Tag: Halin Da Muke Ciki

  • Halin Da Muke Ciki

    Halin Da Muke Ciki

    Sun dai kai mu sun bari sun dawo
    Kuma ni sai nake ga mu muka jawo
    Wani sunansa Baba wani Babawo.

    Alƙawari sukai na za su yi aiki
    Har ma rantsuwar mutanen kirki
    Yau mun wayi kanmu ba imfaƙi.

    Babu tsaro ƙasarmu komin haske
    To in kai dare kwa sai dai waske
    Sai a siye ka tsaf kamar ɗanwake.

    Yau mun wayi kanmu ba jin daɗi
    Wai kuma gwamnati akai tajdidi
    Ko mu sai a lahira jin daɗi?

    Wancan shi ya fara kai mu kushewa
    Muka jure mukai ta daddagewa
    Har ya gama ya bai wa ɗan yarabawa.

    Al’umma tana cikin lahaula
    Babu abinci kana babu sulalla
    Ba nutsuwa gare mu bayin Allah.

    Magidanci babu ba mai ba shi
    Ba mai ba shi sadaka ko bashi
    Kai wallahi dole sai an tashi!

    Yau talakan ƙasarmu ba shi da hali
    Na siyan taliya catorn ko kwali
    Ko shinkafa-kaza ba shi da hali.

    Yau in ya siya ana daɗa kuɗɗi
    Gobe siyanta sai su Alhaji Mudi
    Jibi kwa sai irin gidan ɗanmoɗi.

    Mun ji kuna da bindigar hana bore
    Kuma ku ne da kurkuku mai ƙyaure
    Naman ‘ƴan maza fa shi ne gyare.

    Ku ba kwa sanin muna ƙunci ne?
    Ba ku ganin abin yana yin worse ne?
    Anya ku kwa ma mutane ku ne?

    Ku yi sata amma ku bar mu mu rayu
    Amma kun ci kun hana mu mu rayu
    Ko so duk kuke mu zamma marayu?

    Yanzu a ce abinci ya wuce kanmu
    Ba mu babu cin abin ƙaunarmu
    To wa za ya share duk kukanmu?

    Ba doka ƙasarmu sai kurari
    Sai cewa anai kamar mai bori
    Mu fa aradu sai mu ɗau gorori.

    Abban Marke

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu