Tag: Hausawa

  • Sunayen Abinci Ko Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 4

    Sunayen Abinci Ko Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 4

    111.Ɗan gauta
    112.Daskasmi
    123.Ɗan gajera
    124.Ɗan sululu
    125.Ɗan bidis

    126.Ɗan boris
    127.Dubulan
    128.Gyaɗa kuriga
    129.Gurbiya
    130.Gyaɗa Amaro

    131.Hanjin Ligidi
    132.Kuɓewa
    133.Kanya
    134.Lubiya
    135.Loga

    136.Maɗi
    137.Muruci
    138.Miyar kuka
    139.Kafi kaza
    140.Shash-shaka

    141.Wake (fari)
    142.Wake (Ja)
    143.Waken Soya
    144.Kwakwameti
    145.Yalon Bello

    146.Goro
    147.Ƙosai (Are)
    148.Yaddo
    149.’Yar fako
    150 Tamatsitsi
    Da sauran su.

    FASIHIN KAITA

    Karanta Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 3

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 3

    Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 3

    71.Kantun nome
    72.Nono
    73.Rabeh
    74.Rummace
    75.Ramah

    76.Soɓo
    77.Sabulun salo
    78.Tabso
    79.Taka- yaga
    80.Tabshe/Taushe

    81.Taura
    82.Tubani.
    83.Tukuɗi
    84.Tumu
    85.Tsaba

    86.Tuwo (gero, dawa, acca, masara, shinkafa)
    87.Talunguba
    88.Tuwon ruwa.
    89.Ungududu
    90.Wake

    91.Waina (gero, masara, shinkafa)
    92.Yaɗiya
    93.Yalo
    94.Yakuwa
    95.’Yar kumbu

    96.Kwalshi, kwalo, tantalibo
    97.Aya
    98.Gudun kurna
    99.Ɗorowa
    100.Zure

    101.Zogale
    102.Zumah
    103. Gwanda
    104.Gwaba
    105.Faru

    106.Fara
    107.Tabar Malan
    108 (ƙuli-ƙuli, guru, buriji)
    109.Aduwa
    110.Tsaba-da-wake

    FASIHIN KAITA

    Karanta Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 2

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 2

    Sunayen Abinci Da Abin Sha Na Hausawa Kashi Na 2

    36.Ganda
    37.Gauta
    38.Gaskami
    39.Gawasa
    40.Giginya

    41.Gindi- kwalo
    42.Gumba
    43.Gurasa
    44.Goriba
    45.Halawa

    46.Jimɓiri
    47.Kifi
    48.Kamu
    49.Ƙato-da-lage
    50.Koko

    51.Kunu (zaki, kanwa, fari, tsamiya)
    52.Ƙwai
    53 Kantun Gana
    54.Ƙosai
    55.Kwaikwaye

    56.Kulele
    57.Kwarbebe
    58.Kilishi
    59.Kurna
    60.Kauci

    61.Lula
    62.Lulaye
    63.Makani (gwaza)
    64.Mandaƙo
    65.Masara

    66.Magarya
    67.Mai (gyada, shanu)
    68.Mangwaro
    69.Nama
    70.Nakiya

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Abincin Hausawa Kashi Na 1

    Edita@rumasau-kallamu

  • Makaman Da Hausawa Ke Amfani Da Su Wajen Faɗa Ko Yaƙi

    Makaman Da Hausawa Ke Amfani Da Su Wajen Faɗa Ko Yaƙi

    1. Adda
    2. Adaka (bindiga)
    3. Barandami
    4. Baushi
    5. Garkuwa

    6. Gariyo
    7. Ƙaho
    8. Kibiya
    9. Ƙota
    10. Kokara

    11. Kansakali
    12. Kwari da baka
    13. Bakan danƙo
    14. Lifidi
    15. Mashi

    16. Sulke
    17. Takobi
    18. Tsitaka
    19. Gorah

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Wasu Kayan Aikin Rini

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sunayen Wasu Wanduna Da Takalman Hausawa

    Sunayen Wasu Wanduna Da Takalman Hausawa

    WASU WANDUNAN HAUSAWA

    1.Buje
    2.Feto (Kaliso)
    3.Tsala
    4.Tsaitsaye
    5.Tumazagi
    6.Zinah
    7.Zabuni
    8.Tarangama

    WASU TAKALMAN HAUSAWA

    1.Balka
    2.Ɗangarfai
    3.Fadde
    4.Markuɓi
    5.Sambatsai
    6.Wufi
    7.Asho

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Wasu Kayan Kiɗan Hausawa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Kayan Kiɗan Hausawa

    Wasu Kayan Kiɗan Hausawa

    1.Banga
    2.Dundufa
    3.Ganga
    4.Goge
    5.Gurumi

    6.Garaya
    7.Gadangama
    8.Jauje
    9.Jinjintu
    10.Kalangu

    11.Kazagi
    12.Kukuma
    13.Kuntigi
    14.Kurkutu
    14.Kotso
    15.Kuge

    16.Kwamsa
    17.Kurya
    18.Molo
    19.Shantu
    20.Talle

    21.Tandu
    22.Turu
    23.Zari
    24.Duman girke

    FASIHIN KAITA

    Karanta Yadda Sunayen Wasu Hulunan Hausawa Suke

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Sunayen Wasu Hulunan Hausawa Suke

    Yadda Sunayen Wasu Hulunan Hausawa Suke

    1. Bakwala
    2. Dara gajera
    3. Dara doguwa
    4. Dankwara
    5. Gurus
    6. Gurumfa
    7. Haɓar Kada
    8. Kalaɓus
    9. Kube
    10. Markiyo

    11. Mu-haɗu-banki
    12. Iya kwandishin
    13. Mangadara
    14. Saki
    15. Siniya
    16. Sallau Musa
    17. Tashi-da-kwakwa
    18. Zita
    19. Zanna Bukar

    FASIHIN KAITA

    Karanta Sunayen Wasu Kifin Hausa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waiwaye Kan Tattalin Arzikin Hausawa Na Gargajiya

    Waiwaye Kan Tattalin Arzikin Hausawa Na Gargajiya

    TUNA BAYA SHI NE ROKO: WAIWAYE KAN TATTALIN ARZIKIN HAUSAWA NA GARGAJIYA

    DAGA

    Kabiru Abdulkarim

    Kabiruabdulkarim996@gmail.com  08034510967

    Da

    HauwaMuhammadMaikudi

    hawwammaikudi@gmail.com  08098191994

    School of Languages,

    Kano State College of Education and Preliminary Studies.

    Takardar da aka gabatar a Bikin Taron Ranar Hausa ta Duniya a Kwalejin Ilimi da Share Fagen Shiga Jami’a Ta Kanoa ranar Talata 26 ga Agusta, 2025.

     TSAKURE

    Hausawa kan ce “Waiwaye adon tafiya”. Wannan takarda ta yi waiwaye ne a kan tattalin arziƙin Hausawa na gargajiya domin abin nan da Bahaushe ke cewa “Tuna baya shi ne roƙo”. An yi nazarin sana’o’in gargajiya na Hausa, saboda su ne ginshiƙan rayuwa da tattalin arziƙin yau da kullum na Hausawa (Garba 1991:1).

    Takardar ta gano cewa watsi da aka yi da waɗannan sana’o’i  namu na gargajiya, shi ya jefa mu cikin wannan hali na ƙaƙa-ni-ka-yi da matsin tattalin arziki da muke fama da shi a halin yanzu. Sannan an kawo shawarwari da ake ganin za su iya taimakawa sosai wajen rage wannan raɗaɗi da ake ciki da kuma mawuyacin hali da matasannmu suka tsunduma kansu a ciki na shan miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya da kuma faɗan daba.

    Gabatarwa

    An shirya wannan takarda ne da nufin yin waiwaye kan tattalin arziƙin Hausawa na gargajiya, ba don komai ba sai don a waiwaya a kuma gyara halayyar da Hausawa suka ɗauka a halin yanzu na watsi da sana’o’inmu na gargajiya, muka koma bilayi da bilinbituwar neman arziƙi ta wasu hanyoyi da ba su dace da mu ba, sannan kuma suke wahalar da mu, har suka ke neman kai Hausawa ƙasa warwas.

    Bahaushe a da ba shi da wani abin da ya sanya a gaba sai sana’a, wato neman na kansa. Amma a halin yanzu an bar sana’a an koma neman wasu hanyoyi da za a azurta kai da gaggawa, kuma arziƙin ya ƙi samuwa. An koma ba mu ga tsuntsu ba mu ga tarko. Bahaushe yana cewa “Sana’a Sa’a, kuma rashin sana’a Sata” (Mu’azu da Satatima 2013:61).

    Daga nan za mu fahimci cewa lallai Hausawa na wannan zamani, musamman matasa an doshi hanyar rugujewar al’umma. Don haka,  ya zama wajibi a koma ga sana’o’inmu na gargajiya domin ita ce kaɗai hanya mai ɓillewa wadda kuma ba ta da tangarɗa.

    Wannan tattalin arziƙi da muke magana a gargajiyance ya ƙunshi hanyoyin da Hausawa suka bi a dauri, suka zauna cikin ƙoshin lafiya da kwanciyar hankali da wanzuwar arziƙi, har ya kasance sun zama abin koyi da kuma ban sha’awa a idon duniya.

    Hausawa dai su ne al’ummar nan waɗanda harshen Hausa shi ne harshensu, kuma al’adunsu da ɗabi’unsu suka yi kama da na addinin Musulunci (Zarruq 1992:2). Gargajiya kuma tana nufin hanyoyin da aka saba bi na rayuwa. A nan gargajiyar Bahaushe ta kasu gida biyu: (a) kafin zuwan Musulunci da kuma (b) bayan zuwan Musulunci.

    • Kafin zuwan Musulunci: A nan ana nufin duka abubuwan da Hausawa suka saba yi na rayuwa tun daga farkon samuwarsu , wato lokacin Maguzanci har zuwa lokacin da suka haɗu da Larabawa.
    • Bayan zuwan Musulunci: Addinin Musulunci ya zo ƙarsar Hausa a tsakiyar ƙarni na sha huɗu zamanin Sarkin Kano Aliyu Yaji (1349-80), (Maiyama 2008:40-41), kimanin shekaru 676 da suka gabata. Bayan zuwan Musulunci Hausawa sun karvi addinin hannu bi-biyu. Dukkanin wasu kyawawan halaye da ɗabi’u sai suka cigaba da su, amma duk wasu abubuwa da suka ci karo da koyarwa da tarbiyyar addinin Musulunci sai suka yi watsi da su. Dalilin daɗewar musuluncin a ƙasar Hausa, sai ya sanya su ma al’adun da aka samu daga Larabawa, sai suka zama gargajiyar Bahaushe.
    • Lokacin zuwan Turawa(zamani):Zuwan Turawa tare da mulkin mallaka shi ne ake kira zamani. Turawa sun karɓe ikon ƙasar Hausa a 1903. Don haka duk wani abu da ya samu bayan zuwan Turawa ƙasar Hausa, to shi ba gargajiyar Bahaushe ba ne ya zama na zamani ke nan.

    Togaciya: Wannan takarda ta yi togaciya kan abubuwa kamar haka:

    • Akwai sana’o’i da dama da takardar ba ta dube su ko nazarce su ba, domin an tsara wasu Makarantu ko Kwalejoji  za su gabatar da su a wannan taro na ranar Hausa ta Duniya. Sana’o’in sun haɗa da Saƙa, Sassaƙa, Koli, Ƙira (babbaƙu), Dillanci da sauransu.
    • Akwai wasu sana’o’in da ko dai Hausawa na tababarsu cikin sahihancinsu kamar roƙo da raraka da tsibbu da makamantansu, takardar ba ta dube su ba. Haka sana’ar ƙunshi da wasu ke kallonta a gargajiyance kamar ba sana’a ba ce wato kwalliya ce, daga baya ne zamani ya ba ta gurbi ta zama cikakkiyar sana’a kuma mai gwaɓi.
    • Sana’o’in da takardar ta yi bayani, ana so ne a kafa hujja ko buga misali da su, ba wai su kaɗai ne suka fi sauran muhimmanci ba.
    • Wasu sana’o’in kuma an haƙura ba a kawo su ba saboda yanayin lokaci da gudun ka da abin ya yi yawa wai “shege da hauka”, misali Arkomi,da Asako,da Kiri,da Bugu,daAikatau wato Dakau,da Sirfau,da Niƙau da makamantansu.

    SANA’A

    Garba (1991:1) ya dubi sana’a da cewar ita ce ginshiƙin rayuwa da tattalin arziƙin yau da kullum na Hausawa tare kuma da ɗaya daga cikin muhimman manyan hanyoyin gano martabar mutum da ƙasaitarsa da matsayinsa cikin al’umma. Watau ban da noma wadda take ruwan dare, Hausawa suna kuma ƙara wa kansu wata sana’a wadda da rani ana samun abinci ta hanyarta, har ma ko da daminar akan taɓa wasu sana’o’i ƙari a kan noma.

    Umar (1983) a cikin D/Iya (2006:1) ya bayyana sana’a da cewa; “wata hanya ce da ɗan Adam kan ta’allaƙa a kanta domin samin abin masarufi wadda ta shafi sha’anin kasuwanci, wato sha’ani na saye da sayarwa”. Ya ci gaba da cewa; “sana’o’in suna da babban matsayi a al’adun kowacce al’umma”. Ga Bahaushe su ne ƙashin bayan tattalin arziƙinsa.

    A nan sana’a ta zo da sigogin ma’ana, akwai zaɓaɓɓun lokuta da yanayi ke tabbatar da sana’a. Wannan ya yi dai dai da azancin da ke cewa lokacin abu a yi shi. Ma’ana kowace sana’a da lokacin yinta, wannan yana haska yadda Al’ummar Hausawa suke da abin yi rani da damina, dare da rana, mace da namiji, yaro da babba. Haka shi yake nuna ba sa zaman kashe wando  koyaushe akwai abin yi.

    Rabe-raben Sana’a

    Masana da dama sun yi ƙoƙarin bayyana ko tsara sana’o’in Hausawa bisa kashi-kashi dangane da ra’ayoyinsu da fahimtarsu.

    Yahya da Ɗangambo (1986:173-174) sun tsara rabon sana’o’i zuwa gida uku. Sana’ar noma, da sana’ar sarrafa wani abu domin samar da wani abu. Misali ƙarfe-ƙira; zare – saƙa; fata – dukanci; sai sana’ar sarrafa jari da ƙwarewa, misali, kasuwanci, da gini, da tallau, da sauransu.

    Haka kuma Yahya (1992:4) su ma a cikin littafin sun raba sana’o’i zuwa gida uku inda suka tsara sana’o’i na noma da kasuwanci da waɗanda suke dafe-dafe.

    Ragowar rabe-raben sana’o’in na Hausawa, su ne rabo ta ɓangaren jinsi, ma’ana an raba sana’o’in a ɓangaren jinsi zuwa gida uku, jinsin maza da jinsin mata da kuma na tarayya. Abin nufi a nan shi ne, bisa ƙa’idojin al’adun Hausawa, ba kowacce sana’a kowa yake yi ba, a a kowace da mai yinta, waɗansu na mata ne, waɗansu na maza ne, waɗansu kuma kowane jinsi na iya aiwatar da su. Misali:

    Na maza Na mata Na tarayya

    Ƙira (babbaƙu) kitso saƙa

    Dukanci sussuƙa ƙira (farfaro)

    Jima dafe-dafe d.s dillanci

    rini aikatau

    wanzanci, da makamantansu.

    Noma

    Noma tushen arziki,

    Noma na duƙe tsohon ciniki,

    kowa ya zo duniya kai ya tarar.

    A bisa tsarin gargajiya, noman nan shi ne tushen rayuwa, domin ta nan ne ake samar da abinci da kuma bunƙasar tattalin arzikin al’umma. Burin kowanne magidanci ne ya noma isassahen abincin da zai ci da iyalinsa tsawon shekara. Haka kuma dole ne akwai buƙatar a noma abin sayarwa irin su auduga da gyaɗa don samun ‘yan kuɗin biyan buƙatun rayuwa. Haka kuma sana’ar noma ta haifar da wasu sana’o’i musamman na abinci daban-daban.

    Al’adar sana’ar noma ta yi wa rayuwar Bahaushe riga da wando, har ma da hula da takalmi. Bayan wadatuwa da abinci da abin masarufi, noman nan ya hana Bahaushe ragwanci da zaman kashe–wando. Ya tsare masa gabas da yamma ta fuskar cikar mutunci da kwarjini da cancanta ta kowace fuska. Don haka sana’ar  noma ta haifar da wasu sana’o’i irin su kiwo da saƙa da kaɗi da akasari sana’ar abinci da mata kan aiwatar daga cikin gida.

    Fawa

    Maza na Sarkin fawa,

    Kuna yawa ana rage gona,

    Fawa ko ta kwana ta fi tallan ƙosai,

    Sarkin fawa rikici gado,

    Kaɗauki bashi ka biya bashi,

    Na Inna kashin shanu,

    Hankaka mai da ɗan wani naka,

    Bungare mai billen ‘yanci,

    Na kulluru mayen ɗanye,

    Maƙiyinki ya dama fura ya fasa.

    Fawa sana’a ce ta yanka dabba a feɗe ta, a yanka ta gunduwa-gunduwa, tsoka-tsoka domin sayarwa ta yadda za a iya amfani da naman yadda ake sonsa. Ana iya sayar da shi a ɗanyensa, ko a gasa, wato tsire ko balangu ko kilishi da makamantansu.

    Farauta

    Gwarzon daji,

    Mai tsare ƙauyuka,

    Barde mai tsaron daji,

    Wanda baya tsoron daji,

    Masanin dabarun naman daji,

    Kai ne mai kawo tsoron-tsoro.

    Farauta ita ce sana”a

    Su

    Mai su uwar ɗaka.

    Wanda ke kawo ɗanɗano ga abinci,

    Mai ba wa duniya ƙanshin ƙanshi,

    Ɗawisu na alheri,

    Mai zuba wa rayuwa ɗanɗano.

    Su sana’a ce ta kamun kifi, musamman ga waɗanda suke zaune a gefen ruwa. Sana’a ce da ake kama kifi don ci ko don sayarwa.

    Jima

    Romon Jaɓa,

    Mai yi wa saurayi aure,

    Mai sai wa saurayi wando,

    Mai kula da lafiyar mutane

    Jima hannun magani,

    Ka sha baƙar wahala don farar fata,

    Ka zama ma ji ɗaukar alhini.

    Jima sana’a ce da ake tusarrufi da fata. Jima dai ita ce sana’ar sulluɓe fata don fitar da gashin da ke jikinta (Alhassan da wasu,1980:43) Jima tsohuwar sana’a ce a ƙasar Hausa da har yau take cin ganiyarta. Kamar yadda Alhaji Sule Garo, shugaban masu Masana’antun jima na zamani, ya faɗa a wata hira da aka yi da shi (a Radiyo France International,R.F.I.ranar Litinin,17 ga watan Augusta,2009 da misalin ƙarfe 3:17 na yamma), cewa ya yi duk da shigowar zamani, har yanzu sana’ar jima ta gargajiya tana da tasiri. Domin kamar yadda ya faɗa, su kamfanonin sarrafa fatar sun fi buƙatar waɗanda aka jeme su a gargajiyance don haka ma sukan yi masu ƙima ta musamman wajen saya (Ɓatagarawa 2013: 328).

    Rini

    Baban dubu mai kamu,

    Kowane ganye ya ruɓe ya lalace,

    Amma ban da kai na Sarkin Marina,

    Katsi katse tsiya,

    Toka takore tsiya na Makaman Marina,

    Kowa ya bar ka gidansa a sha lami.

    Rini kuwa sana’a ce ta gargajiya da ta shafi canza launin tufa ko zare daga fari ya koma wata kala daban. Wajen rini ana amfani da abubuwa irin su muciya da kwatarniya da guga da itace da baba da katsi da shuni da tukunyar baba da ruwa da sauransu

    Rini, sana’a ce ta gargajiya da a waɗansu wurare a ƙasar Hausa, har yanzu ana ado da ita. Duk da cewa an sami hanyoyi da dama na zamani inda ake amfani da launuka iri daban–daban, amma duk da haka har yanzu ana ba wa sana’ar ƙima  daraja ta musamman.

    Wanzanci

    Kala-kala magani gizo Ɗan Wanzam,

    Aska na cikin kube tana cin gashi,

    Ka ci gashi ka sha jini na Magaji Aska,

    Kai wa Sarki rotse ka tashi da martaba.

    Wanzanci sana’a ce da ake yin amfani da aska da ƙaho da tankolo da ƙugiya wajen aiwatar da ita. Masu wannan sana’a wato wanzamai suna tallafa wa rayuwar al’umma ta fuskar aiwatar da abubuwa kamar aski da ƙaho da kaciya (shayi ko kugunu) da tsagar anfill da shasshawa da cire beli ko hakin wuya da makamantansu.

    Ɗinki

    Ɗinki sana’a ce da ake amfani da zare a samar da sutura ingantacciya, yalwatacciya kuma kyakkyawa. Ɗinki hikima ce ta yin amfani da sililin zare, tare da allura a riƙa haɗa geffan kyallayen yadudduka a samar da tufafi ga maza da mata. Ɗinki ya rabu gida biyu wato ɗinkin tufafi da kuma ɗinkin huluna.

    Ƙira

    Huntu ubangijin mai riga.

    Ƙira sana’a ce mai dangantaka da ma’adanai da tsirrai da dabbobi. Sana’a ce da ake sarrafa ƙarfe da itace don samar da ma’aikaci. Ita ma wannan sana’a a iya cewa tana daga cikin sana’o’in farko-farko ma’ana tun lokacin da ɗan Adam ya fara zama wuri ɗaya. Ƙira ta zama tamkar uwa ma ba da mama a wurin sauran sana’o’i domin maƙeri ne yake samar masu kayan aikin sana’ar su.

    Sana’ar ƙira ta kasu gida biyu. wato maƙeran fari, da kuma maƙeran baƙi. Maƙeran fari su ne masu ƙera abubuwa dangin farin ƙarfe da azurfa da zinare da makamantansu. Su kuma maƙera baƙi su ne suke sarrafa  baƙin ƙarfe  dangin tama da tagulla.

    Ta hanyar ƙira ake samar da abubuwan amfani (ma’aikaci) irin su wuƙaƙe da gatura da adduna da faretani, da kuma makamai irin su takubba da masu da da kibiyoyi da makamantansu. Ka ga wannan ba ƙaramin tasiri suke da shi ba ta fuskar tattalin arziki da kuma harkokin tsaro a gargajiyance.

    Fatauci

    Fatauci sana’a ce da ta danganci kasuwanci. Akan bar gari a tafi wani garin domin kai haja can, sannan kuma a sayo wata a kawo gida. Masu wannan sana’a ana kiransa fatake. Da wannan sana’a ta fatauci Hausawa suka shahara a idon duniya. Sukan ɗauki kaya (haja) kamar fata da gyaɗa da auduga su kai sauran sassa na kudancin ƙasar nan ko ƙasashen ƙetare su sayo wasu kayan da ba a samunsu a ƙasar Hausa.

    Sukan ya-da zango a wasu garuruwa. Wanda a halin yanzu waɗannan wurare suka zama mallakin Hausawa a wajen ƙasar Hausa misali Zango ta Gwanja a ƙasar Ghana in da daga nan ne ake kawo goro zuwa ƙasar Hausa.

    Gini

    Gini sana’a ceta sarrafa abubuwa don samar da muhalli, daɗaɗɗiyar sana’a ce a ƙasar Hausa. Hasali ma dai a iya cewa ga al’ada kowa magini ne. Ma’ana ko da dai ba a nuna ƙwarewa ba to a ƙalla kowa yana iya sarrafa ƙasa, ko laka don yin gini. Waɗanda suka ƙware, sukan maishe ta sana’a, kuma su ake cewa magina. Magina sun kasu kashi biyu, akwai magina na ƙasa ko laka (siminti a zamanance) da suke sarrafa ƙasa don samar da muhalli.

    A ɗaya ɓangaren kuma akwai magina na yumɓu, waɗanda suke sarrafa yumɓu su samar da abubuwa irin su tukwane da kasake da murahu (amare) da tuluna da asusu da butoci da mazubai iri daban-daban. Akwai ire-iren waɗannan magina masu tarin yawa a ƙasar Hausa, kuma sun taka muhimmiyar rawa wajen baza harshe da al’adun Hausawa a wurare daban-daban ciki da wajen ƙasar Hausa. Adamu (1978:34).

    Matsayin Sana’a Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙin Hausawa:

    Ma’anar Tattalin Arziki

    Tattalin arziki shi ne yadda al’umma ke samar da abin da take buƙata da yadda take sarrafa shi, da amfani da albarkatun ƙasa domin samun ci gaba da walwala da biyan bukatunsu na yau da kullum.

    Ibrahim (2010) ya bayyana ma’anar tattalin arziki da cewa: “Tattalin arziki shi ne tsarin da al’umma ke bi wajen samar da abin da take buƙata daga albarkatun da ke hannunta da kuma yadda take sarrafa su.”

    Bunza (2002) ya bayyana cewa, “Tattalin arziki shi ne yadda al’umma ke tsara rayuwarta ta hanyar albarkatun da take da su, domin ci gaba, zaman lafiya da kuma walwala.”

     Bunƙasar Tattalin Arziƙin Hausawa

    Tattalin arzikin Hausawa ya bunƙasa sakamakon waɗannan sana’o’i da suke gudanarwa. Babu shakka Hausawa sun tsaya tare da jajircewa da bin wasu hanyoyi da ƙarfafa wa juna domin ganin tattalin arzikinsu ya bunƙasa daga waɗannan sana’o’i.

    Saboda irin jajircewar da suke yi a kan sana’o’insu har sai da ya zamo sun yi fice a fuskar noma ta inda suke noma, wannan ba ƙaramin bunƙasa tattalin arziƙinsu ya yi ba a wancan lokaci. Daga cikin hanyoyin da suka taimaka wajen bunƙasa wannan tattalin arziƙi sun haɗa da:

    Yadda wasu sana’o’in suke haifar da wasu sana’o’in: Ta hanyar haifuwar wasu sana’o’in a dalilin wasu, tattalin arzikin Hausawa ya bunƙasa matuƙa. Hakan na faruwa ne sakamakon duk lokacin da aka fari wani abu na sana’a to babu shakka za a samu majuɓunta a kan abin da suke samarwa.

    Wannan zai haifar da samun kuɗi ga masu wannan sana’a kai tsaye da ma sauran al’umma baki ɗaya. Misali Sana’ar noma, ta haifar da sa sana’o’i irin su kasuwanci, fatauci, ban gishiri na ba ka manda da nakamantansu.

    • Kiwo ya haifar da sana’ar fawa.
    • Fawa ta haifar da sana’ar jima.
    • Jima ta haifar da sana’ar dukanci.
    • Sana’ar kaɗi ta haifar da sana’ar saƙa da rini.
    • Saƙa ta haifar da sana’ar ɗinki.

    Bayan wannan akwai Sana’o’in da yawa da suka haifar da wasu sana’o’in, hakan ba ƙaramin bunƙasa tattalin arziƙin Hausawa ya yi ba.

    Samar da kayayyakin da suke na buƙatu a matakin farko: Yawa-yawan kayan da Sana’o’in suke samarwa, kaya ne da ake buƙatar su ko ma a ce suka zama dole a mallake su. Hakan ya sa da zarar an samar da su da an saye su (ga waɗanda ake ƙirƙira ko samarwa) Haka abun yake ga sana’o’i na hidima irin su aski, kitso da makamantansu. Ƙarin bayani a nan, a zamanin da Hausawa ba su fiya ɗora kansu a sana’o’i na jin daɗin rayuwa ba da suke haifar da almubazzaranci da rashin adani ba.

    Hanyoyin Bunƙasa Tattalin Arziƙin Hausawa

    Akwai hanyoyi da dama waɗanda suke taimaka wa Hausawa wajen bunƙasar tattalin arziƙi. Kaɗan daga ciki sun hada da:

    Gado: A da mutane suna gadar sana’o’i da suke yi ne daga magabatansu (gida). Wannan ya sa da wuya ka samu wanda yake ba shi da sana’ar yi, don kuwa mutum tun yana ƙarami yake koyan sana’ar da ya gani ana yi a gidansu. Hakan kan sanya ƙwarewa da kishin sana’ar ga masu yin ta. A dalilin haka da wuya ka ga mai zaman banza a wancan lokaci. Wannan ya sa kowa yana da abin yi, kuma tattalin arziƙin al’umma ya daɗa bunƙasa.

    Ban gishiri na ba ka manda: Wannan wani kasuwanci ne da ake yi ba da kuɗi ba. Ana yin sa ne ta hanyar musaya na abubuwan buƙata. Misali manomi zai iya ɗaukar hatsinsa ya kai wa mai fawa don ya ba shi nama. Ko ya ba wa wanzami don ya yi masa aski. Wannan shi ake kira da ban gishiri na ba ka manda . Haƙiƙa wannan ya taimaka wajen bunƙasa tattalin arziƙin Hausawa domin kuwa babu yadda za a yi kana da sana’ar ka ka rasa wani abu da kake buƙata ko da kuwa ba ka da kuɗin saye.

    Kiwo: Kiwo sana’a ce mai sirrin gaske ga al’ummar Hausawa. Ga mata har ma mazan a da ba a rasa su da yin kiwo. Idan biki ya taso ko haihuwa ko wata buƙata, mutum kan kama wata dabba tasa ya je ya sayar ya samu kuɗin biyan bukata nan take. Baya ga wannan, a lokacin da ake ciyar da dabbobi ciyawa akan zuba a ƙasa, to duk lokacin da dabbobin suka yi kashi, kashin kan haɗe da ragowar ciyawar da suka ci suka rage.

    Idan sun ruɓe sai su ba da takin noma. Irin wannan taki ya fi ba da albarkar noma da lafiya ga abin da aka shuka a gonar da aka zuba shi. Wannan ba ƙaramin kawo bunƙasar tattalin arziki ya yi ba a zamanin da, musamman idan an kwatanta shi da zamanin yanzu da ake sayen taki da tsada.

    Haɗin kai da tallafa wa juna: Yanayin yadda Hausawa suke aiwatar da sana’o’insu ya taimaka musu matuƙa wajen ƙara hada kawunansu. A sanadiyyar haka ya zamo akwai taimakon juna a duk lokacin da buƙatar hakan ta taso. Misali ko ba ka da jari za ka samu aron kayan aiki daga ‘yan’uwa ko abokan arziƙi don gudanar da sana’arka. Wannan shi ma ba ƙaramin taimaka musu ya yi ba wajen bunƙasa tattalin arziƙinsu.

    Mafi yawan masu sana’oi’n nan, suna ba da taimakon magunguna a cikin sana’o’in nasu, wannan yana ƙara masu kuɗaɗen shiga, kuma ya ƙara bunƙasa tattalin arziƙinsu. Misali manoma ne ke bayar da maganin ciwon baya da maganin rana.

    Haka kuma maƙera ne suke ba da maganin ƙunar wuta. Su kuma marina ana samun maganin lalurar fata kamar ƙyasbi da  ƙurajen bar- ni-da-mugu da katsi ga masu juna-biyu. Masunta suke bayar da maganin sanyi da ƙayar kifi. Mahauta suke bayar da maganin kaifi da kuma tsini da sauransu.

    Shawarwari

    • Saka gasa a wajen samar da kayayyaki daga lokaci zuwa lokaci don bunƙasa sana’o’in kamar yadda Ƙungiyar Zauren Hausa Nijeriya ta ɗauki gaɓaren yi.
    • Hukumar ilimi ta sanya shi a manhajar makarantu domin sanya shi cikin manyan darussa koyarwa a matakai daban-daban na ilimi.
    • Masu riƙe da sarautun gargajiya lallai ne su zama sun yi kira da wayar wa da jama’a kai tare da cusa sha’awa don amfani da irin kayayyakin da sana’o’in na gargajiya suke samarwa.
    • Jama’ar gari su ma ba a bar su a baya ba, lallai ne sai sun dawo daga rakiyar da ba ta ƙarewa, wato sun yi riƙo  hannu bibiyu wajen rungumar kayayyakin da sana’o’in mu suke samarwa.
    • Ba da tallafi na kuɗi da kayan aiki ga masu sana’o’in da shawarwari da dabaru daga ƙwararru na masana iri daban-daban.
    • Hukumomi na gwamnati su dinga amfani a kayayyakin da ake samarwa ta fuskar sana’o’in Hausawa na gargajiya.

    Kammalawa

    Waiwaye a kan sana’o’in gargajiya na Hausawa ya nuna cewa jajircewa da tsayawa tsayin daka a kan wasu sirrika da taimakon juna su ne tushen tattalin arziki da ci gaban al’umma a wancan lokaci, kuma har yanzu suna da daraja wajen kare martabar al’adu da samar da ayyukan yi a cikin al’umma.

    Manazarta

    Adamu, M. (1978), The Hausa Factor In West African History. Zaria/Ibadan A.B.U. and Oxford,.

    Alhassan H. da wasu, (1980), Zaman Hausawa, Littafi Na Ɗaya  Zaria. .I.E.P.,A.B.U.

    Aliyu, U. (2015). Kasuwanci da Cigaban Al’umma. Zaria: Ahmadu Bello University Press.

    Aminu, K. (2000). “Saka Sana’ar Sarrafa Auduga a Kasar Hausa: Tasirinta da Muhimmancinta.” Kundin Degree na Farko. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

    Asiru, A. (2017). Sana’ar Dinki Da Ci Gabanta. Zaria: Amadu Bello University Press Limited.

    Bashir, I.S. (1990). “Take da Kirarin Sana’o’in Gargajiya: Nazarin Ma’anarsu da Muhimmancinsu ga Rayuwar Hausawa.” Kundin Digiri na Biyu. Jami’ar Bayero, Kano.

    Batagarawa , S.A.(2013). Nason Wasu Al’adu a Kan Sana’o’in  Gargajiya na Hausawa Mazauna Lokoja. Takardar da aka gabatar a taron ƙarawa juna sani na kasa da kasa mai taken “Tavarvarewar Al’adun Hausawa a Yau” wanda Sashen Koyar da Harshunan Nijeriya  na Jami’ar Umaru Musa Yar’adua tare da hadin gwiwar Hukumar Adana Tarihi da Al’adu ta Jihar Katsina a ranakun 25-26 ga watan Yuni, 2013.

    Dan’iya, M. A. (2006). Tasirin Kimiyya da Ƙere-ƙeren Zamani a kan Sana’o’in Hausawa na Gargajiya. Kano: Kabs Print Services Nigeria.

    Garba, C. Y. (1991). Sana’o’in Gargajiya a Ƙasar Hausa. Ibadan: Spectrum Books Ltd.

    Ibrahim, M. (2010). Tattalin Arzikin Hausawa. Kano: Benchmark Publishers.

    Madabo, M.H. (1979). Ciniki da Sana’o’i a Kasar Hausa. Lagos: Nelson.

    Madauci, I. da wasu (1968). Hausa Customs. Zaria: Northern Nigeria Publishing Company Ltd.

    Maiyama, U.H. (2008): Sata A Zamantakewar Hausawa (Nazarin Waƙoƙin Barayi Na Muhammadu Gambo Fagada) Kundin Digiri Na Uku Da Aka Gabatar A sashen Nazrin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.

    Mu’azu, A da Satatima,I.G. (2013). Kwaɗon Al’adun Hausawa da na Wasu Ƙabilu. Takardar da aka gabatar a taron ƙarawa juna sani na kasa da kasa mai taken “Tavarvarewar Al’adun Hausawa a Yau” wanda Sashen Koyar da Harshunan Nijeriya  na Jami’ar Umaru Musa Yar’adua tare da hadin gwiwar Hukumar Adana Tarihi da Al’adu ta Jihar Katsina a ranakun 25-26 ga watan Yuni, 2013.

    Sani, A. (2003). Hanyoyin Rayuwa da Aikin Yi a Najeriya. Kaduna: Fisbas Media.

    Smith, A. (1776). An Inquiry into the Nature and Causes of the Wealth of Nations. London: W. Strahan and T. Cadell.

    Yahya,  I.Y. da Ɗangambo, A. (1986). Jagoran Nazarin Hausa. Zaria: Northern Nigeria Publishing Company Limited.

    Yahya, I. Y. da wasu (1992). Darussan Hausa don Manyan Makarantun Sakandare. Ibadan: University Presss Plc.

    Karanta Hanyoyin Zamantakewar Hausawa 

    Edita@rumasau-kallamu

  • Nason Al’adun Baƙi Maƙwabta Na Kusa A Wanzancin Hausawa

    Nason Al’adun Baƙi Maƙwabta Na Kusa A Wanzancin Hausawa

    Wannan babi an yi bayani ne a kan nason al’adun baƙi maƙwabta na kusa waɗanda suka haɗa da Fulani da Barebari da Buzaye da Nufawa da Yarabawa da sauran ƙananan ƙabilu a kan wanzancin Hausawa. Da farko an fara kawo bayani kan ƙaura da shigowar waɗannan baƙi ƙasar Hausa, daga nan kuma sai aka ci gaba da kawo bayanai dangane da fannonin sana’ar wanzanci waɗanda aka sami nason al’adun waɗannan baƙi a cikinsu.

    Shigowar Fulani Ƙasar Hausa

    Mazaunin Fulani na farko a Afrika ta Yamma yana a yankin Senegal, amma a yanzu ana samun su a Chadi da Kamaru da Gambia da Sudan da Habasha (Abubakar, 1977:27). A wannan zamani yawan al’ummar Fulani ya fi miliyan shida kuma fiye da rabinsu suna zaune a Arewacin Nijeriya (Johnston, 1970:20). A lokaci mai tsawo da ya gabata al’ummar Fulani ta kasu zuwa kashi uku. Akwai Fulani Mbororore’en da Fulɓe Na’i da Fulɓe Shi’e.

    Dangane da shigowar Fulani ƙasar Hausa, a haƙiƙa yana da matuƙar wuya a ce ga takamaiman lokacin da suka fara shigowa wannan ƙasa, amma duk da haka manazarta ƙaura da shigowar baƙi ƙasashe sun yi kintacen wata ƙungiyar Fulani maƙaurata ta shigo ƙasar Hausa a farkon ƙarni na goma sha huɗu (Abubakar, 1977:29). Wannan kuwa ya faru ne sakamakon ƙaura da suka yi daga yankin Senegal zuwa gabas domin neman wuraren kiwo masu kyau.

    A farkon ƙarni na goma sha shida akwai al’ummomin Fulani da daman gaske a ko ina cikin ƙasar Hausa. Daga ƙasar Hausa ne wasu Fulani suka yi kudu-maso-gabas har suka kai gewayen kogin Gongola a cikin ƙarni na goma sha bakwai.

    A bayanan da aka samu daga Katsina an bayyana cewa kafin kafuwar mulkin Muhammadu Korau a Katsina cikin shekarun 1450 wasu Fulani da ake kira Sissilɓe (Sulluɓawa) sun baro Futa-Toro da niyyar zuwa Masar, amma sai suka tsaya a Katsina (Nadama, 1977:170). Su ne suka kafa garuruwan Kanwa da Ƙusa da Zandam da Bugaje da Shinkafi a kusa da Birnin Katsina (Usman, 1972:191-192).

    Wasu Fulanin kuma sun haɗa da Yerimawa da Gallawa (Gallanko’en) da Daɓawa da kuma Dallazawa, dukkan su sun sauka a garuruwan da suke iyakar ƙasar Katsina ta gabas. Yerimawa sun mamaye ƙasar Yamel. Su kuma Gallawa sun zauna a arewacin Yamel suka kafa ƙauyen Kantche a cikin Jamhuriyar Nijar.

    Daga nan ne kuma wasu suka matsa gaba suka kafa ƙauyen Daɓawa wanda yake kusa da garin Kaita, wasu kuma zuwa garuruwan Sirika da Gallu, dalilin kiran su da sunan Sirikawa. Daɓawa kuwa sun zauna ne a kan iyakar da, a yanzu ta raba Nijeriya da Jamhuriyar Kanembakashe duk a ƙasar Katsina. Su kuma Dallazawa sun zauna a arewacin wuraren da Yerimawa suka zauna suka kafa ƙauyen Dallaje (Usman, 1972:190-191).

    A cikin ƙarni na goma sha takwas Fulanin da ake yi wa laƙabi da Yerobawa waɗanda daga cikinsu ne ake sa ran Malam Na’Alhaji ya fito, suka shigo ƙasar Katsina. Al’ummar Fulani sun fara shiga ƙasar Kano a lokacin mulkin Sarkin Kano Yakubu (1452-1463), kuma sun fara zama a Ɗanbatta da Rano da Sumaila da Kazaure da dai sauran wurare da dama a cikin Kano da kewayenta (Palmer, 1970:106).

    Akwai kuma wasu Fulani da suka shigo ƙasar Kano don yin yaƙin jihadi a farkon ƙarni na goma sha tara. Waɗannan Fulani ne suka kafa unguwanni Yola da Danbazau da Galadanci da Daneji duk a cikin Birnin Kano (Baƙo, 1990:73). Torankawa Fulani zuri’ar da Shehu Usmanu Ɗanfodiyo ya fito daga cikinta sun sauka a Ƙwanni arewacin ƙasar Zamfara a ƙarƙashin shugabansu Malam Musa Jokollo a cikin shekarun 1450.

    A sakamakon ƙaura da shigowar Fulani ƙasar Hausa an sami wata al’umma wadda a yau ake kira Hausa/Fulani. Wannan kuwa ya faru ne sakamakon cuɗanya da auratayya wadda ake yi a tsakanin waɗannan al’ummomi fiye da dukkan wasu ƙabilu da suke cikin Nijeriya da kuma na maƙwabtanta. Haka kuma ayyukan da masu jihadi suka yi wanda ya haifar da Daular Sakkawato ta ƙara taimakawa wajen samuwar wannan al’umma ta Hausa/Fulani.

    Nason Al’adun Fulani a Kan Wanzancin Hausawa

    A lokacin da Fulani suka shigo ƙasar Hausa sun riƙa gudanar da harkokin rayuwarsu na yau da kullum cikin kwanciyar hankali da lumana. Wannan ne ya ba su damar aiwatar da al’adunsu cikin Hausawa ba tare da fuskantar wasu matsaloli ba. Haka su ma Hausawa da aka tarar a ƙasarsu suna tafiyar da nasu al’adun a kan idanun Fulani. A lokacin da suke yin wasu al’adu kamar bikin aure ko haihuwa da dai sauransu sukan gayyaci juna.

    Watau a lokacin da Fulani suke yi sukan gayyaci Hausawa, haka kuma idan Hausawa suna yi sukan gayyaci Fulanin. Wannan dangantaka ta taimaka ƙwarai wajen musayar al’adu da fahimtar juna a tsakanin waɗannan al’ummomi. A sakamakon haka ne aka riƙa samun nason al’adun Fulani cikin al’adun wanzancin Hausawa. Wannan al’amari ya yi babban naso a kan yadda Hausawa suke tafiyar da al’adun wanzanci musamman yadda ake gudanar da aski da gyaran fuska da cire belun-wuya da tsayar da gemu da kaciya da tsagar kwalliya da dai sauran ayyukan wanzanci.

    Yanzu za a bi diddigin ire-iren waɗannan ayyuka na wanzanci don gano tasirin da al’adun Fulani suka yi a kansu.

    Aski da Gyaran Fuska

    Ta fuskar aski da gyaran fuska al’adun Fulani sun yi tasiri a kan wanzanci musamman ire-iren aski da gyaran fuska da ake yi masu. Su dattawan Fulani askin ƙwaryar molo ake yi masu, a wurin gyaran fuska ne aka sami nason al’adunsu a kan wanzanci. Dattawan Fulani suna yin irin gyaran fuska wanda Hausawa suke kira ƙahon barewa.

    Gyaran Fuska Ƙahon Barewa

    Wannan nau’i na gyaran fuska dattawan Fulani ne ake yi wa irinsa. Ana yin irin wannan gyaran fuska don a aske gashin da yake a wurin fuska da haɓa a lokacin da suma ba ta yi yawan da za a aske ta ba. A wannan lokaci ne sai wanda yake da buƙatar ya je wurin wanzami don a yi masa. A irin wannan gyaran fuska ana gyara gashin da yake wurin goshi a kuma aske dukkan saje tun daga wurin da ya haɗu da sumar kai har zuwa wurin gemu.

    Ba a aske gemu sai dai a kwakkwafe shi ya yi siriri da tsawo. A lokacin da aka zo yin irin wannan gyaran fuska, sumar da take wurin goshi ana kwakkwafe ta har a taɓo wadda take a gefen goshin. Ana ɗan shiga ciki yadda wurin zai yi kyau sosai.

    Irin wannan aski Hausawa musamman dattawa waɗanda suke yin hulɗoɗi da Fulani ko waɗanda suke zaune a wuri ɗaya da Fulani na kwaikwayon yin irinsa. A yanzu ana samun wasu Hausawa a ƙasar Katsina da Kano da Zamfara da cikin Jamhuriyar Nijar waɗanda ake yi wa irin wannan gyaran fuska.

    Tukkayen Fulani

    A lokacin da jariri namiji ya kai kimanin wata biyu zuwa uku da haihuwa ana yi masa tukkaye uku a bisa kansa. Ana yin ɗaya a goshi ɗaya tsakiyar kai ɗayan kuma a ƙeya. Waɗannan tukkaye ba za a aske su ba, sai a ranar da za a yi wa wannan yaro kaciya, wasu ma sukan bar irin waɗannan tukkaye har sai sun girma sosai sun isa aure. Idan suka yi tsawo, sai a riƙa yi masu kitso. Akwai Hausawa waɗanda suke kwaikwayon yi wa ‘ya’yansu ire- iren waɗannan tukkaye, amma su ba sa yi wa ‘ya’yansu kitso.

    Zanƙo

    Wani nau’in aski irin na Fulani wanda ya yi naso cikin al’adun wanzancin Hausawa shi ne zanƙo. Ana yin zanƙo ta hanyar aske gashin kai na ɓangaren hagu da na dama a bar gashin tsakiyar kai kamar layi tun daga goshi har zuwa ga ƙeya.

    Ana yin zanƙo ga yaro namiji ban da mace a aski na biyu bayan askin suna watau askin ya da wanka. A duk lokacin da za a yi wa wannan yaro aski ba a aske wannan zanƙo, sai dai a gyara shi. A al’ada wannan aski na Fulani ne, don kuwa a ƙasar Katsina lokacin da Malam Ummarun Dallaje ya kafa mulkin Fulani a wannan ƙasa zuri’arsa suna yi wa ‘ya’yansu irin wannan aski na zanƙo.

    Daga nan ne wasu daga cikin Hausawan ƙasar Katsina suka riƙa kwaikwayon yin irin wannan aski har ya kai matakin sun mayar da shi askin gado wanda suke yi wa ‘ya’yansu.

    Domin karanta Yadda Tsayar Da Gemu Yake A Al’adar Fulani danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Matsayin Hausawa A Yau

    Matsayin Hausawa A Yau

    Wannan duniya da muke ciki tana ƙunshe da al’ummomi daban-daban masu magana da harsuna da adabi da al’adu mabambanta. An ƙiyasta a yanzu akwai al’ummomi masu magana da harsuna daban-daban kimanin dubu shida da ɗari shida da sittin (6660) a wannan duniya tamu, kuma kowane daga cikin su na cin gashin-kansa. Misali, akwai Larabci da Turancin Ingilishi da na Faransanci da na Jamusanci da Sinanci da Indiyanci da dai sauransu.

    Kowane daga cikin waɗannan harsuna suna da masu yin magana da shi, kuma kowane yana da sigogin yaɗuwarsa. Daga cikin su za a tarar wani harshen masu yin magana da shi ‘yan ɗaruruwa ne a wani tsukin wuri, wani kuma za a tarar mutane ne dubbai suke yin amfani da shi, wani kuma miliyoyi ne waɗanda suka barbazu a wurare na nahiyoyin da suke cikin wannan duniya (Yahaya, 1991:3).

    Idan muka dawo nan gida Afrika akwai al’ummomi daban-daban waɗanda suke magana da harsuna kimanin 1850 wanda harshen Hausa na daga cikinsu. Yana daga cikin harsunan Afrika irinsu Swahili da Mande da Wolof da Ashanti da Yoruba da Bambara da sauransu. Daga waɗannan harsuna 1850 da suke Afrika an tantance an gano akwai kimanin harsuna 394 waɗanda ake yin amfani da su a sassa daban-daban da suke cikin Nijeriya.

    Duk da kasancewar waɗannan harsuna suna da dangantaka da wasunsu kowane daga cikinsu yana zaman kansa a matsayin harshe. Daga cikin harsunan da ake amfani da su a Nijeriya baya ga harshen Hausa akwai Yarbanci da Ibo da Fulatanci da Barbarci da Efik da Nufanci da Ibibio da Tiv da Angas da Edo da Bade da Igala da Idoma da Igbirra da Mandara da Karekare da Kanakuru da sauransu. A halin yanzu ana amfani da waɗannan harsuna a tsakanin al’ummomin da suke magana da su don yin hulɗoɗin rayuwa na yau da kullum (Yahaya, 1991:3-4).

    Hausawa suna daga cikin manyan al’ummomin da suke a wannan duniya a wannan zamani, kuma harshen Hausa wanda Hausawa suke magana da shi a matsayin harshen uwa na daga cikin manyan harsunan wannan duniya. Idan aka ɗebe harshen Larabci, masu magana da harshen Hausa a matsayin harshen uwa sun fi kowace al’umma yawa a duk faɗin Nahiyar Afrika, harshen Swahili ne kaɗai yake yi masa cin dudduge.

    Haka kuma harshen Hausa ne harshen da kowa yake yin magana da shi a mafi yawancin sassan arewacin Nijeriya ciki har da waɗanda ba Hausawa ba (Schuh, 1982:1). A Jamhuriyar Nijar mafi yawancin mutanen wannan ƙasa na magana da harshen Hausa (Hira da AHSA, a garin Agadez, a ranar 8/5/2005).Wannan ya bayyana mana ke nan, masu magana da harshen Hausawa sun fi kowace al’umma yawa a duk faɗin Afrika.

    Idan muka dawo kan batun da muke son magana a kansa watau matsayin Hausawa a yau, za mu ga kamar yadda aka yi bayanai a baya, kasancewar al’ummar Hausawa sun fi kowace al’umma yawa a duk faɗin Afrika, ya taimaka ƙwarai wajen yaɗuwa da haɓakar harshe da adabi da al’adun Hausawa da kuma mamaye na maƙwabtan ƙasar Hausa. Kamar yadda wani ɗan ƙabilar Babur ta jihar Borno ya bayyana min cewa: “Hausawa al’umma ce wadda take mamaye dukkan wata al’umma da ke kusa da ita” (Hira da AYB, a ranar 24/9/2004).

    Wani Badakkare daga Zuru ya bayyana min cewa: “Al’ummar Hausawa da harshensu da al’adunsu da adabinsu suna ƙara haɓaka a kullum, don kuwa ba wani wuri da mutum zai shiga a cikin Nijeriya da kuma ƙasashen waje da ba a san Hausawa ba”(Hira da IIPZ, a garin Zuru, a ranar 18/9/2005).

    Ga kuma ra’ayin wani ɗan ƙabilar Ibo mutumin jihar Anambra kan matsayin Hausawa a yau: ”Al’umma ce mai harshe wanda ake magana da shi a duk faɗin Nijeriya ta Arewa da maƙwabtanta ciki har da ma waɗanda ba Hausawa ba, kuma Hausawa mutane ne masu saurin karɓar baƙi, kuma masu son zaman lafiya”(Hira da DIJ, a Birnin Kabi, a ranar 16/9/2005).

    Haka kuma wani ɗan ƙabilar Ibo daga jihar Abia ya bayyana min cewa: “Hausawa al’umma ce mai yawan gaske, kuma suna samun bunƙasa a duk harkokinsu na rayuwar yau da kullum”(Hira da MAO, a Birnin Kabi, a ranar 16/10/2004).

    Wani Banufe bayyana min ya yi cewa: “Al’ummar Hausawa mutane ne da suka yi fice a dukkan al’amuran duniya, wannan ne ya sa suke da manyan mutanen da duniya ta san da zamansu a wannan zamani”(Hira da MNM, a garin Bida, a ranar 23/9/2004).

    A ra’ayin wani ɗan ƙabilar Ekoi ta jihar Cross Riɓer bayyana min ya yi cewa: “Al’ummar Hausawa mutane ne masu gaskiya da riƙon amana da kuma karɓar baƙi cikin mutunci. Kuma mutane waɗanda suke bin dokokin addininsu sau da ƙafa. Haka kuma harshensu ya yaɗu a kowane lungu da saƙo da yake cikin Nijeriya da maƙwabta (Hira da EEO, a garin Gusau, a ranar 10/9/2005).

    Wata Bayarabiya kuma bayyana min ra’ayinta ta yi kan matsayin Hausawa a yau kamar haka: “Al’ummar Hausawa mutanen kirki ne wanda a yanzu yana da matuƙar muhimmanci ga dukkan ‘yan Nijeriya su koyi harshen Hausa don samun sauƙin tafiyar da harkokin rayuwarsu ta yau da kullum”(Hira da MGAA, a garin Zariya, a ranar 30/9/2004).

    Bisa la’akari da waɗannan ra’ayoyi da waɗanda ba Hausawa ba suka bayar kan matsayin Hausawa a yau, na tabbata za a amince da ni al’ummar Hausawa suna da babban matsayi a wannan zamani a idanun mafi yawancin mutanen da suke cikin Nijeriya da ma waɗanda suke a ƙasashen da suke maƙwabta.

    Haka yake a idanun mutanen da suke ƙasashen da suke nesa da ƙasar Hausa don kuwa a wata hira da na gudanar da wani wanda ya ziyarci Ingila ya bayyana min cewa “A ƙasashen Turai al’ummar Hausawa suna da babban matsayi, kuma ana duban su a matsayin mutanen kirki saboda halayensu masu kyau sun sanya da wuya ka same su suna aikata munanan laifuffuka irinsu sata da zamba cikin aminci da fashi da makami da rashin gaskiya” (Hira da AASD, a garin Katsina, a ranar 14/12/2005.

    Saboda matsayin al’ummar Hausawa da harshensu a wannan zamani ya sa harshen Hausa ya zama na farko daga cikin harsunan Afrika ta Yamma da aka fara rubuce-rubuce da shi. Haka kuma shi ne harshe na farko da aka fara gabatar da labarai da shirye-shirye a gidajen Radiyon ƙasashen waje kamar a Sashen Hausa na BBC London da Muryar Amirka (ƁOA) da Muryar Jamus (Radiyo Deutche Welle) da Radiyo China da Radiyo Alƙahira da Radiyo Iran da dai sauransu (Yahaya, 1991:10 – 11).

    A nan gida kasancewar Hausawa suna da tsararren mulki wanda suka riƙa tafiyar da harkokin rayuwarsu lokaci mai tsawo tun kafin zuwan Turawan Mulkin Mallaka, ya sa sun mamaye fagen siyasar Nijeriya a wannan zamani. A halin yanzu duk wani mai son mulkin ƙasar nan dole sai ya haɗa kai da Hausawa zai ci nasara.

    Saboda haka ne Hausawa a wannan zamani suka shahara a fagen tafiyar da harkokin mulki cikin nasara da kwanciyar hankali, kuma suka zama jagora ga dukkan al’ummomin da suke a cikin wannan ƙasa. A iya ganin haka idan aka waiwaya aka duba waɗanda suka shugabancin Nijeriya tun daga samun mulkin kai zuwa wannan zamani. Daga cikin shugabanni goma sha biyu da suka shugabanci Nijeriya shida ko bakwai daga cikinsu Hausa/Fulani ne.

    Na farko Alhaji Abubakar Tafawa Ɓalewa da Janar Murtala Ramat Muhammad da Alhaji Shehu Usman Aliyu Shagari da Janar Muhammadu Buhari da Janar Ibrahim Badamasi Babangida da Janar Sani Abacha da Janar Abdulsalam Abubakar da kuma Alhaji Ummaru Musa ‘Yar’aduwa.

    Haka kuma a ƙasashe maƙwabta waɗanda Hausawa suka yi ƙaura suka koma, sun sami babban matsayi a waɗannan ƙasashe. Wannan kuwa ya faru ne sakamakon ire-iren gudummuwar da suke bayarwa don ci gaban waɗannan ƙasashe. A ire-iren waɗannan ƙasashe akwai Hausawa da daman gaske waɗanda suka yi fice a harkokin tafiyar da mulki da na soja da na tattalin arziki da na ilimi da dai sauran fannonin rayuwa.

    Misali, a yanzu Mataimakin Shugaban Ƙasar Ghana Alhaji Aliyu Muhammad Bahaushe ne wanda asalinsu mutanen Talatar Mafara ta jihar Zamfara ne. Bayansa akwai ‘Yan Majalisar Dokoki ta Ghana waɗanda Hausawa ne (An samo wannan bayani daga wani rahoto da Idi Ali, Wakilin Sashen Hausa na BBC London a Accra, Ghana).

    Duk da kasancewar al’ummar Hausawa suna da babban matsayi a wannan zamani akwai matsalolin da suke neman dakushe wannan matsayi. Wannan kuwa ya faru ne saboda wasu daga cikin waɗanda suke jagorancin al’ummar Hausawa da kuma wasu waɗanda ake jagoranta na neman su watsar da kyawawan al’adu waɗanda aka san Hausawa da su kamar nuna ƙauna da ‘yan’uwantaka da kara da alkunya da haɗin kai da nuna gaskiya da riƙon amana da dai sauran ire-iren waɗannan kyawawan al’adu.

    A yanzu ire-iren waɗannan Hausawa suna son su zama marasa gaskiya da nuna son kai da son tattara abin duniya da rashin taimaka wa al’umma da rashin haɗin kai da dai sauran munanan abubuwa. Saboda haka matuƙar ba a gyara waɗannan matsaloli ba, to matsayin Hausawa na jagorancin al’ummar Nijeriya zai fita daga hannunsu kuma mutuncinsu ya zube.

    Kamar yadda aka gani, wannan babi an yi bayani a kan farfajiyar ƙasar Hausa jiya da yau. An kuma duba yanaye-yanayen ƙasar Hausa da mutanenta da halin zamantakewarsu da shugabancinsu da addininsu da kuma hanyoyin tattalin arzikinsu da bayani kan ƙaura da shigowar baƙi a sassa daban-daban na ƙasar Hausa da dalilan da suka sanya su zaɓar ƙasar Hausa don yin zama na ci-rani ko zama na dindindin da kuma matsayinsu a yau.

    Don karanta Ƙaura Da Shigowar Baƙi Ƙasar Hausa danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu