Tag: Farfesa Mu’azu Sa’adu

  • Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Daga Salmanu Faris Kudan, Shugaban Ƙungiyar Marubutan Arewa ta Ƙasa Nijeriya

    1.

    A yau mun taru cikin alkunya,

    Domin girmama gwarzonmu mai dubayya,

    Haske ya sake yalwata cikin Hausaniya,

    Da samun Farfesa Mu’azu a mai kyan halayya.

    2.

    Ka jima kana hura wutar hikima,

    Kana tsarkake harshenmu ba taƙama,

    A makarantu sun ɗauki darusa ba gardama,

    Sun zame wa ɗalibai hasken tafarki mai tsunduma.

    3.

    Mu’azu Sa’adu, ginshiƙin Hausar mu ta dauri,

    Ka ɗaukaka harshen da kakanni suka bari.

    A yau an saka maka rawanin girma tuturi,

    Ka zama damina mai sanyaya shuka ba fari.

    4.

    Salmanu Faris Kudan na taya ka murna,

    Da wannan matsayi mai jan hankalina,

    A madadin marubutan Arewan zaurena,

    Muna yi maka fatan ƙarin nasarori da zayyana.

    5.

    Girmanka ya zama abin jingina ba wariya,

    Ƙwararrun marubuta suna sanya ka a zuciya.

    Ka zama tubalin da ya ƙara ɗaure ginin Hausaniya,

    Harshen da ke ɗaukaka Arewa da Nijeriya.

    6.

    Muna yi maka addu’ar fatan alheri,

    Rayuwa mai cike da ƙarin annuri.

    Allah Ya saka maka cikin mafi alheri,

    Ya ƙara nisan kwana bisa tsari.

    Karanta Waƙar Murnar Zama Farfesa Ga Mu’azu Sa’adu Muhammad

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Associate Professor Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Tarihin Associate Professor Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    An haifi Dr. Mu’azu Sa’adu Muhammad a ranar 13/3/1964 a unguwar Tsauni garin Kudan, Ƙaramar hukumar Kudan Jihar Kaduna. Mahaifinsa Malam Adamu Muhammad (Andiyo) mahaifiyarsa Zainab (Tadabai) Bashir Kudan.Ya zauna a Kano ƙofar Nasarawa wajen wani kakansa Alhaji Aliyu Gwarzo, ya yi karatun allo daga shekara 1969 – 1972, ya dawo Kudan 1972, ya shiga firamare 1973-1979, ya wuce Sakandiren Gwamnati ta Kagoro a ranar Alhamis 24/11/1979-15/09/1981, sai Sakandaren Gwamnati ta Maƙarfi 18/09/1981-01/06/1984. (G.C.E).

    Ya wuce kwalejin zurfafa ilimi (C.A.S) Zariya 15/01/1985- 10/08/1987 (I.J.M.B), sai ya kama aiki da hukumar ba da tallafin karatu ta Jihar Kaduna (Kaduna State Scholarship Board) a sashen kuɗi (Account Section) 09/02/1988 -15/02/1995. Ya wuce ƙaro karatu digirin farko a Jami’ar Usman ɗan Fodiyo Sakkwato 30/7/1994 -31/05/1998. (B.A Hausa).

    Ya koma ma’aikatar ilimi ta Jihar Kaduna (Ministry of Education) a sashen mulki (Admin. Section)15/02/1995-2003, ya koma Jami’ar Sakkwato yin digiri na biyu (M.A Hausa) 2/09/2003 -07/09/2007. Ya koma Kwalejin Tunawa da Sardauna Kaduna 18/12/2003 a matsayin malami.

    Ya yi ritaya a 31/1/2010 yana da shekaru 22 a aikin gwamnati. Ya yi sana’ar tela shekara 30, 1977-2007. Ya koma Jami’ar Sakkwato 12/04/2011-07/11/2015 Yin digiri na uku Ph.D Hausa. Ya yi aure ranar 11/3/1990 yana da ‘ya’ya goma (10).

    Sunayen matan 5 

    1. Asma’u.

    2. Ummukhulsum

    3. Zainab

    4. Hafsat

    5. Fatima

    Sunayen mazan 5

    1.Muhammad Bashir

    2. Abubakar Sadik

    3. Umar Faruk

    4. Suleman

    5. Muhammad Irfan

    Ya yi aikace- aikacen wucin-gadi na koyarwa a:-

    Sashen remidial (KASU) Jami’ar Jihar Kaduna 2007-2008

    2. Kwalejin Adeyemo (Adeyemo College) Kaduna 2009 zuwa 2010.

    3. Kwalejin Shabab (Shabab College of Arabic and Islamic Studies) U/Dosa Kaduna 2006-2010

    4. Kwalejin Albidaya (Albidaya College) Kaduna 2013- 2014.

    5. Ya zama malami Jami’ar Sule Lamido Kafin Hausa Jihar Jigawa 2014-Zuwa yau. A yanzu haka, shi ne shugaban sashin harsunan Najeriya na jami’ar Sule Lamiɗo da ke kafin Hausa ta jihar Jigawa.

    Sunayen maƙalolin sa

    1. Muhammad M.S.(2019); Juga Nabiso. . Takardar da ya gabatar da ita a international Conference da ke jami’ar jihar Kaduna.

    2. Muhammad M.S.(2017); Tashe Majigin Bahaushe. Takardar da ya gabatar da ita a taron shekara-shekara karo na (4th Annual International Conference) a jami’ar jihar Kaduna.

    3. Muhammad M.S.(2017); Muhammadu Ashiru Sarkin Kudan. Takardar da ya gabatar da ita a taron shekara-shekara karo na uku (3rd Annual International Conference) da ke jami’ar jihar Kaduna.

    4.Muhammad M.S.(2019); Kasuwa A Kai Miki Dole: A University Research sponsored by the Sule Lamido University Kafin Hausa.

    5. Muhammad M.S; Sakin Na Hannu. Hausa Prose-Fiction Reader Project. Association of Nigerian Authors, Kano State Branch.

    6.Muhammad M.S; Dabbobi A Tunanin Bahaushe (Ph.D Thesis 2016).

    7. Muhammad M.S; Effect Of Football (P.G.D.E Project 2010).

    8. Muhammad M.S; Hauka A Idon Bahaushe (M.A Disertation 2007).

    9. Muhammad M.S; Zumuncin Bahaushe (B.A Project 1997).

    10. Muhammad M.S; Ire-Iren Abincin Hausawa (I.J.M.B Project 1987).

    11. Muhammad M.S; Kasuwa A Kai maki dole(SLU University Research 2018)

    12. Muhammad M.S; Jirwayen Maguzanci A Rayuwar Mu Ta Yau.

    13. Muhammad M.S; Bauta Da Cinikin Bayi

    14. Muhammad M.S; Kagaggen Zumunci.

    15. Muhammad M.S; Wace Ce Mace ?

    16. Riga-kafi Ya fi Magani

    17. Muhammad M.S; Jibadau Kayan Nauyi (Wanda Yace Babu Yi Masa Aka Yi)

    18. Muhammad M.S; Ballagazar Uwa

    19. Muhammad M.S; Baƙin Bature (Baƙin Mutum Da Kan Banasare)

    20. Saɓalikita Mijin Hajiya (Sunɓulallen Uba)

    21. Ƙawalliya Romon Jaɓa.

    22. Ilimi Farkonka Maɗaci ƙarshenka Zuma.

    23. Maraya da Maraici A Yau – 2014.

    24. Rowa. (Hali, Wayau, Ko Ciwo?).

    25. Kyauta. (Ɗabi’a Ko Baiwa Ko Wauta?).

    26. Ɗa, Na Kowa Ne.

    27. Me Ka Fi, Me Ya Fi Ka, Me Kuke Dai-dai ?

    28. Dokin Zuciya, Ba A Hawanka Sai An Yi Nadama.

    29. Halayen Dabbobi A Bakin Narambaɗa.

    Sunayen Litittafansa 

    1. Bahaushiyar Al’ada.

    2. Tsufa Rigar ƙaya.

    3. Maraya da Maraici.

    4. Mace Babbar Halitta.

    5. Maza Gumbar Dutse.

    6. Haƙƙoki Abin Kulawa.

    7. Ƙuruciya A Al’adar Bahaushe.

    8. Sana’a Sa’a

    9. Tarihin Garin Kudan.

    10. Ziyara A Musulunci.

    11. Zuciya Sarauniya ce.

    Lambobin yabo

    1. Ƙungiyar ɗalibai na jihar Kaduna wanda suke karatu a Jami’ar Usman ɗanfodio a 1997.

    2. Ƙungiyar ɗalibai ta Hausa na Jami’ar Usman Ɗanfodio sokoto a 1997.

    3. Darul tahfizul ƙur’anil kareem Islamiyya Unguwar Dosa Kaduna a 2006.

    4.Markazul Alh Adamu Liddarasatul Islamiyya Unguwar Dosa Kaduna a 2007.

    5. Age Mate association Kafin Hausa a 2019.

    6. Arewa Writers Association of Nigeria (AWAN).

    Sannan kuma, a yanzu halin da ake ciki yana da mataye guda biyu, wato ya ƙara aure. Sannan kuma ya zama mataimakin Farfesa (Associate Professor).

    (Mun samu waɗannan jawaban ne daga Dr. Mu`azu Sa’adu Muhammad Kudan ta hanyar rubutawa da ya yi, ya turo min ta imail ɗi na a ranar Alhamis 02/07/2020).

    Domin karanta rayuwar ‘ya mace a ƙasashen turai da kuma a musulunci danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu