Tag: Mijin Marigayiya

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Huɗu

    Kwanci tashi cikin wannan rayuwar da Khadeeja take a gidan Mustapha har ta gama level 2 a karatunta ta shiga level 3, kuma shekararsu biyu kenan da Rashida mai aikinta. Zaman dai haka ake yinsa cikin dagewa da dagiya; idan Mustapha yana son buƙatarsa a wajenta sai ta ji kamar ba shi ba saboda yanda yake kwantar da kai ya samu buƙatarsa ta biya.

    Amma kuma da zarar ta yi maganar karatunta ko wani abu da zai sa ta fita daga gidan ba tare da ta tafi da yara ba to sai ya nuna ɓacin ransa. Domin a halin yanzu kowa a danginsu ya santa da ‘yayanta domin tare ake ganinsu ko bikin wa ake yi. Gidan Mommy kuwa sun mayar da shi kamar gidan kakarsu, kuma da yake sun sami karɓuwa sai suka sake sakewa.

    Karatunta yana tafiya daidai tunda ta saka auduga ta toshe kunnenta daga duk wata mita ta Mustapha, sai dai kawai kullum a gajiye take daga aikin gida da kuma aikin tunanin abinda za ta yi Mustapha ya daina nuna mata halin ko in kula. Yaran ba su saba ba ta matsala ba a da, amma zuwa yanzu duk tana neman ta rasa kansu; musamman Afaf da Nasreen.

    Idan dai aiki ta saka su ba za su ce ba za su yi ba amma idan ba su ga dama haka za su yi kunnen uwar shegu da ita sai dai ko ta yi aikinta ko kuma ta sa Rashida ta yi mata. Sannan kuma yanzu Afaf ta ƙulla ƙawance da Samira ‘yar wajen Yaya Jidda, don haka kusan duk wani motsi na Khadeeja Afaf sai ta gayawa Samira wadda take kai wa uwarta rahoto na kai tsaye; don haka ne ma matsawar da Yaya Jidda take wa Khadeejan ta ƙaru.

    Sai dai a yanzu ba wannan ne damuwar Khadeeja ba, babbar damuwarta ita ce rashin haihuwa. Tun bayan da ta yi ɓari a loakcin corona ko ɓatan wata ba ta sake yi ba ga shi ana neman shekaru biyu. Zaman gidan ba ya mata daɗi, ba ta jin daɗin yanda yaran suke mata, musamman Afaf wadda a da take tunanin sun zama ɗaya. Tana fatan ita ma Allah ya ba ta nata ‘yayan waɗanda za su kalle ta a matsayin uwa.

    Ta riga shi kwanciya kamar yanda suka saba saboda yanda ta kula idan ta zauna jiransa su kwanta tare ita ake cuta tunda dole ta tashi kafin asuba ta shirya yara. Sai wajen sha biyu saura sanna ya gama abinda yake ya kwanta a kusa da ita, ta juya ta gyara kwanciyarta.

    Yana kwance amma ya ɗaga waya yana chattinga kamar yanda ‘yan kwanakin nan ta kula kullum kafin ya kwanta sai ya yi chatting. Ta miƙe ta je ta yiwo fitsari, ta sha ruwa sannan ta dawo ta kwanta, zuwa lokacin ya gama chatting ɗin ya ajiye wayar yana azkar. Ta kwanta ta gyara kwanciyarta, bayan da ta kula ya gama azkar ɗin ta lalubo hannunsa ta riƙe cikin sanyin murya tace ‘Abban Afaf.’

    ‘Umm.’ Ya amsa yana kallonta duk da hasken da yake cikin ɗakin bai kai ya kawo ba. ‘Uhm, gaskiya ina son zuwa asibiti na ga gynae doctor.’ Ta faɗa tana wasa da hannunsa wanda ta riƙe. Ya riƙe hannunta a cikin nasa ya ƙara ba ta hankalinsa yace ‘Baki da lafiya ne?’

    ‘No ba wani specific issue. Ka san dai kwanaki nace maka ina son na je a duba a ga abinda yasa har yanzu ban sake samun ciki ba, kada na je wata matsala ce na yi ta zama gara na je a duba. Ya gyara kwanciya ya ƙara matsowa kusa da ita ‘Kina dai so ki ɗorawa kanki damuwa, har yanzu fa ba a yi shekaru biyu da ɓarin ba.

    Iya wannan ya isa ya sa ki san cewa lafiyarki ƙalau, kawai Allah ne bai kawo ba tunda wancan ɗin ma ba asibiti kika je kika samo ba ko? Na sani, amma dai gaskiya ina so na je a duba ni ɗin na sami nutsuwa. Tunda ka ga idan na je aka ce min lafiyata ƙalau ai dawowa zan yi kawai na cigaba da addua’a, idan kuma matsala ce sa na nemi maganinta.’

    ‘Babu wata matsala kina dai son tonowa kanki matsalar. Ke yanzu ma da kike neman ciki ido rufe ya za ki yi da karatun? Tunda ga shi kin shiga level 3 kuma ke da kanki kina cewa ya fi wahala. Ya za ki yi da laulayi ga karatu? Ko har kin mata ne? Ai zai fi sauƙi idan ma dole ne sai kin je asibitin ki bari ki gama karatun kafin ki kwantar da kanki.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, kowa da abinda yake tunani. Jimawa kaɗan tace ‘Ina son zuwa gaskiya, amma dai ina jin zan bari mu gama exams ɗin wannan semester in ya so kafin a koma hutu sai na samu na je. To Allah ya kai mu.  Tana son ta haihu duk da dai Mommy ma tace mata lafiyarta ƙalau amma ita gaskiya tana so ta je a duba ta.

    Kuma yanda Mustapha yake gwada mata halin ko in kula idan ana maganar haihuwa ya sa gaba ɗaya ta fara tunanin ko bai damu da ta haihu ba; to ya ma za a yi ya so ta haihu tunda shi masoyiyarsa ta haifar masa yara har uku? Haka ta yi ta saƙe-saƙe tana juyi, sai gefin asuba sannan bacci ya ɗauke ta.

    Kamar kullum yana shiga office ɗin yau ma damuwarsa ta yaye; musamman yanda ƙamshin turarenta ya yi wa ƙofofin hancinsa maraba bayan da ya shiga office ɗin nasa ya rufo ƙofar. Wannan ya tabbatar masa da cewa ta riga ta zo office ɗin wataƙila wani office ɗin ta je. Ya ajiye jakarsa a kan table ya ƙarasa ya zauna a kan kujerarsa cike da farin ciki.

    Sabuwar sakatariyarsa Naja’atu Musa Bello; watanta uku da fara aiki amma soyayya mai ƙarfi ta ƙullu a tsakanisu. Duk wata damuwa da Khadeeja za ta ɗora masa da ya shigo office ɗin ya ganta yake mantawa da ita, idan kuma an tashi daga office ko a ranakun da babu aiki ya kan je gidansu zance. Duk da dai manya ba su riga sun shiga zancen ba amma dai yana ji a jikinsa Naja’atu tasa ce.

    Bai daɗe da zama ba ta turo kofar ta shigo, daga tsaye ta sakar masa kyakkyawan murmushinta wanda ba ya gajiya da kalla. ‘Ranka ya daɗe barka da shigowa.’ Ta faɗa tana juya ƙwayar idonta. ‘Good Morning my dear.’ Ya amsa yana ta faman murmushin da yake barazanar ƙarawa bakinsa faɗi.

    Ta ƙarasa ta zauna a kujerar gabansa, sannan ta ɗauki file a kan teburin ta miƙa masa. Nan take ya buɗa ya fara karantawa yana mata tambayoyi tana yi masa bayani. Bayan sun gama ya ajiye file ɗin a gefe ya dube ta yace ‘To meye labari? Ta yi dariya ta sunkuyar da kai a kunyace tace ‘Komai normal. Good. So na yi mana order ɗin lunch ko? Don na san ko an ce ki zo mu je mu ci a waje ba kya son zuwa eateries, sai shopping ko?’

    Ta yi dariya tace ‘Gara dai a yi order ɗin. Ba damuwa, ki yi mana order ɗin sai ki turo min account number na tura kuɗin.’ Yes Boss, an gama. Suka yi dariya gaba ɗaya. Tana shirin tashi yace ‘Yauwa, gobe ana open day a school ɗin su Afaf, please idan kika shigo around 10am sai ki je musu, ki jiyo min duk bayanansu da performances ɗin su.’

    Ta gyara zama tace ‘Uhm, ok. But Madam ba ta nan ne ko ba ta jin daɗi? Ya gyara zama ya fara lilo a kujerar da yake kai yana kallonta sosai sanna yace ‘No, lafiyarta ƙalau but na dai fi son ke ki je ki jiyo min komai. Cike da farin ciki ta sake faɗaɗa murmushinta tace ‘Yes Sir, Allah ya kai mu. Kuma Allah ya sa kada ka sa yayata ta ba ni query saboda na shiga aikinta duk da dai ni ma ‘yayana ne.’

    Ya yi dariya ‘Kada ki damu, ba ki da matsala da ita. Suka sake ɗan taɓa hira sannan ta fice ta koma office ɗinta cike da farin cikin yanda alaƙarsu take tafiya ita da ogan nata. Ba za ta taɓa bari Mustapha ya kufce mata ba don ta ga mijin aure. Ta gama degree ɗinta har ta yi masters, saurayinta na ƙarshe har sun zo gaisuwa haka kawai ya daina zuwa sai ji kawai ta yi ana bikinsa da ‘yar uwarsa.

    Duk da ta san ba wasu shekaru ne da ita masu yawa ba domin shekarunta 28 kacal, amma dai ta san an matsu ta yi aure a gidansu; musammam ummanta wadda aikin ma so ta yi ta hana ta sai ta yi aure. Sai ga shi ashe mijin yana wajen aikin. A hankali suka saba, har suka kai yanzu da take jin za ta iya cewa ta fi matarsa sanin halin da yake ciki da inda yake a kowanne lokaci.

    Don haka ma take jin cewa ƙwace shi a wajen Khadeeja kamar ƙwace goruba ne a hannun kuturu, domin tun yanzu tana jin ta fara samun nasara tunda kullum ita yake kawowa ƙarar Khadeejan sai ta ba shi haƙuri, ta riga ta fahimci irin zaman da suke yi da Khadeejan don haka ta gama shirya musu; lokaci kawai take jira.

    Ƙarfe sha ɗaya take da lecture don haka sai da ta gama shirya yaran dukansu suka fita makaranta sannan ita ma ta ƙarasa ayyukanta ta shirya. Ƙarfe goma da minti biyar tana zaune a gaban mudubi tana gyara fuska ta tuna jiya da daddare Shukra ta ce mata Anty tace kowa ya zo da Mommy ɗinsa open day 9am to 11am sannan sai a zarce da sports.

    Kuma idan dai ba ta manta ba ma Afaf ta gaya mata duk da section ɗin su Afaf ɗin daban da na su Shukra. Sai dai ba su yi maganar da Abbansu ba, bai gaya mata ita ce za ta je ko shi ne zai je ba gaba ɗaya ta manta ba ta tambaye shi ba. Ta miƙe ta ɗauko wayarta wadda take ajiye a gefen gado ta dannan masa kira.

    Sai da ta kirawo sau uku duka wayar ba ta shiga ba, don haka ta yanke hukuncin idan ta fita sai ta fara tsayawa a makarantar tasu tukunna kada ta je sai ta wuce makaranta ya bugo waya yace ita ce za ta je ya jiƙa mata aiki. Nan da nan ta ƙarasa shiryawa ta saka jilbab ɗinta me kalar lilac sanna ta saka baƙin sneakers ɗinta ta sallami Rashida sannan ta wuce.

    Tana zuwa makarantar kai tsaye ajinsu Shukra ta wuce, duk malaman nasu sun santa saboda zuwa ɗaukansu don haka ba tare da ɓata lokaci ba aka ba ta bayanan Shukra da kuma results ɗinta na CA. Tana gamawa ta ja hannun Shukra suka wuce ajinsu Nasreen inda nan ma aka haɗa mata komai, Nasreen tana cikin waɗanda za su yi wasan tsere don haka ba ta samu ta fita daga aji ba Khadeeja ta ja Shukra suka nufi secondary section don ta karɓo sakamakon Afaf da Habib.

    Tun kafin su ƙarasa kofar secondary section ɗin ta hango Afaf tare da wata mata sanye da baƙar abaya da brown envelops a hannunta, suna tafe suna hira; ga dukkan alamu a dai malama ce a nan makarantar duk da ita Khadeeja ba ta taɓa ganinta ba. Da suka ƙara matsowa kusa Shukra ta zare hannunta daga na Khadeeja tana cewa ‘La, Anti Naja ce ga su nan ita da Yaya Afaf.’ Ta ƙarasa wajensu da gudu.

    Da fara’arta ta cimmusu, suna haɗuwa ta ƙara faɗaɗa murmushinta cike da girmamawa tace ‘Sannu Anti. Cike da mamaki ita ma ta ɗan yage baki mai kama da murmushi tace ‘Yauwa, sannunmu. Ya aiki ya yaran?’ ta kula da yanda ta ke magana kamar da ƙyar don haka kafin ma ta ba ta amsa ta mayar da hankalinta ga Afaf tace ‘Yaya Afafa mu je na karɓo muku CA report ɗinku ke da Habib na wuce don ni ma school zan je.’

    Ta ɗan ɗaga gira cikin halin ko in kula tace ‘Anti Naja ta karɓar mana ai, dama na su Shukra za ta je ta karɓa yanzu. Ta kalli Afaf ɗin sannan ta kalli malamar da aka kira Anti Naja tana mamaki tace ‘Me yasa? Anti ai da kin bar shi na zo gashi sun saka ki aiki. Ta kawar da kai ta ɗaga gira tana cewa ‘No ba wani aiki, ai Abbansu ne yace na karɓar musu.’

    Ita ma Khadeeja ta dan zaro ido tace ‘Oh, ya zo kenan ko yaushe yace a karɓar musu?’ Afaf ta fahimci Khadeeja ba ta san Naja ba kuma ba ta ma san da zamanta ba, sabanin ita da ƙannenta waɗanda a cikinsu za ta iya cewa Shukra ce kawai ba ta san Naja ba ko kuma ta santa amma ba ta san wacece ita ba. Ta ɗan yi gyaran murya tace ‘Anti ba fa malamarmu ba ce, sakatariyar Abba ce kuma shi ne ya turo ta daga office ta zo mana open day ɗin.’

    Mamakin Khaddeja ya ƙaru, ta sake ƙarewa Naja kallo na ɗan takaitaccen lokaci sannan ta buɗe baki za ta yi magana sai kuma ta fasa. Ta ɗan yi murmushi da gefen baki sannan ta kalli ƙasa ta ɗago suka haɗa ido da Najan wadda take mata kallon da ta kasa fassarawa sanna tace ‘Oh, ok, Umm.’

    Kafin ta ce wani abu Habib ya ƙaraso wajen yace ‘Yauwa Anti kin ƙaraso? Dama ke nake jira; don Allah zo mu je ki cewa uncle ni ba na son basket ball team ya bar ni na shiga football team. Haka kawai wai saboda ni dogo ne sai na yi basketball. Kafin Khadeeja ta yi magana Najan tace ‘Au shi ne ba ka gaya min ba Habib, ai da ka gaya min na yi masa magana.

    Dama Anti nake jira.’ Ya faɗa cikin halin ko in kula ya zari envelop guda ɗaya daga hannun Najan ya miƙawa Khadija yana dariya yace ‘Anti guess what? Ta ɗan yi murmushi yayin da suka bar Naja da baki buɗe, tace ‘What? Ya zaro takarda ɗaya ya miƙa mata yana cewa 38 naci a Hausa yau don haka yau da shawarma zan yi dinner ko?’

    Ta karɓa tana dariya sannan ta ba shi hannu suka tafa tace ‘Iyye, ai dole ka ci shawarma tunda yau ka wuce gori. Haba ko kai fa, kullum komai ka ci A da B amma a Hausa ka dinga cin D da F. Ya miƙawa Khaddeja envelop ɗin yana cewa ‘To za ki ga Uncle ɗin? Tace ‘No, tunda yanzu ka ga kun riga kun fara games ina jin ka bari sai gobe sai na zo na gan shi.

    Kafin nan mun tattauna a kan football da basketball ɗin kuma mun yi magana da Abbanka ko? Ya gyada kai ‘Eh, haka ne. Naja ta yi sauri tace ‘Idan kina sauri ne ai sai na je naga Uncle ɗin. Tace ‘No ba sauri nake ba, kamar dai goben zai fi dacewa kawai. Habib ya katse su yana miƙawa Khadeeja envelope ɗin yana cewa ‘Anti sai mun dawo, goben kya zo kawai.’ Ya wuce ya bar su a nan.

    Naja ta miƙawa Khadeeja hannu tana cewa ‘Ki kawo na tafi wa da yallaɓai takardun tunda office zan koma. Ta ɗan yi murmushi tace ‘No ina ga gara ni na tafi masa da su tunda a gidansa zan kwana. Ta ɓata rai tace ‘Um, sai an jima. Ta wuce riƙe da takardun Afaf da suke hannunta Afaf ɗin tana biye da ita suna hira.

    Khadeeja ta bi bayansu da kallo tana mamaki; to yaushe ya yi sabuwar sakatariya? Tunda da dai ta san sakatarensa namiji ne. kuma har yaushe sakatariyar ta kai matsayin ta zo wa yara open day har tana wani cewa a ba ta takardu ta kai masa? Tukunna ma; kamar dai yaran nan sun sa wannan sakatariyar, ita ce ba ta santa ba.

    To kenan har ya yi introducing ɗinta a wajen yaransa a matsayinta na wa? Me yasa suka kwana tare bai ce mata tazo open day ba kuma bayan ya fita ma ya kasa kiranta? Wanda tunda ta aure shi duk wata harkar makarantar yara ita ce take zuwa kuma shi yake saka ta ta zo. To me yasa wannan ya sa sakatariya? Naja? Ba ta son ta yanke hukunci cewa akwai wani abu tsakanin Mustapha da Naja amma dai tabbas tana da tarin tambayin da zai amsa mata.

    Sai da ta raka Shukra aji sannan ta nufi fita daga makarantar. Tun kafin ta gama fitowa daga cikin ginin makarantar zuwa farfajiyar wajen da ake ajiye motoci ta hango su, tana riƙe da hannun Afaf suna magana har suka ƙarasa bakin motar gefen direba ta sa mukulli ta buɗa motar; ta dan ja baya ta labe. Me take gani ne? Motar Mustapha? To shine ya kawo ta ko me? Tana nan a laɓe ta hango su; Naja ta buɗe motar ta zauna a kujerar direba sannan ta yi wa Afaf sallama ta ja motar.

    Sai da ta karanta lambar motar a fili domin ƙara tabbatarwa motar Mustapha ce; kanta ya ɗaure gaba ɗaya. To me hakan yake nufi? Ya aiko sakatariyarsa ta zo wa yara open day kuma a motarsa. To haɗa kuɗi suka yi suka sayi motar a tare? Ko kuwa dai tsabar ƙauna ce ko rashin hankali ya sa suke sharing motarsa da sakatariya? Me yasa bai aiko ta a motar haya ba ko a motar office? Wato motar da ita idan dai makaranta za ta ko a rage mata hanya ba ta isa ya yi ba ita ce ya ba wa sakatariya take yawo a gari.

    Kai! Gaskiya Mustapha ya raina ta. Ta yi sauri ta fito daga inda ta raɓe lokacin da ta hango Afaf ta nufo wajen. Ta yi mata sallama sannan ta wuce ta fice daga harabar makarantar. A bakin titi ta tsaya, motocin haya sai tsayawa suke ba tare da ta hau ba; gaba ɗaya ma ta manta inda za ta saboda yanda zuciyarta take zafi; me Mustapha yake nufi da ita?

    Har ta juya za ta koma gida saboda yanda take jin ba za ta iya zuwa lecture ɗin ba sai kuma ta tuna idan ta je gidan me za ta yi? Rufe kanta kawai za ta yi a ɗaki ta yi kukan da ba zai mata maganin komai ba; don haka ta sake juyawa ta koma bakin titi ta hau motar BUK. Ta kalli waje ta tagar motar, ta yi murmushi ita kaɗai; wai ita ce a motar haya yayin da ga wata can tana yawo a motar mijinta.

    Ta kawar da kai ta share ƙwalla. Ko da ta ƙarasa makarantar ta san an riga an yi nisa da lecture ɗin kuma ko ta shiga ma ta san babu abinda za ta gane, don haka kai tsaye ta wuce hostel ɗakinsu Rahma inda suka saba zuwa su huta; duk da dai ta san suna wajen lecture amma ta san inda suke ajiye mukullansu. Tana shiga ɗakin ta yi watsi da kayanta ta faɗa gadon Rahma ta kwanta ta fashe da kuka.

    Sai wajen ƙarfe ɗaya da kwata sanna suka shigo ɗakin suka same ta a kwance ta ci kuka ta ƙoshi. Suna shiga Farida tace ‘Haba Malama, tun ɗazu muke kiranki a waya kin ƙi ɗaga wa ashe kina nan abunki. Suka ƙarasa suka faɗa kanta Asiya tace ‘Ko dai abun ya zo ne a tanadi goro da ledar amai. Ta sake fashewa da sabon kuka.

    Suka yi tsuru-tsuru. Rahma ta shafa bayanta tace ‘Kawata kina faɗar mana da gaba fa, don Allah me ya faru? Ko Babe ba shi da lafiya ne? Haka suka yita jero mata tambayoyi, ita kuwa ta yi banza da su har suma suka gaji suka yi shiru, suka zauna kawai suna jiranta. Sai da ta yi mai isarta sannan ta ba su labarin abinda ya faru.

    Rahma tace ‘kada fa na yi ashar ƙawata, kut! Wannan wanne kalar wulaƙanci ne mutumin nan yake miki? Farida tace ‘Motar da yake ƙyashin ɗaukanki ya je ya ba wa budurwa ko ma karuwa take yawo a titi? Lallai an gaida uban Afaf. Rahma tace ‘Gaskiya idan ya dawo yau ya kamata ya yi miki bayani na ganewa, duk da babu wani explanatin da zai sa na yarda babu wani abu a tsakanishi da ita ba sakatariya ba ko DG ce wallahi.

    Ya yi miki bayani kuma kema ki karanta masa; wannan ai zubar da mutunci ne kina yawo a motar haya wata side chick tana yawo a motar mijinki? Mijinki na sunna fa, Haba! Gaskiya dai ya kamata ki san yanda za ki yi ki ƙwaci kanki a hannun mutumin nana tunda shi ga alama bai san mutunci ba.’

    Amina tace ‘Don Allah ku bar ta ta bi abun a hankali. Ta kalle ta rai a ɓace ‘A hankali Amina? Shi a hankali kika ga yana yi min? Ni budurwarsa take cewa wai na kawo takardun yara ta kai masa saboda tsabar samun waje? Haba mana! Farida tace ‘Toh shi dai na gani, aure ai ba hauka ba ne. Wallahi ya kamata ki dage ki gaya masa abinda yake ranki tunda dai an daɗe ana ruwa ƙasa tana shanyewa, ai ba siyo ki ya yi a bakin rimi ba da zai mayar da ke kamar wata sokuwa.’

    Amina tace ‘Don Allah ku bari a bi abun a hankali, miji fa ba kamar saurayi ba ne haba!’ Rahama ta ja hannun Amina tace ‘Taso ‘yar uwa mu nemo abinci wannan batun na masu aure ne ba namu ba kin ji. Haka ta wuni a makarantar nan Amina tana ba ta baki yayin da Farida da Rahma suke ƙara jaddada mata ya kamata ta ɗauki mataki idan ba haka ba rainin zai wuce haka. Sai bayan la’asar sannan ta kwaso kayanta ta dawo gidan.

    Wunin ranar haka ta ƙarasa shi cikin ƙunci, sai da ta cewa yara ba ta da lafiya sannan suka ƙyale ta don kowa yana so ya ba ta labarin sports day. Rashida ce ta ƙarasa duk wata hidimar gida da ta yara, har abincin ma da ba ya so Rashidan ta girka yau cewa ta yi ta girka don a yanda take jin ko ta dafa ba zai yi daɗi ba.

    Sai bayan sallar magriba sannan ya dawo gidan, bayan ya gama hayaniya da yara ya wuce ɗakin ya same ta. Tana kwance ba ta ko juyo ta kalle shi ba don haka ya yi zaton bacci take yi. Sai kawai ya kintsa ya fice daga ɗakin. Ba ta son yi wa yaro alƙawari ta karya don haka tun da ta dawo ta sa Rashida ta haɗa mata duk wasu kayan da take buƙata na haɗa shawarma sanna ta kwaɓa mata fulawar, yanda idan ta fito bayan isha’i sai ta haɗa shawarma kamar yanda ta yi wa Habib alƙawari idan ya yi passing Hausa.

    Suna zaune shi da yaran ta wuce su ta shiga kitchen, nan da nan ta fara ƙoƙarin ɗorawa. Tana daga kitchen ta jiyo yana amsa waya yana kwatancen gida; ta ja tsaki a fili tana fatan Allah ya sa ba baƙo zai yi ba don ko me zai yi ba za ta gaisa da wani baƙo ba balle ta ba shi ko da ruwa. Sai dai ya yi duk abinda zai yi. Kafin ta gama wannan tunanin ta ji shi yana cewa yanzu zai fito, inda ba tare da ɓata lokaci ba ta ji fitarsa.

    Jimawa kaɗan ya shigo da leda ya wuce ya same ta a kitchen tana yayyanka fulawa za ta fara gasawa. Ya miƙa mata ledar yana cewa ‘Ga wannan shawarma ce; sakatariyata ce Naja ta aiko delivery man ya kawo a ba wa yara. Sai ki duba ki zubo a tray mu ci don na ji kamar da yawa’Ta kalle shi da jajayen idanuwanta waɗanda suka koɗe saboda kuka da tsabar mamaki; ta yi murmushi mai ɗaci sannan ta kashe wutar abinda ta ɗora a wuta ta nufo shi yayin da ya miƙa ledar a zaton za ta karɓa.

    Ta bigi kafaɗarsa ta wuce ta shige ɗaki ta bar shi a nan tsaye. Ya bi bayanta da kallo cike da tsananin mamaki saboda Khadeeja ba ta taɓa yi masa irin wannan wulakancin ba; kuma a gaban yara don duk biyo shi suka yi da suka ji yana maganar a juye a ci. Nan take ya ajiye ledar kan sink sanna ya bi bayanta ɗaki; yana shiga ya same ta a tsaye a gaban mudubi tana cika tana batsewa kamar ma jiransa take yi.

    ‘Wannan wane irin wulaƙanci ne ina miki magana za ki yi min tsaki a gaban yara saboda raini.’ Ya tambaya cikin jin kai da isa. Ta kalle shi ta ɗauke kai tana murmushin takaici tace ‘Ji na yi kamar zagina ka yi. Kallon takaicin da yake mata ya koma na mamaki, ya tsare ta da ido kuma ita ma ta ƙi ɗauke nata idon. Yace ‘Ni na zage ki? Ko kuwa dai ke kika zage ni?’

    Ba tare da ta ba shi amsa ba tace ‘Wacece Naja Mtseww!’ ya ja tsaki sannan ya cigaba ‘Sakatariyata ce; shi ne kike nema ki zage ni saboda nace ta kawowa yara abu? Ba ka gaya min ka mayar da ita wakiliyarka a makarantar yara ba, har sai da na je musu open day sannan sai na ganta wai kai ka tura ta. Har tana cewa wai na ba ta takardun yara ita kace ta karɓo.’

    ‘Eh, ai ni nace ta karɓo tunda na fita ban gaya miki ba. Kuma ka kasa yi mi waya kamar yanda kafin yau duk abinda kake so a yi na yaran kake min waya ko da ina sama jannati ne na je na yi? Ya fara hasala saboda yanda take maganar a tsiwace ga wani kallon raini da take masa.

    ‘Ba fa na son wulaƙanci khadeeja; ni na tura ta ta karɓo ko ban isa ba ne? Na zata za ki yi murna tunda kullum cikin ƙorafi kike da mitar hidimar yaran saboda kina gani ba ke kika haife su ba, ke naki karatun ne a gabanki. Ta yi murmushi tace ‘Ka isa har ka yi yawa, kuma alhamdulillahi tunda an sami mai karɓa ta yanzu kam zan huta da wasu abubuwan. Kuma na gane ni ce ban isa na shigar maka mota ba shi yasa ita da kake ganin mutuncinta ka koya mata mota har ga shi nan ta kai ta ɗauki motarka ta fita yawo.’

    Ta ɗaga ƙafa za ta shige banɗaki sai kuma ta tsaya ta kalle shi suka haɗa ido sannan tace ‘Bayan hidimar yaran sai kuma wacce hidimar take maka? Ko ma dai ka aure ta ne ni ce ban sani ba? Ba fa na son iskanci Khadeeja! Kina ji nace miki sakatariyata ce kike wannan maganar banzar. Na aike ta don haka na ba ta mota ta ta je ta dawo, shi ne kike wannan rashin kunyar?

    Idan da kina hidimar yaran ba tare da ƙosawa ba ai babu wanda zan nema. Na san idan na gaya miki sai kin yi mita don haka na nemi wadda za ta yi cikin walwala na saka ta, sai dai duk abinda za ki yi ki je ki yi amma idan kika zage ni wallahi ba za ki ji da daɗi ba. Ta yi murmushi ‘Hmmm! Ka fi ƙarfin zagi yallaɓai, amma tabbas ka yi yanda kake so don haka ni ma zan yi yanda nake so.’

    Ta juya ta shige banɗaki ta turo ƙofar ta bar shi nan tsaye. Haka ya gaji da tsayuwa ya juya ya fice daga ɗakin; tana jin fitarsa ta fito ta saka mukulli ta kulle ɗakin ta bar mukullin a jiki ta koma ta kwanta. Tun a office Naja’atu ta sanar da shi haɗuwarsu da Khadeeja, kuma ita kanta sai da ta nuna rashin jin daɗinta a kan ya san Khadeeja za ta je ya tura ta.

    Sai da ya yi ta faman ba ta hakuri sannan ya samo kanta. Bai taɓa zaton Khadeeja za ta ba shi matsala, don ya zata idan yace mata sakatariyarsa ce za ta fahimce shi, yanzu ga shi ita ma Khadeejan so take ya lallashe ta. Yana da niyyar auren Naja don sun ma yi magana da Alhaji kwanan nan ma za a kai kuɗin aure; kawai dai bai shirya gayawa Khadija ba saboda bai shirya ba, ya fi so sai magana ta tsaya an kusa biki sai ya sanar da ita.

    Kafin lokacin ya gama gininsa sai su tashi su koma don a can yake so amarya ta tare. Yanzun ma kuma da hakan ta faru ba gaya mata zai yi ba, idan ta gama fushin nata ya san me zai gaya mata. Tun yana saka rai za ta buɗe ƙofar ɗakin har dare ya fara yi ba ta buɗe ba, yara har sun gaji da tambayarta. Haka ya sa Rashida ta ba su abinci sannan ta taya su suka shirya suka tafi suka kwanta, shi ma ya shiga ɗakinsa ya kwanta yana sauraron lokacin da zai ji motsinta.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Uku

    Ba a daɗe da sallacewa ba kuma aka buɗe gari, a hankali kowa ya koma harkokinsa. Ranar Lahadi da daddare bayan yara sun yi bacci; suna zaune a parlor shi yana kallon ball a TV yayin da ita kuma take chatting a waya; ta ɗago daga kallon wayar ta dube shi tace ‘Babe gobe fa za a koma makaranta.’

    Ba tare da ya ɗauke kai daga kallon TV din ba yace ‘Kin gaya min fa tun last week, kuma na siyo duk wani abu da ake buƙata. Ta gyara zama ta ajiye wayar tace ‘Ni ma zan shiga school ɗin na gano, wata ƙila an kafe timetable, amma sai wajen goma zan fita.’
    ‘Ok, to za ki dawo kafin 12:30pm kenan ko? Saboda ɗauko ‘yan makaranta tunda ni kin ga ina office.’

    ‘Eh, zan yi ƙoƙari na dawo kuma idan ban dawo ba ma kafin na fita zan je da Rashida ta ga makarantar tasu idan lokaci ya yi ban dawo ba sai ta je ta ɗauko Nasreen. Ya gyara zama ya kalle ta kamar a firgice ‘Wai wannan yarinyar ce za ta dinga ɗauko yaran daga
    makaranta kuma ta zauna ta zauna da su a gidan ita kaɗai?’

    Cikin halin ko in kula tace ‘To ya za a yi, ai ka ga dai ni ma dole na je makaranta ko? They will be fine fa, yarinyar tana da hankali sannan kuma ka ga ga Afaf tana nan idan ta dawo. Su ma ita da Habib na gaya musu idan an tashi daga makaranta su taho tunda na ga ko ni ce ma na je ɗauko su idan muka rasa napep a ƙasa muke tahowa.’

    Ya ƙare mata kallo sanna yace ‘Wai me kike faɗa ne? Su Afaf ɗin ne kike so su dinga tahowa daga makarantar su kaɗai kuma a ƙas, sannan har da Nasreen? Wadda sai an tashe ta da minti talatin sannan a tashe su? To babe ya za mu yi? Ai ka ga dai kamar Afaf ba shi da wani amfani a ce sai Rashida ta je sannan za su taho tare ko?

    Ni kuma duk lokacin da ta kama ina gidan zan je na ɗauko su. Suka yi shiru na ɗan lokaci kowa da abinda yake tunani. Jimawa kaɗan yace ‘Ni barin wannan yarinyar taki ma a gidan ita kaɗai gaskiya bai yi min ba, ya za a yi duk mu fice a barta ita kaɗai kuma a bar mata mukullin gidan? Ai idan muka dawo sai abinda muka gani kenan, za ma ta iya fara shigo da maza gidan ko a yi mata wayo a yi mana ɓarna idan aka gane ita kaɗai ake bari a gidan.’

    ‘To yanzu ya kake so a yi? Ka ga dai da ni da yaran ai dole duk mu je makaranta ko?’
    ‘Ni ma ban sani ba, kece za ki san yanda za ki yi. Za ki ma iya fita da ita ki rufe gidan in ya so sai ku dawo tare ki ɗauko yaran, duk yanda dai kuka yi. Amma dai gaskiya wannan tsarin na barinta a gidan bai yi min ba.’

    Ranta ya fara ɓaci; me yake nufi ne? So yake yace ta bar makarantarta kawai saboda ta zauna masa da yara ko kuwa mai aikin yake so ya korar mata? Wannan bayanin da yake yi ma sam ba zai yiwu ba gara dai ya sake lissafi ko kuma shi ya dinga baro office yana zuwa yana ɗauko su.

    Tace ‘Uhm, to ai ka ga ba ni nake rubutawa kaina timetable ba, wani malamin ma sai 1pm yake fara lecture kuma dole na yi attending idan dai ina son na gama degree ɗin. Sai dai ko ka kawo wata dabarar da kai kake ganin za a yi da ɗauko su in ya so ita Rashida idan zan fita sai na fita da ita duk lokacin da na gama lecture sai mu dawo tare.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan ya tashi ya jefar da remote ɗin TV ɗin da yake hannunsa ya shige ɗaki. Ta bi bayansa da kallo tana mamaki; wai me mutumin nan yake nufi ne? Shikenan sai ta jingine rayuwarta ta zauna ta kular masa da yara? To ai ita ko ‘yayan da ta haifa ma haka ko tana so ko ba ta so za ta dinga barinsu da mai aikin ta tafi makaranta tunda dai haka ta ga masu yaran suna yi.

    Ko kuwa da yake ta auri tuburarre haƙura za ta yi da komai ta zauna sai yanda suka yi da ita? Haka suka kwana a wannan daren kowa da abinda yake ransa. Ko da gari ya waye tun asuba ta tashi ita da Rashida wadda ta taya ta nan da nan suka shirya
    yara sannan suka haɗawa kowa abinci.

    Kamar yanda ya saba sai ƙarfe bakwai da kwata sannan ya fito, zuwa lokacin sun shirya suna jiransa; ya kwashe su ya kai su ya dawo. Sai wajen ƙarfe tara da rabi sannan ya gama shirinsa, lokacin fitowarta kenan daga wanka saboda sai da ta tsaya ta gama abincin rana ta juye a flask sannan ta fara shirin. Ya same ta a ɗaki tana shafa mai riƙe da mukullin motarsa, yana daga tsaye a bakin kofa yace ‘Ni na fita.’

    Ta juyo da sauri tana cewa ‘La! Babe don Allah bari na yi sauri na saka kayana sai ka ba ni lift. No ba ta hanyarku zan bi ba, ki wuce kawai sai na dawo. Kada ki manta min da yara.’ Ya faɗa yana ficewa daga ɗakin. Ta bi bayansa da kallo da baki buɗe; lallai ma mutumin nan.

    Ƙiri-ƙiri dai shi baya son ya ɗauke ta a motarsa idan dai makaranta za ta, in banda haka ai ko ba hanyar makarantarsu zai bi ba ya sauke ta a bakin titi ya rage mata tafiya. Ta juya ta cigaba da shiryawa cikin sanyin jiki tana tunanin son kai irin na Mustapha. Allah ya so ta ma Baffa magana ya tura mata kuɗi kuma ya sanar da ita duk wata zai dinga turo mata kuɗi saboda karatunta, idan tana son wani abu sai ta yi masa magana.

    Tabbas ta san da a ce da Mustapha ta dogara da sai dai ta haƙura da karatunta ta zauna ta kular masa da yara. Nan da nan ta ƙarasa shiryawa ta fito ta sallami Rashida wadda ta bar su tare da Shukra bayan ta yi mata duk wani bayani da take buƙata sannan ta kama hanya zuciyarta cike da damuwa da wasi-wasi.

    Kafin sha biyu ta gama duk wani abu da take yi a makarantar sai dai ba ta son ta dawo ta ɗauko yara; ba wai yaran ne ba ta son ɗaukowa ba amma ba ta son ta ɗauko su Mustapha ya ga kamar faɗansa ne ya sa don haka duk lokacin da za ta fita ya za ta zai yi mata faɗa ta dauko masa yara.

    Don haka suka nemi inuwa ita da ƙawayenta suka zauna suna hira, sai wajen 1;30pm sannan suka ƙarasa masallaci suka yi sallah kowacce ta kama hanyara gida. Ko da ta zo gida ba ta tarar da wata matsala ba, Rashida ta kai Shukra gidan su Ummi ta ɗauko
    Nasreen daga makarantar kamar yanda ta ba ta umarni. Su kuma Afaf da Habib kusan tare da ita suka shiga gidan.

    Ko da ya dawo tana jin sa yana tambayar yaran wanda ya ɗaukosu daga makaranta suna ba shi amsa, musamman Shukra wadda yake ta tambayarta me suka yi ita da Rashida a gidan bayan Anti ta fita. Haka ta yi banza da shi ta cigaba da harkokinta.

    Haka suka cigaba da yi, sai ya zama kuma da yake ba a fara lecture sosai ba sati biyun farko kullum Khadeeja ba ta fita da wuri sanna kuma tana dawowa kafin ya dawo gidan, don haka matsalarsu da sauƙi tunda zai zo ya tarar da ita tana ta hidimar yara.

    Sati ɗaya da komawa aka kafe wa su Khadeeja timtable, kuma da yake babu lokaci sosai timetable ɗin a matse take. Haka dai suka cigaba da karatun. Ranar Alhamis shi ne take da lecture 8am to 6pm, don haka ta san dole ta shirya ta fita tare da yara. Tun dare ta gama komai, ta yi rabin aikin abincin safe sannan ta fitowa da kowa kayansa.

    Ta yi wa Rashida duk wani bayani da take buƙata tunda yaran idan sun dawo daga makarantar boko babu islamiyya don haka nan za su wuni a gidan. Tun kafin asuba ta tashi suka fara aiki tare da Rashida. Bayan Mustapha ya dawo daga masallaci
    sallar asuba ya same ta a kitchen, tana ta fama kai wa da kawowa tsakanin dankalin da take soyawa da kuma haɗawa yara abincin makarantarsu a lunch box.

    Bayan ya amsa sannu da zuwanta yace ‘Wai kin yi sallah kuwa? Na ga kamar a nan na bar ki fa. Ta yi ‘yar dariya tace ‘Haba dai, na yi sallah mana. Sauri nake na gama saboda yau 8am to 6pm ne da ni kuma 8am din nan idan Prof. ya riga ni shiga aji rufe min ƙofa zai yi wallahi shi yasa nake ta sauri don kullum sai ya yi attendance.’

    ‘Oh kenan yau sai 6pm za ki dawo gidan? Eh.’ Ta amsa a gajarce tana kwashe dankalin da ya riga ya soyu. Ya ƙara haɗe girar sama da ƙasa sanna yace ‘To a ina za ki bar yara wuni guda? Ba ta son hayaniyarsa don ba ta son abinda zai ɓata mata rai, ba tare da ta bar abinda take yi ba tace ‘A nan mana gidansu; Rashida za ta ɗauko Nasreen su kuma su Afaf idan suka dawo za su same ta a gidan sai su yi zamansu kafin na dawo, they will be just fine.’

    ‘Haba ai daɗewar ta yi yawa, kenan haka za su zauna su yi duk abinda suka ga dama ba tare da wata kulawa ba.’ Ya faɗa a fusace. ‘Kada ka damu Rashida za ta kula da su.’
    Kafin ya ba ta amsa suka jiyo ihun Nasreen daga ɗakinsu tana cewa ‘Wayyo Anti.’
    Ta riga ta san rigimar Nasreen, idan dai aka tashe ta da sassafe zuwa makaranta sai ta yi kuka ko ma waye ya tashe ta, shi ma kuma ya san da haka.

    Amma ba tare da ɓata lokaci ba ya nufi ɗakin da sauri. Ganin haka ita ma Khadeejan ta ajiye abinda take yi ta bi bayansa, kusan a lokaci ɗaya suka shiga ɗakin. Nasreen tana zaune a kan gadonsu da hawaye shaɓe-shaɓe a idonta yayin da Rashida take tsugune a gaban gadon tana riƙe da towel. Me aka yi miki kike kuka Nasreen?’ Ya tambaya kafin ya karasa shiga ɗakin.

    Khadeeja tana shiga ɗakin ta sauko daga kan gadon ta rungume ta tana cewa ‘Anteee.’
    Ya shafa kanta ‘Me aka yi miki? Cikin shagwaɓa tace ‘Rasheeda ce. ”Ya juya ya dubi Rashidan a fusace yace ‘Me kika yi mata? Nan da nan jikinta ya hau rawa tana gyara tsuguno, kafin ta yi magana Khadeeja ta shafa kan Nasreen tace ‘Nas me Rashida ta yi miki?’

    ‘Tashi na ta yi daga barci. To ai kin ga shirya ki za ta yi ki tafi school ko? Ko kina son ki makara Uncle ya koro ki gida ne? Ya yi tsaki ya fice daga ɗakin ba tare da ya sake cewa komai ba. Ta lallaɓa Nasreen ta tura ta banɗaki sannan ta juyo za ta fito, kafin ta fito ta jiyo shi yana dawowa ɗakin yana cewa ‘Dankalin da kika bari a wuta ya kone, ki je ki duba na kashe miki wutar.’

    Ta wuce shi ta ƙarasa kitchen ɗin da gudu inda ta sami dankalin ya ƙone, ta kwashe sannan ta sake kunna wutar ta ɗora. Ya ƙaraso ya tsaya a kofar kitchen ɗin, ya ɗan ɗauki lokaci yana kallonta tana zubawa yara abincin rana wanda ta sauke a babban flask. Jimawa kaɗan yace ‘Kin ga irin abinda yasa bana son ki bar su da yarinyar nan ita kaɗai ko?

    Ya za a yi ta iya kula da yara tunda ga shi nan ba ta ma iya tashinsu daga bacci ba?’
    Ta kalle shi cike da mamaki tace ‘Nasreen ce fa, ko kai ne ma ka tashe ta sai ta yi rigima, ko ka manta ne? Kuma kai ne ka ce ba ka son Rashida ta dinga yi maka girki kuma ka ga dole abu ɗaya zan yi a lokaci guda ba zai yiwu ina girka muku abinci ba kuma ina shirya yara.’

    Ya juya ya fice ba tare da ya ce komai ba. Ta ja tsaki ta share ƙwallar da ta taru a gefen idonta sannan ta cigaba da aiki. Ba ta ma san me take ji ba, ƙoƙari kawai take ta fita daga gidan idan ta je makaranta ta samu ta yi tunani ta fahimci me take ji. Bayan ta gama abinci ta wuce ɗaki ta same shi bayan ta zubawa yara abinci suna ci.

    Yana kwance a gefen gado yana fama latsa waya ta wuce har ta kusa shiga wankan yace ‘Idan na kai yara dawowa zan yi kin sani, sai wajen 10am zan fita, ita wannan yarinyar taki haka za ki bar min ita a gidan daga ni sai ita? Cikin halin ko in kula tace ‘Eh, ita da Shukra za su zauna idan za ka fita kawai ka gaya mata don ta san cewa ka fita ta cigaba da aikinta.’

    Har za ta shige banɗakin yace ‘Gaskiya ba na so, kuma ke ma kin san bai dace ba ki bar ni a gida daga ni sai mai aikinki mace. Irin haka ne kuma idan an ce za a auri mai aikin ku ce ba ku yarda ba. Duk ɓacin ran da take ciki sai da ya ba ta dariya, duk da dai dariyar takaici ce tace ‘to ai ga ka nan ga ta nan ka aure ta mana, ai ita ma mace ce.’

    ‘Ni dai na gaya miki bana son ki bar ta a gidan idan ina nan tunda ke ba kya nan, ki sami inda za ki ajiye ta idan na fita sai ta dawo gidan. ‘Uhhm!’ Ta amsa sannan ta shige wankan cike da takaicinsa, har ji take kamar zuciyarta tana turiri. Zuwa makaranta lecture kawai ya zama wata drama.

    Nan da nan ta ƙarasa shiryawa ta shirya yaran, ta haɗa tea ta zauna tana sha. A haka Mustafa ya fito ya same su lokacin 7:15am. ‘Ku tashi mu je.’ Ya faɗawa yaran.
    Ta miƙe riƙe da kofin shayinta tace ‘Bari na ɗauko hijab dina na saka ku rage min hanya.’
    ‘A a za ki makarar da mu ne fa, ga shi ko shayi ba ki gama sha ba kuma kin san idan suka makara koro su za a yi.

    Ya juaya ga yaran wadanda sun riga sun miƙe kowa da kayansa a hannu yace ‘Mu je.’
    ‘Anti sai mun dawo.’ Suka faɗa sannan suka juya suka fice ya bi bayansu. Ta bi bayansa da kallo cike da mamaki; ta kasa gane motarsa ce ba ya son ta dinga shiga ko kuwa tsabar baƙin ciki ne a kan za ta fita yake hana shi rage mata hanya.

    To amma kuma yana kai ta unguwa, kodayake wannan fita ce da shi ya ga dama kuma kusan duk inda za ta tunda ta aure shi tare yake kai ta da yaran suna biye da ita. To me yasa idan dai makaranta za ta tafi sai ya san yanda ya yi ya tafi ya bar ta ba tare da ya ko da rage mata hanya ba?

    Haka har ta gama shirinta ba tare da ta samo amsar tambayarta ba; ta fito ta sami Rashida a kitchen tace ‘Idan babansu ya dawo ki koma ɗaki ki zauna in ya fita sai ki fito ki cigaba da aikin; idan Shukra ta zauna a wajensa shikenan idan kuma ta taho wajenki to don Allah kada ki bari ta yi kuka ya ji.’

    Ta yi mata sallama ta fice tana sauri saboda 7:20am ta riga ta yi kuma ba ta da tabbas ɗin za ta iya kai wa BUK kafin 8:00am. Ta kusa isa titi Mustapha ya karyo kwana ya shigo layin, ta ɗauke kanta daga kallon inda yake; ba ta sani ba ko ya ganta ko bai ganta ba.

    Ta ƙarasa titi cikin sanyin jiki ta hau Napep tambayoyi daban-daban suna ta yawo a kanta; wai ina babe ɗinta ne? Wanda yake son ta? Wanda kafin aurensu har so yake ya ɗauko ta daga makaranta ya kai ta unguwa ko ya kai ta gida don dai tana hana shi ne saboda ta san Baffa ba zai bari ba a lokacin. To shikenan soyayya ta ƙare ko me
    Mustapha yake nufi da ita? Shekara ɗaya fa kenan da ‘yan watanni da aurensu.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyu

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyu

    Ranar Sallah yana tashi ruwan shayi kawai ya sha ya shirya ya fice; bayan an idar da sallar idi kai tsaye gidan Mama ya wuce wajen yaransa. Yana gamawa da su ya wuce gidan Mommy wajen Khadeej; ko da dai ya ji haushin yanda ta yi zamanta a gidansu ta ƙi dawowa amma ya san ya yi kewarta.

    Duk wani haushi nata da yake ji ya riga ya huce, abu ɗaya yake so a yanzu shi ne ta dawo gida ya samu ya daina fama yawo shi da yaransa sai kace wasu waɗanda ba su da gata. Ya kalli kayan sallarta waɗanda ya taho da su ya kai mata ko za ta ƙara, ya kau da kai ya cigaba da tuƙinsa.

    Shi ya ga ma kamar ba ta damu da kayan sallar ba tunda da ita aka kai ɗinkin amma da yake ta so ta yi sallah a gida ko bi ta kansu ba ta yi ba sai ma ce masa da ta yi Baffa ya yi mata kayan sallah. Haka dai ya yi ta tunani kala-kala har ya ƙarasa gidansu Khadeeja.

    Lafiya ƙalau suka gaisa cikin mutunci kamar babu wanda yake jin haushin wani a tsakaninsu; ya shiga ya gaida Mommy sannan ya gaida Baffa. Suka dawo ita da shi suka zauna a parlor ɗin baƙi inda ba tare da ɓata lokaci ba ta kawo masa tuwon sallah da lafiyayyen zobo mai sanyi. Suka zauna yana ci tana yi masa hira.

    Bayan ya gama ya huta ya yi wa Baffa sallama inda Baffan ya sanar da shi jibi ya zo ya ɗauki matarsa. Suka fito tare da Khadeejan ta rako shi bakin mota. Tana tsaye riƙe da murfin kofar motar yayin da shi kuma yake zaune a kujerar direba ya juya kujerar baya ya ɗauko ledar da take ajiye a kan kujerar ya miƙa mata yana cewa ‘Ga kayan sallarki duk da na ga ba ki damu da su ba.’

    Ta yi ‘yar dariya tana tura masa ledar tace ‘Ka koma da su ka ajiye min a ɗakina tunda jibi zan dawo. Shi ma dariyar ya yi yana mayar da kayan yana cewa ‘Ko dubawa ma fa ba ki yi ba. Haba kayan da na riga na sansu, idan na dawo zan duba sannan na yi kwalliyar sallah ta.’

    Cike da farin ciki da walwala suka yi sallama sannan ya wuce gidan Hajia. Yana shiga gidan ya tarar da Hajia a parlor ɗinta suna hira ita da Yaya Jidda, yaranta kuma suna ta kai wa da kawowa a tsakar gidan. Bayan ya gaida Hajia ya yi mata barka da sallah ya juya suka gaisa da Yaya Jidda wadda take ta faman shan kunu tana basarwa saboda kar ya yi mata wata magana.

    Bayan sun gaisa sun ɗan taɓa hira da hajia ya dubi Yaya Jiddan yace ‘Yaya bari na ba ki account number ki turo min 10k ɗin da na tura miki ta yi wa yara sayayyar kayan shayi; tunda sun ce min ba a saya ba ko? Ta sake haɗe girar sama da ƙasa ta kalli hajia sanna ta kalle shi tace ‘Ban gane ba a siya ba, an siya mana.

    Kawai dai ba ranar da ka bayar ba don kafin ka turo kuɗin masu kantunan sun rufe. Shi yasa ba a samu an saya ba har sai ranar da aka sake buɗe gari, ranar da ka zo kenan ka kwashe su. Da safen da ka tafi da su ai da sun zo za su tarar da kayan komai an saya don har ciko ma nayi.’

    Hajia tace ‘Ai kuwa ka ga babu maganar dawo da kuɗi tunda an sayi kaya.’Takaici ya kama shi don ko ɗaya bai yarda da wannan zancen nata ba, ya kawar da kai sannan ya sake dubanta yace ‘Haka ne, to shi kenan, sai a ɗauko min ragowar na tafi da su tunda jibi yaran za su dawo har Khadeejan kuma ko suga babu a gidan sai na sake siya.

    Ki aika a ɗauko min su tunda kusan ma ba a yi amfani da su ba kenan tunda ranar da aka siyo ranar suka tafi. Kafin ta yi magana Hajia tace ‘To su sauran yaran gidan ba ‘yayanka ba ne da ba za a ba su ba, kayan shayin kawai ba wani abu.’ Ta dubi Jiddan tace ‘Ko da yake bari na barku wataƙila suna nan ki ba shi ya kai gidan nasa.’

    Ta sake kicin kicin sannan tace ‘Hajia kema dai kin san yaran nan ba za su bari ga kayan shayin har da Indomie su bari na ajiye ba tare da na ba su ba. Sai dai kawai idan biyansa zan yi na yi wa babansu waya ya biya abinda ‘yayansa suka ci tunda yana kallo suna ci kuma ya san ba shi ya siyo ba.’

    Hajia tace ‘A a ba za a yi haka ba, sai kace a garin matsiyata ake.’ Ta dubi Mustaphan tace ‘Kai Mustapha ka yi haƙuri, ba na son wannan rigimar taka. Wannan ma ai ba wani abu ba ne da za a ɗaga tunda daga yaranta har nakan duk ‘yayanka ne. Muryarsa a maƙogoro yace ‘Shikenan Hajiya.

    Ya miƙe tsaye yana cewa ‘Bari na je wajen Alhaji mu ci tuwon tare, ko da yake ma a ƙoshe nake me sanyin kawai zan sha. Yana shigewa Jidda ta kalli Hajia tace ‘Kin gani ko Hajia, a kan kayan shiya zai yaga min rigar mutunci, wallahi yaron nan har yanzu bai yi hankali ba.’

    Tace ‘Ya fi ki gaskiya, ya za ki karɓi kuɗinsa kuma ki dinga bar masa yara da yunwa?Hajia wallahi na gaya miki ƙarya yaran nan suke yi, kawai don sun san za a biye musu ne suke abinda suka ga dama. Idan banda haka ya za a yi na hana su abinci na ba wa su Nawwara tunda ai duk tare suke wuni suna wasansu; kawai dai suna so su nuna su ubansu mai kuɗi ne.’

    ‘Ki dai bi shi a hankali kin ji na gaya miki. Bari ma ya fito na ji sai yaushe zai kawo min yaran yawon Sallah ko kuma ni ma laifin naki ne ya shafe ni ya kai yaran wajen wadda da ba ya son ya bar mata su?’

    Haka yana ji yana gani ya haƙura ya ƙyale Yaya Jidda; daman ya riga ya san Hajia ba za ta taɓa bari a ga laifinta ba. Kamar yanda aka yi alƙawari ranar uku ga sallah tun wajen ƙarfe tara na safe ya tafi ɗaukan Khadeeja; da yake sun riga sun yi waya a shirye ya same ta don haka ba tare da wani ɓata lokaci ba ya ɗauko ta ita da mai aikinta Rashida suka kama hanya.

    Sai da suka tsaya a gidan Mama suka kwashi yara sannan suka wuce gidan Hajia. Nan suka zauna a parlor ana ta hira yayin da yara suke ta kai wa da kawowarsu. Jimawa kaɗan Yaya Jidda ta dubi Khadeeja tana nuna Rashida tace ‘Wannan yarinyar taki kuwa za ta iya wani aikin kirki? Kada fu ku je a kama ku da child abuse?’

    Ta yi dariya duk da yanda maganar ta ɓata mata rai tace ‘Ah haba dai, shekarunta fa sha biyar yaya don dai kawai ba ta da girma ne. Aiki kam ta iya sosai ko a gida ma Mommy ta koya mata.’‘To amma idan Habi ta dawo sai a mayar da ita ko? Tunda na ji Habi ɗin tace baku da wata matsala da ita kuma tana nan ita ma tana shirin dawowa.’

    ‘Uhm, sai a haɗa biyu ma tunda kin ga ga hidimar gida ga ta yara, kuma ina zuwa makaranta. Haba wace hidima ce sai an haɗa ‘yan aiki har biyu a wannan gidan? Hidimar har nawa take? Kafin ta ba ta amsa Mustapha ya shigo yana cewa ‘Ku tashi mu tafi ko, don na san kuna da aiki a gidan nan don duk ya yi ƙura.’

    Suka fara shirin miƙewa yayin da ita kuma Yaya Jidda ta kalli Mustaphan tace ‘Na ga kun samo ‘yar aiki, Baba Habi ma fa tana nan tana shirin dawowa. Yace ‘Ah ai kawai sai ki ce mata ta yi zamanta tunda dai gaskiya ba mu da inda za mu ajiye ‘yan aiki har biyu. Da nace ta mayar da wannan ɗin idan Baba Habi ta dawo?’

    ‘To ga ta nan ku yi magana idan ta fi son Baba Habi ɗin sai a mayar da wannan ɗin.’

    Ba tare da ɓata lokaci ba Khadeeja tace ‘Uhm ai gara a bar wannan ɗin, in ya so in da wata matsala sai na yi magana a nan ɗin a kawo wata. Haka dai dole Yaya Jidda ta bar su suka tafi ba tare da ta iya gamsar da su cewa Baba Habi za ta dawo ba.

    Kamar yanda ya faɗa kuwa kaca-kaca suka tarar da gidan, sai dai suna shiga suka fara ƙoƙarin gyarawa. Kuma da yake yana ajiye su ya sake fita har da Afaf da Habib aka yi aikin, don haka cikin ƙanƙanin lokaci suka gama.

    A haka rayuwa ta cigaba; sai dai a ɓangaren Mustapha idan dai yana gidan ba a saka masa yara aiki, sai dai su su yi ta gara Rashida komai ita za su aika ko su saka. Khadeeja tana son ta tsawatar musu amma tana tsoron abinda ubansu zai ce tunda ta ga sun ɗan sami natsuwa babu wata hatsaniya, ba ta so ta ja rigima. Don haka haka ta zuba musu ido; abu kaɗan sai a ƙwalawa Rashida kira ko da kuwa aikin Khadeejan take yi dole ta bari ta je ta yi musu yanda suke so.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Ɗaya

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Ɗaya

    Duk da bai ce mata zai zo yau ɗin ba amma dai haka kawai zuciyarta take gaya mata zai zo tunda an buɗe gari kuma tun wancan lokacin da aka buɗe gari ba su haɗu ba. Ta san dai yana jin haushinta daga yanda yake amsa wayarta amma ta nutsu a zuciyarta cewa zai zo ɗin.

    Tun wuri ta tashi ta yi wanka ta shirya don ya same ta a shirye; sai dai ga mamakinta har azahar tana zaune a parlor tana ta faman duba waya, duk wanda ya buga gate da hanzari take tashi ta buɗe tana saka rai Mustapha ne amma har la’asar bai zo ba.

    Dab da la’asar tana zaune a parlor tana ta faman latsa waya tana duba whatsapp ko ya buɗe saƙon da ta tura masa amma ga mamakinta har zuwa lokacin bai buɗe ba. Mommy ce ta fito daga ɗakinta; har ta kama hanyar kitchen sai kuma ta kula da Khadeeja a zaune a parlor ɗin.

    Ta dawo ta tsaya tace ‘Ya na ganki a nan, ina Nabila PA ɗin taki?’ Ta yi dariya tace ‘Tana can tana abinda ta saba wato bacci. Ta wuce kitchen ta bar ta a nan, jimawa kaɗan ta fito ta dawo parlor ɗin ta zauna a kan three seater daga bangareb da yafi kusa da single seater din ta Khadeeja take zaune.

    Ta ɗan yi gyaran murya tace ‘Uhm, ai na zata Mustapha zai zo yau ɗin, ko sai da yamma zai zo?’ Ta ɗan gyara zama tace ‘Umm! Ina jin dai sai da yamman, wataƙila gidansu ya wuce tunda shi da yara ne.’ ‘Um to bari mu gani. Amma dai kuna waya ko?’ ‘Eh, jiya da daddare ma mun yi magana.’

    ‘Ai shikenan bari mu gani. Suka yi shiru na ɗan lokaci; jimawa kaɗan tace ‘Mommy kina neman Mustaphan ne da naga kamar jiransa kike yi? Ta jijjiga kai tana murmushi ‘A a me zai yi min; kawai dai na san ya kamata a ce ya zo ya duba ki ko, ai ko gaisawa ne a yi duk da dai da an sallace za ki koma.’

    Ita ma dariyar ta yi sannan tace ‘Zai zo Mommy in sha Allahu.’ Abu kamar wasa har aka sha ruwa babu Mustapha babu labarinsa’ haka dai ta lallaɓa ta ci abincin ba tare da tana jin daɗinsa ba. Tana kula da yanda Mommy ta saka mata ido sosai tana kula da duk wani motsinta tun ɗazu da suka yi magana.

    Sai da aka tafi sallar isha’i lokacin ‘yan gidan duk sun tafi masallaci sannan Mommy ta kirawo ta; ta riga ta san kiran don haka cikin sanyi ta tashi ta wuce ɗakin Mommy ɗin. A zaune a kan dadduma ta same ta don haka ta zauna daga gefenta a kan kafet. Sai da Mommy ta ɗauki lokaci tana kallon fuskarta kamar mai karanta littafi sannan tace ‘Wai ya aka yi Mustaphan bai zo ba?

    Gashi kin san ba za a sake buɗe gari ba sai satin sallah. Ko wani abu ne ya tare shi?’ ‘Umm! Kin san sai sun je office da zarar an buɗe gari. Sai da aka fara kiran magariba sannan ya kirawoni yake gaya min a lokacin yake barin office ga shi yana so ya isa gida kafin a fara tare hanya.’ Ta sharo ƙarya.

    Ta sake kakkafe ta da ido na ɗan loakci sannan tace ‘Umm! Ko dai fushi yake don an ce ba za ki koma sai bayan sallah? Na ga fa bai sake zuwa ba tun wancan lokacin da ya zo ɗaukanki ba ki bi shi ba.’

    Ta sunkuyar da kai tana ‘yar dariya tace ‘Umm, ya ma gama fushin ai. Da farko ne ya fara fushin ya zata zan fasa zama har bayan sallar amma daga baya da ya ga ba zai sami yanda yake so ba ya hakura.’ ‘Umm! To ko shi yasa bai zo ba?’

    ‘A a fa Mommy, na gaya miki ya je aiki ne shi yasa ya makara bai zo ba. Idan aka sake buɗe gari ko kuma ranar sallah zai zo.’ ‘To Allah ya kai mu. Idan dai da akwai wata matsala gara ki faɗa tun kafin ki koma a san matakin da za a ɗauka don na kula kamar akwai abinda kike ɓoyewa.’

    Ta ɗan yi murmushi sannan tace ‘Babu wani abu fa Mommy, aiki ne kawai da raino; kin san harkar yara. Bana samun lokacin kaina kullum cikin hidimarsu nake. Shi yasa tunda Biba ta tafi ban sami natsuwa ba. Kin ga yanzu kin ce kafin sallah za a samo min yarinya sai mu koma tare, daga wannan babu wata matsalar.’

    Ta kalle ta da alamomin tambayoyi domin jikinta yana ba ta kamar akwai abinda Khadeejan take ɓoye mata, amma babu wani abu da za ta iya yi a kai tunda ba ta ma san menene matsalar ba. Tace ‘To kuma shi Mustaphan ba ya baki wata matsala? Ta yi dariya ‘Mommy kema dai kin san da da matsala da tuni na gaya miki fa, babu komai.’

    Dole Mommy ta haƙura ta ƙyale ta da tambayoyin nan ba don ta gamsu da amsoshin da ta bayar ba. Sai da ta yi da gaske sannan ta hana kanta kiran Mustapha a wannan daren; ta yi wa kanta alƙawarin daga yanzu ba za ta sake kiran shi ba har zuwa bayan sallah. Idan ya zo su koma, idan kuma bai zo ba ita dai to ba za ta neme shi ba. Haka ta kwana tana matse ƙwalla.

    Duk yanda ya so ya daure zuciyarsa daga sharewar da Khadeeja ta yi masa zuwa yanzu ya gaza; ya riga ya saba tana kiransa tana lallaɓa shi da ba shi haƙuri amma shiru. Yana kallon kiranta ranar Asabar ya ƙi ɗauka don ya san za ta ce ya zo gidansu ne; shi kuma ba zai je ba in dai ba ɗaukanta zai je yi ba. Don haka ya ƙi ɗaukan kiran yana sa ran idan dare ya yi ma za ta sake kira, a lokacin sai ya ba ta uzurin dare ya yi.

    Sai dai har ya kai yaran gidan Mama ya wuto gida ya gama duk abinda zai yi ba ta sake kira ba; lokacin da ya tashi sahur ma wayar ya fara dubawa ya ga ko ta kirawo yana bacci amma ga mamakinsa babu kiranta ko ɗaya. Haka ya yi sahur ya gama ibadarsa ya kwanta.

    Sai da gari ya waye zuwa azahar sanna ya tuna akwai messages ɗinta na whatsapp da ta turo bai buɗe ba don haka ya je ya lalubo saƙonnin ya buɗe. Ya bi su ɗaya bayan ɗaya ya tura mata amsa, wanda tambayarsa take yi ko zai zo sannan tana gaya masa kayan da zai ɗauko mata a ɗakinta ya taho mata da su.

    Har zuwa la’asar ba ta amsa saƙonninsa ba sai dai sun nuna alamar sun shiga; ya buɗa whatsapp sau babu iyaka amma har zuwa lokacin ba ta karanta saƙonninsa. Ba ta taɓa share shi haka ba; to ko dai ba ta da lafiya ne? kada fa ya je wani abu ne ya same ta don idan dai Khadeeja ce ya san za ta neme shi.

    Zuciyarsa tana gaya masa wulaƙanci ne kawai take so ta yi masa don haka ya rabu da ita duk da yanda ya kasa cire tunaninta daga ransa. Haka suka zauna ba sa waya kuma ga saƙonninsa nan ta gani amma ta ƙi ta ba shi amsa. Ranar jajiberin sallah ya kasa jurewa shiru ɗin don haka ya kirawo ta; wayar tana dab da tsinkewa sannan ta amsa.

    Murya ƙasa-ƙasa cikin halin ko in kula tace ‘Bana kusa da wayar ne. Kwana biyu na jiki shiru ne, kuna lafiya? Lafiya Alhamdulillahi. Ya yarana?’ Suna nan ƙalau, suna gidan Mama. Allah sarki, don Allah in ka je kace ina gaida su maman.’ Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan yace ‘Kin yi zamanki a gida gaba ɗaya kin manta da ni ko?’

    Ta yi ‘yar dariya tace ‘Ka dai manta da ni. Ko kayan sallarki ma ba ki tambaya ba. Uhm, akwai wasu ma a nan da Mommy ta ɗinka min. To ya kike? Lafiya dai kike ko?’ ‘Lafiya ƙalau. Suka ɗan taɓa hirar haka wadda duk gaba ɗaya kusan shi ne yake ta daddagewa don ita ma ta ji haushin abinda ya yi mata, daga baya yace ‘Gobe fa Sallah, yaushe zan zo mu taho gida?’

    ‘Umm, in dai ka cire jibi duk lokacin da ka shirya za ka iya zuwa mu tafi, tunda an riga an samo min mai aiki ga ta har ta koyi duk wani aiki da nake so. Uhm, dole dai sai kin sani cin tuwon sallah a gidan hajia ko? To ina laifi, idan ka ci ni ma ka yi min take away.’ Haka suka cigaba da hirararsu a hankali suna sakewa, daga baya suka yi sallama a kan ranar sallah zai zo ya ci tuwo kafin ya wuce gidan Hajia.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma

    Karo na babu iyaka kenan da ta ɗauki wayarta ta buɗo whatsapp ta duba; har yanzu bai amsa messages ɗinta ba kuma bai biyo whatsapp call in da ta yi masa ba. To me yake faruwa ne? Allah dai yasa lafiya Mustapha yake da shi da yaran. Da farko da ta ga ta yi magana ta whatsapp bai kula ta ba kuma ta kirawo shi ta whatsapp ɗin bai ɗaga ba sai ta zata ko fushi ya yi, amma dai zuwa yau kwana uku abun ya fara ba ta tsoro kada ta je ko wani abu ne ya same shi.
    Ta riga ta san babu credit a wayar don haka ko balance ma ba ta duba ba; shi ɗin ba mutum ne mai son saka mata credit ba, idan ma ta yi magana sai yace wa za ta kirawo ko kuma me za ta yi da data ɗin. Idan aka yi albashi dai idan ta yi magana yana saka mata naira ɗari biyar, shi ne za ta samu ta raba ta sa data sauran ta ɗan yi waya.
    Don haka yanzun ma babu na wayar sai dai data ɗin da ta yi mata saura. Ta yi tsaki sannan ta sauka daga kan gadon Nabila inda take kwance ta wuce ɗakin Mommy.A parlor ta sami Mommy tana zaune tana kallon tafsiri a tashar Sunnah TV, ta zauna a kusa da ita bayan ta yi sallama ta amsa. Sai da suka ɗan yi jim kaɗan ta kula dai Mommy babu abinda za ta ce mata sannan tace ‘Mommy don Allah ki ɗan saka min 1k a waya mana.’
    Ta kalle ta tana dariya tace ‘1k kuma? Ina Mustaphan ko kuma yau ba nashi kike so ba tunda kina gidana nawa kike so?’ Ita ma dariyar ta yi ta ƙara langaɓe kai ‘A a Mommy, don Allah dai ki taimaka, wallahi ya saka min ƙararwa na yi kuma dai kin san ba ni da kuɗi. Ke kenan kullum ba ki da kuɗi?’
    ‘Mommy bari dai na fara aiki. Uhm, shi Mustaphan ko ɗan na kashewa ba ya yaga miki balle ga ki ‘yar makaranta?’ Ta ɗan marairaice ‘To ai kin ga yanzu an yi hutu Mommy, duk ‘yan sauran canjin ma na kashe. Shi yasa kike maula kuma? To ɗauko min wayata a ɗaki na saka miki a cikin wanda mijina ya ba ni.’
    Ta miƙe tana dariya tace ‘Mommy. Baffanta ba wai millionaire ba ne amma dai ta san yana da kyauta; duk da Mommy tana sayar da ‘yan kunnaye da sarƙoƙi amma duk wata sai ya tura mata kuɗin kashewa account ɗinta sai dai ko ya tura babu yawa amma fa sai ya tura.
    Kuma idan dai ta buƙaci wani abu bayan wannan to yana iya bakin ƙoƙarinsa wajen ganin ya yi mata sai dai ko idan babu hali. Ta yi zaton haka za ta je ta samu a wajen Mustapha, musamman da yake yana yawan yi mata kyaututtuka da saka credit a waya lokacin da yana neman aurenta.
    Sai dai bayan ta shiga gidan sai ta tarar ba haka ba ne; don wani lokacin a kan ya saka mata kati a waya ya gwammace ya ba ta aron wayarsa ta yi waya. Ko da ta koma makaranta ma ta yi zaton zai ɗan dinga ba ta kuɗin makaranta da kuɗin kashewa sai dai tun a ranar farko da gane ba zai jure ba.
    Domin da farko bayan ta gama shiryawa ta yi zaton zai kai ta ne, amma sai dai suna fitowa da aka zo inda zai ɗauke hanya ya wuce office ɗinsu sai yace ta sauka a nan ta hau motar haya. Da ta yi maganar kuɗin mota kuma sai yace mata wai ya zata tana da kuɗi; ta dai samu ya ba ta naira dubu kamar ba da son ranshi ba.
    Tun daga ranar ma sai ya zama ta daina damuwa ta yi sai ta shirya ta bi shi, yawanci sai ta jira idan ya fita sai ta kama hanya a motar haya. Kuɗin motar ma tana shirin ta tambayi Baffa ya dinga ba ta aka shiga lockdown; kuma har yanzu tana da niyyar kafin ta koma gida ta sanar da Baffanta kawai ya dinga tura mata kuɗin mota.
    Tana ta wannan tunanin ta je taɗdauko wayar ta kawo wa Momy; ba tare da ɓata lokaci ba ta tura mara katin naira dubu kamar yanda ta buƙata. Nan da nan ta koma ɗaki ta sake hayewa kan gadon Nabila sannan ta danna masa kira. Sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ya ɗauka, cike da isa yana magana da ƙyar ya amsa sallamarta, haka ma gaisuwarta kamar ba zai amsa ba.
    Wannan ya sa jikinta ya yi sanyi kuzarin da ta fara wayar da shi duk ya gushe. Cikin sanyi murya tace ‘Babe, ya na ji ka haka? Ko ba ka da lafiya ne?’ Sai da ya ɗan yi jinkiri sannan ya amsa ‘Umm, lafiyata ƙalau. Ke kin damu da lafiyata ne da kike wannan tambayar? Ba dole ki ji ni haka ba tunda kin zaɓi ki nesanta kanki da ni?’
    Nan ta fahimci inda zancen ya dosa, amma da yake so take ta waske sai tace ‘Haba Babe ya za a yi na guje ka? Tunda da kuka tafi daga nan nake ta yi maka message ta whatsapp, ba ka gani ba ne? Kuma wallahi wayar ma ka san ba ni da credit, yanzun ma da ƙyar na samu Mommy ta saka min ɗari biyu shine nake kiranka fa. Haba Babe ya za a yi kace ban damu da kai ba?’
    ‘To idan kin damu da ni ya za a yi na zo har gidanku ga azumi kin sani kuma ga shi ana lockdown? Amma kina kallonmu ni da yarana duk muna ta murna za ki dawo amma kika ce ba za ki dawo ba sai bayan sallah. To ai na gaya maka wannan ba ni na tsara haka ba, Mommy ce. Kuma ka san dai idan mace ta haihu dai ana yin gyara da sauransu, sallar nan fa kuma saura bai fi kwana goma sha shida ba.
    Haba Babe to meye na fushin?’ Shiru ya yi ba tare da yace mata komai ba suna sauraren numfashin juna. Ita ce ta gaji da sauraro tace ‘Ya na ji shiru ne? ina yara na?’ ‘Ai ba ki damu da su ba shi yasa suna ta cewa ki biyo su kika ƙi. ’Ta fara gajiya da wannan mitar tasa da duk abinda tace sai ya ce ba ta damu da su ba shi da ‘yayansa, to wai ita ba ta buƙatar a damu da ita ne ko me yake nufi?
    Shi ba zai iya kula da ita ba kuma ya bar ta ma cikin natsuwa a inda za a kula da ita ta ɗan sami natsuwa yana nema ya hana? Ta ɗan yi murmushi mai sauti ta danne fushinta sannan ta saita muryarta tace ‘To don Allah ka yi haƙuri ka daina cewa ban damu da ku ba, kai ka san na damu daku. Kamar yau ne za ka ga lokacin ya yi ai na dawo, ko ba shikenan ba.’
    ‘Umm, amma dai da za ki dawo yanzu ai da ya fi ko? Haka kawai ni ba gwauro ba kin saka ni azumi babu mata. Kawai idan an buɗe gari na zo na ɗauke ki mu tafi, shi ne kawai zan san kin damu da ni. Ta dan ɗaga murya tace ‘Ah, Babe to me zan cewa Mommy, ni daɗi miji zan bi mijina kenan ko me?’
    ‘Ba wani daɗi miji, ai aure ne kuma ita ma ta sani. To gaskiya dai ka bari sai bayan sallar kawai.’ Haka dai suka ɗauki lokaci suna waya ba tare da ta amince za ta dawo ɗin ba, maimaita masa kawai take sai bayan sallar. Don haka kusan a fusace ya katse wayar ba tare da sun yi wata sallamar kirki ba.
    Ta jefa wayar a kan gadon kusa da ita ta ja tsaki, sai kuma ta kifa kanta a kan pillow sai hawaye. Ta godewa Allah Nabila tana ɗakin Mommy tana bacci da sai ta gayawa Mommy tana kuka. Ta fara nadamar sakawa da ta yi Mommy tace ta zauna a gida har bayan sallah, yanzu gashi yana fushi da ita.
    Ita ba ta zata wannan abun zai sa ya yi fushi ba don da ta san zai yi fushi ma da ko gidan ba za ta taho ba za ta haƙura ya je ya ɗauko ta. Bata sani ba ko za ta iya jure jinsa a cikin damuwa har na tsawon sati biyu ko uku, amma dai za ta gwada. Don da kunya tace a barta sai bayan sallah sannan yanzu kuma ta zo tace za ta koma.
    Haka ta ƙarasa wunin ranar cike da damuwa da nadamar zaman da ta zaɓa za ta yi a gida. Haka ta cigaba da haƙuri tana buga masa waya wanda kullum idan ta buga gaisawa kawai suke yi babu wata magana mai daɗi, kamar ma shi dole take masa. Abun yana matuƙar damunta don haka ta fara rama wadda Mommy ta zata don ta cigaba da azumi ne tunda ta sami lafiya; idan ta yi zuru-zuru aka yi magana sai tace azumin ne da wahala.
    Tun da ya kai su gidan Hajia bai sake zuwa ba tunda garin a rufe yake ba a fita, sai yau Asabar a lokacin saura sati ɗaya sallah. Yana fita ya tsaya a shagon telansa ya karɓar musu ɗinkunan kayan sallansu wanda tun kafin a fara azumi ya kai; wanda har da na Khadeeja a ciki, ya tsaya aka ba shi leda ya ware nata waɗanda ba shi da niyyar kai mata gidansu.
    Ya dai yarda zai ajiye mata a ɗakinta duk lokacin da ta dawo ta gani. Yana karɓa kai tsaye ya wuce gidan Hajia cike da kewar yaransa. Tun daga nesa ya hango Habib a zaune a kofar gida tare da wani yaro, ba wasa suke yi ba a zaune suke kawai sun yi shiru kowa da abinda ya dame shi.
    Kafin ya ƙarasa tsayar da motar ya taso da fara’arsa; ya gyara tsayuwar motar ya buɗe kofa yana sake ƙarewa Habib din kallo wanda ya yi zuru-zuru kamar wanda ya kwana da yunwa. ‘Abba sannu da zuwa.’ Muryar Habib ta katse shi. ‘Yauwa Habib, ya naganka kamar kana jin yunwa ko azumi kake ya fara ba ka wahala tun da safe haka?’
    Idonsa ya ɗan yi rau-rau yace ‘Eh, azumi nake yi. To ba ka yi sahur ba ne?’ ‘Ba sosai ba, baƙin tuwo ne kuma ba na ci ga shi kuma babu wani abincin a gidan sai shi, na ɗan ci kaɗan dai. To ba sai ka fasa yin azumin ba? ɗa safe ka yi breakfast.’ ‘Hajia ma haka tace na fasa yin azumin amma ni nace zan yi, idan ma ban yi ba ba abinci zan samu ba sai an sha ruwa.
    Tunda muka zo ma sau ɗaya na sha azumi.’ Cike da tsananin mamaki yace ‘Ban gane ba abincin kake samu ba sai kace wani almajiri? Ba a ba ka abinci ne a gidan? Ina Baito? Ai Baito sai da rana take zuwa, kuma safiya tana yi Hajia take cewa mu tafi gidan Anti Jidda mu yi wanka a can mu ci abinci a can. Kuma idan mun je sai Anti Jiddan tace babu abinci sai dai kawai wata ran ta ba mu baƙin shayi da ragowar ƙosai ko doya.
    Idan kuma mutum ya dame ta sai ta yi masa faɗa, ita ma Shukra da Nasreen ragowar kunu ne kawai ko kuma idan an yi sa’a an rage abincin shan ruwa shi ne ake ba su.’ Mamakinsa ya ƙaru, yace ‘A a, ai na turowa Anti Jidda kuɗi a sayi indomie da cornflakes har da madara, ba a siya ba ko me ya faru da su.’
    Ya ɗan zaro ido ‘Tab, tunda muka zo ba mu taɓa cin indomie ba ko cornfalkes. In an sha ruwa dai da yake muna gidan Hajia shi ne aka haɗa mana shayi da madara har da ƙwai ma ake soya mana da kaza, amma dai da rana babu wanda yake ba mu abinci. A wajen Hajia ma muke shan ruwa tare da ita da Alhaji.
    Ya yi matuƙar mamaki kuma ya ji tausayin Habib; amma kuma yana matuƙar mamakin yanda za a yi a ce Yaya Jidda ta bar masa yara da yunwa. Ranar da ya kawo su bayan ya tafi ta kirawo shi tana tambayarsa kuɗi a sayi kayan shayi da indomie, kuma a take ya tura mata naira dubu goma don a siyo da wuri. To me ya faru da kuɗin da ake hora masa yara da yunwa?
    Tare suka jero da Habib ɗin suka nufi cikin gidan, suna daf da shiga suka ci karo da Afaf tare da Shukra da Nasreen kowacce sanye da hijabinta, nan da nan suka faɗa jikinsa suna murna ‘Abba, Abba. Bayan ya amsa gaisuwarsu yace ‘Ina za ku je?’ Afaf tace ‘Gidan Anti Jidda za su je su yi breakfast.’
    ‘Ke kina azumin ne?’ ‘Eh ina yi.’ ‘To ku zo mu wuce ciki ku yi breakfast ɗin a nan.’ Nasreen ta yi dariya tace ‘Tab ai babu abincin, da an gama shan ruwa Baito take juye duk wani ragowar abinci ta tafi da shi. Kuma Hajia cewa take mu je gidan Anti Jidda a dafa mana indomie amma idan mun je ba a dafa bana, baƙin shayi ake ba mu da ragowar ƙosai ko kunu.’
    Ya ɗauki shukra ya ja hannun Nasreen yana cewa ‘ku zo mu je. Bayan sun gaisa da Hajia tace ‘To ka bar su su je gidan Jidda ta dafa musu indomie ɗin su karya sai su dawo ko? Yunwa suke ji ga su nan.’ Nan suka yi wa Hajia bayanin abinda ake ba su idan suka je gidan yaya jidda; ita ma ta yi mamaki sosai. Tace ‘To me yasa ba ku taɓa faɗa ba?’
    Nasreen ta zumɓuro baki tace ‘Yaya Meena ce tace duk wanda ya faɗa sai ta ci ubansa ta karta masa rashin mutunci don ta san mu da tsinin baki.’ Daga Hajiyan har Mustaphan mamaki ne ya kama su, Meena ita ce babbar ‘yar Yaya Jidda. To amma me zai sa ta yi haka bayan Jiddan da kanta ta gayawa Hajia ya turo kuɗin indomie da kayan karin kumallon yaran?
    Tace ‘Lallai daga Aminan har Jiddan za su zo su same ni.’ Saboda tsabar takaici Mustapha kasa magana ya yi. A nan ya sake ba da kudi Habib ya fita kanti ya siyo musu indomie, yana kawowa Afaf ta dafa musu da ƙwai tunda dama da akwai ƙwai a gidan. Haka ya saka su a gaba duka sai da suka karya azumin suka ci suka ƙoshi.
    Nan ya zauna suka cigaba da hira wajen Hajia tunda shi ma Alhaji ya fice; sai dai har la’asar ta  kawo jiki Yaya Jidda bata zo gidan ba saboda yaronta Abdallah ya shigo gidan lokacin suna cin indomie shi ma ya zauna aka ci da shi kuma yana gamawa ya koma gida ya gayawa uwarsu Abban Afaf ya zo har ma ya sa an dafa musu indomie da ƙwai.
    Don haka tana sane ta ƙi zuwa saboda rashin gaskiya. Haka ya wuni a gidan ransa a ɓace yana tunanin mafita; tabbas duk Khadeeja ce ta janyo masa wannan wulaƙancin. To yanzu ya zai yi da yaran? Idan ya tafi da su ba za su bar shi ya zauna a nutse ba, kuma ma ya san Hajia ba za ta yarda ya tafi da su gida su zauna tare da shi ba.
    Sai dai kamar yanda ta riga ta faɗa ya je ya siyo abubuwan da suke buƙata ya kawo ita sai ta dinga dafa musu kafin Baito ta zo; domin ita ma Baito ɗin mijinta ne ba shi da lafiya take jinyarsa shi yasa ba za ta iya zuwa da safe ba. La’asar tana matsowa ranshi ya sake ɓaci, kuma har lokacin Yaya Jidda ba ta iso ba.
    Bayan ya idar da sallar la’asar yana zaune a kan dadduma yana tunanin mafita Habib ya shigo ya same shi. Bai daɗe da zama ba yace ‘Abba da ma ka kai mu gidan Mama, ka ga dama mun daɗe ba mu je ba tunda muka koma gida. Um, to ai da sallah za ku je ko? Ko ba kwa son zama a nan ɗin ne? Ai ka ga yanzu Hajia da kanta za ta dinga ba ku breakfast ɗin ko?’
    ‘Um, nan ɗin ma muna son zama amma can ɗin ma muna so, in ya so idan Anti Khadeeja ta dawo sai mu dawo.’ Nan sauran yaran suka shigo suka saka shi a gaba a kan su gidan Mama suke so su je; shi ɗin ma yana so ya kai su don ya san ba za a bar su da yunwa a can ba tunda ko babu mai aiki akwai ‘yan mata. To amma yanzu hakan yana nufin kenan ba za a iya riƙe masa yaransa a gidansu ba ko me?
    Ita kuma Yaya Jidda me take nufi? Gashi ta ƙi zuwa, shi kuma ba zai je gidanta ba don ya fi so ta zo su yi a gaban Hajia. Haka dai yaran nan suka saka shi a gaba dole ya amsa zai wuce da su. Ita ma Hajia da ya gaya mata zai kai su sai da ta nuna ɓacin ranta don gani take kamar fushi ya yi da yanda ya sami yaran, sai da Alhaji ya sa baki kuma suka ga Nasreen tana nema ta saka musu kuka sannan suka bari ya kwashi yaran suka wuce gidan Maman su Ma’u.
    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Tara
    Edita@rumasau-kallamu
  • Mijin Marigayiya Babi Na Tara

    Mijin Marigayiya Babi Na Tara

    Kamar yanda aka sanar ranar Asabar aka buɗe gari, ba ƙaramin daɗi wannan buɗewar ta yi wa Mustapha ba. Tun waje ƙarfe takwas ya shirya sannan ya shirya yaran gaba ɗaya, sai dai da ya duba lokaci ya ga safiya ta yi da yawa ya bari zuwa wajen tara da rabi sai su fita; domin so yake su je su ɗauko Khadeeja sannan idan ya kawo ta gidan ya bar su ita da yaran ya wuce gidan hajia ya gaishe su.

    Sai wajen goma saura sannan suka kama hanya. Tun kafin ya gama tsayar da motar yaran suka ɓalle ƙofofi suka fice suka shiga gidan da gudu, bayan sun gaida Mommy wadda take zaune a parlor tace su shiga ɗakin Anti Nabila su taso Antin tasu inda take barci.

    Jin su kawai ta yi a kanta suna shewa, ba shiri ita ma ta miƙe. Nan take aka shiga ba ta labarin abubuwan da suke faruwa a gidan. Ita ma ta yi kewar yaran kuma ta ji daɗin ganinsu sosai. A farfajiyar gidan Mustapha ya tsaya sai da Mommy ta tura Nabila ta shigo da shi, ta buɗe parlor ɗin baƙi ta yi masa iso inda Baffa yake jiransa don shi ma fita zai yi jin isowarsu ya sa ya tsaya.

    Bayan sun gaisa Baffa ya tambaye shi wajen su Alhaji sai ya yi gyaran murya yace ‘Yauwa, ina ga za ka bar Khadeejan ta ɗan ƙara kwana biyu don mahaifiyarta tace akwai abubuwa suke yi na gyara wanda al’ada ta tanada. Don haka ina ga ka bar ta ta ɗan ƙara kwana biyu mu gani.’

    ‘Eh, kuma da zuwa muka yi mu tafi da ita Baffa.’ ‘Allah sarki, ina ga a ɗan ɗaga musu ƙafa su gama shirye-shiryensu, ba za su ɗauki lokaci ba su ma na sani in sha Allah.’ Babu yanda ya iya kwarjinin Baffa ya sa ba zai iya yi masa wani dogon musu ba, don haka sai kawai ya sunkuyar da kai.

    Baffa ya yi masa sallama ya fice ya bar shi a nan cike da taƙaici; yaya Baffa zai yi masa haka? Wannan ɗin shawarar Mommy ce ko kuwa dai Khadeejan ce ba ta son ta koma? Amma dai bari Khadeejan ta fito ya ji daga bakinta. Ya gyara zama ya haɗiye malolon da ya tokare masa maƙogoro ya daɗa saita fuskarsa da ya ji motsi ana taɓa ƙofar daga cikin gida, ya miƙe ya koma kan kujerar zaman mutum ɗaya ya zauna.

    Khadeeja ce ta shigo da sallama, bayan ya amsa ta nemi guri ta zauna a kan three seater ta gefen da ya fi kusa da shi, bayan sun gaisa tace ‘Ya kuke kai da yara? Sun ce min ku kaɗai ne a gida ko gidan Hajia ba ka kai su ba. To ina zan kai su gari yana kulle, dole haka muka zauna mu kaɗai; don ma dai Ummi tana taimakawa, jiya ne kawai da shekaranjiya aka ce ba ta da lafiya.’

    ‘Allah sarki ai iyayenta suna mana kirki gaskiya, Allah ne kawai zai biya su.’Suka yi shiru na ɗan lokaci; idan ma da yana da niyyar gaya mata wasu kalamai masu daɗi to Baffa ya goge masa haddarsu, yanzu haushin kowa ma yake ji. Sai dai fatansa ɗaya ya ga ko zai iya tsara Khadeejan ta canza wanna tsarin don yana jin idan tace tana son ta koma ba za a hanata komawa ba.

    Yace ‘Uhm, da ni fa zuwa na yi mu tafi amma na ji Baffa yace kamar za ki yi wanka ne ko gyara wai sai an kwana biyu za ki dawo.’ Ta ɗan gyara zama ‘Eh, Mommy tace a bar ni sai na yi wankan jego kuma dai da ‘yan gyare-gyare na ƙara hutawa sai na koma.’

    ‘Wai ba ki gayawa Mommy cikin bai ƙarasa wata uku ba ma, na zata haihuwa ake wa wankan jego. Ke dai idan akwai wani dalili ki gaya min sai mu ga yanda za a yi.’ Ta yi ‘yar dariya ‘Shi ne dai dalilin ga shi na gaya maka, don ka ga har yanzu ma ban gama jini ba kusan kwana biyar kenan.’

    ‘Uhm! To yanzu babu yanda za ayi mu koma yau, na san ai duk wani gyara ba zai gagare ki ba tunda kin sami lafiya ga laulayin ma yanzu babu. Gaskiya ka yi haƙuri kawai mu yi yanda Baffa ya faɗa, kwana nawa ne za ka ga ma na dawo gidan. Ya sunkuyar da kai; tabbas wannan tsarin na Khadeeja ne sai dai bai san laifin me ya yi mata ba take son ta yi purnishing ɗinsa haka.

    Muryarta ce ta katse masa tunani ‘Kada ka damu in sha Allahu zuwa bayan sallah zan dawo, ka ga kafin nan ma Mommy ta samo min mai aiki. Bayan sallah? Haba! Wajen sati uku fa kenan? Ai na zata duk inda aka kai nextweek kin gama hutawar. Kuma mai aiki ai Habi za ta dawo bayan sallah ko?’

    ‘Ban sani ba, wai dai don kada ta ba ni mamaki gara a samo min wata tunda ga aikin gida ga hidimar yara sannan ga makaranta zan koma idan an buɗe gari ka ga ina buƙatar taimakon mai aiki ko.’ Sai a lokacin ma sannan ya tuna ashe tana zuwa jami’a; amma dai shi har yanzu bai gane dalilin da yasa ba za ta koma yau ɗin ba har sai nan da sati biyu.

    Ya dai fahimci so take kawai tace aikin gida da na yara ya mata yawa, kuma shi bai ga wani wahala a ciki ba tunda Ma’u ma ko sau ɗaya ba ta taɓa ɗaukan mai aiki ba haka take komai da kanta. Kawai dai ya fahimci Mommyn Khadeeja tana da son zuciya da iko shi ne take son ta juya shi kamar yanda take juya Baffansu, kuma gaskiya shi ba zai ɗau wannan ba.

    Haka dai ya gama kwana-kwanarsa ya tashi ya kwashi yaransa suka wuce gidan Hajia cike da takaicin Mommy Khadeeja wadda duk ita ya ɗorawa laifi, gani yake kamar ita ce take juya Khadeeja da Baffan gaba ɗaya.Tuni Mommy ta ba da umarni a samo mata ‘yar aiki.

    Ransa a ɓace ya shiga gidan Hajia. Yana shiga ya tarar da Yaya Jidda a gidan ita da yaranta, suna zaune a parlor ɗin Hajia suna hira. A gaggauce yaran suka gaisa da Hajia da Yaya Jidda suka shige wajen Baffa da gudu inda yake zaune yana jiran Kamal ɗan autan gidan ya dawo daga shan mai ya kai shi unguwa.

    A nan Mustapha ya zauna wajen Hajia da yaya Jidda, bayan sun gaggaisaya dubi Yaya Jidda yace ‘Ke Yaya sai kace jira kike a buɗe gari ki taho, har ma kin riga ni zuwa.’ Ta yi dariya tace ‘Ni dama babu ni a lockdown in dai gidan nan ne kullum sai na zo, Alhaji ma ya gaji ya bar ni.’

    Hajia ta dube shi tace ‘Ya jikin Khadeejan?’ Ya ɗan karkata kai yace ‘Da sauƙi. Jiya ma mun yi waya da Mommyn tata ai, ta dawo gidan ko sai kun fita daga nan za ku ɗauko ta?’ ‘Mtseww!’ Ya ja gajeran tsaki sannan ya cigaba ‘Daga can muke, wai Mommyn tace ba ta gama hutawa ba kuma sai an mata wanka da gyara za a dawo da ita zuwa bayan sallah.’

    Hajia ta gyara zama ta kama haɓa ‘Ikon Allah, to kai kuma sai kace me?’ To Hajia ya zan yi da su; shi ma baban nata bayan tuni muka gama magana da shi yace nazo na ɗauke ta ina zuwa kuma ya canza zance; yace wai na bar ta. Ita ma kuma Khadeejan kamar haka ta zaɓa, kin ga kenan babu yanda zan yi da ita. Da a ce ma ta ba ni haɗin kai ne da za ta iya canzawa Mommyn ra’ayi don na kula kamar wannan shirin duka nata ne.’

    Kafin Hajia tace wani abu Yaya Jidda tace ‘Ai kuwa lallai shiri, ɓarin ne sai an yi wani wanka da gyara? Lallai matan nan, ni fa dama shi yasa yaran ‘yan bokon nan ba sa wani burge ni, ciki fal iyayin tsiya.’ Hajia tace ‘To me suke nufi? Wannan duk ranar da ta haihu ai sai ta shekara sun gyara sannan za su ba ka ita. To yanzu ya suke so ka yi da waɗannan ‘yayan, ko kuwa don ba ita ta haife su ba?

    Tunda ai da nata ne haɗawa za su yi da su ko kuma ita da kanta ma ba za ta yarda ta tafi ta bar su ba. Wannan ai ba tsari ba ne ba ma, sai dai da yake dama an bar gidan a hannun mace ai dole a ga son zuciya irin wannan.’ Ya gayara zama yace ‘Hmmm! Su suka sani kuma.’

    ‘To yanzu ya za ka yi da yaran? Ko kuwa haka za ku haƙura ku yi zamanku tunda dama babu fita?

    Ko kuma nan za ka bar mini su sai mu yi zamanmu, ka ga na sha allura a wajen Dr. Nasreen. Ya dubi Yaya Jidda sannan yace ‘Da tunani nake na bar su wajen Yaya Jidda sai na koma na ɗauko musu kayansu, in ya so sai a bar su iyayen Khadeejan mu ga lokacin da zasu dawo da ita.’

    Har hajia ta buɗe baki za ta yi magan Yaya Jidda ta tari numfashinta ‘Eh to kuma ka ga da sai mu yi zaman mu, sai dai ka san gidan namu ƙarami ne wajen kwanan zai iya yi musu kaɗan gaba ɗaya da nawa yaran. Ko nan ɗin ma ka bar su wajen Hajiyan ai duk muna tare tunda kullum ni nake zuwa na tsaya a kan hidimar gidan.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci kowa da abinda yake tunani, jiamwa kaɗan hajia tace ‘To hakan ma ai ya yi, ka bar min su a nan tunda ga Baito nan tana nan za ta iya duk wata hidimarsu. Tunda ka ga ai ba ma tsari a ce kana zaune a gida daga kai sai yaranka yaran ma mata.’

    ‘Ba damuwa, zan je na ɗauko kayansu kafin biyar ɗin ta yi. Ya tashi ya fice wajen Alhaji. Yaya Jidda ta bi bayansa da kallo; ya ba ta tausayi amma gaskiya ba za ta karɓi su Afaf ba, gara dai a nan ɗin. Can gidanta ita ma ga nata yaran waɗanda idan ta ga dama nan take turosu wajen Hajia su ci abinci su yi komai sannan kuma a ƙara mata wasu? Gaskiya ba za ta iya ba.

    Sai da la’asar ta kusa sannan ya fita yaje gidan ya haɗo musu kayansu ya kawo sannan ya koma ya bar su a nan

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Takwas

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Takwas

    Mijin Marigayiya Babi Na Takwas

    Shi da yara suka zauna suka gama shan ruwan sanna ya sa Afaf ta kwashe kwanukan, nan suka zauna suka cigaba da kallo suna wasannisu. Har lokacin kwanciyar bacci babu wanda ya ba shi matsala a yaran. Ya tasa su a gaba ya raka su ɗakinsu domin su yi shirin bacci; yana shiga ɗakin zarni ya doki hancinsa.

    Ya dubi Afaf yace ‘Ba na ga Ummi ta fitar da katifun nan ba? Me yasa suke zarni?’ ‘Ta fitar Abba, sai da yamma sannan ta shigo da su gaba ɗaya. Ban sani ba ko katifar Habib ce ba ta bushe ba don ba mu san an yi fitsari ba sai wajen la’asar sanna ya gaya mata Shukra ta yi masa fitsari bayan asuba da ka kwantar da ita.

    Shi ne aka shanya, to ina jin ita ce ba ta gama bushewa ba.’ Ya ƙarewa ɗakin kallo, ko shimfiɗa ba a yi ba a kan gadon don haka ya sa Afaf ta yi musu shimfiɗa yayin da shi kuma ya wuce da su banɗaki don su yi brush. Nan da nan kowa ya shirya bayan sun fito sun kwanta ya cewa Afaf ‘Wai sai yaushe katifun nan za su daina zarni ne?’

    ‘Ni ma ban sani ba Abba, kuma fa idan ba ka saka su sun yi fitsari da daddare ba haka gobe ma za su sake yin fitsarin nan fa. Dama Anti ce kullum take tashinsu, Nasreen sau ɗaya ita kuma Shukra sau biyu shi yasa basa yi a kwancen. ‘To ƙarfe nawa take tashinsu?’

    ‘Wallahi Abba ni ma ban sani ba, kawai dai tana tashinsu.’ Ya amsa sannan ya fito ya dawo parlor ya zauna; to shi yanzu ya za a yi ya san ƙarfe nawa zai saka su wani fitsari, ga shi kuma ga dukkan alamu idan ya bar su suka cigaba da fitsarin nan a kwance to lallai gidan zai daina zaunuwa.

    To amma ƙarfe nawa zai saka su? Wataƙila sai dai kawai idan ya tashi kwanciya bacci ya saka su shikenan. Nan ya zauna a parlor ɗin ya cigaba da kallonsa yana chatting, har ya sami Khadeejan ma online suka ɗan yi hira.

    Ba su fi awa ɗaya da kwanciya ba ya jiyo kukan Shukra daga ɗakin, da sauri ya dire wayar da take hannunsa ya nufi ɗakin. Tana zaune a kan gadon tana ta faman kuka har da hawaye. Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita yana cewa ‘Menene Shukra?’ ‘Kashi zan yi.’

    ‘To ai ba sai kin yi kuka ba Shukra, sauko mu je na saka ki a toilet.’ Ya sauke ta daga kan gadon ya ja hannunta suka wuce banɗaki, suna shiga ya cire mata wando ya fara ƙoƙarin ɗora ta a kan toilet ta dafe duwawu tana juyi tana cewa ‘Ina fo na Abba a shi zan yi.

    ’Cikin muryar lallashi yace ‘To ai ba a ganshi ba ki yi haƙuri ki hau toilet. ‘Mu je ka duba banɗakin Anti fo ɗina yana nan Abba a shi zan yi kashin.’ Ya ɗauke ta gaba ɗaya ya ɗora a kan toilet yana cewa ‘To ki gama kashin kada ya fito in ya so idan kika gama sai mu je mu dubo fo ɗin.’

    Kafin ya rufe bakinsa ta zame ta sauka daga kan toilet ɗin, tana kuka. Ta cigaba da bubbuga ɗuwawunta tana shirin ficewa daga banɗakin tana cewa ‘Fo na yana banɗakin Anti bari na ɗauko a shi zan yi kashin.’ Cike da tsananin mamaki da takaici yake kallonta, ga dukkan alamu kashin ya matse ta amma ita ba ta da niyyar zama a toilet ɗin nan so take dole sai ya ɗauko mata fo; fo ɗin da ya riga ya jefar ba tare da kowa ya sani ba.

    Ya kai hannu ya damƙota tana shirin ficewa daga banɗakin, ya mayar da ita kan toilet ɗin ya zaunar da ita yana cewa ‘Anti ta kulle ɗakinta ta tafi da mukullinta sai ta dawo za ta buɗe mana, ki yi kashin a nan.’ Ta sake direwa ta sauka daga kan toilet ɗin tana buga ɗuwawu har da juyi saboda yanda kashin ya matse ta tana cewa ‘Ka zo na nuna maka Abba ba ta rufe ba, a buɗe ɗakin yake ɗazu ma na shiga.’

    Kafin ya yi wani abu kashin ya ƙwace mata, ɗan kaɗan ya faɗo ya zame daga ɗuwawunta ya ɓata tsawon ƙafarta sanna ya dire a ƙasan toilet ɗin. Ya yi wuf ya ɗauketa ya daka mata tsawa yana cewa ‘Ki zauna a nan ki yi kashin nace, kalli yanda kika ɓata jikinki kika ɓata toilet ɗin da kashi.’

    Ta sake fashewa da kuka tana yi tana shessheƙa, takaici ya sa ko magana ba zai iya yi mata ba don haka ya ƙyale ta kawai yana tsaye tana rungume da ƙafarsa yana jira ta gama. Ko minti ɗaya ba ta yi ba tace masa ta gama kashin, ya leƙa toilet ɗin shi bai ga komai ba. Yace ‘Idan fa kika yi min kashi a wando zane ki zan yi Shukra gara ki gama kashin nan a nan.’

    ‘Na gama. Ya ɗauketa cak ya ajiye ta a wajen wanka, ya ɗauki sprayer ɗin yin tsarki ya fesa mata ruwan da ƙarfi ta yanda ruwan ya wanke kashin jikinta, sannan ya saɓi sabulu ya wanke mata da hannunsa. Ya ɗauke ta ya fitar da ita ya shirya ta ya kwantar da ita sannan ya koma banɗakin; ya tsaya daga bakin kofa ya ƙarewa banɗakin kallo.

    Ga guntun kashin da ta jefar a ƙasa sannan gashi duk ta shafe na jikinta a jikin toilet ɗin banɗakin har ya fara wari. Ya yi tsaki ya juya ya fice, jimawa kaɗan ya dawo ɗauke da tissue paper, ya warware kusan rabinta sannan ya yi amfani da ita ya ɗauke guntun kashin jefe a toilet ɗin. Sannan ya sake warwarowa ya goge toilet ɗin ya yi flushin sannan ya fito ya dawo parlor ya zauna cike da takaici da gajiya.

    A nan a parlor ɗin bacci ya kwashe shi, wataƙila saboda tsabar gajiya domin bacci ya yi masa nauyi sosai. Maganar Shukra ce ta farkar da shi wadda ta je tashinsa tana sanar da shi za ta sha shayi. Ya tashi zaune yana mittsike ido, ya lalubi waya ya duba lokaci; ƙarfe ukun dare saura.

    Haka ya tashi ya haɗo mata shayin ya zo ya ba ta ta shanye sannan ya ja hannunta suka koma ɗakin. A nan ya tarar ita da Nasreen duk sun riga sun yi fitsarinsu a kwance; ya canzawa Shukra kaya ya lallaɓa ya kwantar da ita a gefen da bai jiƙe ba kusa da Afaf. Ya ɗan tsaya ya ƙarewa ɗakin kallo, sai kuma ya juya ya fice.

    Gaba ɗaya kansa ya kulle; wai dama haka yaran nan suke ko kuwa don sun ga mahaifiyarsu ba ta nan ne kuma Khadeeja ba ta nan suka saka shi a gaba suka hana shi sakat, domin wasu abubuwan da suke yi ma kamar da gayya musamman Shukra.

    Har zai zauna a parlor ɗin kuma ya tuna sai ya dafa abinda zai yi sahur don haka y wuce kitchen, ya janyo indomie ya ɗebo park uku sannan ya nemi tukunya ya ɗora; Afaf da Habib sun yi ta fushi a kan jiya bai tashe su sahur ba don haka yau idan ya gama dafa abincin sai ya tashe su.

    Nan da nan ya dafa idomie ya zubawa kowa a plate ya ɗora a dining table sannan ya haɗawa kansa shayi. Bayan ya gama ya wuce ɗakinsu, ya kunna fitila sannan ya ƙarasa ya tashi Afaf, ta zauna a kan gadon tana mittsike ido sanna ya wuce ciki ya tashi Habib. Yana juyawa ya buɗe ido yace ‘Abba asuba ta yi ne?’

    ‘No da saura, sahur za mu yi tukunna ga indomie can na dafa.’ Ya ba shi amsa. Ya gyara kwanciya yana janyo abun rufarsa yana cewa ‘Ni ba zan yi azumi ba Abba, sai gobe.’ Ya rufe ido ya cigaba da baccinsa ba tare da ya sake bi ta kan Abban nasa ba. Afaf wadda take zaune a bakin gadonsu ta juyo tace ‘Abba wai sahur za mu yi.’

    ‘Eh.’ ‘To Abba ai jiya ne ya kamata mu yi azumi kuma ba ka tashe mu ba, ni ma dai gaskiya yau ba zan yi azumin ba sai gobe. Dama haka muke yi da Anti; mu yi ɗaya mu sha ɗaya.’ Ta faɗa cikin halin ko in kula. Ba ta ma tsaya ta saurari amsar shi ba ta koma ta kwanta ta rufe ido.

    Nan ya tsaya yana kallonsu cike da mamaki; wai su yaran nan me yake damunsu ne? yanzu za su ce za su yi abu kafin wani lokaci sun canza ra’ayi. Gaskiya ya jinjinawa mata, ai idan ba mace ba babu wanda zai iya raino; jiya fa Afaf fushi ta yi da shi saboda bai tashe ta ba amma yau kuma ita yake tashi tana ce masa wai yau bai kamata ta yi azumi ba.

    Yana fitowa daga ɗakin ya haɗa indomie ɗin ya juye a tukunyar ya rufe ya ajiye musu a kan idan gari ya waye sa ci abincin safe, sannan ya dawo ya ƙarasa sahur ɗinsa.

    Kamar yanda suka saba yau ɗin ma da tun asuba suka tashe shi a kan yunwa suke ji, haka ya shiga kitchen Afaf ta taimaka masa ya haɗawa kowa cereal domin duk sun ce ba za su ci indomie ba don ta yi sanyi kuma ba sa son ɗumame, da ya takura musu ma sai Nasree cewa ta yi ‘Abba kai fa idan ka dafa indomie ba ta daɗi, ka bari idan Anti ta dawo ta koya maka.’

    Don haka kawai sai ya mayar da indomie ɗin ya rufe. Tun wajen goma na safe yake sa ran shigowar Ummi don ya riga ya gaya mata yau ma ta zo, sai dai ga mamakinsa har wajen sha ɗaya saura ba ta shigo ba; gashi har na fara yi masa ƙorafin yunwa kuma ana ba shi warning ba za a ci indomie ba sai da taliya ko macaroni.

    Yana shirin fita ya je gidan su Ummin aka buga gate; ƙanwarta ce wadda suke kira Nana, wadda ba ta fi shekaru bakwai ba. Bayan ta gaishe shi tace ‘baba yace na gaya maka Ummi ba za ta sami zuwa wajen su Afaf ba yau don ta tashi da mura me zafi tana kwance, yace sai dai ko zuwa gobe idan ta sami sauƙi za ta shigo.’

    Jiki a sanyaye ya amsa ‘To, kice ina mata sannu kuma ki ce ina gaida Baban. ’Ya rufe kofar ya koma cikin gidan gwiwarsa a sanyaye; ya zai yi da yaran ga gidan kace-kaca musamman kitchen ɗin, ko ina kwanuka. Tukunna ma; mura fa aka ce Ummi take yi. Inna lillahi wa inna ialaihi raji’un! Allah ya sa yarinyar nan ba Covid-19 ta kwaso ba garin yawon tsiya, don tabbas idan ta kwaso to ta shafawa yaransa.

    ‘Subhanallah!’ ya faɗa a fili yana daf da ƙarasawa cikin gidan. Bayan ya shiga gidan ya yi musu bayanin Ummi ba ta da lafiya. Yana ji yana gani haka ya haƙura Afaf ta dafa musu jallof macaroni, bayan sun gama ci kuma ta kwaso wanke-wanke ta fice da shi waje ta wanko; duk da ƙoƙarinsa na hana ta amma haka ta dage ta wankesu.

    Sannan ta umarci Halifa da ya share cikin gidan wanda shi ma nan da nan ya yi, suka dawo suka zauna. Wunin ranar haka ya yi shi yana gyangyaɗi domin ko ya rufe ido da niyyar bacci haka wani zai rugo kai ƙara har Afaf ɗin ma, ko kuma a zo a ce masa ana buƙatar wabi abu; ita kam Shukra haka kawai ma da ta ga ya shiga ɗaki binsa take yi, idan kuam a parlor ne da ya rufe ido za ta kirawo sunanshi tace ya buɗe ido ta nuna masa wani abu.

    Haka har aka kusan magriba sannan ya samu da taimakon Afaf ya soya musu dankalin bature kuma ya dafa musu indomie ta ɗan yi daɗi. Wuni yaran suka yi suna ciye-ciye amma ko da ka sha ruwa ma saka shi suka yi a gaba ana cin abinci suna masa surutu da rigingimu kala-kala; shi dai zai iya cewa ba a hayyacinsa ya ci abincin nan ba. Haka ya dinga ci yana ƙwarewa.

    Ya cika bakinsa da dankali Shukra ta miƙe ta jefar da dankalin da yake hannunta tana dafe ɗuwawu tana cewa ‘Kashi Abba.’Ji ya yi wani malolo ya tokare masa maƙogoro; wai ita Shukra ba ta tashi kashi ne sai mutum yana tsaka da wata sabga? Lallai yanzu ya tabbatar Khadeeja tana da ƙoƙari don kusan tunda aka fara azumin nan sai ana tsaka da cin abinci sannan Shukra take cewa za ta yi kashi kuma ta tashi ta sakata; idan ma ta yi jinkiri shi ne yake nuna damuwarsa.

    Ya dubi Afaf wadda ya kula kamar ta ɓata rai ne yace ‘Yaya Afaf ki saka ƙanwarki a toilet ta yi kashi.’ Ta tashi a fusace ba tare da ta amsa ba ta dire kofin shayin da take sha a ƙasa, tana ɗaga kafa ta yi fatali da kofin shayin ya zube ya fallatsa ya ɓata Habib wanda yake kusa da ita. Ya miƙe a fusace yana nunata ‘Dalla malama ji yanda za ki ƙona ni da shayi saboda kashin wata.’

    Ita ɗin ma a fusace tace ‘To ka matsa mana, ko ba ka gani ne?’ Abbansu ya buɗe baki zai yi magana Shukra tace ‘Kashi Abba.’ Ya tuna yanda suka yi cikin dare ya tabbatar bai shirya wanke kashi a parlor ba don haka ya miƙe ya wuce su ya ja Shukra ya nufi banɗaki da ita. Sai da ta gama kashin ya wanke mata ya fito sannan ya saka su a gaba ya yi musu faɗa, ya sa Afaf ta gyara inda ta ɓarar da shayi.

    Ya kurɓi shayinsa da ya bari ya ji ya yi sanyi, haka dai ya haƙura ya shanye ya ɗan ƙara cin abincin. Haka ya haƙura ya nemi waje ya zauna yana tunani don zai iya cewa ba ƙoshi ya yi ba ya dai haƙura da abincin ne kawai, haka ya dinga bin su da kallo suna ta wasanninsu har loakcin kwanciyar bacci.

    A cikin wannan halin Mustapha ya ƙarasa kwanaki biyu shi da yaran a jigace, ga shi duk wanda ya yi atishawa ko tari a cikin yaran sai ya firgita saboda gani yake kamar corona ce ta kwantar da Ummi kuma su ma sun shafa a wajenta.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Bakwai

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Bakwai

    Mijin Marigayiya Babi Na Bakwai

    Haka Khadeeja ta kwana a asibitin ƙarƙashin kulawar Anti Iyami. Tun dare likita ya gama da ita aka ba ta duk wasu magungunanta, ya sanar da Anti Iyami za a iya tafiya da ita gida. Don haka gari yana wayewa ƙarfe takwas na safe Anti Iyami ta gama aiki za ta tafi gida ta shiga ɗakin da Khadeejan take.

    Bayan sun gaisa tace ‘Yanzu akwai inda yake miki ciwo Khadeeja.’ Ta jijjiga kai tace ‘A a, ko ina ya warware, yanzu ma na gama breakfast ɗin da kika aiko min da shi.’ ‘Ok, so ki kirawo Mustapha kice masa zan wuce da ke gida sai mu tafi na kai ki gidan Mommy ɗin.’

    Ba ta son ta yi magana da shi sai ta je gidansu don haka cikin sauri tace ‘Ai yanzu na kirawo shi bai ɗauka ba, ina jin yana bacci ko baya kusa da wayar amma na san da ya gani zai kira. Mu wuce kawai tunda tun jiya na gaya masa za mu wuce gidan.’

    ‘Ohk, to tashi mu tattara kayan mu wuce. Ni ma tun dare na kirawo Mommyn naki na sanar da ita, da safe ma mun yi waya. Na dai ce mata kada ta kirawo ki ne don duk lokacin da na shigo sai na same ki kina bacci, shi yasa nace ta bari idan kin tashi zan kirawo ta ku yi magana.

    But ba komai idan mun je za ta ganki tunda mun shirya.’ Nan suka haɗa kayan Khadeejan waɗanda daman ba yawa ne da su ba suka shiga motar Anti Iyami suka kama hanya.

    Khadeeja tana zama a mota ta lalubo wayarta ta saka ta a silent ta jefa a jaka don ba ta so Mustapha ya kirawo ta a gaban Anti Iyami domin ba ta san me zai ce ba idan ya ji ta wuce gidan Mommy. Duk inda suka je checkpoint aka tsayar da su da an ga uniform ɗin Anti Iyami kuma ta nuna ID card sai a bar su su wuce, haka har suka isa gidan Mommy.

    Tun suna asibitin Anti Iyami ta sanar da Mommy za su taho don haka kafin su isa an ɗorawa Khadeeja ruwan wanka, suna shiga ta wuce ɗakin Mommy inda Azumi mai aikinsu ta sirka mata ruwan a banɗaki. Ba tare da ɓata lokaci ba ta faɗa wanka.

    A parlor Mommy suka zauna da Anty Iyami; bayan sun gaisa sun jajantawa juna Mommy tace ‘Ina Mustaphan? Ai na zata tare kuke da shi.’ Ta gyara zama tace ‘Bai zo ba ma yau da safen duk da dai tace ta gaya masa nan za mu huto, amma don Allah ƙawata a duba yarinyar nan.’

    Cike da kulawa Mommy tace ‘In sha Allahu kuwa, ke ma kin san ba zan barta haka ba ko akwai wata matsala ne da ta samu ko rashin lafiya.’Ta jijjiga kai ‘Babu fa, kawai dai tace min tana son dawowa gida. Duk dai wasu tambayoyi da zan yi mata na yi ta nuna min babu komai, to amma kin ga akwai yaransa guda huɗu.

    Wataƙila hidimar gida da ta yaran ce take mata yawa ga ciki shi yasa ta sume masa. Baccin da ta dinga yi kawai ya tabbatar min da cewa ba ta samun isasshen bacci wallahi, don shi yasa ma na ƙi tashinta ku yi waya. Gaskiya ku bincika, ya nema mata mai aiki ko ya san yanda zai yi da yaransa.’

    ‘Umm! To kin ga dai idan ma da wata matsala ba ta faɗa ba, koda yake kwanaki tace mai aikinsu ba ta nan a bata aron Nabila amma Baffansu ya ƙi amincewa. Wataƙila saboda babu mai aikin ne abun ya yi mata yawa ga laulayi.’

    ‘Gaskiya dai ku duba, ko da za ta koma ku bar ta ta huta ta sami natsuwa sannan kuma a ɗaukar mata mai aiki.’ Suka ƙarasa hirarrakinsu daga baya suka yi sallama Anti Iyami ta kama hanya.

    Bayan ta fito daga ta tarar da farfesun kaza mai rai da lafiya wanda Mommy ta dafa mata sannan ga shayi mai kauri Azumi ta haɗa mata da burodi a gefe, cikin sauri ta gyara jikinta ta sa kaya sannan ta shimfiɗa dadduma a gaban gado ta miƙe ƙafafu ta zauna ta fara cin abinci.

    A nan Mommy ta shigo ta same ta ita ma ta zauna, sai da ta gama cin abinci sanna ta fara yi mata tambayoyi. Ba ta ɓoyewa Mommy komai ba ta sanar da ita halin da ake ciki, ta tabbatar mata cewa idan dai da mai aiki musamman babba wadda ba za ta sa ta surutu ba.

    Sai dai ta kasa gaya wa Mommy cewa gaba ɗaya ma ko da da mai aikin ita ji take kamar ma Mustaphan baya ƙaunarta, gani take kamar yanda take zama kullum cikin hidima ya sa ba ta gane kulawarsa a gareta. Don haka ta bar wannan a ranta tana fatan idan an sami mai aiki ya zama suna samun lokaci a tare to za ta fuskanceshi.

    Muryar Mommy ce ta katse ta tana cewa ‘To yanzu yaushe zai zo ya ɗaukeki?’ Ta kalle ta suka haɗa ido ta sunkuyar da kai sanna cikin muryar shagwaɓa tace ‘Mommy kin ga yanzu mai aikin ba ta dawo ba, kuma na gaya miki shi ba zai taya ni komai ba kuma ba zai bari yaransa su tayani ba.

    Kawai ki bar ni sai bayan sallah ko kuma duk lokacin da mai aikin ta dawo ko aka sami wata.’ Mommy ta jijjiga kai tace ‘Na fahimce ki, amma me kike so na gayawa Baffanku? Shi kuma Mustaphan wane dalili za a ba shi na riƙe ki a nan ɗin. Tunda dai ciki ya fice an riga an wake; kuma ga ki nan kowa yana ganinki ras.’

    Ta karyar da kai kamar abin tausayi tace ‘Umma ni dai don Allah ki san yanda za ki yi a bar ni na huta. To bari mu gani. Idan kuma akwai wani abun da Mustaphan yake yi miki wanda kike so a yi masa magan to ki gaya min.’

    ‘Babu komai tunda ma bai hana a ɗauki mai aikin ba, in sha Allahu da ta dawo ko kika samo min wata zan koma.’ Ta gyara zama ta kafa tagumi ‘Hmm! bari mu ga yanda za mu yi da Baffan naki tukunna.’

    Sai da suka gama wannan hirar sanna ta tuna tunda suka shigo ba ta ma nemi wayarta ba, ta san yanzu haka Mustapha yana ta faman kiranta. Cikin sauri ta miƙe ta ɗauko wayarta daga jakarta, ai kuwa tana dubawa taga missed calls ɗinsa har guda goma sha ɗaya.

    Tana gani danna masa kira, ko ringing ba ta yi ba ya ɗauka ‘Hello, wai ina kika shiga ne naje asibiti ina ta nemanki? Na rasa mai ba ni tsayayyiyar amsa, sai ce min kawai ake kin tafi da Anti Iyami, na za ta gida za ta kawo ki na dawo gidan kuma baku zo ba. Kin sa ina neman haukacewa na rasa wanda zan kira don ban san me zan ce musu ba.’

    ‘Subhanallah! Ka yi hakuri Babe, wallahi ka ganni nan ai gidan Mommy ta kawo ni. Na kirawo ka ba ta shiga ba kuma shi ne na jefe wayar a jaka na manta sai yanzu da na fito daga wanka na tuna. Amma shi ne ba ki gaya min ba? Kin san wulaƙancin da aka dinga yi min a checkpoint kuwa?’

    Ta tausasa murya ‘Sorry Babe, wallahi laifi na ne don tun a asibitin Anti Iyami tace na kirawo ka sai wayar ta ƙi shiga.’ Ya ɗan saki numfashi ‘To me yasa ba ku taho nan ba ko kuma a jirani na zo? Me ya sa za a kai ki gidan Mommy?’

    Ta ɗan yi shiru, shi ma bai yi magana ba yana sauraronta; ta murguɗe baki kamar yana kallonta tace ‘Ai ka san dai idan an haihu ana zuwa wanka gida, may be shi yasa da suka yi waya Mommy tace a kawo ni gida.’

    ‘To kuma shi ne aka rasa wanda zai gaya min.’ Cikin ƙosawa tace ‘To ba ga shi na gaya maka ba, kuma ai nace maka mantawa na yi.’ Ya ɗan ja numfashi ‘Uhm! To ya jikin naki? Shike nan an gama yi miki alluran?’

    ‘Na sami sauƙi, ga ragowar magungunana na taho da su daman yawanci na kwana bakwai ne, amma na sami sauƙi. To idan an buɗe gari sai na zo na ɗauke ki, ina ga ranar Saturday za su ɗan buɗe mu, nan da kwana uku kenan.’

    ‘Uhm, to ka dai zo amma gaskiya sai bayan sallah zan dawo kafin nan na dan huta na gama arba’in tunda ka san shi ma ɓarin ai sai an yi wanka. Ɓarin, gaskiya ban taba ji ba. Ma’u ma fa su biyu tana yin ɓarin amma na biyun babu wanda ma muka gaya wa a nan ta yi zamanta ta cigaba da hidimarta.

    Hutawa kawai ta yi na kwana biyu. Idan ka zo dai ma yi maganar.’ Ta tamabye shi yaran ya ba ta su suka gaisa sannan suka yi sallama suka ajiye waya.

    Tunda yake bai taɓa ganin son zuciya irin wannan ba, ya za a yi a ɗauke masa mata kuma a ce sai bayan sallah za ta dawo? Kawai saboda ta yi ɓari. Asma’u ma ai ta yi ɓari har sau biyu ma; na farkon shi ne bayan haihuwar Habib, bayan an yi mata wankin ciki a ranar suka dawo gida.

    Ko maganar ta je gidansu ma ba a yi ba kawai dai an kawo mata ƙanwarta tunda dama tana da mai aiki. Na biyun kuwa ma bayan haihuwar Nasreen babu wanda suka gaya wa, suna zuwa asibiti aka ce musu ya fice gaba ɗaya ba sai an yi wankin ciki ba aka ba su magunguna suka dawo gida.

    Kawai dai ya san ba za ta koma ɗakinsa ba sai bayan kwana arba’in, kuma ba shi da matsala da wannan. Amma su iyayen Khadeeja saboda son zuciya sai akwai su ɗauke ‘yarsu? Kuma ko gaya masa ba za ayi ba.

    Haka ya gaji da saƙe-saƙensa ya sake daga wayar ya kirawo Alhaji ya gaya masa, don bai gaya musu cewar a asibiti ma ta kwana ba yana so ya je da safen ya gani tukunna. Shi ma Abban ya nuna rashin jin daɗinsa da aka tafi da ita, musamman da ya gaya masa ba su ma tambaye shi ba suka tafi da ita.

    Bayan sun gama waya da Alhaji ya kirawo Ummansu ita ma ya sanar da ita. Suma su Afaf sai da ya yi musu bayani don tunda ya dawo ba su ganshi tare da Khadeeja ba suke ta faman yi masa tambayoyi. Babu yanda za a yi ya iya ɓarin Khadeeja ta zauna a gidansu, ya suke so ya yi?

    Ga lockdown an hana mutane fita sannan kuma su ɗauke masa mata. Kwana ukun nan ma da zai yi da yaran bai san ta ina zai fara ba don yana tuna yanda a kwana ɗayan nan suka gama firgita shi; ga gari a kulle balle ya kai su gidan Umma. Gaskiya da an buɗe gari ranar Asabar zai je ya ɗauko ta tunda dai ko shi ya tambaye ta jiki ta ce da sauƙi.

    Sai can da yamma dabara ta faɗo masa; ya ɗauki waya ya kirawo Baffan Khadija, bayan sun gaisa ya jajanta masa jikin Khadeejan sannan ya sanar da shi cewa ranar Asabar idan aka buɗe gari zai zo ya ɗauki Khadeejan.

    Ba tare da matsala ba kuma Baffan ya amsa masa da hakan ya yi, don haka cikin walwala ya ƙarasa wuninsa. Bayan Ummi ta gama haɗa musu kayan shan ruwa shi da yara ta wuce ta tafi gidansu ta bar su.

    Tun bayan dawowar Khadeeja gidan sau ɗaya Baffanta ya shiga ɗakin Mommy ya same ta ya yi mata sannu. Yana zaune a parlor bayan ya dawo daga sallar tarawih Mommy ta shiga ta same shi, ta zauna a gefensa suna kallon labarai a tashar Aljazeera tare. Bayan sun ɗan taɓa hira yace ‘Ɗazu Mustapha ya kirawo ni yana duba Khadeeja, ya ma ce min idan an buɗe gari ranar Asabar zai zo su tafi.’

    Ta ɗan gyara zama ‘Ranar Asabar fa kwana uku kenan, haba ai sai ta kwana arba’in. A ah to ai ni na za ta sun gama magana da ita ne a kan hakan.’ Ta jijjiga kai tace ‘Gaskiya dai ba su yi wata magana ba don da kanta tace min tana so ta yi arba’in ɗin. Suna zuwa da na sa ruwan zafi nayi mata wanka ta ji dadin jikinta da kanta tace a bar ta ta yi arba’in ɗin.

    Haba, kuma haka za a mayar da ita haihuwar fari babu wani gyara? Sai kace ‘yar tsana.’ ‘To ai na ga ɓari ne ba haihuwa ba.’ ‘To ai Baffan Nabila ɓari ya fi haihuwa wahala sosai ma, sannan kuma na fari ne haka za a ba shi matar ya ma kasa ɗaga mata ƙafa a kwana arba’in ɗin.’

    ‘To na ga dai ai matarsa ce ko? Ina laifi, kuma ma ai shi ma ba zai ce bai san waɗannan hukunce-hukuncen ba tunda ga yara nan har huɗu an haifa masa.’ Ta sake gyara zama ‘Ku dai yi haƙuri Baffa a bar ta ta yi kwana arba’in ko a ƙalla talatin, kafin nan ta ji daidai a jikinta sai ta koma.’

    Ya ɗaga wayarsa ya cigaba da dubawa yana cewa ‘To ai shikenan idan ya zo sai ku yi masa bayani, ni bani da matsala da hakan.’ ‘Yauwa, ai lalacewar zamanin ba ta kai an daina wanka da gyara a haihuwar fari ba. Amma dai idan ya zo sai ka yi masa bayanin idan kana nan tunda ka ga kai ya nema, gara ku cigaba da magana man to man.’

    Ya yi dariya yace ‘To babu laifi.’ Ya san halin matarsa da kishi, yanzu haka haushi ta ji shi Mustaphan bai kirawo ta ya duba Khadeejan ba ko a ƙalla ya gaya mata zai tafi da Khadeeja ranar Asabar tunda ya san ita ce za ta shirya Khadeejan amman ya kirawo Baffa. Jimawa kaɗan kuma ta fice ta ba shi waje.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Shida

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Shida

    Mijin Marigayiya Babi Na Shida

    A gajiye ya shiga gidan wajen ƙarfe tara na dare, yana shiga yaran suka taso da gudu gaba ɗaya tun kafin ya gama rufe ƙofar motar suba cewa ‘Abba ina Anti Khadeeja?’ Ya ɗauki shukura ya kama hannun Nasreen yana cewa ‘Tana asibita, likita ya kwantar da ita, amma gobe in sha Allahu zan je na taho da ita.’

    Ya tattara su suka shige cikin gidan. Yana shiga bayan Ummi ta yi masa sannu da zuwa ya sallame ta ya fito ya raka ta sai da ta shiga gida ta kirawo masa babanta ya yi godiya sannan ya koma gida. Sai da ya biya sallar Magriba da Isha’I duk da yunwar da yake ji sannan ya zo ya zauna a parlor a gajiye, ya dubi Afaf wadda take kwance tana yin game a tab ɗinta yace ‘Afaf ɗauko min flask da kayan shayi.’

    Ta miƙe ta shiga kitchen ɗin, jimawa kaɗan ta fito ɗauke da kayan shayin bayan ta ajiye tace Abba babu ruwan zafi a flask ka jira na dafa maka, wanda Anti ta zuba mun sha shayi da shi mu da Ummi.’

    ‘No, bar shi kawai. Ɗauko min zoɓo ki kawo min ragowar abincin da kuka ajiye na ci, yunwa nake ji.’ Kafin ta ba shi amsa Habib yace ‘Abba ai tun kafin ku fita zoɓon ya ƙare a nan, ka manta? Kuma dama shi kenan wanda Anti ta zuba ragowar na jiya ne.’

    Kafin yace wani abu Afaf tace ‘Abba babu fa abincin ma sai dai ragowar rice and stew, gaba ɗaya dankalin muka cinye kuma da peppersoup ɗin, amma akwai ragowar watermelon a fridge. Ko na dafa maka indomie?’

    Ya kalle ta yana shafa kai na ɗan lokaci, ya ma rasa me zai ce mata saboda yanda gaba ɗaya ya jigata saboda yunwa, coke kawai ya samu a asibiti da wani guntun burodi ya ci. Ya zata za su rage abincin amma wai duk sun ciye. Muryar Afaf ce ta katse shi tana cewa ‘Bari kawai na dafa maka indomie ɗin Abba.’

    ‘No, bari na shiga kitchen ɗin na gani.’ Ya faɗa yana miƙewa tsaye. Ya ɗan ɗauki yana kallon kitchen ɗin bai ma san ta inda zai fara ba; har ya ɗauki tukunya zai dafa indomie sai kuma ya tuna ai akwai cereal, don haka ya mayar da tukunyar ya ajiyeta a muhallinta.

    Ya zuba ruwan zafi a kettle ya tafasa ya haɗa cereal, ya ajiye ya fiddo kankana daga fridge ya yanka sannan ya ɗauko ya dawo parlor ɗin. Yana zama Shukra ta matso tana dariya ‘Abba zan sha golden morn ɗin.’Ya bi ta da kallo da cokali a hannunsa; ba ta taɓa ba shi takaici ba kamar a wannan lokacin don ya tabbatar sun ƙoshi tunda gashi sun cinye duk wannan uban abincin da Khadeeja ta dafa.

    Ya dubi Afaf yace ‘Tashi ki ɗauko cereal, ki haɗo min da tea flask da komai na haɗa mata.’ Kafin Afaf ta dawo Nasreen tace ‘Abba ni ma zan sha.’ Don haka tana kawowa ya sa ta koma ta ƙaro kofi, ya haɗa musu cereal ɗin su biyun.

    Babu wadda ta sha cokali uku a cikinsu, suka tashi suka bar masa a nan. Kafin ya gama cinye nasa abincin duk sun fara gyangyaɗi don haka ya sa Afaf ta ɗauko musu kayan baccinsu ya shirya su bayan ya raka su sun yi brush sun yi fitsari. Bayan sun kwanta sannan Afaf da Habib su ma suka shirya, Afaf ta zauna a gefen gado ta yi tsuru-tsuru shi ma Habib sai ya hau katifarsa ya kwanta yana zare ido.

    Yana tsaye daga bakin kofa yace ‘Yaya dai Afaf? Ki kwanta mana, ko akwai wata damuwa ne?’ Ta jijjiga kai tace ‘Kawai tunawa na yi da Mommy, ita ma muna bacci ta mutu.’ Ya gaji sosai ga kansa yana sarawa, babu abinda zai iya yi musu na lallashi, ya buɗe baki a gajiye yace ‘In sha Allahu babu abinda zai sami Anti, ku yi addu’a ku kwanta ku yi bacci kawai.’

    Habib shi ma ya tashi zaune yana share ƙwalla ‘Wallahi Abba ni ba zan ma iya baccin ba, Allah ya sa dai kada Anti Khadeejan ma ta mutu ta bar mu. Har yanzu idan na tuna Mommynmu sai na yi kuka.’ Kafin ya yi magana ita ma Afafa ɗin hawaye ya fara bin fuskarta, ta sunkuyar da kai ta sa masa kuka har da shassheƙa.

    Ji ya yi kamar ya ɗora hannu a ka ya sa ihu; ina ma yaran nan za su bar shi ya huta, yanzu ya zai yi da su? Manyan cikinsu da yake ganin su ne ba za su bashi matsala ba su ne suke so su hana shi bacci. Ya ƙarasa ya zauna a kusa da Afaf ya rungumota yana cewa ‘In sha Allahu babu abinda zai sameta, ku daina kuka ku yi mata addu’a Allah ya ba ta lafiya. Goben nan ma zaku ga an sallamota.’

    Ta fara share hawayenta, Habib wanda shi ma ya taso ya dawo kusa da ita yace ‘Abba to ka kirawo mana ita a waya mu yi mata sannu.’ Ya zaro wayarsa daga aljihu yana cewa ‘To ai da bana son kiranta saboda kar na dame ta don an yi mata allurai, ban sani ba ko har da ta bacci a ciki. Amma bari na kirawo ta sau ɗaya idan ta ɗaga shikenan idan kuma ba ta ɗaga ba sai mu haƙura da safe ma sake kira.’

    Ya lalubo lambarta ya danna mata kira, sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ta ɗaga. Murya ƙasa-ƙasa tace ‘Hello.’Yace ‘Hello, Khadeeja ba ki yi bacci ba?’ ‘Na ɗan yi, farkawa dai na yi kuma na ji wayar tana ringing. Ai tun ɗazu aka gama wankin cikin har na ɗan ci abinci.’ ‘Sannu. Wankin cikin ba wahala kenan?’

    ‘Hmmm! Akwai wahala ba kaɗan ba, kawai dai da an gama aka ba wa mutum maguguna sai ya sami relief.’ ‘Sannu. Afaf ce dama ita da Habib wai ba za su iya barci ba sai sun yi miki sannu.’ Ta yi murmushi mai sauti domin ta ji daɗi har cikin ranta, ta tabbatar cewa yaran nan suna ƙaunarta kuma da zai barta da su komai nasu zai zo da sauƙi amma shi komai gani yake kamar za ta cuce su.

    Muryar Afaf ce ta katse ta bayan da Abbanta ya ba ta wayar ‘Anti.’ ‘Na’am Afaf, ya aka yi ba ki yi bacci ba.’ ‘Babu komai Anti, ya jikin naki? Ke ya aka yi ba ki yi baccin ba? Ta yi ‘yar dariya tace ‘Yanzu zan yi Afaf, kuma na sami lafiya don likitan ma ya ce gobe za a sallame ni.’ Suka ɗan taɓa hira sannan ta yi mata sallama ta miƙawa Habib wayar. Bayan sun gama gaba ɗaya ya karɓi wayar ya katse ya yi mata sai da safe. Ya yi musu sai da safe suka kwanta, har zai kashe fitilar Afaf tace ‘Abba kada ka kashe mana fitilar, in an jima ka zo ka kashe.’

    Haka ya bar musu fitilar ya fice. Can bayan awa ɗaya ya gama abinda yake yana so ya kwanta saboda ya gaji ya zo zai kashe musu fitilar, yana kashewa Afaf da Habib suka haɗa baki a lokaci guda suka ce ‘Abba kada ka kashe fitilar.’ Da mamaki yace ‘Kai! Me kuke ba ku yi barci ba?’

    Afaf tace ‘Abba to ni dai na kasa bacci, da ma za ka taya mu kwana.’ Habib yace ‘Eh wallahi Abba don ni wallahi tsoro nake ji.’ Takaici ya kama shi, to yanzu ya zai yi? Taya su kwanan zai yi ko kuwa barinsu zai yi a haka suna zare ido ya je ya kwanta? Wannan wacce irin fitna ce a daren nan ga shi ya gaji.

    Baya son barinsu su kaɗai don haka ya wuce ɗakinsa yaje ya shirya ya rufo gidan sannan ya dawo nan ɗakin; katifar Habib ƙarama ce ya san ba za ta ishe su ba don haka kawai ya gyarawa Nasreen da Shukra kwanciya ya ɗan sami waje a gefen gadon ya kwanta bayan Afaf ta kwanta a ɗaya gefen. Ya yi addu’a ya tofa musu sannan yace kowa ya rufe idonsa kada ya sake jin motsinsu.

    Tunda ya kwanta yake jin wani ɗan ɗoyi haka, idan iska ta busa sai ya ji kamar ɗoyin ya buso cikin ɗaki idan iskar ta wuce kuma sai ya daina ji. A haka bai san lokacin da bacci ya ɗauke shi ba. ‘Subhanallahi!’ ya faɗa bayan ya yi firgigit ya tashi, ya kai hannunsa ya taɓa inda yake kwance daidai ɗuwawunsa ya ji shi a cikin ruwa sosai. Ya ɗaga hannun yana kallo da tsananan mamaki ‘Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.’ Ya sake fada a fili.

    To fitsarin kwance ya yi ko me? Gashi yaran duk sun yi bacci balle yace wani ne ya zuba masa ruwa; tunda shi dai ya san ba ya fitsarin kwance. Motsin Shukra da ya ji a kusa da shi ne ya tabbatar masa da cewa ita ce ta yi fitsarin, ya miƙa hannu ya taɓata ya ji ta a jiƙe amma tana ta baccinta hankali kwance.

    Ya kai hannu zai janye Nasreen daga kusa da ita ya jita itama a jiƙe ‘Tab!’ ya faɗa a fili. Kenan duka su biyun suke fitsarin kwance ko kuwa yau suka fara? Don shi tunda Khadeeja ta tare a gidan nan sau ɗaya ya taɓa ji an ce Shukra ta yi fitsari. Ya kalli Afaf wadda ita tana can ta takure a ƙarshen gadon tana baccinta, ya danna wayarsa ya kalli lokaci ya ga ƙarfe biyun dare.

    Ba zai iya tashin yaran nan ba don haka ya lallaɓa ya sauka daga kan gadon ya fice ya shiga ɗakin Khadeeja ya samo zanin gado ya zo ya rufe su saboda kar sanyi ya dinga kaɗa su ga danshi. Bayan ya gama rufe su ya zo ficewa daga ɗakin ɗoyin da yake ta ji ya sake dukan hancinsa; wannan ɗoyin ai sai ya kumburawa mutum ciki.

    Kamar daga banɗaki ɗoyin yake fitowa don haka ya koma ya buɗe ƙofar banɗakin ya shiga, ya karasa ya leka toilet din ya tarar babu komai a ciki duk da haka dai ya danna flushing ya juya zai fita. A daidai bakin kofa daga jikin bango ya ci karo da fo ɗin Shukra wanda ɗazu Afaf ta cire wandon Shukra mai ɗauke da kashi ta jefa a ciki. Pant ɗin yana nan da kashin a yanda ta ajiye har ya fara bushewa amma duk ya ɗumame bandaki da ɗoyi.

    Ya ɗan ja baya kamar a firgice, to wa Afaf ta ajiyewa wannan kashin? Yanzu ya zai yi da shi ga shi duk ya ɗumame gidan da wari. Ya ɗaga hannuwansa ya zuba a aljihu, danshin da ya ji ya tuna masa cewa wandon a jiƙe yake da fitsrin Shukra ce ko Nasreen shi ma bai sani ba. Ya yi tsaki ya fito daga banɗakin ya wuce ɗakinsa yana tunanin yanda zai yi da kashin, ga shi a jikin pant yake balle ya sa a toilet ya yi flushing.

    Sai da ya yi wanka ya canza kaya sannan ya fito daga ɗakin, yana fitowa ya ji warin kashin nan har parlor ɗin saboda ya bar kofar a buɗe. A fusace ya wuce kitchen ya ɗauko ƙatuwar baƙar leda ya zo ya ɗauki fo ɗin ya ƙulle a ledar, ya sake ɗauko wata ledar ya ƙara ƙullewa sannan ya ɗauki mukulli ya buɗe ƙofa ya fice ya jefa a shara; gari yana wayewa zai sami yaro ya fitar masa da sharar.

    Ya san dai Shukra ta iya hawa toilet yanzu, duk da idan ta so rigima sai tace sai ta hau fo amma shi dai ya zubar don ba zai iya wankin kashi ba kuma ba zai iya bari Afaf ta yi ba ta zo ta yi musu jagwalgwalo da kashi. Yana dawowa cikin parlor ɗin ya kalli agogon bango ya ga ƙarfe uku har ta wuce, abinda ya yi masa saura bai fi awa ɗaya da rabi ba a yi assalatu.

    Sai a lokacin ya tuna ba shi ma da abincin sahur, ga shi kuma ko a lokacin ma yunwa yake ji balle yace zai yi ɗore. Kai tsaye ya wuce kitchen ya ɗora indomie sannan ya tafasa ruwan shayi; nan da nan ya juye indomie ɗin a plate ya ɗumama stew ya zuba sannan ya haɗa shayi, ya kwaso ya dawo dining table ya fara ci.

    Tun kafin ya haɗiye lomar farko ya fara jiyo hayaniyar Shukra a ɗakinsu, yana zuba loma ta biyu ta buɗo ƙofar ɗakin ta fito tana kuka tana ‘Antiiii..’ Ya ajiye cokalin yace ‘Menene Shukra?’ ‘Shayi zan sha Abba’ Har cikin zuciyarsa takaicinta ya kama shi, to amma ya zai yi da ita? Haka ya kirawo ta ya zaunar da ita a kan kujera, tun kafin ya gama gyara mata zamanta zarni ya cika masa hanci; sannan ma ya tuna ta yi fitsarin kwance.

    Ya gyara mata zama yace ‘Bari na gama sahur sai na haɗa miki shayin.’ Ya ɗauki cokali ya zuba loma a bakinsa yayin da ita kuma ta fara mutssike ido tana kuka. ‘Menene kuma?’ ya tambayeta ‘Yunwa nake ji, shaaayiii.’ Ya duba agogon wayarsa, saura bai fi minti goma sha biyar ba a yi assalatu ga shi ba ya jin zai kai azumin nan idan bai yi sahur ba, ya kalle ta yanda take ta kuka kamar wadad aka ciza.

    Bai taba jin haushin Shukra kamar yau ba, amma babu yanda zai yi. Haka ya juye mata rabin shayin da ya haɗa zai sha ya saka mata madara da milo ya miƙa mata sannan ya cigaba da cin abincin. Yana yi yana kallon lokaci saboda kar a kirawo assalatu. Haka ya ci abincin nan ya yi sauri ya kwankwaɗe shayinsa rabin kofi sannan ya ɗora da ruwan sanyi duk a lokaci guda.

    Yana ajiye kofin aka fara kiran assalatu, ya kwantar da kansa a jikin kujerar yana mayar da numfashi. Shukra da take kan kujera tana gyangyaɗi bayan ta shanye shayinta ta taɓo shi tana cewa ‘Abba kashi zan yi.’ A ɗan zabure ya dube ta yace ‘Kashi Shukra?’ Cikin halin ko in kula tana murje idonta tace ‘Um.’ Ta fara ƙoƙarin sauka daga kujerar da take zaune.

    Ya jijjiga kai cike da takaici; su wai yara ba a hutawa da hidimarsu ne? Tunda ya dawo daga asibiti ake abu ɗaya ga shi duk yana neman fita daga hayyacinsa amma babu alamar sauƙi. So yake ma ya sami natsuwa ya turawa Khadeeja message ta whatsapp ya ga ko tana online amma ba su ba shi time ba, a halin yanzu ma kansa ciwo yake ga bacci duk kansa ya cushe bai ma san ta ina zai fara ba.

    Haka ya bi bayanta har banɗaki, Allah ya taimake shi ba ta ma nemi fo ba ya taimaka mata ta hau toilet ta yi kashinta. Yana zaune a gefen gadonsu ya jiyo ta daga banɗakin tana cewa ‘Abba na gama. Gaban shi ya faɗi da ya tuna wai shi take sa rai ya yi mata tsarki; ya juya ya kalli Afaf wadda take baccinta hankali kwance.

    Ya san idan ya tashe ta za ta yi mata tsarkin to amma fa ita ma bata kwanta da wuri ba. Ya jijjiga kai ya mike bayan da ta sake maimaita masa ta gama a karo na uku. Haka ya tashi ya shiga banɗakin ya wanke mata kashin ya wanko hannunsa ya fito ya canza mata kaya ya mayar da ita ya kwantar da ita a kusa da Habib saboda katifar kan gadon ta jiƙe; zuwa lokacin masallatai duk sun riga sun tayar da sallah.

    Yana fitowa daga ɗakin yayi alwala ya ta-da sallah a ɗakinsa, yana zaune a kan dadduma yana azkar Nasreen ta turo ƙofa ta shigo ɗakin, ta ƙaraso ta faɗa jikinsa tana cewa ‘Abba na tashi, ba ka dawo mana da Anti Khadeeja ba?’ ‘Eh, sai an jima.’ Ya faɗa yana ture ta. ‘Ki je ki ce Ant….’ Sai kuma ya tuna Antin ba ta nan don haka ya gyara zance yana ƙoƙarin miƙewa ‘Mu je na wanke miki jiki ki canza kaya sai ki yi sallah.”

    ‘Abba ni yunwa nake ji.’ Ya ɓata rai yace ‘Sai an canza kaya kuma kin yi sallah.’ Haka ya yi ta fama da yaran nan, ga shi ita Afaf ma fushi take da shi saboda bai tashe ta sahur ba tunda Anti tana tashinta tana yin azuminta. Sai wajen ƙarfe takwas na safe sannan ya tashi ya koma ya roƙo Baban Ummi ta shigo ta karɓi yaran don yana son ya tafi asibiti wajen Khadeeja. Yana shiga ɗakinsa ya zauna a gefen gado ya danna mata kira.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Biyar

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Biyar

    Mijin Marigayiya Babi Na Biyar

    Ko da gari ya waye Khadeeja ba ta ma san lokacin da Ummi ta zo ba don tun daga bakin gate ya tare ta yace ta koma kada ta sake zuwa sai bayan Sallah. Sai wajen sha ɗaya sannan ta fito ta ɗan gayggyara gidan, wanke-wanke ne ma ya ɓata mata lokaci don yana da yawa sosai. Haka ta wanke su gaba ɗaya a famfon waje sai da shigo kifewa sannan Afaf ta taya ta.

    Tana gamawa ta shige ɗakinta ta kwanta; ba ta taɓa jin gajiya irin wannan ba a rayuwarta, ga shi duk wata gaɓa da take jikinta ciwo take yi. Tun 3pm ta shiga kitchen ta fara ƙoƙarin haɗa kayan shan ruwa; dankali da ƙwai za ta soya sai jollof sphagetti sannan ga peppersoup ɗin nama. Da akwai ragowar zoɓo na jiya don haka ba za ta sake haɗa wani ba.

    Yaran suna zaune a parlor ta zo ta wuce ta shiga kitchen, tana wucewa Afaf ta bi bayanta. Ta so ta koro Afaf ɗin daga kitchen amma dai ta haƙura ta bar ta, suna yin aikin. Ba su daɗe da farawa ba Habib ya shigo kitchen ɗin, ya kalli dankalin da aka ajiye a tsakiyar kitchen ɗin yace ‘Anti wannan ferayewa za a yi?’

    Tace ‘Eh, so nake na ɗora kifin nan sai na zauna na feraye shi.’ ‘Kawo wuƙa na feraye Anti.’ Ya faɗa yana buɗe cabinet, ya zaro roba ya tara ya ɗebu ruwa. Tace ‘Ka bar shi Habib zan feraye. Ya sa hannu ya ɗauki wuƙa a kan sink yana cewa ‘Na iya feraye dankali fa Anti, idan na feraye miki sai ki yanka.’

    Bai saurari amsarta ba ya tsuguna ya fara feraye dankalin. Afaf ta ajiye kayan miyan da ta gama wankewa a kusa da Khadeejan tace ‘Anti na wanke kayan miyan.’ ‘To ki yanka mana albasar nan, rabi slicing za ki yi rabi kuma ki yanka ƙanana sai a saka a soup da fried egg.’ Ta ɗauki albasar ta wanke ta zuba a chopping board ta fara yankawa.

    Ba su ji lokacin da Mustapha ya ƙaraso bakin ƙofar kitchen ɗin ba; a dai-dai lokacin nan wuƙar da Afaf take yanka albasa ta goce ta yanke mata hannu. Ta dire albasar ta make murya tana cewa ‘Waiyo Anti na yake.’ Da sauri ta saki abinda yake hannunta ta nufi wajen Afaf ɗin tana murmushi cike da kulawa tana cewa ‘Sorry, garin yaya Afaf. Ki…’Da sauri ya ƙarasa ya kama hannun Afaf ɗin yana cewa ‘Garin Yaya kika yanke, me ya sa kika dauki wuka?’

    Ya juya ya dubi Khadijan yana cewa ‘Na gaya miki sai kin san aikin da za ki dinga sa yaran nan amma ke gani kike kamar kawai bana son su taya ki aiki ne. Yaushe Afaf za ta iya wani yanka albasa.’ Afaf ta zare hannunta daga nashi hannun ta juya ta wanke a sink, ta dube shi tace ‘Ya ma daina jinin Abba bari na je na daure.’

    Yana juyawa ya dubi Habib wanda yake ta ferayar dankali ya daka masa tsawa ‘Ka ajiye wuƙar nan ka tashi, namiji da kai kana wani feraye dankali. Tashi ka ba ni waje.’ Ya juya kan Khadeeja wadda ta riga ta cigaba da aikinta kamar ba da ita yake magana ba, yace ‘Na gaya miki ki daina sa yaran nan aikin da ya fi ƙarfinsu, bana so. Shi Habib ma da yake namiji me ya haɗa shi da wani harkar girki? Bana so.’

    Bai ga alamar za ta ba shi amsa ba don haka ya juya shi ma ya fice suka barta ita kaɗai a kitchen ɗin. Ta rasa me ma za ta yi, ta goge fuskarta ta cigaba da aikinta. Haka ta lallaɓa ta gama komai, zuwa magriba ta zubawa kowa aka sha ruwa. Ta gaji iya gajiya don haka ba ta ma da kuzarin da zata iya wani musu da shi, ta dai riga ta gama yanke wa kanta hukunci da zarar an buɗe gari za ta tafi gidansu ba za ta dawo ba sai ta haihu ko kuma ya ɗauki mai aiki.

    A haka aka cigaba da azumi, kullum cikin wannan yanayin Khadeeja take haɗawa da hidimar gidan da ta yaran ta yi ta fama. Kullum sai ta yi wa Shukra da Nasreen wanka, tsarkin kashi tsarkin fitsari duk ita take musu. Duk wata fitinarsu ita ce me kulawa. Ga shi tana fama da Shukra wadda sai yanzu ne da suka kwana biyu ta fara hana ta kashin wando.

    Yanzu idan dai ba wasa take yi ba ba ta kashin wandon ta iya zuwa ta gayawa Anti za ta yi kashi. Amma idan tana wasa haka za ta tsuguna a wajen wasan sai ta gama kashinta sai dai a ji wari. Haka dai take ta fama.

    Juma’a ce yau ɗin, gaba ɗaya a jigace take jin ta saboda azumi na sha ɗaya kenan za a kai kuma kullum ita kaɗai take hidimar gidan da ta yara. Gashi kuma ta ƙi ta ajiye azumin saboda ko ba ta yi azumin ba ma ba iya cin abincin kirki take ba. Haka dai ta tashi jikinta duk babu ƙwari, ta ɗan yi iya abinda za ta iya ta koma ta kwanta.Tun wajen 2pm ta taso ta fara aikin abincin shan ruwa don tana so ta gama da wuri, tunda zuwa yanzu yaran ma sun hakura sun daina yunkurin tayata.

    Sai dai ita ɗin ma ta rage aiyukan da yawa don duk abinda ta kasa rabuwa take da shi. Dankali da ƙwai kawai ta soya ta dafa shinkafa ta ɗumama ragowar stew ta juye a flask, ta kawo ruwan shayi ta zuba a flask. Saura wajen rabin awa a sha ruwa ta gama ta kawo komai ta jera, ta wuce ɗaki ta kwanta bayan ta gayawa Afaf ta kula kada kannenta su yi ɓarna.

    Ba ta yi minti goma da kwanciya ba Nasreen ta shigo ɗakin da gudu tana taɓa ta tana cewa ‘Anti Shukra ta yi kashi, Abba ya ce ki zo ki wanke mata.’ Ta tashi zaune tace ‘A toilet ɗinku ta yi kashin?’ ‘A wandonta ta yi Anti.’ ‘Je ki ina zuwa.’ Ta ja tsaki ta koma ta kwanta bayan Nasreen ta fice daga ɗakin. Jiri take ji sannan a wani ce ta zo ta wanke kashi, kashin da tace a daina yi mata a wando.

    Ta yi zaton ma a toilet ta yi kashin ta je ta yi mata tsarki. Kafin ta gama yanke hukuncin da za ta ɗauka Abbansu ya shigo, bayan ta amsa sallamarsa yace ‘Ki zo ki wankewa Shukra ta yi kashi.’ Ta dafe kanta ta tashi tana cewa ‘Ba lallai na iya ba ne don wallahi jiri nake ji gashi yau tun safe marata take ciwo.’

    ‘To na ce ki ajiye azumin kin ƙi, ki bar shi haka ki huta. Ki taso ki gyara mata alwala zan je na yi an kusa kiran sallah.’ Ta miƙe a hankali ta biyo bayansa suka fito daga ɗakin. Tana shigowa parlor ɗin Shukra ta sunkuyar da kai, ta harare ta tace ‘Kin sani ai mara kunya, nace ki daina yin kashi a wando amma kin ƙi ko? Yau gidansu ƙyanƙyaso za ki kwana a can ake kashi wando.’

    ‘Don Allah ki yi mata a hankali, komai lokaci ne ai za ta daina ne a yi mata haƙuri.’ Ya faɗa yana shirin komawa ɗakin ya yiwo alwala. Ta tsuguna za ta ɗauke ta ta ji kanta ya biyo ta kamar zai faɗo, ta dafe goshi ta koma ta tsaye tace ‘Kai! Ba zan iya ba fa.’ Ya juyo ya tsaya ‘Menene?’

    ‘Ba zan iya tsugunawa ba fa, jiri kwasa ta yake.’ ta ƙarasa kan kujera ta zauna ta dafe goshi. Ta dubi Afaf tace ‘Ba ni ruwa na sha Afaf, ga kiran Sallah nan an fara. ’Nan da nan ta cika Kofi da ruwa ta miƙa mata, ta sha kaɗan ta jingine kanta tana riƙe da ruwan. Kukan Yusra ne ya katse su tana cewa ‘Anti na daina ba zan kuma ba, mantawa na yi daman.’

    Ta yunkura za ta miƙe Afaf ta yi sauri ta dafe ta. Abbansu ya dubi Khadija yace ‘Don Allah ki lallaɓa ki wanke mata kashin nan, Wannan wane irin abu ne? Yanzu wa kike so ya wanke mata kashin?’ Afaf ta aika Nasreen ta ɗauko fo a toilet ta cire wandon da yake cike da kashi ta jefe a fo ɗin sannan ta ɗauke Shukran ta nufi banɗaki. Ta wanke mata sannan ta dawo ta gyara wajen, zuwa lokacin Abbansu ya fito daga alwala.

    Ya zauna ya sha ruwa sannan ya miƙe zai tafi masallaci. A daidai lokacin ita ma Khadeeja ta ɗago kanta tace ‘A dawo lafiya.’ Yana jin ta ya yi banza da ita saboda yanda yake jin haushinta, kuma tabbas sai ya kora mata bayani in an sha ruwa. Daga yau ma ba za ta sake yin azumin ba tunda dama mai ciki tana da damar ajiyewa. Ta miƙe tana gatsina fuska, kawai sai gani ya yi ta sulale za ta faɗi.

    Ya zabura zai tare ta ya yi fatali da casserole ɗin dankali, a lokaci guda Habib ya saki jug ɗin zobon da ya fito da shi daga kitchen ya tarwatse a wajen ya ƙarasa kanta. Duka su biyun kafin su ƙaraso ta zube. Abbansu ya ɗago kanta yana jijjigawa ‘Khadeeja, Khadeeja, Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun, Khadeeja.’ Ko motsawa ba ta yi.

    Ya sunkuce ta ya kwantar da ita a kan three seater, ya ƙara gudun fanka sannan ya kunna AC. Ya cire mata ɗankwalin da yake kanta ya fara yi mata fifita. Yaran gaba ɗaya suka jeru a kanta suka yi tsuru-tsuru; Afaf ta leƙa fuskarta ta kafaɗar Abbansu tace ‘Abban ita ma mutuwa za ta yi ta bar mu ko?’

    ‘Ke bana son rashin hankali, ba mutuwa za ta yi ba.’ A take yaran suka saka masa kuka mai ban tausayi. Afaf ta rungume Nasreen da Shukra suka haɗa kai suna kuka. Habib ya taɓa shi yace ‘Abba ka kai ta asibiti kada ta mutu ta bar mu.’ ‘Kai rufe mana baki.’ Gaba ɗaya shi ma ya ruɗe, jikinsa har rawa yake yi. Ya janyo jug ɗin ruwan sanyi ya jiƙa hannunsa ya shafa mata a fuska. Ta ja numfashi ta buɗe idonta, sai kuma ta mayar ta rufe.’Khadeeja.’

    Ya kirawo sunanta da ƙarfi yana jijjiga ta. Da gudu su Afaf suka ƙarasa kanta suna kira ‘Anti, Anti.’ ‘Khadeeja.’ Ya kara kiran sunanta a firgice. Ta buɗe ido ta sake rufewa. Ya miƙe tsaye ya ɗan tura yaran yana cewa ‘Ku zauna na ɗauko mukullin mota, asibiti zan kai ta yanzu, babu abinda zai same ta in sha Allahu.’

    Ba tare da ɓata lokaci ba ya ɗauko mukulli ya fito, ya je ya buɗe kofar motar ya dawo ya ɗauke ta bayan ya yafa mata mayafi ya wuce yaran suna biye da shi ya kwantar da ita a bayan motar. Bayan ya rufe ƙofar motar ya juyo ya kalli yaran yana tunani; to yanzu ya zai yi da su? Wa zai bar wa su? Ya san shi kansa ma sai ya amsa tambayoyi a checkpoints ga shi ma’aikatan asibitin ma kamar tsoron mutane suke balle ya kwashi yara su tafi.

    Ya shafa kai sannan ya sake kallonsu cike da damuwa; da a ce gari a buɗe yake da sai ya wuce da su ya ajiyesu gidan Hajiya to amma ya san ba zai yiwu don zai yi ta ɓata lokaci a checkpoint. A take dabara ta faɗo masa. ‘Ku tsaya a nan ina zuwa.’ Ya ba su umarni sannan ya fice daga gidan ya turo gate ɗin.

    Yana fitowa ya ƙarasa gidan su Ummi, ya yi sa’a yana tsayawa maigidan yana dawowa daga masallaci. Bayan sun gaisa ya sanar da shi so yake Ummi ta zo ta zauna masa da yara ya je ya kai Khadeeja asibiti. Ya janjanta masa sannan ya shige gidan ya turo masa Ummin. Haka ya sako ta a gaba ya dawo gidan ya bar mata yaran ya ja motar ya nufi Aminu Kano Teaching Hospital da ke Kano.

    Yana zuwa asibitin aka nuna masa gynae emergency inda nan ne ake karɓar masu ciki waɗanda suke buƙatar taimako na gaggawa, nan da nan suka karɓe ta aka fara duba ta; duk da dai su kansu ma’aikatan za ka gane cewa suna cikin yanayi na tsoro saboda Covid19. A nan wajen aka nuna masa benchi ya zauna yayin da ita kuma aka tura ta a kan gadon marasa lafiya aka shige da itaɗdakin bincike.

    Tana kwance a kan gadon yayin da take amsa tambayoyin ma’aikaciyar jinya sai wata ma’aikaciyar wadda ta ji suna kira matron ta shigo, ma’aiakaciyar ta juya tana kallon matron tana cewa ‘Matron wannan fa sai an yi mata scaning, cikin nan na jikinta kamar ficewa zai yi duk da dai tace ba ta fara bleeding ba amma dai tana jin alamunsa.’

    Matron ɗin ta ƙaraso ta tsaya a kanta, tace ‘Ah! Wannan ai Khadeeja ce, wa ya kawo ta?’Jin an ambaci sunanta ya sa ta buɗe idonta a hankali, ta yi murmushi a gajiye lokacin da suka haɗa ido ta gane wadda ta ambaci sunan nata. Cikin sanyin murya tace ‘Anti Iyami.’ ‘Na’am, Khadeeja. Wa ya kawo ki?’ ‘Mustapha ne.’

    Ta juya ta kalli abokiyar aikin nata tace ‘’Yata ce ai, ita ce wadda muka yi biki kwanaki fa yarinyar Habiba wadda nace miki childhood friend ɗina ce.’ Da fara’a tace ‘Aaah! Allah sarki, to abun ya zo kenan haihuwa yaƙin mata.’ ‘Ai kuwa. Bari na kirawo Dr. Jamil ya zo ya duba min ita sai mu je na kai ta scanning ɗin mu ga ko za a iya sallamarta a daren nan.’

    Har ta juya za ta fice Khadeeja ta riƙo hannunta, ta juyo tana cewa ‘Akwai wani abu ne Khadeeja?’ Ta yi murmushin yaƙe ta goge ƙwallar da ta gangaro daga gefen idonta tace ‘Kada ki sallame ni Anti Iyami, ki yi wa Mommy waya ta zo ta ɗauke ni gida zan tafi.’ Ta ɗan ranƙwafo tana shafa kanta tana duban fuskarta tace ‘Ok, kada ki damu, ki samu ki huta tukunna likita ya duba ki. In sha Allahu yanzu zan kirawo ta ko ba ta zo ba da safe idan na tashi daga aiki sai na tafi da ke gidan Mommy ɗin. Kada ki damu.’

    Ta juya ta fice yayin da Khadijan ta mayar da idonta ta rufe. Tare da likitan suka dawo, bayan ya duba Khadeeja aka je aka yiwo scanning tare da Mustaphan aka dawo. Bayan likita ya duba scanning ɗin yace cikin jikinta ya lalace fita zai yi, don haka za a yi mata wankin ciki sannan akwai allurai da ruwa da za a saka mata.

    Da kansa ya je ya siyo komai ya kawo sannan suka koma wajen Khadeeja tare da matron; a nan Khadeejan take sanar da shi cewa martron kawar Mommy ce. Ya sake gaisheta cike da girmamawa, bayan ta amsa ta dubi Khadeejan tace ‘Likita ya ce cikin jikinki ya lalace don haka za a yi miki wankin ciki, ga magunguna kuma ya rubuta miki sannan ga drip idan an gama wankin cikin zan saka miki kin ga yau a nan zamu kwana da ni da ke.’

    Ta yi murmushin yake, ta dubi Mustapha tace ‘Ka tafi, ka bar yara a gida. Anti Iyami za ta kirawo ka  idan akwai wani abu tunda ka ga tare zamu kwana ma, zuwa da safe za mu yi waya in sha Allah. Matron ta fice ta ba su waje. Bayan ta fice ya matsa kan Khadeejan yana shafa fuskarta yace ‘Sannu, kin ba ni tsoro fa.’

    Ta yi murmushi.Ya cigaba ‘Kafin safiyar ta yi sai ki samu ki yi min message ɗin duk abinda kike so na taho miki da shi, idan kuma Allah ya sa da safen za su sallame ki ma shikenan sai kawai na zo mu tafi. Na yi maganar abinci ma Anti Iyami tace na bari za ta kawo miki, but in ana son wani abu kiyi min magana sai na saka miki kuɗi a account ɗinki ko transfer ne sai ki yi musu.’

    Ya sa hannu a aljihunsa ya zaro wayarta ya miƙa mata yana cewa ‘Ga wayarki, ba zan kirawo ki ba don kada na dame ki ko na tashe daga bacci, but please da kin farka ki kirawo ni.’ Ta karɓa tana murmushi tana cewa ‘Ok, ka gaishe min da su Yaya Afaf.’ Ya fice ya bar ta a kwance. Yana fitowa ya sami Anti Iyami da abokan aikinta a station ɗinsu, ya yi mata sallama bayan ta ƙarbi lambar wayarsa sannan ya wuce.

    Tun a daren Anti Iyami ta kirawo Mommy ta sanar da ita halin da ake ciki, sai dai ba ta gaya mata cewa Khadeejan tace gida zata taho ba. Ta dai sanar da ita cewa tana hannunta idan akwai wani abu za su ji zuwa wayewar gari. Tana tsaye aka yi wa Khadeeja wankin ciki sannan aka ba ta ɗaki, ta saka mata drip da alluranta sannan ta haɗa mata shayi mai kauri.

    Ta sakata a gaba bayan ta shanye sannan ta zuba mata shayi da kwai ta cinye sannan ta ajiye mata saucer da kankana da lemon ɓawo tace ta shanye kafin a jima. Ta sha tambayoyi a wajen Anti Iyami wadda take ƙoƙarin gane dalilin da yasa Khadeejan take son tafiya gida; sai dai ba ta sami komai ba don da a tunaninta ko Mustaphan yana abusing ɗinta ne. Ita kuma ta sanar da ita kawai ba ta da lafiya ne sannan kuma ga aikin gida da raino wanda ya yi mata yawa shi yasa take son ta je gida ta huta.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu