Tag: Kudan

  • Tarihin Garin Kudan

    Tarihin Garin Kudan

    BABI NA ƊAYA
    Allah mai yin yadda Ya so. Garin Kudan, tsohon gari ne da ya ginu bisa mutunci, tsoron Allah da kuma kishin al’umma. Tsuntsaye sukan tashi da sassafe suna rera waƙar alfijir, iska tana taɗa ganyayyaki kamar mai kiran mutane zuwa sabuwar rana. Ko da yake gari ne na tarihi, amma yana da zuciya mai sabuntawa kamar ruwan rafi da ba ya gushewa.

    A tsakiyar wannan gari ne ake samun jarumin da tarihinsa ya cika duniyar maƙwabta,wato mai girma Hakimin Kudan (Alhaji Ishaƙ Ashir), mutum mai tarbiyya, mai hangen nesa da kuma don ginshiƙin zaman lafiya. Hakimi mutum ne da ake cewa:

    “In ka ji ana yabon gida, to ka san akwai wanda ya kafa.”
    A zamaninsa, Kudan ya ɗauki salo na ci gaba, wanda ba kowa ba ne zai iya jagoranta ba. Mutanensa suna kiransa “Uban Kowa,” domin ko gida na makoki ne ko na suna, ko ɗaurin aure, ko taron al’umma, sai ka gan shi cikin mutane, ba tare da girman kai ko zunzurutun mulki ba.

    Allah ya yi masa tarin tulin baiwa ta samun ‘ƴa’ƴaye mata da maza kamar: Halima, Mariya, Hindatu, Usman (Ɗanladi), Nafi’u, Balarabe, Isma’il, Mas’ud, Gaddafi, Nasiru, Imrana, Abdulshahid, Umar, Abubakar, Yunusa, Muzammil, Sha’awanatu, Furaira (Hajiyayye), Karimatu, Aisha, Shamsiyya, Raliya… jerin sunaye da ke kamar gini-gini masu ɗora gari kan tushe.

    Hakimi kalmarsa ɗaya: “Gari ba ya ci gaba sai al’umma sun zama tamkar juna.”

    Ranar damuwa

    Ranar Lahadi, 3 ga Yuni 2024, wannan gari mai farin ciki ya shiga duhu. Rana ta fito, amma kamar ba ta da ƙarfi. Tsuntsaye ma sun yi shiru, tamkar suna jin wani abu mai nauyi na shirin faruwa. Sai labari ya bazu cikin ‘yan mintoci:
    “Hakimi ya rasu…!”

    Kalmar ta yanke zukata tamkar takobi. Mata suka zube suna hawaye, maza suka tsaya cak tamkar dutse. Kudan ta yi shiru, irin shiru mai ciwo. Wani dattijo ya ce:
    “Mutum mai kyau idan ya tafi, gari yakan yi kamar ya faɗi.”

    Mutanen garin sun yi zaman makoki, sun yi kuka, amma kuma suka yi nazari, domin Hakimi ya riga ya bar saƙon da ba ya mutuwa: al’umma su zama ɗaya.
    Bayan jana’iza, gari ya cika. Mutane sun tashi da kalmar:
    “Idan ka ga alheri ya dusashe, to ka san akwai wanda bai tsaya a kansa ba.”
    A wannan rana aka fara sabuwar tafiya.

    BABI NA BIYU

    Ranar da aka binne Hakimi, dare ya sauka da wata irin nutsuwa da ba a saba gani ba. Kafin wannan lokaci, Kudan gari ne da yake da annuri da hayaniya, amma wannan dare ya yi kamar an ɗaure shi da sarƙar jimami. Ko iska tana motsawa cikin ladabi saboda mutumin kirki ya yi hijirar da ba a dawo wa.

    Amma cikin wannan nutsuwa akwai wani haske da ba kowa ke gani ba, wato hasken da ke fitowa daga zukatan waɗanda Hakimi ya taɓa rayuwarsu da kyawawan ayyuka. Kamar wutsiyar wuta a duhun daji, hasken na neman ya tayar da mutanen gari daga dogon tunani.

    Farfesa Mu’azu (Makiyayi mai raya zukatan mutane da ilimi)

    Bayan sallar Isha’i, Farfesa Mu’azu ya zauna a gindin bishiyar ɗorawa a cikin gidansa, yana kallon taurari tamkar yana karanta tarihin mutane cikin sararin samaniya. Shi mutum ne mai nutsuwa, mai hikimar magana irin ta magabata. Ana cewa:

    “Idan ka ga dattijo yana shiru, ka sani yana magana da zuciyarsa.”
    Ya shaida rayuwar Hakimi, ya san jajircinsa, kuma ya yi imani cewa “labarin gari” ba zai kammala ba sai an rubuta tarihin waɗanda suka wakilci zuciyar jama’a. Saboda haka, ya zaro littafi ya fara rubutu cikin dare, yana cewa:

    “Ba don jarumtakarsa kaɗai ba, amma don darasin da ya bar mana.”
    Farfesa Mu’azu mutum ne da ke haɗa mutane, mai sauƙin kai, mai taimakon marayu, mai ɗaukar nauyin ɗalibai. Hakan ya sa mutane suke kallonsa tamkar hasken fitila a duhun daji. Mutane suna cewa:

    “Mai ilimi kamar ruwan sama ne; ko ka ƙi, ko ka so,idan ya sauka, ya yi maka alheri. Shi ne ya fara kiran al’umma zuwa taro a fadar masarauta, bayan kwana uku da rasuwar Hakimi.

    Malam Aliyu Labaran (Damo sarkin haƙuri)

    A cikin jama’ar Kudan, akwai gwarzon da ba shi da aiki sai ibada da ilimi, wato Malam Aliyu. Mahaddacin Alƙur’ani ne mai ladabi, mai haƙuri da juriya. Idan ya yi magana, harshensa ya yi taushi kamar ruwan zuma.

    A taron farko bayan rasuwar Hakimi, shi ya tsaya ya ce: “Gari kamar jiki ne, idan ɗaya ya ji zafi, dukkan su sun ji. Don haka mu yi aiki tare, don cike giɓi. ”Kalmar ta shiga zukata tamkar wuta a cikin busasshiyar ciyawa.

    Malam Surajo Yunusa (bango majingina)

    Kodayake Malam Surajo ya rasu tun 06/04/2017, amma mutanen gari suna yawan tuna wa da shi. Mutum ne da ya rayu wajen koyar da mutane Alƙur’ani, yana zuwa gidaje ɗaya bayan ɗaya yana cewa: “Ilimi shi ne garkuwar mai rai.”

    Rayuwarsa ta zama misali ga matasa. A wannan lokacin da ake neman sabuwar hanya, mutane da yawa suka fara tunanin yadda Malam Surajo zai yi da ya kasance a raye. Wannan tunanin ne ya fara tayar da sha`awar komawa makarantu da karatu.

    Idan ka yi tafiya cikin dare a Kudan, za ka ji matasa suna karanta Alƙur’ani a ƙananan makarantun allo da ya bari. Wani kamar ya ce: “Mutum ya mutu, amma alherensa suna raye.”

    BABI NA UKU

    A gefe guda kuma, Salmanu Faris wanda ya kasance matashi, marubuci, manomi, ɗan jarida kuma almajiri. Bayan bayan taron sai ya ɗora alƙalamin rubutu. Idanunsa sun yi ja, saboda rashin bacci, amma zuciyarsa cike take da wuta irin wutar da ta ratsa zuciyar mai son ci gaban gari. Shi ne ke cewa:

    “Idan ka ga gari ya tashi, to matasa sun ce ba za su yi shiru ba.”

    Faris ya ga mutanen gari sun shiga tunani, kuma ya yanke shawarar cewa wannan shi ne lokacin da zai tashi tsaye ya rubuta labarin mutanen gari, ya faɗaɗa tunani, ya tunzura matasa, ya yaɗa kiran ci gaba a kafafen sada zumunta da jaridun yankin.

    Shigowar Mawaƙa (Murya Mai Ƙarfafa Zuciya)

    Labaran, Ashiru, Salahu, Ali (Na Annabi) da Rabilu, su ne mawaƙa, sha’irai, kuma manoma. Sun saba da rubutu da waƙoƙi, amma wannan lokaci suka fito da wani sabon salo. Suna cewa:

    “Waƙa ba ta zama waƙa ba sai ta gina zuciya.”

    Suka shirya waƙar “Rayuwar Hakimi” wadda ta zama kamar taken sabon tafiya. Yara da matasa suka rera kanta a tituna, manya suka saurare ta cikin kukan sha’awa. Ta zama kamar ƙaho na farfaɗo da al’umma.

    Kungiyar Malamai (Garkuwar Zuciya da Ilimi)

    Auwal, Salim, Abdulrazaƙ, Abdulhafiz, Sani, Salisu, Abba, Yahaya, Abubakar, Muhammad (Prof), Yasir, su ne suke riƙe da guraben ilimi. Wanda suka kasance malamai na boko da na addini, duk masu haƙuri, nutsuwa da hangen nesa.

    Suka yi taro suka yanke shawarar:

    1. A buɗe darussa na koyar da rubutu da karatu.

    2. A ƙarfafa zaman lafiya.

    3. A koyar da matasa sana’o’in dogaro da kai.

    4. A fahimtar da al’umma mahimmancin zaman lafiya.

    Malam Auwal ya ce:

    “Idan ka ilimantar da ɗa, ka ilimantar da al’umma baki ɗaya.”

    Abubakar Suleiman (mutum na mutane)

    Abubakar, matashi mai arziki, kuma ɗan kasuwa. Ya yi na’am da wannan sabuwar tafiya. Mutum ne da ke da juriya da zuciya mai tausayin talakawa. Ya ce:

    “Ku kafa tsari, ni kuma zan tallafa.”

    Nan take ya ɗauki matasa 25 aiki, ya ba da kayan aiki, ya ba da tallafi ga makarantu da masu koyarwa. Mutane suka fara ce wa juna:

    “Gari zai tashi. Gaskiya gari zai canza.”

    Karanta Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Hajiya Halima Jumare Kudan

    Tarihin Hajiya Halima Jumare Kudan

    An haifi Hajiya Halima Jumare a garin Kudan, ƙaramar hukumar Kudan, jihar Kaduna a ranar 11th Afrilu a shekara ta 1964, ta yi karatu a Girls’ Boarding Firamare School, Zaria a shekara ta 1976, ta yi karatu a Women Teachers’ College, Kaduna (GR.II) a shekara ta 1981, ta yi a karatu a College of Education, Kafanchan (NCE) a shekara ta 1985, ta yi karatu a Ahmadu Bello University, Zaria (B.ED) a shekara ta 1990, ta yi karatu a Ahmadu Bello University, Zaria (PGDM) a shekara ta 2001, ta yi karatu a Ahmadu Bello University, Zaria (MBA) a shekara ta 2005.

    Guraren Da Ta Yi Aiki

    1. 1985-1990 ta yi aiki a Government Science Secondary School, Ikara a matsayin malamar aji (Class room teacher), a ƙaramar hukumar Ikara, jihar Kaduna.

    2. 1991-1993 ta yi aiki a GGSS Maraban Kubau, a matsayin mataimakiyar shubaga (Vice Principal), ƙaramar hukumar Kubau, Jihar Kaduna.

    3. 1993-1997 ta riƙe Senior Education Officer, ƙaramar hukumar Maƙarfi, Jihar Kaduna.

    4. 1997-2007 ta riƙe Education Secretary, ƙaramar hukumar Kudan, Jihar Kaduna.

    5. 2007-2008 ta riƙe Assistant Director, School Services, SUBEB, Jihar Kaduna.

    6. 2008-2015 ta riƙe Deputy Director, School Services, SUBEB, Jihar Kaduna.

    7. 2015-2018 ta riƙe Director, School Services, SUBEB, Jihar Kaduna.

    8. 2018- Yau tana riƙe da Quality Assurance Evaluation (KAE) ta Jihar Kaduna.

    Lambobin Yabo

    Ta samu lambobin yabo a gurare da dama, sakamakon yanayin ƙwazon aikin ta, wajen hidimtawa mutane a gurare daban-daban kamar haka;

    1. 1997/1998 ta samu takardar karramawa daga ma’aikatar ilimi da kuma ci gaban matasa (Ministry of Education and Youth Development) ta Jihar Kaduna.

    2. 1997/1998 – ta samu takardar karramawa daga LGEA UNICEF Assisted Model Primary School, Kudan, ƙaramar hukumar Kudan.

    3. 1999 ta samu takardar karramawa daga Jihar Kaduna Firamare Education Board on the judicious utilization of funds, Schools Development and Improvement, effective management of staff.

    4. 1999 ta samu takardar karramawa daga ƙaramar hukumar Kudan.

    5. 1999 ta samu takardar karramawa daga Kudan Development Association, Kaduna Chapter.

    6. 2000 ta samu takardar karramawa daga Farin Wata Youth and Drama Organization T/Wada, jihar Kaduna.

    7. 2001 ta samu takardar karramawa a matsayin jajirtacciyar magatakardar ilimi ta ƙaramar hukuma ta uku (3rd Best Education Secretary) daga ma’aikatar ilimin farkon na Jihar Kaduna.

    8. 2001 ta samu takardar karramawa daga NYSC Area Inspector, Kudan Local Government.

    9. 2004 ta samu takardar karramawa daga ma’aikatar ilimi da LGEA Firamare School, Sabon Garin Hunƙuyi, ƙaramar hukumar Kudan.

    10. 2004 ta samu takardar karramawa daga LGEA Firamare School, Nasarawan Kudan, ƙaramar hukumar Kudan.

    11. 2004 ta samu takardar karramawa daga LGEA Central Firamare School, Likoro, ƙaramar hukumar Kudan.

    12. 2004 ta samu takardar karramawa daga LGEA Firamare School, Yakubu ƙaramar hukumar Kudan .

    13. 2004 ta samu takardar karramawa daga Hunƙuyi Education Development Committee, ƙaramar hukumar Kudan.

    14. 2007 ta samu takardar karramawa daga Kaduna COPHON Award for Education Secretaries.

    15. 2009 ta samu takardar karramawa daga ƙungiyar ɗalibai ta Ikara Students Association, Bayero University, Kano.

    Danna nan don karanta ƙa’idoji goma sha ɗaya na samun nasara a rayuwa.

    16. ta samu takardar karramawa daga LGEA Firamare School, Hunquyi, ƙaramar hukumar Kudan.

    17. Ta samu takardar karramawa daga Ashiru Memorial Qur’anic Recitation Competition, ƙaramar hukumar Kudan.

    18. 2018 ta samu takardar karramawa daga gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i for our involvement in the development of the education sector in Jahar Kaduna.

    19. 2018 ta samu takardar karramawa daga Taskira Newspaper for the most outstanding service to humanity.

    20. 2018 ta samu takardar karramawa daga UK AID (Teacher Development Programme) in recognition for an outstanding performance in implementing the in-service Reforms in Jihar Kaduna.

    21. 2019 ta samu takardar karramawa daga Model Primary School Hunƙuyi in recognition of an outstanding contribution towards the development of the school.

    Tarurrukan da ta halarta

    1.Ta halarci taron ƙarawa juna sani na shekara-shekara (Annual Conference) na ƙaramar hukuma wanda Education Secretaries of Nigeria suke shiryawa a 1998 zuwa 2007.

    2. Ta halarci taron ƙarawa juna sani akan Effective Management of Firamare Schools a jihar Kaduna wanda Firamare Education Board suka shirya a 19th-20th December, 1994.

    3. Ta halarci taron ƙarawa juna sani akan ” Enhancing Productivity and School Personnel for the Success of UBE Programme” organized by Guidance and Counseling with Educational Administration and Planning Sector Department of Education, ABU, Zaria. 20th October, 2000.

    4. Ta halarci taron ƙarawa juna sani na tsakiyar shekara(Biennial Conference) na ƙungiyar National Association of local government Education Secretaries of Nigeria wanda aka yi a jami’ar Jos, jihar Plateau a 20th-25th December 2000.

    5. Ta halarci taron ƙarawa juna sani na ƙungiyar National Association of Educational Planners and Managers (NAEPM) Congress Conference on Planning and Management of Education in Nigeria; A key success to sustainable development: takardar da aka gabatar da ita akan “Management of Universal Basic Education Programme Towards Effective Goals Management” wanda aka yi a tsakanin 12th-14th October, 2004 a jami’ar ABU, Zaria.

    6. Ta halarci taron ƙarawa juna sani, wanda aka yi akan “Capacity building training on Effective School Management”, Classroom Assessment in 2011.

    7. Ta halarci taron ƙarawa juna sani, wanda aka yi akan “Due Process of Financial and Administrative Management of SUBEB and LGEA’s” wanda a Hamdala hotal da ke jihar Kaduna a tsakanin 27th-28th April, 2006.

    8. Ta halarci taron ƙarawa juna sani, wanda aka yi akan “Planning and Management of Basic Education” wanda aka yi a Jahar Kaduna ƙarƙashin ƙungiyar “State Education Sector Project (SESP)” an Intervention by the department for International Development (DFID) United Kingdom in 2000-2011.

    9. Ta halarci taron “Joint Consultative Committee on Education (JCCE)” wanda aka yi a Lokoja, jahar Kogi a 2011.

    10. Ta halarci taron ƙarawa juna sani na sati uku (three week) wanda aka yi akan “Strategic Management for Senior Managers” an yi taron ne a Cape Town, a cikin kudancin Africa, 14th March zuwa 1st April 2011. Ƙarƙashin “Ministry of Education”da kuma kulawar “State Sector Education Programme [SESP]”.

    11. Ta halarci taron ƙarawa juna sani, wanda aka yi akan “New Methods Mathematics, Nigerian Firamare English, Basic Science and Basic Social Studies” wanda ƙungiyar Learn Africa PLC ta shirya, an yi taron ne a Multi-purpose hall da ke Kaduna a ranar 12th June, 2012.

    12. Ta halarci taron ƙarawa juna sani akan ”Planning and Management of Basic Education in Kaduna”ƙarƙashin “Education State Sector Project in Nigeria (ESSPIN)” tare da ƙungiyar “United Kingdom, department for International Development (DFID)”.

    13.Ta halarci taron “Heart of Europe Schools Debate Competition” wanda aka yi a Olumouc, a cikin ƙasar Czech a June, 2016.

    14. Ta halarci taron “Management Development Services Ltd” wanda aka yi akan “Result –Driven Total Project Management, an yi taron ne a tsakanin Monday 5th to Friday, 9th December, 2016.

    15. Ta halarci taron “Executive Leadership and Management of Senior Civil Servants working in Girls Education Programming in Northern GPE” ƙarƙashin ƙungiyar “National Institute of Policy and Strategic Studies, Kuru (NIPSS)”a tsakanin 19th – 21st December, 2016.

    16. Ta halarci taron ƙarawa juna sani na ɗalibai maza da mata yara akan “Child Education Programmes”wanda aka yi a Tafawa Ɓalewa hotal a cikin ɗaki na goma sha bakwai, a jihar Kaduna a ranar 10th 11th March, 2017.

    17. Ta halarci taron ƙarawa juna sani akan “Tsangaya Education Programme” wanda aka yi a ranar 24th – 25th March, 2017 wanda aka yi a Tafawa Ɓalewa hotal a cikin ɗaki na goma sha bakwai, a jihar Kaduna .

    18. Ta halarci taron “Stakeholders Meeting on Recruitment and Deployment of Effective Teachers in the Firamare Schools”wanda aka yi a ranar 5th-6th of April, 2017 a Tahir Guest Palace, Kano.

    19. Ta halarci taron “training of the trainer (TOT) capacity building workshop on implementation of professional standards for Nigerian Teachers” na ƙungiyar “Teachers’ Registration Council of Nigeria” daga 12th-15th June, 2017 a U.l Conference Centre; a cikin U.l Hotel, lbadan, jihar Oyo.

    20. Ta halarci taron “Heart of Europe International Debating Tournament” wanda aka yi a July, 2017 a Olomouc, a ƙasar Czech, an yi taron ne a ranar 12th-19th July, 2017.

    22. Ta halarci taron ƙarawa juna sani na shekara-shekara “National Council on Education (NCE)” a July, 2017.

    23. Ta halarci taron “Training on Result-Driven Monitoring and Evaluation for optional Performance of Educational Projects” wanda aka yi a Silver Sand hotel, Katuru Road, Kaduna 7th-11thAugust, 2017.

    24.Ta halarci taron “Teaching of Literacy and Numeracy, Leadership Skills to Head teachers in Jihar Kaduna” wanda ƙungiyar ESSPIN and TDP suka shirya daga 2012-2018.

    25. Ta halarci taron “Computer Training on Human Resource Approval at Federal Polytechnic, Kaduna” ƙarƙashin kulawar gwamnatin Jihar Kaduna.

    26. Ta halarci taron “Trainings on the Teaching of Jolly Phonics to Firamare School Teachers”.

    Ayyuka na musamman 

    1. Ta zama Member – Committee on Teacher Competency Test for Kaduna State teachers;

    2. Ta zama Member – Committee on Teacher Competency Test In Kaduna L.G.A;

    3. Ta zama Member – Teacher Development Programme (ESSPIN/TDP)

    4. Ta zama Member -Teacher Registration Council (TRCN)

    5.Ta zama Component Lead -Teacher Professional Development (TPD) under the Grand Partnership in Education/Nigeria partnership in Education Programme (GPE/NIPEP). STRENGTH:Prudent management of resources, Commitment to the service for good result and respect for constituted authority.

    (Mun samu waɗannan jawabai ne daga bakin Hajiya Halima Jumare wanda ta turo min ranar bakwai ga watan yuni 2020 ta imel ɗi na).

    Domin Karanta tarihin hakimin Kudan danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu