Tag: A murɗe

  • Duka A Murɗe

    Duka A Murɗe

    Afwan yau jikin kamar wani mai laulayi

    Haka na yini ta har daren Allah haka na yi

    Ban aika ba babu wanda kuma nace ya yi

    Shi ai so fa ba abin dama ba ya yi.

     

    Ita waccen tana faɗin ni ce taka ɗai

    ‘Ƴar dangi na faɗin ba mai min kwaɗai

    Abba fa nawa ne ki jini na ni ni kaɗai

    Gogan naku ko yana kwance kishingiɗe

     

    Babu fa wanda za ya ce bai son nasa kam

    Sai dai in ya zam yana ɓoyewa kurum

    Ba a makara idan handset kwai alarm

    Babu ruwansa sai ya yo ma ƙara daram.

     

    Maganar gaskiya fa waccen na riƙa sila

    Tun da kamar muna ƙanana fa ya ‘ƴan shila

    Ba ko hantara bare zancen matsala

    Tun ma kan tsayinta ɗinnan fa ya kammala

     

    Haka siddan ki zo ki ce sai min banƙara

    Daga haddar izawaƙa kika nufi baƙƙara

    Kika bar nan kika wuce ƙarshen saɗɗara

    Fazuƙu falan-nazidkum ki yi hattara.

     

    Maganar gaskiya kamata fa ki hanƙura

    Tinda gidanku na sani ba mai takura

    Ba mai ji kama da kamun da ta kumbura

    Ko mai na ci ya beban da ya ke bara.

     

    Kin ga fa ni gidanmu ni ne ɗai salimi

    Kar fa ki sa mutan gidajenmu a zullumi

    Kar ki bari na dinga jin zafi ba gumi

    Sai dai in jikin ga nau to da akwai shimi

     

    Kin ga idan akwai rabo wataƙil za ya zo

    Ko duk duniya su taru su yo dandazo

    In dai Rabbi ya hana to dai ba ya zo

    Ba na son kira a ce min to je ka zo.

     

    Tabbas na sani kina so na Mahira

    Kuma ni ma fa da hakan take ya Ɗahira

    Amma yanzu kam a ƙyale ni na tsahira

    Ɗandagus da shi da Ɗanbello Jira! Jira!!

     

    Afwan ni fa ba na yin ƙusƙus duk dare

    In ka ganni kan icen kuka maza ɗare

    Ba akuya kana sannan kuma ba kare

    Sai ‘ƴa’ƴan fire a mota fal maƙare.

     

    Afwan duk da na sani ba kya jin bari

    Mai suna Karima ce aka cewa Kari

    Mai son shi a kai shi police bai jin bari

    Sai ya je shi dole wata ƙila da ma mari.

     

    Allah ya sani fa ba so ne ba na yi

    Da harawa da garera a haɗa da ƙamayi

    Duk akuyar da tai ta kushe haka so ta yi

    Tattauna shi gunta ko ba ranar ta yi.

     

    Domin ni fa ɗan titis nake sam ba nawi

    Ba Li’irab bare a ce mini annahawi

    Shi farce yana da aiki ran ƙaiƙayi

    Allah dai ya sa abin da ake so na yi.

     

    Abban Marke

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu