ‘Yan Amshi:    Sannu Mamman Sakwkato Kyaftin.

    Akwai mawaƙa da dama da suka kawo irin wannan yanayi inda mutum ke amfani da waibuwar magani. Misali Gambu mai waƙar ɓarayi ya kawo irin wannan waibuwa cikin waƙar Jibril Mugun Tsoho inda yake cewa:

    Jagora: Sai ga Hausawa irinmu,

    Ihu ɓarawo,

    Nic ce, an yi ɓarna,

    Wanga bawa ba kaiwa zai ba,

    Tun wada na hanga hakan ga,

    Sai yana tahiya tai yanga-yanga,

    Ba mai jiha ko bugawa,

    Sai dai nuni sai a ɓatai.

    A nan Gambo ya kawo labarin inda aka yi wa ɓarawo ihu domin a kama shi. Sai dai saboda tsabar waibuwar ɓarawon (magani), sai kowa ya kasa kaiwa gare shi, ballantana har a samu wanda zai doke shi. A maimakon haka, sai shi ɓarawon ya ci gaba da tafiyarsa cikin yanga. Duk dai wannan na nuni ga waibuwar Bahaushe a ɓangaren magani.

    4.0 Kammalawa

    Nazarin ya lura da cewa, a lokuta da dama Bahaushe na danganta ɗaukaka da buwaya da kuma cuɗanya da aljani. A tunaninsa, hulɗa da aljani hanya ce mafi sauƙi na samun buwaya. Wannan ne ma ya sanya, mawaƙa da dama ke amfani da waibuwa a matsayin tubalin ginin saƙonnin waƙoƙinsu. Kamar dai yadda Shata ya yi amfani da waibuwa a matsayin dalilin samuwar jarumta da magani.

    Mawaƙa na ba wa mutum wata ɗabi’ar aljani domin ɗaukaka buwayarsa da kambama shi da fito da shahara da gagararsa a fili. Lura da misalan da suka gabata daga cikin waƙoƙin Shata inda ya yi amfani da waibuwa a matsayin manyan tubalan ginin kambamar zulaƙe da jarumta da ma magani; za a iya cewa a tunanin Shata, ƙololuwar buwaya da za a iya ba wa mutum shi ne a danganta shi da aljani. Wannan bai rasa nasaba da yanda aljani yake a tunanin Bahaushe, wanda hatsabibanci da buwaya na samuwa ta hanyar ta’ammuli da shi. 

    Manazarta

    A’azamiyun, W. (1962). Sha’irul Islami: Hassan Bin Sabit Al’ansari. Alkahira: Madaniyyun.

    Abdlƙadir, D. (1975). The Role of an Oral Suɓey in Hausa/Fulani Society. Unpublished Ph. D. Thesis Bloonimgton, Indiana Uniɓiɓersity, USA.

    Abdullahi, I.S.S. (2008). “Jiya ba Yau ba: Waiwaye a Kan Al’adun Matakan Rayuwar Maguzawa na Aure da Haihuwa da Mutuwa.” A Ph. D. thesis submitted to the Department of Nigerian Languages, Usmanu Danfodiyo Uniɓersity, Sokoto.

    Abdullahi, S. M. (2017). “Kuɗi A Idan Mawaƙan Hausa Na Baka Da Rubutattu, Waƙar Kuɗi Ta Alhaji Audu Wazirin Ɗanduna Da Ta Alhaji Mamman Shata Da Kuma Gambo Hawaja” Kundin digiri na farko da aka gabatar a Sashen Harunan Nijeriya, Jami’ar Usamnu Ɗanfodiyo Sakkwato

    Ahmad, A. (2010). Figure of speech and idiomatic eɗpressions. In Mastering the Basics of English Language. Zaria: Ahmadu Bello Uniɓersity Press Limited.

    Amaechi, M. I. (2010). Comprehensiɓe Literature in English for senior secondary schools. Lagos: A. Johnson Publishers LTD.

    Becker, S. W. & Eagly, A. H. (2004). The heroism of women and men. In American Psychologist Ɓol. 59. Pp 163-178.

    Bello, S. da wasu (eds) (2006). Ƙamusun Hausa. Zaria: Ahmadu Bello Uniɓersity Press Limited.

    Birnin-Tudu, S. Y. (2002). Jigon salon rubutattun waƙoƙin fura’u an ƙarni na ashirin. A Ph. D. thesis submitted to the Department of Nigerian Languages, Usmanu Danfodiyo Uniɓersity, Sokoto.

    Bunza, A. M. (1988). “Nason Kirari Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa na Ƙarni na 20.” Maƙalar da aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

    Bunza, A. M. (1995). Magungunan Hausa a rubuce: Nazarin gudummuwar ayyukan malaman tsibbu. A Ph. D. thesis submitted to the Department of Nigerian Languages, Bayero Uniɓersity, Kano.

    Bunza, A. M. (2015). Hyperbole as the Peak of Stylistic Adornment in the Hausa Oral Songs. Being a lead paper presented at the 3rd Annual Conference and 12th NFS Congress organized by Nigerian Folkloric Society, Center for Research in Nigerian Languages and Folklore, Bayero Uniɓersity, Kano, with the theme: Oral Poetry In Nigeria: Prospects And Challenges In The 21st Century, Monday, October 26th – 27th, 2015 at Musa Abdullahi Auditorium, Bayero Uniɓersity, Kano.

    Dangambo, A. (1973). “Shata da waƙoƙinsa. An undergraduate project submitted to the Department of Nigerian Languages, Bayero Uniɓersity, Kano.

    Douglas, M. S. & Mathew, C. (2012). Heroism and risk of harm. In Psychology Ɓol. 13, No. 12S, pp. 1080-1090

    Fitry, I. (2010). A figuratiɓe language analysis on Sylɓia Plath poems. Retrieɓed on 30th June 2017, from: repository.uinjkt.ac.id/dspace

    Franco, Z. E., Blau, K. & Zimbardo, P. G. (2011). Heroism: A conceptual analysis and differentiation between heroic action and altruism. In Reɓiew of General Psychology. Doi: 10.1037/90022672, pp. 99-113.

    Furnish, G. (1996). Poetry, prose and popular culture in Hausa. London: Edinburgh Uniɓersity Press.

    Gobir, Y. A. (2009). Tasirin Iskoki a Cikin Waƙoƙin Sata: Nazari Daga Waƙoƙin Gambo Mai Waƙar Ɓarayi. Takardar da aka gabatar a taron }ara wa juna sani a kan “Tubar Gambo daga Wa}o}in Sata”, wanda Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sakkwato ta shirya, Asabar, 28 ga Fabrairu, 2009.

    Gobir, Y. A. (2012). Tasirin iskoki ga cututtuka da magungunan Hausawa. A Ph. D. thesis submitted to the Department of Nigerian Languages, Usmanu Danfodiyo Uniɓersity, Sokoto.

    Gusau, S. M. (1996). Makaɗ a da Mawaƙan Hausa. Kaduna: Fisbas Media Serɓices.

    Gusau, S. M. (2003). Jagora Nazarin Waƙar Baka. Kano: Benchmark Publishers.

    Gusau, S. M. (2003). Waƙoƙin Alhaji Mamman Shata, Diwani na Ɗaya (ed). Bugawar Hukumar Binciken Tarihi da Kyautata Al’adu ta Katsina. Katsina: Goɓernment Printing Press.

    Habibu, L. (2001). “Bunƙasar Rubutattun Waƙoƙin Hausa a Ƙarni na Ashirin (20).” Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato.

    Habibu, L. (2001). Gudummuwar finafinan Hausa a ƙarni na ashirin (20). An undergraduate project submitted to the Department of Nigerian Languages, Usmanu Danfodiyo Uniɓersity, Sokoto.

    Kankara, A. I. (2013). Mahadi mai Dogon Zamani: Shata da kundin waƙoƙinsa. Kaduna: Labson Prorduction.

    Maiyama, U. H. (2008). Sata a zamantakewar Hausawa: Nazarin waƙoƙin ɓarayi na Muhammadu Gambo Faraga. Kundin digiri na uku wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

    Marriam Webster, (2017). Sorcery. Retrieɓed on 8th July 2017 from; www.marriam-webster.com/dictionary/sorcery

    Melony, A. (1999). Preference ratings of images representing archetypal themes: An empirical study of the concepts of archetypes. In Journal of Analytical Psychology, Ɓol. 44. Pp 101-116.

    Omosowane, J. O. & Nelson, A. A. (2003). Comprehensiɓe English language for senior secondary schools. Lagos: A. Johnson Publishers LTD.

    Ƙaura, H. I. (1994). “Ƙawancen Salo a Tsakanin Rubutattun Waƙoƙin Wa’azi da Madahu da Kuma Siyasa.” Kundin kammala digiri na biyu (M.A.) wanda a aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.

    Samaram, G. (2008). Witchcraft and sorcery: Social and medical perspectiɓe. Retriɓed on 8th July 2017 from http.atheistcenter.in/pdfs

    Sani, A-U. & Tsaure, M. B. (2016). An Image of Northern Nigeria’s Marital and Gender-based Controɓersies: A Surɓey of Abubakar Gimba’s Sacred Apples. Being a paper presented at the 13th International Conference on Ethnic Nationalities, Cultural Memory and the Challenges of Nationhood in 21st Century Literature, held at The Uniɓersity Auditorium, IBB Uniɓersity, Lapai, from 30th August to 2nd September 2016.

    Sani, A-U. (2016). Hausa Literature Beckons National Integration: An Insight Into Waƙar Haɗin Kan Afirka by Abubakar Ladan Zariya. Being a paper presented at the 1st National Conference of Faculty of Arts and Islamic Studies on the Role of Language, History and Religion, in the Deɓelopment, Integration and Security in Nigeria, held at Uniɓersity Auditorium Usmanu Danfodiyo Uniɓersity, Sokoto, between 1st to 3rd March, 2016

    Science Daily, (2014). Culture Influences Young People’s Self-esteem: Fulfillment of ɓalue priorities of other indiɓiduals important to Youth. Retrieɓed on 21st June, 2017 from www.sciencedaily.com

    Sheme, I., Ƙanƙara, A. I., Albasu, T. Y., Kano, A. M. (2000).  Shata Ikon Allah. Kaduna: Espee Publications

    Yahya, A. B. (1996). Jigon Nazarin Waƙa. Kaduna: Fisbas Media Serɓice.

    ‘Yar’aduwa, T. M. (2010). Jagoran Nazarin Rubutaccen Adabin Hausa. Ibadan: HEBN publishers PLC.

    Zurmi, A. D. (2006). “Tsoratarwa a Cikin Waƙoƙin Wa’azi na Nana Asma’u.” Kundin digiri na farko wanda aka gabatar a Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato.

    [1] A ƙoƙarinsa na ba da misalin kambamar zulaƙe, Bunza, (2015) ya rawaito Muhammadu Sani Ɗanbolɗo a waƙarsa ta Zaura, inda yake kambamar zulaƙe yayin yaba siffar wata mace. Yana cewa:

    Farar fatat ta ka ruɗa ni

    Dun nar rice

    Tsawon hancinta misali nai

    Ya kai mil goma misalin dogon hanci.

    (Muhammad Sani Ɗanbloɗo: Waƙar Zaura)

    Da ma dai, Bahaushe ya ɗauki dogon hanci a matsayin babban abu wajen nuna kyawun mace. Domin fito da tsawon hancin matar da Sani yake yi wa waƙa fili, sai ya yi amfani da kambamar zulaƙe, inda yake nuna ai tsawon nasa ya kai har mil goma (Da a magana ce ta yau da kullum, sai a ce zuge ta malle!).

    [2] Hasan Sarkin Dogarai wani dogari ne da aka taɓa yi a fadar Kano, wanda ya yi zamani da Sarkin Kano Mai Martaba Ado Bayero. Al’umma ta tafi kan cewa, Hasan yana da tsananin waibuwa sosai. Saboda haka, kambamar zulaƙe da Shata ya yi masa, bai rasa nasaba da wannan fahimtar mutane game da Hasan, wato waibuwar da yake da shi.

    [3] Gambu ya yi haka ne domin ya nuna yadda Tsoho Tudu yake da zunzurutun waibuwa, wanda babu wani ɓarawo da ya isa ya masa sata.

    [4] Shago ɗan dambe ne da ya yi matuƙar shahara a ƙasar Hausa. An tabbatar da cewa, sau da dama Shago na kai abokin karawarsa ƙasa da bugu guda kawai.

    [5] Siddabaru dai shi ne amfani da dabara da hikima maɗaukakiya domin aikata wani aikin da zai ɗaure kan masu kallo ko saurare. Sau da dama idan aka yi siddabaru, masu kallo (musamman waɗanda ba su gane dawar garin ba) kan samu wasu-wasi tare da ɗaukar mai siddabaru a matsayin wanda yake da waibuwa ta musamman.

    Danna nan don karanta Maƙala Mai Taken: “Zamo Mini Tubali in Zam Miki Hoto”

    Edita@rumasau-kallamu

  • Maƙala Mai Taken Kasuwanci A Duniyar Intanet: Ƙalubalen Hausawan Ƙarni na 21

    Maƙala Mai Taken Kasuwanci A Duniyar Intanet: Ƙalubalen Hausawan Ƙarni na 21

    Cite this Article as: Sani, A-U., Yankara, M.M. & Baba N. (2023). Kasuwanci a duniyar intanet: Ƙalubalen Hausawan ƙarni na 21. Yobe Journal of Language, Literature and Culture, 11, 224-253. ISSN: 2449-0660.

    Kasuwanci a Duniyar Intanet: Ƙalubalen Hausawan Ƙarni na 21
    Na
    Abu-Ubaida Sani
    Department of Languages and Cultures
    Federal University Gusau, Zamfara State, Nigeria
    Mail: abu-ubaidallah@fugusau.edu.ng, abuubaidasani5@gmail.com
    Phone: +2348133529736
    Da
    Muhammad Musa Yankara
    Hausa Department
    Federal University Dutsin-Ma
    mymuhammad@fudutsinma.edu.ng
    Da
    Nasir Babba
    Hausa Department
    Federal University Dutsin-Ma
    babbanasir@gmail.com

    Tsakure

    Sannu a hankali al’ummun duniya na ƙara rungumar kasuwancin duniyar intanet. Ciki har da Hausawa. Wannan ne babban dalilin gudanar da binciken inda aka nazarci nau’uka da yanaye-yanayen kasuwancin kan intanet da alfanu da ƙalubalen da ke tare da su da kuma hanyoyin fuskantar waɗannan ƙalubale.
    Manyan dabarun da aka yi amfani da su wajen tattaraa bayanai su ne nazartar bayanan kan intanet kai tsaye da kuma hira da Hausawan da abin ya shafa. An ɗora aikin a kan ra’in Pulatoriyya (Platonism) inda aka kalli kasuwancin duniyar intanet a matsayin mai cin gashin kansa daga kasuwancin duniyar zahiri (duk da cuɗanyar da suke yi da juna a waɗansu lokuta). Binciken ya gano nau’ukan kasuwancin intanet guda biyar da Hausawa ke gudanarwa.
    A ɓangare guda kuwa, binciken ya gano cewa, kasuwancin kan intanet ya kasance cigaba duk da waɗansu ƙalubale da ya ƙunsa. Daga ƙarshe binciken ya ba da shawarwari da suka haɗa da sa hannun gwamnatoci da hukumomi da ɗaiɗaikun mutane domin bin matakai da amfani da dabarun kauce wa gurɓata muhalli da yanayi yayin gudanar da hada-hadar kasuwanci a duniyar intanet.
    Fitilun Kalmomi: Kasuwanci; Intanet; Pulatoriyya

    1.0 Gabatarwa

    Kamar yadda duniya ba a wuri guda take tsaye ba, [1]haka ma al’amuran da ke cikinta kullum na kan sauyawa. Waɗannan sauye-sauye sun shafi dukkannin ɓangarorin rayuwa da wanzuwar dukkannin halittu. [2] A ɓangarori da dama na rayuwa, sababbin abubuwa da zamani ke zuwa da su na kasancewa hanjin jimina, wato akwai na ci sannan akwai na zubarwa.
    Hakan ne kuma ya sa yake da matuƙar muhimmanci da a riƙa nazartar sababbin abubuwan da zamani ya samar. Wannan zai ba da damar cin gajiyar alfanin da ke tattare da sauye-sauyen tare da samar da nagartattun matakan fuskantar ƙalubalen da ke tattare da su.
    Fannin kasuwancin Hausawa babban bagire ne da har kullum ke sanya rigar zamaninsa. Ƙarni na ashirin da ɗaya (Ƙ21) ya zo da sauyi na musamman a wannan fannin. A ƙarnin ne aka samu bunƙasar intanet. Sannu a hankali intanet ya mamaye ɓangarorin rayuwa, ciki har da lamarin kasuwanci. Sannu a hankali har aka kai bagiren da a yau kasuwanci ba ya bunƙasa ya kai matakin ƙoli har sai ya rungumi duniyar intanet.
    Hausawan wannan zamani ba a bar su a baya ba wajen tsunduma harkar kasuwanci da ke da alaƙa da duniyar intanet. Wannan kuwa ya kasance cikin salailai daban-daban, tun daga kan dillanci, talla, har zuwa nau’ukan ayyukan da ke buƙatar ƙwarewa da ilimummukan fannoni na musamman.
    Bisa wannan, akwai buƙatar gudanar da bincike domin nazartar yanaye-yanayen kasuwancin Hausawa a duniyar intanet. Kai tsaye wannan takarda ta mayar da hankali kan:
    (i) nazartar nau’uka da fasalce-fasalcen kasuwancin Hausawa a duniyar intanet,
    (ii) ƙalubale da alfanun da ke tattare da kasuwancin, da kuma
    (iii) matakan fuskantar ƙalubalen tare da inganta harƙallolin.

    1.1 Dabarun Gudanar Da Bincike

    Kadadar wannan bincike ta taƙaita ne ga kasuwanci da ke da alaƙa da intanet. An sake taƙaita kadadar ga kasuwancin Hausawa. Ba a iyakance waɗansu kafafe da za a mayar da hankali a kansu ba. Dalili kuwa shi ne, binciken ya ƙudiri aniyar waiwaitar duk  nau’ukan hada-hadar kasuwancin kan intanet da ake damawa da Hausawa.
    An tattara bayanan majiyar farko (primary source) ta hanyoyi guda biyu. Hanya ta farko ita ce binciken kai tsaye a kafafen intanet da ake gudanar da hada-hadar kasuwanci. Hanya ta biyun kuwa ita ce hira da Hausawa da ke gudanar da sana’o’i masu alaƙa da intanet domin samun bayanai daga tushe.
    An bi dabarun tantance bayanan da aka samu daga tattaunawar ta hanyar maimaita tattaunawa da waɗansu mutane na daban da kuma ta hanyar tabbatar da bayanai daga ƙididdigar alƙaluma da ke wallafe a kafafen intanet.
    Wuraren da aka tattara bayanai da ke matakin majiya ta biyu (secondary data) sun haɗa da littattafai da mujallu da muƙalu da kuma bidiyoyi da hotuna da rubuce-rubucen da ke kafafen intanet daban-daban. Duk waɗannan sun taimaka wajen share hanya da ƙarin haske tare da yin jagoranci wajen fayyace muhamman batutuwa da suka shafi binciken.

    1.2 Ra’in Bincike

    An ɗora wannan bincike a kan ra’in Pulatoriyya (Platonism).[3] Kamar yadda Gerson, (2005: 253) ya bayyana, wanann ra’i ne da ya ginu kan fahimta da falsafofin Plato, [4]duk kuwa da cewa yakan samu sauye-sauye daga lokaci zuwa lokaci. Ra’in na iƙirarin cewa, duniya tamkar kashi biyu take; duniyar zahiri (bayyananniyar duniya) da kuma ta baɗini (ɓoyayyiyar duniya). Lamura na gudana a waɗannan duniyoyi sannan suna iya cuɗanya da juna. Haka kuma, al’amuran da ake gudanarwa a ɗaya daga cikin duniyoyin na iya shafar ɗayar.
    A bisa wannan ra’in, takardar na da hasashen cewa, akwai nau’ukan kasuwancin da ake gudanarwa a duniyar intanet ta sigogi makamantan yadda ake gudanar da su a duniyar zahiri. Haka kuma, kasuwancin da aka fara a duniyar zahiri na iya komawa duniyar baɗini (intanet). Ana kuma iya ɗauko kasuwanci daga duniyar baɗini a dawo da shi duniyar zahiri.
    Ra’in Pulatoriyya ya yi jagoranci a binciken ta fuskar fito da nau’in alaƙa da ke tsakanin kasuwancin duniyar zahiri da duniyar intanet. Ya kuma nuna wuraren da ɓangarorin biyu ke cin gashin kansu da kuma wuraren da suke cuɗanya da juna cikin salon shigar giza-gizai. Bugu da ƙari, ra’in ya taimaka wajen ƙwanƙwancewa da ƙalailaice bayanan da binciken ya tattara.

    2.1 Taliyon Kalmar “Kasuwanci” A Kadadar Al’adun Hausawa

    “Kasuwanci” da “sana’a” kalmomi ne masu tafiya kafaɗa da kafaɗa. Duk da alaƙar da ke tsakanin kalmomin biyu, akwai marubuta da suka yi ƙoƙarin ba da ma’anar sana’a da ta kasuwanci a keɓance.
    Rumbun Ilimi (n.d.) ya bayyana cewa Hausawa na sana’a tun wajajen shekarar 1349, inda kuma ya ce sana’a: “kalma ce da aka aro ta daga Larabci, kuma take ɗaukar ma’ana ta samar da wani abin amfani ta hanyar hikima a Hausance.” Ya ɗauki kasuwanci abu mai cin gashin kansa a matsayin hanyar saye da sayarwa. Wannan ra’ayi ya yi daidai da na Buhari, (2021: 1)1 inda yake cewa:
    Kasuwanci dai yana nufin saye da sayarwa na wani abu ko kuma haja wanda abun nan yana iya kasancewa wanda ake gani ne kuma wanda ba a gani[5] ne kamar mutum ya yi wani aiki a biya shi to duka suna ɗaukar ma’anar kasuwanci. Buhari, (2021: 1)1
    A fahimtar wannan takarda, tattauna kasuwanci a kadadar al’adun Hausawa ba zai kammala ba har sai an haɗa shi da sana’o’in Hausawa. Hasali ma a bagire da dama suna iya wakiltar juna. Muhammad, (2020: 224) ya bayyana ma’anar sana’a a matsayin “hanyoyin da ake gudanar da saye da sayarwa.
    “Kai tsaye za a iya cewa wannan ma’ana tana bayani ne a kan kasuwanci. Ta yiwu cuɗeɗeniyar da ke tsakanin sana’a da kasuwanci ne ya ja hankalin Muhammad wajen ba da wannan ma’ana.
    Ko Rumbun Ilimi, (2020: 1) da Buhari, (2021: 1)1 da Buhari, (2021: 1)2 da suka rarrabe tsakanin kasuwanci da sana’a, akwai wuraren da bayanansu ke nuna ba a iya rabe su. Misali, Buhari ya kawo “noma” da “kiwo” da “ɗinki” a cikin misalan kasuwanci. Ya yi hakan ne a ƙoƙarin nuna yadda Hausawa ke samun kuɗi da su.
    Idan har sai an ƙalailaice bambancin da ke tsakanin sana’a da kasuwanci, to ana iya cewa sana’a ita ce hanyar amfani da fasaha da hikima da kuma kayan aiki domin sarrafa wani abin amfani da za a iya sayarwa ko a musanya da wani abu mai daraja. Kasuwanci kuwa fasaha ce ta saye da sayarwa ko musanyen abubuwa masu daraja domin samun riba.
    Ko ba komai, za a tarar da cewa duk sana’ar da za a gudanar (kamar ƙira, saƙa, wanzanci da sauransu) to sai kasuwanci ya shiga ciki (ciniki, talla, da sauransu). Haka kuma duk kasuwancin da za a gudanar, to ana yi ne ta amfani da kayayyakin da an same su ne sakamakon sana’o’i.

    2.2 Kasuwancin Hausawa A Duniyar Zamani

    Cuɗanyar Hausawa da baƙin al’ummu musamman Larabawa da Turawa da kuma sauyawan zamani sun samar da sauye-sauye da dama a fannin kasuwancin Hausawa.[6] Haka kuma, a har kullum Hausawa na ƙara samun wayewa ta fuskar kasuwanci tare da faɗaɗawa da bunƙasa sana’o’insu. Bunƙasar kasuwancin Hausawa na kasancewa cikin manyan sigogi guda biyu kamar haka:
    Bunƙasar kasuwanci: Bunƙasar kasuwanci na faruwa ne yayin da ribar da ɗan kasuwa ke samu a cikin wani ayyanannen lokaci (misali wata guda) tak. Wannan na iya kasancewa sakamakon ɗaya daga cikin abubuwan da aka zayyano a ƙasa:
    • Faɗaɗar kasuwanci
    • Ɗaukakuwar darajar kasuwanci
    • Raguwar kuɗaɗen da ake kashewa kan sana’a[7]
    Faɗaɗar kasuwanci: Kasuwanci na samun faɗaɗa ne yayin da kayayyakin da yake samarwa ke isa hannun adadin mutane sama da yadda abin yake a baya. Wannan ma na iya kasancewa ta fuskokin da suka haɗa da:
    • Faɗaɗar kasuwanci na cikin gida[8]
    • Faɗaɗar kasuwanci na waje[9]
    Dukkannin matakan biyu (bunƙasa da faɗaɗar kasuwanci) na samuwa sakamakon tasirin zamani. Dalilan samuwarsu sun haɗa da:
    (i) sauƙaƙar hanyoyin sufuri da
    (ii) bunƙasar hanyoyin sadarwa da
    (iii) sababbin matakan sarrafawa da makamantansu.
    Ana iya kallon tasirin zamani kan kasuwancin Hausawa ta fuskoki daban-daban kamar haka:
    • Ƙare-Ƙare
    • Ƙirƙire-Ƙirƙire
    • Hulɗayya
    Kamar yadda masu iya magana ke cewa “ruwa ba ya tsami banza,” akwai dalilai daban-daban da ke samar da waɗannan sauye-sauye a sha’anin kasuwancin Hausawa. Idan aka ce “tasirin zamani,” dunƙulallen zance ne da ke tattare da abubuwa mabambanta. Yayin da aka fasa cikinsa, za a tarar da ɗaiɗaikun sabubban da suka haɗa da:
    Ɗaukar hannu: Wannan ya shafi kwaikwayo daga fasahohin waɗansu al’ummu na daban. Misali, a yau maƙeran Hausawa na samar da kayayyaki daban-daban ta hanyar ɗaukar hannu daga ƙere-ƙeren ƙasashen ƙ Haka ma kafintoci Hausawa ke ƙera abubuwa ta hanyar ɗaukar hannu. Babban misali shi ne bodin babbar mota (roka) da ake amfani da kataki da ƙarafa wajen ƙerawa.
    Yanayi/Tilasci: Sauyin yanayi da ya shafi rayuwa ko muhalli na kai ga an samar da sababbin kasuwanci tare da sauye-sauye a waɗanda ake da su. Kasuwancin sayar da datar intanet da ta POS da Hausawa suka runguma a yau, duk misalai ne na sababbin nau’ukan kasuwanci da suka samu a sakamakon tasirin yanayi. Haka kuma awara/wara/ƙwai-da-ƙwai da ke ƙara mamaye ƙasar Hausa na da alaƙa da yanayin yunwa da talauci da Hausawa ke ciki. A lokacin annobar korona kuwa (2019-2022), Hausawa da dama sun tara kuɗi ta hanyar kasuwancin takunkumin fuska (face mask).
    Yayi: Akan samu lokutan da yayi ne kawai ke sauyawa. Sannu a hankali sai a saki wani abu da aka yi riƙo da shi a koma wani daban. Irin wannan sauyi na kasance cikin yanayin da abu ne mai wuya a iya bayanin mene ne haƙiƙanin dalilin da ya sa aka saki al’adar baya. Sau da dama sai dai a ce “wayewa.”[10]

    3.0 Kasuwancin Hausawa A Duniyar Intanet

    A wannan bagire, kasuwanci na nufin duk wani abin da za a yi domin samun kuɗi ko wani abu mai darajar da zai iya wakiltar kuɗi ko wanda za a iya musanya shi da kuɗi. Wannan ya kasance saɓanin duk waɗansu ra’ayoyi da ke ɗaukar “sana’a” da “kasuwanci” a matayin nau’ukan harƙalloli guda biyu masu cin gashin kansu.
    Takardar ta tsaya kan wannan ra’ayi ne kasancewar harƙallolin biyu na da alaƙa da juna ta yadda ba za su iya cin gashin kansu ko ware kansu daga juna ba musamman a bagiren duniyar intanet.
    Sani, Buba da Mohammad (2019 p. 48) sun rawaito  Poon da Swatman na cewa: “Amfani da intanet a tsakanin masu ƙananan sana’o’i ya zama wani fitaccen lamari (batu) ga manazarta a fannin ilimin kimiyyar intanet da na kasuwanci.” Duniyar intanet shakundum ce ta fuskar tattara kasuwanci daban-daban.
    Mafi yawan motsi/lamura da ke kan intanet kasuwanci ne. Kusan komai da ke kan intanet na da darajar da za a iya sarrafa shi domin samun kuɗi – wato dai za a iya gudanar da kasuwanci da shi. A intanet akan samu har tsofaffin sana’o’in Hausawa da aka fara mantawa da su. Sannan akan iya yin kasuwanci da waɗannan tsofaffin sana’o’i ta hanyoyi daban-daban, kamar sayar da bayanan, sayar da hotuna da bidiyoyin, ko ɗora tallace-tallace a kafafen da suke.
    Wannan ɓangare na takardar zai tattauna lamarin kasuwancin Hausawa a duniyar intanet ƙarƙashin muhimman kanu guda uku, wato nau’o’in kasuwancin da nasarorinsu da kuma ƙalubalen da suke fuskanta.

    3.1 Nau’o’in Kasuwancin Hausawa A Duniyar Intanet

    Tuni Hausawa da dama suka tsunduma cikin hada-hadar kasuwanci da suka shafi duniyar intanet. Nau’ukan kasuwancin kan intanet da ake samun Hausawa ciki na da matuƙar yawa. Duk da haka, ana iya bayanin su cikin manyan rukunoni guda biyar kamar haka:
    • Firilancin na Kan Intanet (Online Freelancing)
    • Baje Haja/Koli
    • Dillanci
    • Kasuwancin Kuɗin Intanet
    • Talla (Advertisement)

    3.1.1 Firilancin Na Kan Intanet (Online Freelancing)[11]

    Aikin wucin gadi na kan intanet ya shafi duk wani nau’in aiki da ke buƙatar wata ƙwarewa ta musamman domin gundanar da ita. Manyan hajojin da masu ire-iren waɗannan kasuwanci ke kasawa su ne basirarsu da ƙwarewarsu. [12] A wannan fannin, ɓoyayyiyar gaskiya ba ta taƙaita ga kasa hajar baɗini ba. A maimakon haka, farfajiyar kasuwancin ma ta baɗini ce, wato duniyar intanet. Ɗaya daga cikin alfanun irin wannan aiki shi ne kamar yadda Downey, (2022 p. 1) ke cewa:
    A freelancer is not an employee of a firm and may therefore be at liberty to complete different jobs concurrently by various individuals or firms…
    Fassara: Firilanca ba ma’aikaci ne da wata ma’aikata ta ɗauka aikin dindindin ba, don haka yana da damar gudanarwa da kammala ayyuka daban-daban a lokaci guda, waɗanda yake karɓa daga mutane ko ma’aikatu daban-daban…
    Daga cikin ire-iren sana’o’in akwai:
    Firilancin da suka shafi kimiyyar harshe (language and linguistic services)
    Ma’aikatan firilancin ƙarƙashin kimiyyar harshe na gudanar da ayyuka da suka haɗa da:
    • Bin ƙwaƙƙwafin ma’ana (linguistic evaluation)
    • Fassara (translation)
    • Fassara da ƙirƙira (transcreation)
    • Karatun bita (proofreading)
    • Ƙirƙirar rubutu (content writing)
    • Subtitling (fassarar kan sikirin)
    • Tafintanci (interpretation)
    • Tsara rubutu (typesetting)
    • Maye sauti (voice over)

    Firilansin da suka shafi intanet da na’urori

    Ma’aikatan firilancin ƙarƙashin intanet da na’urori na gudanar da ayyuka da suka haɗa da:
    • Ba da tsaro ga kafafen intanet da na’urori (cyber security)
    • Gina kafafen intanet (website design)
    • Gina manhajoji (software programming)
    • Gwada inganci da amincin manhajoji da kafafen intanet (beta testing)
    • Gwada kutse (penetration testing)

    Firilancin da suka shafi gyaran hotuna da bidiyoyi

    Ma’aikatan firilancin ƙarƙashin gyara hotuna da bidiyoyi na gudanar da ayyuka da suka haɗa da:
    • Gyara hotuna da bidiyoyi (photo and video editing)
    • Tsara hotuna da zane-zane (graphic design and illustration)
    • Firilancin da suka shafi bincike
    Masu firilancin da ke ƙarƙashin rukunin bincike na gudanar da ayyuka da suka haɗa da:
    • Ƙalailaice bayanai (data analysis)
    • Neman bayanai (data sourcing)
    Ko bayan waɗannan akwai waɗansu masu tarin yawa da suka haɗa da: Jami’in talla (Marketing agent) da watsa labarai (media) da aiki a matsayin ƙwararren jami’i mai ba da shawarwari da suka shafi kuɗaɗe (finance expert) ko shawarwari da suka shafi doka (legal expert) ko mai jigila (gig work) da dai makamantansu.
    Da yawa daga cikin waɗannan nau’ukan sana’o’i akan same su a duniyar zahiri. Sai dai na duniyar zahirin sun yi ƙaranci sosai idan aka kwatanta da yadda hada-hadar kasuwancin take a duniyar intanet. Akwai dalilan da suka sa aka fi samun su a duniyar intanet kamar haka:
    • Domin taƙaita kashe kuɗi ga kamfanoni[13]
    • Domin nisan ƙwararru a fannonin da ake buƙata[14]
    Duk waɗannan nau’ukan firilancin ɗin kan intanet da aka zayyano a sama, a yau akwai Hausawa da suka rungume su.[15] Ƙin ƙarawa ma, har an samu ma’aikatu da kamfanonin Hausawa waɗanda ke gudanar da ire-iren ayyukan nan na firilancin. Daga cikinsu akwai Amsoshi Language Serices (https://www.amsoshilanguageservices.com)[16] da Shawsec (https://shawsec.com)[17] da 3logy (https://3logy.com.ng)[18].
    Duk wanda aka ɗauka daga cikin nau’ukan kasuwanci da ke sama na samar da kuɗin shiga sosai (duk da ya dogara ga alƙaluma daban-daban kamar su lokaci da yanayi da ƙwarewa da sauransu).[19] Nicol, (2022 p. 1) ta kawo cewa, kuɗin hada-hadar kasuwar duniyar fassara kaɗai ya haura dalan Amurka miliyan arba’in ($40,000,000). Yana da wuya a fitar da ƙididdigar kason da Hausawa suka ɗauka daga cikin alƙaluman.

    3.1.2 Baje Haja/koli

    A kullum Hausawa na ƙara rungumar intanet a matsayin kasuwar baje hajojin da suke sayarwa. Wannan na daga misalan harƙallolin da ake gudanarwa a duniyoyi guda biyu (na zahiri da na baɗini). Tun a shekarar 2021, Oyekanmi, (2021 p. 1) ya bayyana cewa rahoton National Bureau of Statistics (Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa) ta nuna cewa kashi 22% na masu ƙananan kasuwanci ne ke amfani da intanet wajen gudanar da kasuwancinsu.
    Hausawa masu ƙanana da manyan kasuwanci da dama na amfani da kafafen intanet daban-daban domin tallata kasuwancinsu. Waɗansu na amfani da kafafen sada zumunta (WhatsApp, Facebook, Instagram, TikTok, da sauransu),[20] waɗansu kuwa na buɗe kafafensu na kansu ko su haɗa guiwa da waɗansu masu kafafen intanet domin sama musu gurabu. A duba misalai a hotunan da ke ƙasa:
    Hoto na 1: Tallan hajoji a kan sitatus ɗin WhatssApp
    Tushe: An ɗauko su daga sitatus ɗin waɗansu Hausawa a WhatssApp.
    Hoto na 1 da ke sama na ɗauke da haɗakar hotuna 4 da aka ɗauko daga sitatus ɗin WhatsApp na mutane daban-daban. 3 na farko mata ne da ke sayar da kayan kwalliya (hoto na 1), takalma da jakukkuna (hoto na 2), da kuma turamen zannuwa (hoto na 3). Hoto na ƙarshen kuma an ɗauko daga sitatus ɗin namiji da ke sayar da shaddodi da yaduna. Duk waɗannan kasuwanci ne ƙanana.
    Hoto na 2: Shafin sayar da littattafan Hausa da ke kan kafar intanet ta WikiHausa.
    Madogara: Daga https://wikihausa.com.ng/product-category/hausa-novels/.
    Saɓanin hoto na 1, hoto na 2 misali ne na kafar intanet ta Hausawa da ke ba da dama ga waɗansu ‘yan kasuwa daban su baje hajojinsu. Yayin da aka yi ciniki, masu kafar za su ɗauki wani kaso daga ribar a matsayin ladan aikinsu.
    Hoto na 3: Kasuwancin katin waya da data da katin lantarki (da sauransu) a kan intanet
    Madogara: Kafar intanet ta Malam Ahmad Ali Galadima (https://sahabdata.com.ng)
    Hoto na 3 da ke sama an ɗauko shi ne daga kafar kasuwancin kan intanet ta Sahab Data. Wannan nau’in kasuwanci ne na kan intanet mallakin Bahaushe. Malam Ahmad Ali Galadima haifaffen jahar Kano ne wanda yanzu ke gudanar da kasuwancinsa a jahar Bauchi. A da dole sai mutum ya je ofishi ko shago ko ya kira waya kafin a saka masa katin waya ko datar burawuzin ko katin talabijin ko na wutar lantarki da sauransu. Da fikira irin ta Malam Ahmad, yanzu mutum zai iya hawa kafar intanet ɗin kasuwancin masu irin wannan kasuwanci ya sayi duk abin da yake buƙatar saya da kansa ba tare da sai ya yi magana da wani ba.

    3.1.3 Dillanci

    Manyan kamfanonin kasuwancin duniya da dama na da tsarin dillancin kan intanet. Wannan binciken ya gano cewa Hausawa masu yawa na cin gajiyar wannan tsari. Yana da sigogi daban-daban sannan ana iya samun bambancin sunaye da kamfanoni mabambanta suka yi masa.
    Duk da haka, a gama-gari an fi kiransa affiliate marketing, wanda a fassarar kai tsaye zai kasance “kasuwancin ɗosane,” amma a haƙiƙanin yadda lamuran ke gudana, “dillanci” ne kai tsaye.
    Kamfanoni da suka haɗa da masu sayar da littattafai, na’urori, ababen hawa, tufafi, abinci, mayuka, da sauransu, duk suna ba da damar dillanci. Dillali zai tallata kayan kamfani. Idan aka saya ta dalilin tallar da ya yi, to yana da kaso cikin ribar, wato dai la’ada (royalty). Akwai manyan nau’ukan dillancin kan intanet guda uku kamar haka:
    • Buɗe reshen kasuwanci
    • Ɗora liƙau da samfuran hajoji a kan kafar intanet ɗin dillali
    iii. Yaɗa liƙau da samfuran hajoji a kafafen sada zumunta
    Hoto na 4: Dillanci ta hanyar ɗora liƙau a kan kafar intanet
    Madogara: An ɗauko daga kafar Amsoshi (www.amsoshi.com).
    A hoto na 4 da ke sama, za a ga misalin yadda aka ɗora liƙau da ke ɓoye cikin hoto a kan kafar intanet da ta kasance ta Hausawa. Yayin da masu ziyarar wannan kafa suka bi liƙau ɗin zuwa kafar masu kamfanin har suka yi hulɗayyar kasuwanci, to masu wannan kafa za su samu kamasho.
    Hoto na 5: Dillanci a kan kafar Paxful.
    Madogara: An ɗauko daga https://paxful.com/ha/buy-bitcoin-kiosk.
    Paxful babbar kafa ce ta hada-hadar kasuwancin kuɗin intanet. Ita ma na da tsarin dillanci. A hoto na 5 da ke sama, an ga yadda Paxful ke ba da damar a buɗe abin da ta kira “shago” a kan kafarta. Wato zai zama tamkar wani ƙaramin shago da mai shi zai riƙa samun kayayyakin da zai riƙa dillanci daga asalin babban kantin Paxful.[21]
    Dangane da tura liƙau ta kafafen sada zumunta kuwa, Hausawa da yawa sun samu kuɗaɗe daga dillancin PalmPay da Kuda da Manhajar Abeg da Chipper Cash da makamantansu.[22]

    3.1.4 Kasuwancin Kuɗin Intanet

    Kuɗin intanet (crypto currency) nau’i ne na kuɗin baɗini da ke wanzuwa a duniyar intanet. Buhari,3 (2021 p. 1) ya bayyana shi a matsayin “kuɗi da ake amfani da su a cikin kwamfuta wanda za a iya saye da saidawa da su a cikin hanya mai sauƙi.” Wani abin burgewa shi ne, ana iya sayen kuɗin intanet ta amfani da kuɗin zahiri, ana kuma iya sayen su ta amfani da wani nau’in kuɗin intanet na daban. Ƙididigar Tripple A (2023 p. 1) ya nuna cewa, ya zuwa 2022, kashi 10.34% na ‘yan Nijeriya sun mallaki kuɗin intanet.
    Batey, (n.d.) ta tabbatar da cewa, kuɗin intanet na farko shi ne Bitcoin wanda aka samar tun a shekarar 2008 sannan aka fara amfani da shi a shekarar 2009.[23] Ya zuwa yau akwai nau’ukan kuɗaɗen intanet daban-daban waɗanda kuma kullum ke ƙara yawa saboda sababbi da ake samarwa. Pi na ɗaya daga cikin waɗanda suka fi ƙaurin suna tsakanin Hausawa, inda har aka samu waƙoƙi[24] da maganganun malamai da masana daban-daban game da shi. Bayan haka, har fim sukutum aka yi game da Pi, mai suna ‘Yan Pi Network.
    Akwai manyan nau’uka ko hanyoyin kasuwancin kuɗin intanet guda biyu da wannan bincike ya ci karo da Hausawa da dama na gudanarwa. Na farkonsu shi ne trading wanda a nan aka fassara shi a matsayin cinikayya. Na biyun kuwa shi ne holding, wanda aka fassara shi da riƙewa.
    Cinikayya shi ne tsarin da ake saye da sayar da kuɗin intanet nan take domin samun ƙaramar riba. Wannan na buƙatar lissafi da kyakkyawan hasashe. M.M. Manga, (keɓantacciyar tattaunawa, 7 ga watan Fabarairu 2023) ya bayyana yadda ake wannan cinikayya. Mutum zai sayi wani nau’in kuɗin intanet bayan yin lissafin cewa darajarsa za ta ƙaru bayan ‘yan kwanaki kaɗan, domin ya sayar ya samu riba. Haka kuma, mutum na iya saya a wurin ɗan kasuwa mai sauƙin farashi, sannan ya sayar wa ɗan kasuwa mai farashin da ya fi inda ya saya domin samun riba.
    Riƙewa shi ne tsarin da mutum zai sayi kuɗin intanet sannan ya ajiye shi na tsawon lokaci. Ana yin haka ne domin bin babbar riba. Akan saya a lokacin da ake kira red market (jar kasuwa – wato lokacin da darajar kuɗaɗen intanet ta faɗi) sannan a sayar a lokacin da ake kira green market (koriyar kasuwa – wato lokacin da darajar kuɗaɗen intanet ta tashi).
    Daga cikin manyan kafofin hada-hadar kuɗaɗen intanet akwai:
    Binance – https://www.binance.com/
    Gate – https://www.gate.io/
    Crypto – https://crypto.com/
    OKX – https://www.okx.com/
    KUCOIN – https://www.kucoin.com/
    Paxful – https://www.paxful.com
    An samu Hausawa da dama da ke bayani game da lamuran da suka shafi kasuwancin kuɗin intanet. Yawanci sukan yi ne a tashoshin kan intanet masu zaman kansu. Daga cikinsu akwai Mujahid Muhammad Manga da ke da kafar TikTok mai suna Abumaher. Shi kuwa Sunusi Danjuma Ali tasha yake da ita a kan YouTube mai suna SunusiCryptoTV.

    3.1.5 Talla (Advertisement)

    A wannan bigiren talla na nufin tallata haja ko ra’ayi ko aƙidar wani ko waɗansu domin samun kuɗi. Kusan wannan nau’in talla ba a samun sa a duniyar zahiri – duk da akan samu makamantansa da ake gudanarwa a gidajen talabijin da na rediyo da kuma cikin finafinai. A yau Hausawa da dama sun yi nisa a wannan harkar kasuwanci. Ana gudanar da tallar kan intanet ta fuskoki daban-daban da suka haɗa da:

    Talla a kan kafafen intanet (Websites and blogs)

    Wanda ke da kafar intanet da ta gawurta, yana da damar ɗora tallace-tallace a kai. Tallar na iya kasancewa ta fuskoki guda biyu, ko dai Adsense[25] ko kuma keɓantattun tallace-tallace.[26]
    Hoto na 6: Talla a kafar intanet
    Madogara: An ɗauko daga https://www.isyaku.com/search/label/FADAKARWA
    A hoto na 6 da ke sama, za a ga yadda aka ɗora talla a kafar Isyaku. Mamallakin wannan kafa Bahaushe ne ɗan jahar Kebbi, mai suna Isyaku Garba.

    Talla a shafuka da zaurukan kafafen intanet

    Waɗanda ke da zauruka da shafuka a kafafen intanet na da damar ɗora tallace-tallace idan sun cika ƙa’idojin da ake buƙata. Waɗannan ƙa’idoji sun danganta da kafar da kuma mutum ko mutane ko kamfanonin da za su ba da tallar. Sannan ƙa’idojin na sauyawa lokaci zuwa lokaci.
    Hausawa da dama na samun kuɗi a YouTube da Facebook da Instagram da TikTok a dalilin irin wannan nau’in tallar. Mawaƙan Hausa na zamani da ‘yan barkwanci Hausawa da dama ta wannan hanyar suka fi samun kuɗi. Tuni masu tsara finafinan Hausa ma suka rungumi wannan nau’in kasuwanci inda suke sakin finafinansu a kan YouTube tare da ɗora tallace-tallace domin samun kuɗin shiga. Fitattun finafinan Hausa masu dogon zango da ake sakewa a kan YouTube sun haɗa da Labarina da Izzar So da Amaryar TikTok da Asin da Asin da makamantansu.
    Daga cikin ‘yan barkwancin Hausa kuwa da suka shahara da kafafen YouTube da TikTok (waɗanda ke ɗora tallace-tallace kan tashoshi ko shafukansu) akwai Abubakar Sadauki da aka fi sani da Aibs_Fulani. Akwai kuma Mu’azu Muhammad da aka fi sani da Bushkido. Sannan akwai Ali Muhammad Idris da aka fi sani da Maɗagwal, I.A. Adam (keɓantacciyar tattaunawa, 11 ga watan Maris, 2023).

    Talla Ta Hanyar Raba Liƙau

    Wannan nau’in kasuwancin kan intanet ya shafi tura saƙonnin talla na wani kamfani a kafafen sada zumunta ta sigar liƙau.[27] Mai wannan kasuwancin na ɗaukar liƙau da za a riƙa ba shi a kowace rana (ko wani lokacin da aka ƙayyade) sannan ya raba a kafafen sada zumunta irin su Facebook, TikTok, WhatsApp, da sauransu.
    Hausawa da dama sun samu riba mai yawa daga wannan kasuwanci. Duk da haka wannan nau’in kasuwanci tamkar caca yake. Dalili kuwa shi ne, sau da dama ire-iren waɗannan nau’ukan kasuwanci na yin ɓatar dabo na farat ɗaya. A haka ake rufewa da kuɗaɗen waɗanda suka yi aiki ba a biya su ba, da kuma kuɗaɗen waɗanda suka sanya hannayen jari.[28] Daga cikin ire-irensu da aka ci kasuwarsu kuma suka watse akwai:
    • Uwork
    • Insme
    • MyBonus

    3.2 Abubuwan Da Mai Kasuwanci A Kan Intanet Ke Buƙata

    Daga cikin nau’ukan ayyukan kan intanet da aka tattauna a ƙarƙashin 3.1.1 zuwa 3.1.5, akwai waɗanda suka kasance gama-gari tsakanin mutanen duniya. Waɗansu daga cikinsu kuwa, ana sa ran su kasance keɓantattu ga Hausawa. Misali, duk aikin firilancin da ya shafi harshe ko al’ada, kai tsaye an fi son ɗan gado ba ɗan haye ba.
    Ma’ana dai, an fi son wanda Hausa ke matsayin harshen uwa gare shi. Ana hakan ne don gudun abin da Bunza, (2015) ya kira “Grammatical Rift” (p. 5) da “Cultural Lacuna” (p. 11) wato “Giɓin Nahawu” da “Giɓin Al’ada.” Bayan haka, abubuwan da ake buƙata na iya bambanta daga kasuwanci zuwa kasuwanci. Duk da haka, akwai waɗanda suka kasance gama-gari kamar haka:
    Na’ura mai sauri da inganci daidai da nau’in kasuwancin da za a gudanar[29]
    Sabis ɗin intanet mai ƙarfi da rashin yankewa
    Wuri mai sirri da rashin hayaniya[30]
    Ƙwarewa sosai a fannin da aka sa a gaba
    Tallar haja (ƙwarewa) a kan intanet[31]
    Girmama lokaci
    Gaskiya da riƙon amana

    3.3 Allah san barka a kasuwancin Hausawa a duniyar intanet

    Samuwar damarmakin kasuwanci a kan intanet ya zo da alfanu ta fuskoki daban-daban ga Hausa. Daga ciki akwai:
    Hutun jiki: Waɗansu daga cikin nau’ukan kasuwanci na da sauƙin gudanarwa. Misali, kasuwancin sayar da data da katin waya da na wutar lantarki da talabijin duk saita su kawai ake yi a bar su a kan intanet. Ɗan kasuwa ba ya buƙatar wata wahalar ciniki ko miƙa kaya. A maimakon haka, kwastomomi su ne za su biya kuɗi kawai su ɗauki kaya. Yana kwance sai dai ya ji shigar kuɗi a akawun ɗinsa.[32]
    Ƙarancin jin rauni sakamakon aiki: Saɓanin ayyukan bayyane da dama da ana iya samun rauni ta dalilinsu (daga kayan aiki, ko faɗuwa, ko haɗari a hanyar zuwa wurin aiki da sauransu), mai aikin kan intanet na da ƙarancin fargabar samun wani rauni sakamakon aikin.[33]
    Cikakken ‘Yanci: Koma bayan ayyukan duniyar zahiri, mai aikin firilancin na da ‘yanci kan lokacinsa. Yana da zaɓi kan ya karɓi aiki ko kada ya karɓa. Yana da damar tsara lokacinsa yadda yake so sannan ya karɓi ayyuka lokacin da ba shi da waɗansu hidimomin rayuwa a gabansa kawai.
    Jari: Akwai nau’ukan kasuwancin kan intanet da ke buƙatar ƙaramin jari kawai. Waɗansu kuwa ba sa ma buƙatar jarin. Misali, a firilancin da ya shafi yaɗa liƙau, ba a buƙatar wani jari. Game da abin da ya shafi fassara kuwa, ɗan jarin bai wuce na sayen waya ko kwamfuta ba, sai kuma ‘yar datar burawuzin da za a riƙa sakawa.
    Sauran alfanu na gama-gari sun haɗa da:
    • Rage cunkoso a kan tituna
    • Rage fitar da sinadaren ababan hawa masu cutar da muhalli

    3.4 Ƙalubale A Kasuwancin Hausawa A Duniyar Intanet

    Duk da ɗimbin alfanun da ke tattare da kasuwancin kan intanet, akwai ƙalubale ko naƙasu da ke tattare da shi. A ƙasa an kawo waɗansu daga ciki.
    Rashin ingantaccen sabis: Har yanzu babu ingantaccen sabis a ƙasar Hausa. Ko wuraren da ke da sabis mai ƙarfin 4G, a waɗansu lokuta akan samu matsaloli.[34] Wannan babban naƙasu ne a harkar kasuwancin kan intanet kasancewar akwai lamuran da ke da ƙayyadden lokacin kammalawa. Sannan akwai kamfanoni da ke buƙatar rahoton ƙarfin intanet ɗin mutum kafin fara harƙalla da shi.
    Matsalar wutar lantarki: Har ya zuwa lokacin kammala rubuta wannan takarda (Maris 2023) babu ingantacciyar wutar lantarki a ƙasar Hausa. Hakan kuwa ƙalubale ne ga nau’ukan kasuwancin kan intanet.
    Talauci da ƙarancin tallafi: Da dama daga cikin nau’ukan kasuwancin kan intanet na buƙatar jari. Wannan ya shafi sayen kayan aiki da datar intanet da waɗansu manhajoji da dai makamantansu (wanda ya danganta ga nau’in sana’ar). Hausawa na fuskantar ƙalubale a wannan ɓangare sakamakon talauci da ƙaranci ko rashin tallafi.
    Rashin koyar da zamanantattun darrusa: Zamani ya fara tsere wa tsarin karatun Nijeriya a matakin ƙasa bai ɗaya, da kuma ƙasar Hausa a keɓance. Misali, wanda ya karanci harshe na da babban gurbi sosai a kasuwancin intanet, domin zai iya shiga a dama da shi a dukkannin nau’ukan kasuwanci da aka tattauna a ƙarƙashin 3.1.1 zuwa 3.1.5 da ke sama. Duk da haka, waɗanda suka karanci Hausa da dama na kasancewa ba tare da aikin yi ba saboda rashin gogewa ta fuskar ire-iren waɗannan nau’ukan kasuwanci.
    Illata muhalli da yanayi: Daga cikin harkoki da hada-hadar kasuwancin intanet akwai waɗanda ke cutar da muhalli. Misali, haƙon kuɗaɗen intanet irin su Bitcoin na illata muhalli matuƙa. Rahoton Osborne, (2022 p. 1) ya nuna cewa, illar da haƙon Bitcoin ke yi wa muhalli na iya kai wanda man fetur ke yi ta fuskar fitar da sinadarin kabon.
    Cutar da lafiya: Duk da babu wani bincike da ya tabbatar da cewa yawan kallon sikirin na haifar da dauwamammen ciwon ido, masanan ido irin su Dakta Colman Kraff sun tabbatar da cewa zai iya haifar da matsalolin da suka haɗa da kallo dishi-dishi da ciwon kai har ma da ciwon wuya idan abin ya yi tsanani.[35] Abiola, (2021 p. 1) ya tabbatar da cewa radiyeshin da ke fita daga jikin kwamfuta na haifar da illoli da dama, ciki har da hana haihuwa ga maza.
    4.0 Sakamakon bincike
    Lamarin kasuwanci ya yi daidai da ikirarin ra’in Pulatoriyya, domin kuwa akwai kasuwancin da ke gudana a duniyar zahiri, akwa kuma waɗanda ke gudana a duniyar intanet. Duniyar zahiri na kan tarewa zuwa nau’in kasuwancin duniyar intanet. Hausawa ma da dama sun bi sahun wannan cigaba.
    Kasuwancin kan intanet  ya rabu zuwa nau’uka daban-daban kamar yadda aka tattauna a ƙarƙashin sashe na 3.1 da ke sama. Binciken ya gano cewa ana damawa da Hausawa cikin dukkannin waɗannan kasuwanci. Waɗanda suka karanci harshen Hausa sun fi samun rawar takawa a abin da ya shafi firilancin da ke da alaƙa da harshe (ciki har da fassara da tafintanci da sauransu da aka kawo  ƙarƙashin 3.1.1).
    Waɗannan kasuwancin kan intanet na da ɗimbin alfanu ga al’ummar Hausa tun daga kan samar da aikin yi har zuwa nisantar haɗurra, da dai sauransu da aka zayyano a ƙarƙashin 3.3 da ke sama. A ɓangare guda kuwa, duk da ɗimbin alfanun da kasuwancin kan intanet ya zo wa Hausawa da shi, yana tattare da ƙalubale kamar yadda aka gani ga ƙarƙashin 3.4 da ke sama.
    Dangane da waɗannan ƙalubale, Hausawa ‘yan kasuwan kan intanet na iya riƙo da dabarar amfani da hanyoyin samun sabis ɗin intanet sama da guda. Wannan zai ba su damar kauce wa shiga halin ƙaƙanikayi sakamakon gushewar ƙarfin sabis ko sabis ɗin kacokan a lokacin aiki. Sannan kada su bari a bar su a baya wajen rungumar sababbin sabis ɗin intanet na zamani masu ƙarfi, musamman yanzu da ake sauraron ƙarasowar sabis ɗin 5G da na Starlink.
    Game da wutar lantarki kuwa, ya kamata gwamnati ta ninka ƙoƙarinta na tabbatar da samuwar ingancin wutar lantarki musamman domin samun cigaba mai ɗorewa. Yayin da gwamnati ke ƙoƙarin wannan, ‘yan kasuwan kan intanet na iya amfani da dabarun da suka haɗa da wutar sola da rumbun cajin kwamfuta (computer power bank) da sauran hanyoyin da ba sa illata muhalli da yanayi.
    Ya kamata a mayar da hankali wajen koyar da abubuwan da suka shafi kasuwancin kan intanet musamman a matakin manyan makarantu. Hakan zai ba da damar samun ƙarin aikin yi tare da rage zaman banza. Da taimakon wannan, Hausawa da yawa musamman waɗanda suka karanci harshen Hausa na iya samun hanyar dogaro da kai a sauƙaƙe.
    Dangane da illolin lamuran kasuwancin intanet a kan muhalli da yanayi, akwai buƙatar gwamnatoci da hukumomi da ɗaiɗaikun mutane su yi huɓɓasa wajen ganin an samu mafita mafi dacewa. Wannan ya haɗa da fito da dokoki da ƙa’idoji da suka dace daga ɓangaren gwamnati, bincike da faɗakarwa daga ɓangaren hukumomi, da kuma bin kyawawan matakai da ke da akwai daga ɓangaren ɗaiɗaikun mutane.

    4.1 Kammalawa

    Nau’ukan kasuwancin kan intanet na da matuƙar yawa. Da wuya a iya nuna wani abu a kan intanet da ba za a iya kasuwanci da shi ba. Sannu a hankali ‘yan kasuwan duniyar zahiri na zamanantar da kasuwancinsu ta hanyar mayar da ita ko wani ɓangare nata zuwa duniyar intanet.
    A yanzu haka duk manyan kasuwancin duniya sun yi gurbi sosai a kan intanet. Da yiwuwar a shekaru masu zuwa duniyar intanet na iya ƙwace ta zahiri a fuskar kasuwanci, inda za a samu mafi rinjayen kasuwanci na gudana ne a duniyar intanet saɓanin ta zahiri.

    Manazarta

    Abiola, R. (2021). Laptop radiation does not cause skin cancer but it can contribute to male infertility. https://dubawa.org/laptop-radiation-does-not-cause-skin-cancer-but-it-can-contribute-to-male-infertility/.
    Batey, N. (n.d.). A brief history of Bitcoin. https://www.jmco.com/articles/tax/brief-history-bitcoin.
    Buhari, I. (2021)1. Samun kuɗi: Kasuwanci guda 10 wanda aka fi saurin samun kuɗi da su. https://www.hausawasite.com.ng/2021/09/samun-kudi-kasuwanci-guda-10-wanda-aka.html.
    Buhari, I. (2021)2. Ma’anar sana’a da kuma amfaninta. https://www.hausawasite.com.ng/2021/11/maanar-sanaa-da-kuma-amfaninta.html.
    Buhari, I. (2021)3. Cryptocurrency da yadda ake samun kudi da shi. https://www.hausawasite.com.ng/2021/10/cryptocurrency-da-yadda-ake-samun-kudi.html.
    Bunza, A.M. (2015, October 20 – 21). Grammatical rift and cultural lacuna: Constraints on English-Hausa and Hausa-English translation busines. National Conference On Translation, Center for Research in Nigerian Languages and Folklore, Bayero University, Kano & Nigerian Institute of Translators and Interpreters (NITI).
    Cropley, D.H. (2019). Problem-solving man: A history of Hunan creativity. Springer.
    Downey, L. (2022). What is a freelancer: Examples, taxes, benefits, and drawbacks. Investopedia. https://www.investopedia.com/terms/f/freelancer.asp.
    Gerson, L. (2013). “Was Plato a Platonist?” From Plato to Platonism (pp. 3-33). Cornell University Press. www.jstor.org/stable/10.7591/j.ctt32b4gd.5.
    Gerson, P. L. (2005). “What is Platonism?” Journal of the History of Philosophy, 42, 253-257. www.doi.org/10.1353/hph.2005.0136.
    Hukumar Binciken Tarihi Da Al’adu Ta Jihar Katsina da ‘Yan Ƙyaure, S.S.F. (n.d.). Ilmin falaki da sanin yadda ake tsara jadawalin watannin Musulunci. Hukumar Binciken Tarihi Da Al’adu Ta Jihar Katsina.
    Kraff, C. (2022). How to protect eyes from mobile and computer screens. https://kraffeye.com/blog/how-to-protect-eyes-from-mobile-and-computer-screens.
    Meinwald, C. C. (2020). Plato (Greek Philosopher). Encyclopedia Britannica. https://www.britannica.com/biography/Plato.
    Muhammad, M.S. (2020). Bahaushiyar al’ada. Bayero University Press.
    Na, S. (2013). Earth rotation – Basic theory and features. http://dx.doi.org/10.5772/54584.
    Nguyen, A. (n.d.). 10 Best freelance websites to hire top talent. Time Doctor. https://www.timedoctor.com/blog/best-freelance-websites.
    Nicol, V. (2022). Translation industry trends and statistics. My Language Connection. https://www.mylanguageconnection.com/translation-industry-trends-and-statistics/.
    Osborne, M. (2022). Bitcoin could rival beef or crude oil in environmental impact. https://www.smithsonianmag.com/smart-news/bitcoin-could-rival-beef-or-crude-oil-in-environmental-impact-180980877/.
    Oyekanmi, S. (2021). Only 22% of Nigerian informal businesses use internet in their business operations – NBS. Nairametrics. https://nairametrics.com/2021/09/23/only-22-of-nigerian-informal-businesses-use-internet-in-their-daily-business-operations-nbs/.
    Rumbun Ilimi. (n.d.). Sana’o’i a ƙasar Hausa. https://www.rumbunilimi.com.ng/HausaSanaa.html#gsc.tab=0.
    Sani, A-U. (2022). Zamani zo mu tafi: Al’adun Hausawa a duniyar intanet. [Kundin digiri na biyu da ba a wallafa ba]. Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato, Nijeriya.
    Sani, A-U., Buba, U. & Mohammad, I. (2019). Wanda ya tuna bara…: Biɗa da tanadi a tsakanin hausawa matasa a yau. Global Academic Journal of Humanities and Social Sciences, 1(2), 44-50. www.doi.org/10.36348/gajhss.2019.v01i02.001.
    Thein, K. (2018). “Soul and incorporeality in Plato.” Eirene Sudia Graeca Et Latina, LIV, 53–95. Centre for Classical Studies Institute of Philosophy of the Czech Academy of Sciences, Prague.
    Triple A. (2023). How many crypto owners are in Nigeria? https://triple-a.io/crypto-ownership-nigeria-2022/.
    Kafafen da Aka Duba
    https://3logy.com.ng
    https://crypto.com/
    https://sahabdata.com.ng
    https://shawsec.com
    https://shehuawwal.com
    https://www.abu-ubaida.com
    https://www.amsoshi.com
    https://www.amsoshilanguageservices.com
    https://www.binance.com/en
    https://www.fiverr.com
    https://www.gate.io/
    https://www.isyaku.com
    https://www.kucoin.com/
    https://www.linkedin.com
    https://www.okx.com/
    https://www.paxful.com
    https://www.proz.com
    https://www.upwork.com
    [1] Ilimin kimiyya da addini da al’ada duk sun tabbatar da cewa duniya na kan juyawa cikin waɗansu nau’uka da salailan tafiya da kowanne ke da tasiri ko sakamako da yake samarwa. Domin ƙarin bayani, ana iya duba Hukumar Binciken Tarihi Da Al’adu Ta Jihar Katsina da ‘Yar Ƙyaure, (n.d.) ko Na, (2013).
    [2] Babu wata halitta da lokaci ba ya tasiri a kanta. Nau’ukan tasirin da ake iya samu na iya kasancewa waɗanda halittun ke da iko a kansu (misali ƙirƙire-ƙirƙire da ƙere-ƙere), ko waɗanda ba su da iko a kansu (misali raguwar girman jikin ‘yan’adam da raguwar yawan shekaru da suke yi a duniya).
    [3] Domin ƙarin bayani kan wannan ra’i ana iya duba Gerson, (2005: 253); Gerson, (2013); Thein, (2018); da Sani, (2022).
    [4] Plato ya kasance ɗaya daga cikin fitattun masana falsafa da suka rayu ƙarnuka huɗu zuwa biyar kafin zuwan Annabi Isa. Domin samun cikakken bayani kan tarihinsa da ayyukansa, ana iya duba Meinwald, (2020).
    [5] Lallai wannan ma’ana ta kasuwanci da Buhari (2021) ta ƙara fito da iƙirarin Pulatoriyya ta cewar gaskiya nau’i biyu ce, wato wacce ake gani da wacce ba a gani. Ma’anar ta Buhari ta ƙara tabbatar da hakan kamar yadda ya bayyana daga cikin kasuwanci akwai waɗanda ba a ganin su.
    [6] Wannan takarda na da ra’ayin cewa, ko da Hausawa ba su yi cuɗanya da kowace al’umma ba, za su samu sauye-sauye da cigaban zamani a harkokin rayuwarsu. A har kullum halin rayuwa na tilasta wa ɗan’adam amfani da fikira wajen sama wa kansa sauƙi da mafita daga ƙalubalen da ke dabaibaiye da matakan rayuwarsa. Saboda haka, yadda kullum yanayin duniya ke sauyawa tare da ɓullo da sababbin ƙalubale da ɗan’adam bai taɓa cin karo da su ba, haka shi ɗan’adam ke ƙara ƙirƙiro hanyoyin fiskantar matsalolin. Waɗannan su ke haɗuwa su samar da cigaban zamani. Cropley, (2019) ya kawo cikakken bayani kan wannan falsafa.
    [7] Ana iya samun raguwar kuɗaɗen da ake kashewa wurin gudanar da sana’a ta hanyoyin da suka haɗa samun kayayyakin sana’a mafiya sauƙi ko samun sauƙaƙan hanyoyin jigilar kayayyakin sana’a zuwa wurin sarrafa su, da dai makamantansu.
    [8] Wannan na faruwa yayin da aka samu ƙarin mutane a muhalli ko maƙwabta ko cikin al’ummar mai sana da suka fara amfani da kayayyakin da mai sana’ar ke samarwa.
    [9] Wannan na faruwa yayin da waɗansu al’ummu na nesa suka fara amfani da kayayyakin da mai sana’a ke samarwa.
    [10] Babban misalin wannan shi ne yadda matasan Hausawa suka riƙi babban wando (fantalo) a matsayin kwalliya (tsukakken wando kuma ya kasance ƙauyanci), har zuwa wajajen shekarar 2008. Daga baya kuma sai yayi ya sauya inda aka ɗauki fantalo a matsayin ƙauyanci, shi kuwa tsukakken wando ya koma wayewa. Duk lokacin da irin haka ya faru, masu kasuwancin wandunan dole su sauya domin samar da abubuwan da mutane za su saya ba waɗanda za su yi kwantai ba.
    [11] Kasancewar wannan takarda ba ta ci kawo da wata amintacciyar fassara ta “online freelancing” ba, an baddala ta zuwa “firilancin na kan intanet.”
    [12] Waɗannan hajoji na daga cikin misalan ɓoyayyun gaskiya da ra’in Pulatoriyya ke magana a kansu.
    [13] Idan kamfani na aiki da ma’aikatan firilancin, to ya huta biyan su albashi kowace wata. A maimakon haka, zai riƙa biyan su ne kawai yayin da ya ba su aiki.
    [14] Misali, kamfanonin fassara da ke nahiyoyin da ke nesa da ƙasar Hausa, ya fi musu sauƙi su riƙa aiki da ma’aikatan firilancin don yi musu fassarori ta kan intanet a maimakon zuwa ƙasar Hausa domin samun mai fassara ko kuma buƙatar mai fassarar ya je can domin samun su.
    [15] An tabbatar da wannan bayani ta hanyar tattaunawa da waɗansu Hausawa gogaggu a harkar firilancin, da kuma bincikawa a waɗansu manyan kafafen baje kolin firilancin na intanet da suka haɗa da Fiverr (https://www.fiverr.com) da LinkdIn (https://www.linkedin.com) da ProZ (https://www.proz.com) da Upwork (https://www.upwork.com).
    [16] Sun shahara a fannin firilancin da ya shafi kimiyyar harshe da bincike (M.U. Arabi, keɓantacciyar tattaunawa, 5 ga watan Maris, 2023).
    [17] Sun shahara a fannin firilancin da ya shafi tsaron kafafen intanet da na’urori (S. Auwal, keɓantacciyar tattaunawa, 5 ga watan Maris, 2023).
    [18] Sun shahara a fannin koyar da ilimummukan zamani kamar na’urori, intanet, saƙago da sauransu.
    [19] A bisa dalilai na sirrantawa, wannan bincike ba zai iya kawo misalan ƙididdigar kuɗaɗen da waɗansu Hausawa masu harkan firilancin ke samu ba. Amma binciken ya ci karo da Hausawan da suke iya aikin har sama da miliyan biyar (#5,000,000) a cikin wata guda.
    [20] Da wuya mutum ya karaɗe sitatus ɗinsa na WhatssApp ba tare da cin karo da hajojin da waɗansu ke tallatawa ba, irin su tufafi, turare, na’urori, da sauransu.
    [21] Fassara illahirin shafin zuwa Hausa na ƙara nuni da yadda Hausawa ke cikin wannan harkar dillanci.
    [22] A. Sani (Keɓantacciyar Tattaunawa, Maris 6, 2023).
    [23] Wanda ya samar da Bitcoin ya bayyana sunansa a matsayin Satoshi Nakamoto. Sai dai har yanzu ba a san mai wannan sunan ba. Ba a ma san mutum guda ne ko ƙungiya ce ba. Domin samun ƙarin bayani, a duba, Batey, (n.d.).
    [24] https://www.amsoshi.com/2021/12/yan-pi-network.html
    [25] Wannan nau’in talla ne inda ake rajista da kamfanin Google. Kamfanin na Google ne zai riƙa karɓar tallace-tallace sannan ya riƙa ɗora waɗanda suka dace a kafar wanda ya yi rajistar (ta la’akari da nau’ukan mutanen da ke ziyartar kafar tasa).
    [26] Wannan nau’in tallace-tallace ne da ake karɓa daga ɗaiɗaikun mutane ko kamfanoni ko ƙungiyoyi. Kai tsaye akan yi ciniki da yarjejeniyar yadda tallar za ta kasance (kamar abin da ya shafi farashi, da shafukan da za a ɗora su da tsawon lokacin da za su ɗauka kafin a sauƙe su).
    [27] A waɗansu lokuta yakan kasance bidiyo ko hoto.
    [28] An samu waɗannan bayanai daga tattaunawa da aka yi da Hausawa da suka ci wannan kasuwa. A. Sani (keɓantacciyar tattaunawa, 11 ga watan Maris, 2023) ya yi cikakken bayanin yadda harƙallolin ke gudana.
    [29] Abubuwan da ake dubawa a wannan fannin sun haɗa da saurin na’ura, girman ƙwaƙwalwarta, faɗin sikirin ɗinta, da nau’inta. Akwai nau’ukan ayyukan da kai tsaye kamfani na iya ba da bayanin nau’in na’urar da za a yi amfani da ita domin gudanarwa. Misali, daga shekarar 2020 har zuwa 2023 Hausawa da dama sun yi aiki da kamfanin Appen. Aikin na buƙatar tattara bayanai ne ta amfani da wayar salulula. Haka kuma, duk wanda ya gwada buɗe manhajar XTM a kan waya domin gudanar da fassara, zai ga jan rubutu na masa gargaɗin cewa dole sai ya yi amfani da kwamfuta.
    [30] Mafi yawan ayyukan kan intanet na buƙatar sirri. Sau da dama akan buƙaci mutum ya cike abin da aka fi sani da NDA (Non-Disclosure Agreement) wato Yarjejeniyar Riƙe Sirri kafin ƙulla harƙallar kasuwanci da kamfani a kan intanet.
    [31] Akwai fitattun kafafen intent da suka shahara a wannan fannin. Masu firilancin na zuwa waɗannan kafafe su baje kolin fikirarsu. Kamfanoni daban-daban a faɗin duniya na ziyartar waɗannan kafafe domin duba hajar da ta musu. Nguyen (n.d. p. 1) ya zayyano waɗansu daga cikin fitattun kafafen kamar haka: LinkedIn da freelancer.com da Toptal da Guru da PeoplePerHour da FlexJobs da 99Designs da Fiverr da Upwork da Freelance Writing Gigs.
    [32] Duk da haka akwai abubuwan da ake buƙata daga gare shi kamar su ƙara kuɗi a lalitoci da duba daidaiton lamura da kuma sauraren koken kwastomomi.
    [33] Duk da haka akan iya samun rauni lokaci zuwa lokaci musamman idan ba a bi ƙa’idojin aiki ba. Misali, ana iya samun ciwon baya ko ciwon wuya sakamakon daɗewa ana zaune ko zama yadda bai kamata ba, da dai sauransu.
    [34] Game da wannan, binciken ya kasance ganau a yankunan Kano da Katsina da Sakkwato da Zamfara da Zariya.
    [35] Domin ƙarin bayani, a duba Kraff, (2022 p. 1).
    Edita@rumasau-kallamu
  • Maƙala Mai Taken Tsattsafin Fanɗare wa Addinin Musulunci: Wata Yasasshiyar Gona a Gandun Waƙoƙin Baka na Hausa

    Maƙala Mai Taken Tsattsafin Fanɗare wa Addinin Musulunci: Wata Yasasshiyar Gona a Gandun Waƙoƙin Baka na Hausa

    Tsattsafin Fanɗare wa Addinin Musulunci: Wata Yasasshiyar Gona a Gandun
    Waƙoƙin Baka na Hausa

    Adamu Rabi’u BAKURA1, Abu-Ubaida SANI
    Department of Languages and Cultures, Federal University, Gusau, Zamfara State, Nigeria

    Tsakure: Rubuce-rubucen nazari da aka yi game da waƙoƙin Hausa sun fi shurin masaƙi. Duk da haka, mafi yawan rubuce-rubucen sun karkata ne kan zaƙulo fasahohi da ke cikin waƙoƙin tare da nuna yadda suke faɗakarwa da ilimantarwa da nishaɗantarwa. Wannan takarda na da fahimtar cewa an bar wani babban giɓi wanda shi ne nazarin fanɗare wa dokokin addini cikin waƙoƙin Hausa.

    Maƙalar nan na da manufar binciko muhallan da ɗiyan waƙoƙin baka na Hausa suka keta
    dokokin da Allah ya shimfiɗa wa bayinsa. An tattara bayanai ta hanyar sauraron waƙoƙin da tsamo misalan ɗiyan waƙoƙin da abin ya shafa, tare da ciro hukunce-hukuncen da suka yi bayani kansu daga Alƙur’ani da hadisan manzon Allah.

    Binciken ya fahimci cewa, akwai tarin misalan fanɗare wa addini a cikin waƙoƙin baka na Hausa. Daga ƙarshe an ba da shawarwarin da suka haɗa da ɗaukar matakan da suka dace domin tabbatar da ire-iren waƙoƙin ba su yi tasiri wajen gurɓata tarbiya nagartacciya ba.

    Fitilun Kalmomi: Waƙoƙi, Addini, Musulunci, Fanɗarewa

    GABATARWA

    Musulmi ba a bar shi kara zube ba. An kafa masa sharuɗɗan tafiyar da rayuwa dukkanta. Ire-iren waɗannan sharuɗɗan suna ƙunshe cikin littafin Allah (Alƙur’ani) da Hadisan Annabi S.A.W. Daga cikin dokokin akwai na tilas, wato abin da Musulmi mai hankali ba zai iya rabuwa da shi ba, komai tsanani.

    Akwai kuma abubuwan ƙi, wato waɗanda ba a so Musulmin ya aiwatar da su ba. Haka akwai haramun, waɗanda aka hana mutun ya aikata su. Idan dukkannin rayuwar mutum ta kasance cikin ɗa’a, kuma ya nisanci saɓo, babu shakka ya kiyaye dokokin Allah Maɗaukakin Sarki.

    A gefe guda kuwa, kamar yadda Chiromawa, (n.d. p. 5-10) ya bayyana, ko da addinin Musulunci ya iso ƙasar Hausa ya tarar da al’ummomi da dama suna aiwatar da kaɗe-kaɗe da waƙe-waƙe nau’i-nau’i da suka haɗa da:
    i. Kiɗan sana’a
    ii. Kiɗan jawo hankali
    iii. Kiɗan lallashi (rarrashi)
    iv. Kiɗan faɗakarwa

    v. Kiɗan zaburarwa
    vi. Kiɗan ƙarfafa zuciya
    vii. Kiɗan jaruntaka
    viii. Kiɗan farin ciki
    ix. Kiɗan ibada

    Duk ire-iren waɗannan kaɗe-kaɗe akan haɗa su ne da waƙe-waƙe. Kasancewar addinin Musulunci, addini ne mai sauƙi da sauƙaƙa wa mabiyansa, bai haramta waɗansu daga cikin nau’ukan kaɗe-kaɗe ba. Ya dai kawo gyare-gyare domin kare mutunci da martabar
    mabiyansa. Ya haramta shi ne yayin da aka aiwatar da abin da Allah ya haramta a cikinsa.

    Hasali ma akwai wuraren da Musulunci ya sunnanta kiɗa da waƙa, kamar a lokuttan ɗaura aure, tamkar yadda Imamu Buhari ya bayyana a “Babin Kaɗa Ganha” a ranar aure da walima. Bayan haka, akwai ranar kai amarya ɗakin mijinta, da ranar idi da ranar suna, da ranar zuwan wani shugaba da ranar komawarsa, da ranar kaciya (kugunu/kuidu).

    Akwai hadisai waɗanda Buhari da Muslim da Tirmizi da Hakimu da Nisa’i suka rawaito da ke nuni ga halaccin kiɗa da waƙa a babin aure da sallar idi. Halaccin kan tabbata ne matuƙar bai haɗa da alfasha ko motsawa zuwa ga saɓon Allah ba. A bisa wannan ne, maƙalar ta ƙuduri aniyar yin ƙwarya-ƙwaryar bincike a muhallan da makaɗan baka na
    Hausa suka keta ƙa’idojin da Allah ya shata ta hanyar kauce musu.

    Duk wasu ɗiyan waƙa da makaɗi ya yi za a yi ƙoƙarin kawo shi tare da auna shi da ma’aunin shari’a da aka ciro daga nassin Alƙur’ani da Hadisan Annabi S.A.W. domin tabbatar da hasashen. Ana iya samun ɗiyan waƙoƙin da ke ƙunshe da gurbin fanɗara a waƙoƙin makaɗan sarauta, da na jama’a da na maza da sauransu, kamar yadda za a gani ɗaya bayan ɗaya.

    Dabarun Gudanar Da Bincike

    Kadadar wannan bincike ta taƙaita ne ga waƙoƙin baka na Hausa a farfajiyar koyarwar addinin Musulunci. A ɓangaren waƙoƙin an ɗauko ɗiyan waƙoƙi da aka tattauna kansu kai tsaye ta hanyar sauraron odiyoodiyo da kallon bidiyoyinsu.

    A ɓangaren hukunce-hukuncen addinin Musulunci kuwa, an ɗauko su kai tsaye daga cikin Alƙur’ani mai tsarki da hadisan Manzon Allah (S.A.W.) ingantattu. An kuma nazarci rubuce-rubucen masana da manazarta a wannan fannin inda suka haska hanya ga binciken.

    Fanɗare wa Koyarwar Musulunci ta Hanyar Zambo

    Makaɗan saurauta sun shahara wajen yin zambo, domin ƙawata waƙoƙinsu. Masana da dama sun bayyana ma’anar zambo gwargwadon fahimtarsu. Gusau, (1984 p. 37) ya tafi kan cewa “Akan yi zambo don adanta waƙa da muzanta wanda ke hamayya da wanda ake yi wa waƙa.” Abba da Zulyadaini, (2000 p.63) sun bayyana zambo da cewa: “… nau’i ne na muzanta mutum ta hanyar ƙasƙantar da shi, ko wulaƙanta shi, domin a baƙanta masa tare da dusashe masa kwarjini a idon jama’a.

    Mawaƙan sun fi shahara da zambo don su aibanta duk wani ɗan sarki da ke ja da ubangidansu. Muhammad, (2005) kuwa na da ra’ayin cewa zambo zagi ne kai tsaye,
    … saboda akan ba da hoton wanda ake yi wa tare da bayyana cikakkiyar sifarsa ta hanyar ambaton duk wani abu da ya dace da shi. A lokacin da aka yi ma wani zambo akan fito da hotonsa ne zahiri, ta yadda duk wanda ya san shi zai gane cewa da shi ake. Muhammad, (2005 p. 28)

    A taƙaice kenan, zambo yana ƙunshe da ma’anar ƙaga wa mutun magana wadda za ta muzanta shi ta ɓata masa suna ba tare da bayyana wanda ake yi wa ba. A dubi misalin zambon da Alhaji Musa Ɗankwairo ya yi wa wani ɗan sarautar Tsafe:

    Kun san zamanin ga ya canza,
    Ga wani ɗan sarki da kandaye,
    Ya shaho hoda kamar Delu.
    (Ɗankwairo: Waƙar Sarkin Tsahe).

    Wannan zambon da Ɗankwairo ya yi wa ɗan sarki ya kai matuƙa wajen aibanta ɗan sarkin ta hanyar kamanta shi da ɗan daudu. Hakan ba ƙaramin muzantawa da dushe masa kima ya yi a idon al’umma ba. Tabbas kuwa hakan ya saɓa wa dokokin addinin Musulunci. An umurci Musulmi da ya tsare (kame) harshensa da yin furucin abin da bai halatta ba, kamar keta mutuncin ɗan uwansa Musulmi ba tare da wani abu mai wajabtawa ba na shari’a. Allah na cewa:

    Lalle Allah na yin umurni da adalci da kyautatawa, da ba wa ma’abocin zumunta kuma yana hani da alfasha da abin ƙi da zalunci. Allah yana yi muku gargaɗi ko da kuna tunawa. (Surar Nahli: 16:90).

    Idan aka dubi wannan ayar za a tarar ta yi hani ga yi wa wani mugun baki (mugun fata), sannan ta yi hani ga alfasha. Ya kuma yi umurni da tausayawa tare da yin abu bisa gaskiya. Daga ƙarshe ta yi hani a kan ha’intar wani ta kowane ɓangare. Wannan na iya
    kasancewa ta hanyar lafazi ko a aikace. Ta la’akari da wannan ɗiyar waƙar, za a tarar mawaƙin ya kauce wa dokar da Allah ya ɗora masa.

    Annabi S.A.W. Ya Ce: Haƙiƙa, mafi sharrin mutane a matsayi wurin Allah a ranar alƙiyama shi ne wanda mutane suka ƙyale shi don ƙiyayyar alfasharsa. (Muslim ya ruwaito). Wanda duk wani mawaƙi ya yi wa zambo, to zai guje shi tare da yin kaffa-kaffa da al’amarinsa.

    Sau da yawa akan ba su kyauta ne bisa tilas don gudun zambonsu. A irin wannan yanayin idan aka nazarci hadisin, za a ga a nan ma sun kauce wa koyarwar Annabi
    S.A.W. A wani Hadisin kuwa Annabi (SAW) cewa ya yi: “Mumini bai kasancewa mai yawan suka ba ko yawan la’anta ko yawan alfasha, ko mai sakin harshe” (Tirmizi
    ne ya ruwaito shi).

    Wannan hadisin ya fito ƙarara ya bayyana mana cewa, duk mawaƙin da ya ba da gaskiya
    ga Allah da ranar lahira da manzancin Annabi S.A.W., zai kasance mai bin dokokin Musulunci kamar yadda suke. Hakan kuwa zai sanya ya guji yi wa Musulmi zambo.
    Akwai misalan wuraren da makaɗan jama’a suka yi wa abokan hamayyarsu zambo ta hanyar zagi kai tsaye.

    A irin wannan lamari ne mawaƙin jama’a kan fito da halayen mutun a fili, sannan ya zage shi. Misali, a waƙar “Gagara Badau,” Alhaji Mamman Shata cewa ya
    yi:
    Shata: Allah ya tsine ma tsohon mazinaci,
    Amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    Shata: Allah ya tsine ma da kai da iyalinka.
    Amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    Shata: Yanzu babban ɗan bai gani,
    Amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    Shata: Babban jikanshi kuma yana kama agwaginmu,
    Amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    Shata: Gida ya lalace.
    Amshi: Gagara badau namiji tsayayyen ɗan kasuwa.

    Dubi yadda Shata yake zagin wani basarake tare da nuna ɗansa ya makance, ya kuma kira jikansa ɓarawon agwagi. Wannan ba ƙaramar fanɗarewa ba ce, domin a shara’ar Musulunci an umurci Musulmi da ya kiyaye da yin zance da bai halatta ba, kamar ƙarya, da zage-zage da keta mutunci Musulmi. Allah na cewa: “…Kuma yana hani da alfasha da abin ƙi da zalunci. Allah yana muku gargaɗi ko da kuna tunatuwa.” (Alƙur’ani,
    Suratul Nahl, 16:90).

    Fanɗare Wa Koyarwar Musulunci Ta Hanyar Habaici

    Habaici ko gugar zana salo ne ko azancin yi da wani a kaikaice ta yadda sai wanda ya san shi kuma ya san abin da ake magana game da shi ne kaɗai zai iya ganewa. Habaici wata hanya ce da makaɗan baka suke amfani da shi a cikin waƙoƙinsu domin ƙara musu
    armashi, ta hanyar ƙasƙantar da wani mutun ko kuma muzanta shi ko su zage shi ko kuma su soka masa wata magana a kaikaice. Misali, a cikin waƙar Mai Dubun
    Nasara Sardauna, Alhaji Musa Ɗankwairo yana cewa:

    Ga kare ga kura kowane ya hangi wani,
    Ga aura ya koma,
    Wagga nan hanya ba mu ga wurin wali ba.
    (Alhaji Musa Ɗankwairo, Waƙar Mai Dubun Nasara, ta Sardauna).

    Yayin da aka dubi ɗiyar wannan waƙar za a ga yadda Ɗankwairo ya siffanta Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato da kura. Ya yi hakan ne domin bayyana irin ƙarfinsa kamar yadda kura ke da shi. Wannan kuwa ya shafi yadda take iya tauna ƙashi da kuma kwarjini da waibuwarta na sanya rashin kuzari ga halittar da ta tunkare ta.

    A gefe guda kuwa, sai ya kira wanda yake yi wa habaici da kare, saboda ba sa zama
    inuwa ɗaya da kura. Hasali ma kare ba ya hangen nesa sosai, kuma mai gidansa yakan yi amfani da shi ne wajen farauta. Kiran mutun kare ba ƙaramin ƙasƙantarwa ba ne
    a al’adance. Wannan ne ya sa makaɗan baka sukan siffanta waɗanda suke son wulaƙantawa da kare saboda nhalayyarsa da ɗabi’unsa.

    Musulunci ya hana keta mutuncin Musulmi ko wulaƙanta shi ko zagin sa ko laƙa masa munanan sunaye, ba tare da haƙƙin shara’a ba. Allah na cewa: “… kuma kada ku jefi juna da miyagun sunaye” (Alƙur’ani, 49:11). Idan muka dubi wannan ayar, za mu ga cewa ta hana a kira Musulmi da sunan da zai kasance tamkar zagi ne gare shi. Yin haka kuma fanɗare wa umurnin Ubangiji ne.

    Annabi S.A.W. ya ce: “Zagin Musulmi fasiƙanci ne, kuma yaƙar sa kafirci ne” (Buhari da Muslim ne suka ruwaito shi). Idan aka dubi wannan hadisin cikinsa da
    wajensa, aka kuma nazarci ɗiyar waƙar da ta gabata, za a tarar cewa, makaɗin ya kauce wa faɗar Annabin S.A.W., ya yi gaban kansa. Yin haka fanɗarewa ne ga dokokin addinin Musulunci.

    Bin dokoki da ƙa’idojin Musulunci kuwa dole ne, inda har Allah ke cewa: “Kuma abin da Manzo ya zo muku da shi, to ku riƙe shi, kuma abin da ya hane ku, to ku hanu” (Surah Al-hashr, 59:9).

    Fito-Na-Fito Da Koyarwar Muslunci

    Akwai misalan inda mawaƙa ke amfani da wasu kalmomin da suka kauce wa ƙa’idojin addinin Musulunci. Akan samu irin wannan fito-na-fito a fannonin da suka shafi sahihan aƙidojin da suka danganci ranar lahira, da matsayin mala’ikun Allah da makamantansu. Ya kuma haɗa da dokoki da ƙa’idojin addinin Musulunci ta fuskar hani da horo. Wannan
    ɓangare na aikin zai mayar da hankali wajen zaƙule irei-ren waɗannan misalai:

    Izgilanci

    Izgilanci ga abubuwan da addini ya zo da su nanuni ga halin ko-oho ga lamarin addinin. Musulunci kansa ya tsawatar da riƙo da dokokin da ke ƙunshe cikinsa ba tare da wargi (wasa) ba. Duk da haka, akan samu wuraren da mawaƙa suka yi izgilanci ga lamarin
    addini. Alhaji Muhammadu Ɗan’anace a waƙar Shago yana cewa:

    Jagora: In da lahira ana kasa dambe…
    ‘Y/Amsohi: Da Walakiri ya ji ƙwal ga gaba nai.
    Jagora: Duk wanda bai yi kallon Shago ba,
    Aradu yana da sauran kallo,
    Ya zaka duniya kamar bai zo ba,
    Kamar zuwan kare ga aboki,
    Tamkar mutum ya mari budurwa,
    Ko ya mutu ba a gafarta mai.

    In aka dubi wannan ɗan waƙar, za a tarar cewa, wannan makaɗin ba ƙaramar kasada ya yi ba. Ya nuna rashin jin tsoron aukawar wani haɗari (hatsari) ko shiga cikin abin da bai san sakamakonsa ba. Allah na cewa: “Kuma kada ka bi abin da ba ka da ilimi a kansa.” (Surar Isra’i, 17:36).

    Idan muka nazarci wannan ayar, za a ga yadda Mahaliccin sammai da ƙassai ya faɗakar da masu imani da su yi kaffa-kaffa ga dukkan lamarin da ba su san haƙiƙanin yadda yake ba. Ko bayan batu kan abin da mutum bai sani ba, batutuwan da ke ƙunshe cikin ɗiyar
    waƙar na tattare da izgilanci ga abin da ya shafi imani da mala’iku da ranar ƙiyama.

    Goyon Bayan Karuwanci

    Kalmar karuwa, suna ne na mace. Jam’i kuwa shi ne karuwai. Karuwa na nufin mace mai zaman kanta wadda mazan banza ke neman ta su ba ta kuɗi domin saduwa (zina) da ita. Zina kuwa tana nufin saduwa (jima’i) da matar da ba ta halatta ga mutum ba ta hanyar aure, wato wadda ba matarsa ba. Tun kafin bayyanar Musulunci a farfajiyar
    ƙasar Hausa, Bahaushe ya ƙyamanci zina.

    Don haka karuwanci bai samu bagiren zama ba, balle a yi zina. Duk da kasancewar akwai al’adar tsarance, a inda saurayi kan gayyaci budurwarsa ta je ɗakinsa har ma ta kwana. Sakamakon irin wannan al’adar ce, ya sanya su amfani da al’adun tsafi domin tabbatar da amarya ba ta taɓa sanin wani ɗa namiji ba (zina) kafin a yi mata aure. A irin
    wannan al’adar ce, idan yarinya ta san maza kafin a yi mata aure, za ta kunyata a cikin jama’a.

    Idan kuma ta ɓoye ba ta faɗa ba, ta mutu, kamar yadda Ibrahim, (1985 p. 5) ya nuna.
    Yayin da addinin Musulunci ya bayyana, sai ya haramta zina. Hasali ma ya sanya ta cikin manyan laifuka, bayan kafirci, wato haɗa Allah da wani da kashe ɗan Adam. Allah yana cewa: “Kuma kada ku kusanci zina, lalle ne ita ta kasance alfasha ce kuma ta munana ga zama hanya” (Alƙur’ani; Suratul Isra’i, 17:32)

    Haka kuma Musulunci ya yi ƙoƙarin toshe duk wata kafa da za ta iya zama sanadin aikata zina ta hanyar wajabta wa mata sanya hijabi. Sanya hukuncin jefe mazinaci da mazinaciya har su mutu a bainar jama’a, idan sun yi aure, ko a yi musu bulala idan ba su taɓa yin aure ba, na nuni da girman zunubin. Duk da wannan umarni na Ubangijin talikai da kuma uƙubar da aka tanadar wa mazinata, sai aka sami wani mawaƙi da ake kira Habibu Sakarci ya yi wa wata karuwa waƙa.

    A cikin ɗiyan waƙar yana cewa:
    Jagora: Shehuwar mata Safiya Kano, Ta gidan ‘Yajja
    Safiya Kano.
    Jagora: ‘Yan birni roƙo suke, Allah ba mu jaka bakwai,
    Mu gano ɗakin Safiya Kano.
    Jagora: Direbobi ma roƙo suke, Allah ba mu jaka
    bakwai, Mu gano ɗakin Safiya Kano.
    Jagora: Mutan birni yanga suke, Domin darajar Safiya
    Kano.

    Yayin da aka nazarci ɗiyan waƙar, za a ga cewa Habibu Sakarci yana tallar wannan karuwa ta hanyar bayyana ta a matsayin ƙasaitacciyar karuwa. Har ma ya nuna ‘yan birni da dirobobi na burin Allah ya ba su kuɗi masu yawa, don su tafi ɗakinta. Hasali ma ya bayyana ta fi sauran karuwan birnin kyau. Wannan ba ƙaramar fanɗara ba ce da keta dokokin Allah.

    Ya zo cikin hadisi
    Annabi S.A.W. yana cewa: Lalle ana rubuta wa ɗan’adam rabonsa daga
    zina, kuma lalle mai risker sa wancananka ne babu makawa. Idanu zinarsu ita ce kallo, kunnuwa kuwa zinarsu ita ce sauraro, harshe kuwa zinarsa ita ce zance. Hannuwa kuma zinarsu ita ce damƙa, ƙafa kuma zinarta ita ce taku, zuciya kuwa saƙa soye-soyenta ne, kuma tana guranta su, farji yana gaskata wancananka ko ya ƙaryata (Buhari da Muslimu ne suka ruwaito hadisin).

    Duk da irin waɗannan nassoshin Alƙur’ani da hadisan Annabi S.A.W., sai ga ya makaɗa na fanɗare musu ta hanyar gayyatar al’umma zuwa ga aikata fasiƙanci. Shi ma Alhaji Mamman Shata ya yi makamanciyar wannan waƙar, a inda ya yi wa wata mata da ake kira Karo Oma:
    Jagora: Duk ɗan birnin da ya riƙa,
    Ni kar ya yi mini yanga,
    In yana so ya isa
    In gan shi gidan Kara Oma.
    (Alhaji Dakta Mamman Shata: Waƙar Kara Oma)

    A nan Shata ya fito ƙarara ya tura ‘yan birni su tafi gidan wannan karuwa idan har sun isa. A ɗaya ɓangaren kuwa cicciɓa ta ya yi da cewa, sai manyan mutane wayayyu ne kawai suka isa su yi hulɗa da ita. Wannan waƙar ba abin da ya raba ta da fanɗare wa
    dokokin Allah da ya shata wa Musulmi.

    A shara’ar Musulunci, an san Musulmi da kunya. Hasali ma kunya tana cikin halayensa, kuma tana daga cikin Imani. Imani kuwa shi ne aƙida da rayuwar Musulmi. Manzon Allah yana cewa: “Kunya da imani suna zozozo da juna. Idan babu ɗayansu, ɗayan ma ba za
    a same shi ba” (Buhari da Muslim ne suka ruwaito shi).

    Goyon Bayan Shan Giya

    Giya, kalmar suna ce da ke cikin jerin sunaye jinsin mata. Ita kuma nau’i ce da ake yi da hatsi ko alkama ko inibi wadda ake sha a yi maye. Ana kuma kiranta barasa, kamar yadda ƙamusan CNHN (2006 p.168) ya nuna. Shan giya a tsakanin al’ummar Larabawa kafin bayyanar Musulunci abu ne sananne. Shi ne ƙashin bayan doron ginin tattalin arzikinsu, kuma giya na daga cikin kayan fataucinsu.

    Har matansu sun kasance shahararru wajen haɗa ta. Hasali ma kowane gida akan
    same ta. Wannan ya sa har suna yabon giya a cikin waƙoƙinsu. Su ma al’ummar Hausawa ba a bar su a baya ba, domin sun mayar da shan giya musamman a lokuttan
    bukukuwan aure da na haihuwa tamkar ƙawa. Yayin da suka samu rabauta na karɓar addinin Musulunci, sai suka guje ta a sakamakon hanin da addinin ya yi gare su.

    Kasancewar Musulunci addini ne mai sauƙi da ke ƙunshe da dabarun magance abubuwan da ke haifar da fitsara da ta’addanci a tsakanin al’umma, sai ya fara bayyana wa muminai rashin kyanta. Daga nan kuma ya hana kusantar wurin ibada yayin da aka sha ta Daga ƙarshe ne kuma ya sauƙar da hani kai tsaye game da shan giya inda aka ce:
    “Ya ku waɗanda suka yi imani, ku sani cewa, giya da caca da gumaka da ƙyaurayen duba ƙazanta ne daga aikin shaiɗan, sai ku nisance su don ku rabauta
    (Alƙur’ani; 5:90).

    A wannan ayar an bayyana wa masu imani munanan ayyuka da ake buƙatar mumini ya nisance su. Kuma duk al’ummar da ta rungume su za ta faɗa cikin masifa da rashin kwanciyar hankali. Ayar ce kuma ta zo da haramcin shan giya kai tsaye. Akwai hadisai da dama da suka tabbatar da haramcin shan giya da kuma abin da ake kira da giya.
    Annabi S.A.W. yana cewa: “Duk abin da ke bugarwa giya ce, kuma kowace irin giya haramun ce” (Muslim ne ya ruwaito shi).

    A Wani Hadisin Kuwa Cewa Ya Yi: Allah ya tsine wa giya, masu shan ta, da waɗanda suka zuba ta, da waɗanda suka sai da ita, da waɗanda suka saye ta, da waɗanda suka tatso ta, da waɗanda suka ɗauki kayan da ake tatsarta, da waɗanda suke ɗauke ta, da waɗanda aka kai wa ita, da waɗanda suka samu kuɗi a gare ta” (Abu Dawuda, da Al-Hakem a isnadi ingantacce, suka kawo shi)

    Yayin da aka dubi waɗannan nassoshi, za a tarar cewa, ƙin bin su sau-da-ƙafa keta shara’ar Musulunci ne, wato fanɗarewa faɗar Allah da annabinsa ne. Duk da haka, an ci karo da waƙoƙin da suka yi kira da a sha gida. Alhaji Mamman Shata Katsina ya waƙe giya. Har ma cewa ya yi:

    Jagora: Ka ji karatun masu bugun ruwa, Waɗanda…
    ‘Y/Amshi: Ke zikiri a Kuloniya, A sha ruwa ba laihi ba ne.
    Jagora: A nan muke sallarmu ta Juma’a, Mu tattara kayanmu mu kai Neja, Ku sha ruwan nan…

    Y/Amshi: Ba laihi ba ne, A sha ruwa ba laihi ba ne.
    Jagora: Ruwa na kwalba ba laihi ba ne, Ai kun ga…
    ‘Y/Amshi: Alhaji Shata sha yake. A sha ruwa ba laihi ba ne.
    Jagora: Yara mu koma wasa Kuloniya, Mu tashi kana
    mu koma Neja,
    ‘Y/Amshi: Nan ne muke zikirinmu na Juma’a. A sha
    ruwa ba laihi ba ne.
    Jagora: Malam ka sha ai ba laihi ba ne, Ga taka ga tau…
    ‘Y/Amshi: Kowa ya aje. A sha ruwa ba laihi ba ne.

    Idan muka nazarci waɗannan ɗiyan waƙar za a ga yadda mawaƙin ya yi fito-na-fito da dokokin Allah da Manzonsa. Allah ya haramta, shi kuma ya halatta. Dubi yadda mawaƙin ya ce a sha giya ba laifi ba ne, bayan Annabi S.A.W. ya ce kada a sha, a inda yake cewa:
    “Kada ku haɗa fulawa da dabino gaba ɗaya, kuma kada ku haɗa busasshen tafarnuwa da dabino sam-sam, ku bar su idan an niƙa su.”

    Yayin da aka niƙa su, nan take suna bugar da wanda ya sha su. Don haka ne Annabi ya umarci masu imani da kada su sha a haɗe yayin da suke niƙe, kamar yadda Munhajul Muslimu Jadawali na uku: Abinci da Abinsha ya nuna. Hasali ma mawaƙin ya bayyana cewa shi ma yana shan giyar tare da yaransa. Akwai hadisai da dama da suka nuna haɗarin Musulmi ya mutu yana shan giya, ko da bai halatta ta ba.

    To ina ga wanda ya halatta shan ta? Daga cikin ire-iren waɗannan hadisai akwai wanda
    Ibni Abbas ya ce: Manzon Allah S.A.W. ya ce: Duk wanda ya mutu yana cikin ɗabi’ar shan giya bai tuba ba, zai tarar da Ubangiji Allah Maɗaukakin Sarki tamkar wanda ya bauta wa gumaka (Muslim ne ya ruwaito wannan hadisin).
    A wata waƙar ta mawaƙin da ake kira Horo/Horu, an ga baitukan da suka nuna ba laifi ba ne shan giya da ma cin mushe. Mawaƙin na cewa:

    Jagora: Arnaaa ku sha giya ku ci mushe, Aljanna mai rabo zai sama.

    A wani wuri kuwa, har ya nuna ma kashi ne ga mutum ya sha giya ‘yar kaɗan kuma ta wahalshe shi. Yana cewa:

    Jagora: Kowa ya sha giya yai yi amai, Ba ɗan halas ba ne, shege ne!
    Jagora: Su wane ‘yan giyan ƙarya ne, Shegu, kwalba guda take ka da su.

    Don karanta Tarihin Garin Rimin Gado danna nan

    Goyon Bayan Sata

    Abubakar (2015, p. 431) ya bayyana cewa, sata “tana nufin ɗaukar abin wani ba da saninsa ko izinin ba. ”Sata na nufin ɗaukar wani abu da hukuncin shari’a ko hankalin tuwo bai mallaka wa wanda ya ɗauka ba, tare da amfani da shi ko musanyensa da wani abu mai daraja kwatankwacin na kuɗi ko kuma mai amfanarwa, ba tare da izinin wanda ko waɗanda ke da mallakin abun ba.

    Sata ta kasu zuwa nau’uka daban-daban. Sun fi danganta da salon yadda aka gudanar da satan. Fitattu daga cikinsu sun haɗa da:
    i. Cuta
    ii. Damfara
    iii. Fashi
    iv. Fizge/Wabce/Fauce
    v. Ƙwace
    vi. Sane

    Sata babbar abar ƙyama ce a farfajiyar Hausa da Hausawa, tun ma kafin bayyanar addinin Musulunci. Sauyawan al’amurra da cuɗanyar Hausawa da baƙin al’ummu sun wanzar da taɓarɓarewar tarbiyya da ƙoƙarin neman tara abin duniya ido rufe. Ta kai ga
    fanɗararru marasa kishin kansu cikin al’umma sun tsunduma a fagen wannan ta’addanci.
    Yayin da addinin Musulunci ya bayyana a ƙasar Hausa, sai ya ƙara ƙarfafa wa Hausawa ƙyamar wannan muguwar sana’a.

    Musulunci ya zo da dokoki domin kawar da duk nau’o’in sata. Allah na cewa:
    Ɓarawo kuma da ɓarauniya sai ku yanke hannayensu ya zama sakamako ne na abin da suka aikata, (wannan horo ne) daga Allah. Allah kuwa mabuwayi ne Gwani. (Alƙur’ani, 5:38). A addinin Musulunci ta kowace fuska ana ƙoƙarin kare dukkanin al’umma ta yadda za a zauna cikin aminci game da dukiyoyi da rayukan al’umma.

    Ita kuwa sata, mugun hali ce da ke haifar da rashin kwanciyar hankali da salwantar rayuwa a tsakanin al’umma. Don haka ne shari’a ta tanadar da hukuncin yanke hannun
    ɓarawo wanda zai hana watsuwar irin wannan muguwar ta’asa a tsakanin al’umma [14]. Allah na cewa: “Kuma kada ku ci dukiyoyinku a tsakaninku ta hanyar cuta ”(Alƙur’ani, 2: 188).

    Ayar tana tabbatar wa masu imani cewa, cuta haram ce. Ba ya halatta ga Musulmi ya yi zalunci ta hanyar zaƙin baki ko dabara. Haka kuma, bai halatta ya yi jagora don a cuci wani ba. Duk da irin waɗannan dokokin da Allah Maɗaukakin Sarki ya shimfiɗa domin samar da kyakkyawan zamantakewa da aminci a doron ƙasa, an samu gungun mawaƙa da ke jayayya da dokokin cikin lafuzzan waƙoƙinsu.

    Bunza, (2014) ya kawo baituka da dama daga bakin Alhaji Muhammadu Gambo Fagada.
    Gambo ya bayyana ƙarara cewa:
    Jagora: Don Waɗanda ka sata nay yi ganga, Ba do wani sarki mai naɗi ba.
    (Alhaji Muhammadu Gambo Fagada: Tsoho Tudu)
    A cikin waƙarsa ta Nazaƙi kuwa, an ga yadda hirarsu ta gudana da Nazaƙi bayan ya tuba daga sata.

    Sannu a hankali har Gambo ya sake zuga shi yadda har sai da ya dawo satan. Gambon da kansa ya bayyana cewa:
    Ɓarawo in ina kusa ba tuba yakai ba,
    Ko ya aje gemu, ko ya yi saje,
    Ko ya fidda farin gashi ga kaina,
    In Gambo na kusa ba tuba yakai ba,
    Ba ko batun shegantaka ba.
    (Alhaji Muhammadu Gambo Fagada: Waƙar Nazaƙi)

    A wannan ɗiyan waƙa, sai da ya jaddada cewa, batunsa ba “batun shegantaka” ba ce kawai. Wato dai haƙiƙanin gaskiya yake faɗa cewa idan yana kusa ɓarawo ba ya tuba domin kuwa zai ziga shi ya hana shi tuban. Wasu makaɗan sukan yi waƙoƙin yabo ne ga
    ɓarayin. Misali Alhaji Mamman Shata ya yi wa wani ɓarawo mai suna Mamman Ɗan’yarbayye waƙa, a inda yake cewa:

    Jagora: Mai hannun taɓa ƙofa in an bacci,
    Masu samame baƙon Ɗanmani.
    Na faɗa maka Mamman.
    In dai ka ɗauko sa’a,
    Har ka buɗe ƙofa,
    Ka tarar an bacci,
    To zari akwati tsakiyar shi ya fi kaya.
    Na saman hoto ne,
    Na ƙasan maganin ƙwari ne.
    Tafi zari akwatin tsakiyar shi ya fi kaya.
    Na Abdu ƙyale dangi sai an bacci,
    Iyalin Mamman, waɗanda ba su so a yi haske,
    Su sun fi so a tabka duhu da ruwa yaf-yaf-yaf.
    Wani don ya taka kara bai mai ƙara ba,
    Sannan ganyen ganji duk ya bi ƙasa.
    (Alhaji Dakta Mamman Shata: Mamman
    Ɗan’yarbayye)

    A waɗannan ɗiyan waƙar, mawaƙin ya yabi ɓarawon tare da ba shi shawarar yadda zai gudanar da sana’arsa ta sata. Wannan ya haɗa da yi masa ishara ga irin lokuta da yanayi da dabarun da zai bi wajen yin satar, da kuma nau’in abin da zai sata da ya fi saura daraja.

    Hakan kuwa karan-tsaye ne ga dokokin addini. Hadisin Manzo (S.A.W.) ya bayyana cewa: “Ɓarawo ba ya sata a lokacin da yake da imani” (Buhari ne ya ruwaito
    hadisin). Allah Maɗaukakin Sarki ya kawo nau’in hukuncin da ya dace a zartar wa masu fashi da makami, a inda yake cewa:

    Ba wani abu ne sakamakon waɗanda suka yi wa (Musulmi masu bin) Allah da manzonsa fashi ba, kuma suke tafiya a bayan ƙasa da ɓarna ba, sai kawai a kashe su ko kuma a tsire su ko a yanke hannayensu da ƙafafuwansu a tarnaƙe, ko kuma a kore su daga ƙasa. (Yin) wancan ƙasƙanci ne a gare su a duniya, a lahira kuma suna da azaba mai girma. (Alƙur’ani, 5:33).

    Allah ya bayyana mana cewa masu yin fashi da makami suna ƙoƙarin ɓata tsarin Allah da Manzonsa ne, saboda aiwatar da fashi ya kauce wa hanyar gaskiya da adalci, waɗanda Musulunci ke ƙoƙarin tabbatar da su a doron ƙasa. 3.5 Goyon Bayan Kisan Kai Kisan kai na daga cikin manyan zunubai masu matuƙar muni a Musulunci. A cikin Suratul Nisa’i, Allah na cewa:

    Wanda kuma ya kashe mumini da gangan, to Jahannama ce sakamakonsa, yana madawwamini a cikinta, kuma Allah ya yi fushi da shi, ya kuma tsine masa, kuma ya
    tanadi azaba mai girma a gare shi (Alƙur’ani, 4:93).

    An jiyo Makaɗa Muhammadu Bawa Ɗan’anace ‘Yar Tsakkuwa, Gandi, Sakkwato yana ziga fitaccen ɗan damben nan Shago domin ya yi kisa. A cikin Bakandamiyar Shago, yana cewa:
    Bayarwa: Yanzu inai maka kuka,
    Ba kukan tuwo ba, Ba na hura ba…
    ‘Y/Amshi: Kukan Ɓaleri ya raga bayi, Suna kirarin banza.
    Bayarwa: Ɗan Abdu ko ga girbin
    ‘Y/Amshi: Gero, bara-bara ta na hana wake….
    A wani wuri yana cewa:
    Bayarwa: Ɗan Abdu kashe mutum a gafarta ma. Ɗan Abdu…
    ‘Y/Amshi: Kashe mutum a gafarta ma.
    (Muhammadu Bawa Ɗan’anace: Bakandamiyar Shago)

    Ba za a ce maganar kisa a nan ta taƙaita ga buge mutum a dambe ba kawai. Ya haɗa da kashewa har lahira. Hakan zai ƙara tabbata yayin da aka yi la’akari da lafuzza da ya riƙa amfani da su cikin waƙar da suka haɗa da:
    i. Kusheyi
    ii. Lahira a kai miki gawa
    iii. Lahira tana yin baƙo
    iv. Uwar mutum ta haifi wani, da sauransu.

    Gambo ma ya yi makamanciyar zigar nan inda yake ziga inda yake cewa:
    Bayarwa: Duw wanda ya ishe mai kuɗi lahiya lau,
    Ya yi sata yab bar mai kuɗi da rai nai,
    In yaz zaka Allah ya isam min za ni ce mai,
    Don wagga ba sata ta ba Gambo.
    (Alhaji Muhammadu Gambo Fagada: Waƙar Kashe Mace)

    A nan, ko bayan ziga zuwa ga yin sata, mawaƙin ya nuna cewa satar ba ta cika har sai an yi kisan kai. Wannan kuwa fanɗarewa ne daga koyarwar addinin Musulunci.

    Goyon Bayan Kisan Kai

    Kisan kai na daga cikin manyan zunubai masu matuƙar muni a Musulunci. A cikin Suratul Nisa’i, Allah na cewa: Wanda kuma ya kashe mumini da gangan, to Jahannama ce sakamakonsa, yana madawwamini a cikinta, kuma Allah ya yi fushi da shi, ya kuma tsine masa, kuma ya tanadi azaba mai girma a gare shi (Alƙur’ani, 4:93).

    An jiyo Makaɗa Muhammadu Bawa Ɗan’anace ‘Yar Tsakkuwa, Gandi, Sakkwato yana ziga fitaccen ɗan damben nan Shago domin ya yi kisa. A cikin Bakandamiyar Shago, yana cewa:
    Bayarwa: Yanzu inai maka kuka,
    Ba kukan tuwo ba, Ba na hura ba…
    ‘Y/Amshi: Kukan Ɓaleri ya raga bayi, Suna kirarin banza.
    Bayarwa: Ɗan Abdu ko ga girbin
    ‘Y/Amshi: Gero, bara-bara ta na hana wake….

    A wani wuri yana cewa:
    Bayarwa: Ɗan Abdu kashe mutum a gafarta ma. Ɗan
    Abdu…
    ‘Y/Amshi: Kashe mutum a gafarta ma.
    (Muhammadu Bawa Ɗan’anace: Bakandamiyar Shago)

    Ba za a ce maganar kisa a nan ta taƙaita ga buge mutum a dambe ba kawai. Ya haɗa da kashewa har lahira. Hakan zai ƙara tabbata yayin da aka yi la’akari da lafuzza da ya riƙa amfani da su cikin waƙar da suka haɗa da:
    i. Kusheyi
    ii. Lahira a kai miki gawa
    iii. Lahira tana yin baƙo
    iv. Uwar mutum ta haifi wani, da sauransu.

    Gambo ma ya yi makamanciyar zigar nan inda yake ziga inda yake cewa:
    Bayarwa: Duw wanda ya ishe mai kuɗi lahiya lau,
    Ya yi sata yab bar mai kuɗi da rai nai,
    In yaz zaka Allah ya isam min za ni ce mai,
    Don wagga ba sata ta ba Gambo.
    (Alhaji Muhammadu Gambo Fagada: Waƙar Kashe Mace)

    A nan, ko bayan ziga zuwa ga yin sata, mawaƙin ya nuna cewa satar ba ta cika har sai an yi kisan kai. Wannan kuwa fanɗarewa ne daga koyarwar addinin Musulunci.

    Hani Ga Bautar Ubangiji

    Ko bayan kira zuwa ga aikata ɓarna da fasadi, akwai misalan ɗiyan waƙoƙi kuma da ke kira ga barin bautar Ubangiji. Na biyu a cikin shika-shikan Musulunci ita ce salla. Tana da matuƙar muhimmancin da har ya kasance kadarko tsakanin mutum da kuma shirka da
    kafirci. Duk da haka, sai ga ɗiyan waƙa da ke hani ga yin salla:

    Bayarwa: Ɗan Abdu ban da sallas swahe,
    ‘Y/Amshi: Domin yawan sallan nan yana rage maka ƙarhi.
    (Muhammadu Bawa Ɗan’anace: Bakandamiyar Shago)

    Sakamakon Bincike

    Ta la’akari da nassoshin Alƙur’ani da Hadisan Annabi S.A.W. da kuma ƙumshiyar wasu waƙoƙin baka na makaɗan Hausa, za a a iya cewa, mawaƙa na wuce gona da iri a waɗansu lokuta. Yawanci hakann na faruwa ne yayin da suka yi ƙoƙarin adanta waƙoƙin nasu domin burge wanda aka yi wa waƙar da kuma sauran masu nsauraro.

    A haka ake samu ɗiyan waƙoƙin sun yi wa dokokin Musulunci karan-tsaye. A wannan nazarin an fahimci cewa duk wani aikin da ɗan’adam ya aikata wanda Allah da manzonsa
    suka yi hani da shi, yin haka nau’i ne na fanɗare wa dokokin Allah. Ya zama tilas kowane Musulmi ya nemi ilimin duk wani lamarin da ya shafi rayuwarsa, (kamar yadda mai Ahalari ya bayyana) don gudun auka wa fushin Ubangiji.

    An kuma fahimci cewa, a Musulunci kowane irin al’amari an ɗora shi a kan mataki-mataki. Wannan ne ya wajabta wa kowane Musulmi ya yi umurni da aikata alheri da kuma hani ga mummunan aiki gwargwadon ƙarfin ikon mutun.

    Kammalawa

    Yin fice da waƙoƙi suka yi wurin ilimantarwa da faɗakarwa da nishaɗantarwa, ba shi ke nuna ba a samun fanɗarewa a cikinsu ba. Nau’ukan fanɗarewa da ake samu cikin waƙoƙin Hausa sun shafi ziga zuwa aikata abin da Ubangiji ya hana, ko izgilanci ga
    abubuwan da Musulunci ya zo da su, ko kuma hani ga abin da Ubangiji ya yi umarni da a aikata.

    Abu ne mai kyau manazarta su riƙa zaƙulo ire-iren fanɗarewa da ake samu a cikin waƙoƙi domin faɗakar da al’umma da su kansu mawaƙan. Malamai da ke jagorantar nazarcenazarcen waƙoƙi a makarantu kuwa, ya kamata su mayar da hankali wajen yin shiri na musamman na faɗakar da ɗalibai ta fuskokin da suka dace yayin da aka ci karo da ire-iren baitukan fanɗarewa a cikin waƙoƙin da suke nazarta.

    Gwamnatoci da hukumomin da abin ya shafa ma na da rawar takawa wajen samar da ƙa’idoji da tsaretsaren tace waƙoƙi kafin sakinsu. Haɗakar waɗannan za su tabbatar da al’umma ba ta rinjayu da kiraye-kirayen waƙoƙin fanɗara ba zuwa taɓewa.

    MANAZARTA

    • Abba, M., & da Zulyadaini, B. (2000). Nazari kan
    waƙar baka ta Hausa. Gaskiya Corporation Limited.
    • Abubakar, A. (2015). Ƙamusun Harshen Hausa.
    Zaria: Northern Nigeria Publishing Company LTD.
    • Al-Munajjid, M. S. (2004). Muharramat: Forbidden
    matters same people take lightly. International
    Islamic Publishing House, Saudi Arebia.
    • Bunza, A. M. (2014). In ba ka san gari ba saurari
    daka: Muryar nazari cikin tafashen Gambo Elkods
    Printing Hausa.
    • Chiromawa, U. A. U. (n.d.). Dalilin kiɗa a cikin
    Alƙur’ani da hadisi.
    • Gusau, S. M. (1984). Nazarin zaɓaɓɓun waƙoƙin
    makaɗan baka na Hausa, littafe na ɗaya.
    • Ibrahim, M. S. (1983). Kowa ya sha kiɗa. Longman
    Nigeria Limited.
    • Magaji, A. (2016). Kassu Zurmi da waƙoƙinsa.
    Spectrum Books Limited.
    • Muhammad, Y. M. (2005). Adabin Hausa. Ahmadu
    Bello University Press Limited.
    • Sani, A. U., & Jaja, M. B. (2019). Zamani Riga:
    Akalar Magungunan Gargajiya a Hannu Addini da
    Zamani. In The Nasarawa Journal of Humanities, 7,
    (1-2), 257-268. ISSN: 1118-6887.
    • Shehu, M., & Sani, A. U. (2019). Intra-Religious
    Conflicts within the Hausa Hausa-folk. In EAS
    Journal of Humanities and Cultural Studies, 1(3),
    145-150. ISSN: 2663-0958 (Print) & ISSN: 2663-
    6743 (Online) Available at:
    https://www.easpublisher.com/get-articles/344.
    • Umar, M. B. (1987). Dangantakar adabin baka da
    al’adun gargajiya. Kamfanin “Triumph” Gidan
    Sa’adu Zungur

    Danna nan don karanta Nazarin Hanyoyin Adana Kayayyakin Hausawa Na Gargajiya

    Edita@rumasau-kallamu